Breaking News

Mutum Da Duniyarsa Complete Hausa Novel

 

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_


                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_©2019_*

*بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ*

_In the name of Allah, the Entirely Merciful, the Especially Merciful._

           *[1......]*

     ............Tafe take tana zirar da hawaye masu d'umi da saka k'unar zuciya. Kasantuwar Nikab d'in dake sakaye da fuskarta ya hana bayyanuwar kukan nata ga mutane, dukda dai hakan bai hana wasu kallonta ba, musamman wad'anda sukeda tabbacin itace.
      Cikin Nutsuwa da sanyi take tafiya, kanta a k'asa dukda kuwa tana sanye da dogon hijjab da nik'ab. Isowarta inda zata yasa ta tura murfin k'ofar gidan kalar madara ta shiga da sallama.
     Dattijuwar da bazata gaza shekara hamsinba ta d'ago daga d'ibar ruwan da take a rijiya ta amsa Mata.
       “Wa'alaikissalam, yanaga kin dawo dandanan? Kobaki iskeshi a gidan bane?”
    Nik'af d'inta ta yaye, kamilalliyar fuskarta ta bayyana, ta d'an sakin guntun murmushi tace, “Eh Umman mu, na tarar har ya tafi kasuwa”.
      Batareda ta jira amsar Umman tasuba ta wuce gaba. Binta da kallo Umma tayi, ko kad'an bata yardaba, tasan ta 6oye mata ainahin abinda yafarune acan kamar yanda ta saba gudun kar ranta ya 6aci. Ta d'an sauke ajiyar zuciya tana girgiza Kai, sannan ta ajiye gugan hannunta ta d'auraye hannun da ruwan data jawo ta nufi d'akin da yarinyar ta shiga.
       Zaune ta isketa ta zabga uban tagumi tana cigaba da kukan, amma jin sallamar Ummansu sai tai saurin share hawayenta ta maye gurbinsu da murmushi. Da kallo kawai Umma ta bita tana mamakin zurfin ciki irinna y'ar tata, ita har tausayinta take gameda zaman gidan aure, idan bata sami miji na gariba sai dai aita cutarta........
      Maganar budurwar ya saka tunaninta katsewa.
     “Umma wai su Zarah basu dawoba har yanzu?".
      Zama tayi kusa da ita tana fad'in “Basu dawoba Nafisar ma ta kirani tace sai zuwa yamma zasu dawo, zasuyi Mata wani d'an aiki”.
       “Humm ni dad'ina da Aunty Nafisa kenan, baka isa kaje gidanta kafito bata nanuk'a maka aikiba, son jikinta yayi yawa wlhy ita da Zarah Umma”.
      Murmushi Umma tayi kawai, amma batace komaiba. Sai da taga budurwar zata mik'ene tace, *“JIDDAH!,* dawo ki zauna muyi magana”.
     Babu musu ta dawo inda ta tashi ta kuma zama, “To Umma gani, wacce magana ce?”
        Numfashi Umma ta sauke, kafin ta tsare Jiddah da idanu, “Jiddah ya kukayi da Abbanku?”.
     “Lah Umma aina cemiki ban iskeshiba, yatafi kasuwa sanda naje”.
       “Ban yardaba Jiddah, nifa mahaifiyarku ce, duk d'inku nasan halin kowanne, ki daina k'ok'arin 6oyemin abinda ba sabo bane a gareni da rayuwata”.
        “Umma kiyi hak'uri, aganina yawan maimaita magana bashida amfani, hak'uri da mantawa da abinda yawuce shine dai-dai”.
       “Duk nasan da hakan Jiddah, kedai fad'amin”.
     “Shikenan Umma tunda kin matsa. Na iske Abba a gida yanama Karin kumallo, bayan mun gaisa dashi da aunty Amarya, saina sanar masa nazone ya taimakemu da kud'i su zarah sun koma hutu, gashi kuma basu biya kud'in makaranta ba belle su kuma, gashi su waleeda Jsce zasu zana a wannan shekaran. Wlhy Umma bakiga yanda Abba da Aunty Amarya suka hayayyak'o minba, har Abba yana fad'i bazai gaji da takaicin *HAIHUWAR y'ay'a mata* ba harya koma ga ALLAH, wai mune muka dabaibaye DUNIYARSA shiyyasa yakasa gaba ya kasa baya, shi baiga amfaninmu ba inama laifin ciyar damu abinci da yakeyi, yariga ya rantse sisin kwabonsa bazai ta6a kashewa akan muyi karatu ba, gara ya sayama su kalifa ice-cream yasan duk tsiya nan gaba zai amfana dasu...........” kuka ya sark'eta takasa k'arasa maganar, saima fad'awa datai jikin Umman.
      Shiru Umma tayi takasa cewa komai, sai k'ok'arin Had'iye wani Abu daya tsaya Mata a mak'oshi takeyi, yayinda hannunta ked'an bubbuga bayan Jiddah.......
      Jiddah takuma katse Mata tunani da fad'in “Umma wlhy Duniyarnan tama fitarmin akai, wataran nakanji tamkar zancen Abba gaskiyane mu Mata bamuda wani amfani acikin wannan al'ummar, kowa gani yake amfaninmu daga a haifemu sai muyi aure mu haihu, babu wata gudunmawa da zamu iya kawowa a duniyarmu, mune muke d'aukar ciki, muyi goyonsa, mu haihu, muyi raino, muyi tarbiyya mutum yakai wani matsayi, amma MACE itace zai fara k'ask'antarwa, MACE itace zai fara d'auka mara muhimmanci, itace zai Fara kira mai k'aramar k'wak'walwa, itace zai Fara kira mai k'aramin tunani, itace wadda yake Fara kallo takalminsa abar takawa ako yaushe, mune jagororin AL-UMMA amma mu ake maidawa MAK'ASK'ANTA, Umma Abbanmu namana haka to yaya Miji zaimana muji haushi? Anya kuwa Umma Abbanmu y..........”
      Da sauri Umma ta rufe bakin Jidda tana fad'in “Kul jiddah karna sakeji, koma dai minene shi mahaifinku ne, bai cancanci kowanne irin furiciba, addu'a itace kawai makaminmu da hak'uri kinji”.
       Kai Jiddah ta d'aga Mata tana share hawaye.
     Umma tace, “Inaga kawai Zan samu Na saida Kujerunnan su koma makarantar, dan duk suna a ga6ar dabai kamata ayi wasa da itaba, kodai karatun secondary d'in suka samu ALLAH ya amfana, mutum dai yasamu abin fidda kai aduk inda ya tsinci kansa, kema da bakiyiba keda y'ar uwarki ALLAH ya baki miji nagari dazai kula dake kamar yanda y'ar uwarki ta dace”.
          “Ameen Umma, amma baikamata a saida kujerunnan ba, mudai jira muga kozai biya d'in kokuma Uncle zai dawo da wuri, dan nasan shima hankalinsa Na nan”.
       “Humm Jiddah kenan. Kema dai kinsan hali basai nafad'aba indai Abbanku ne, mudai jira yahayan kawai”.
    Shiru Jiddah tayi tana had'iye wani Abu mai d'aci daya tokare mak'oshinta, ji take da zata samu wata dama akan MAZA masu irin halin Abba, to lallai shine Wanda zata Fara hukuntawa domin na bayansa su Shiga hankalinsu da koyar yanda zasu *MARTABA Y'AY'A MATA*.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

*ASALIN LABARIN*

*Alhaji Zakari yaro* d'an asalin jihar Adamawa ne, amma mazaunin kano, dan acikin kano ya bud'i ido yagansa tun a zamanin k'uruciya, ALLAH yayima Mahaifinsa rasuwa tuni, amma sai mahaifiyarsa taci gaba da zama bata koma Adamawa ba, ita tacigaba da kula da al'amuransa harya kai munzalin aure. Da kanta tabashi damar nemo matar aure, anan kano kokuwa cikin y'ay'an dangi dake Adamawa.
      Cikin ikon ALLAH ya za6o matarsa cikin dangi, dankuwa acan Adamawa tushensa ya d'akkota, hasalima auren zumincine a tsakaninsu. Sosai mahaifiyarsa tayi murna da za6insa tai ta sanya masa albarka. Babu 6ata lokaci aka shiga shagalin biki Na y'an gata, domin kuwa su biyu iyayensu suka Haifa, dagashi sai k'aninsa yahaya. Ansha biki amarya Aminatu ta tare anan cikin birnin kano. Zamane akeyi mai cike da nagarta da k'aunar juna, dan kuwa suna son junansu, sai da Aminatu ta shekara uku a gidan miji sannan ALLAH yabata ciki, zokaga murna wajen Zakari da mahaifiyarsa da k'aninsa yahaya, a kullum fatan Zakari Aminatu ta Haifa masa d'a Namijine, wataran har takanji haushi a yanda yake nuna k'iri-k'iri yafison a Haifa masa y'ay'a maza, to idan ta haifi mace kenan bayaso? Idan wannan tambayar tazo mata a rai hankalinta yakan tashi, domin tarasa yanda zuciyarta zata iya kar6ar amsar.
     ALLAH da ikonsa ciki ya isa haihuwa, a wani daren lahadi Amina ta tashi da nak'uda, gabannin asuba da taimakon ALLAH dana surukarta ta haifo y'arta mace. Tunda mahaifiyar zakari ta sanar masa abinda aka Haifa saiya canja fuska, murnar da yaketayi takoma ciki, batare da yako d'auki y'ar ba ya buga takalminsa ya fice, bai dawoba sai da daddare, wasa-wasa dai Zakari yak'i d'aukar yarinya, hud'uba ma sai wani makwafcinsu yahaya yakira bisa umarnin mahaifiyarsu akaima yarinya. A kayan shagalin suna da ya saya saiya raba uku yabada kashi d'aya, mahaifiyarsa batasan abinda ke faruwa ba, dan a gabanta 6oyewa yakeyi, sai a daren sunan da taga kayan daya kawo takaici ya kamata, kiransa tai ta nema ba'asi, nanfa yashiga kame-kame, itako ta balbaleshi da fad'a, ta inda take shiga ba tanan take fitaba, yayinda shikuma yaketa bada hak'uri da neman afuwa. A daren yakawo sauran kayan, washe gari akasha shagalin sunan baby dataci suna SAUDA.
        Bayan haihuwar Sauda zaman Amina da Zakari ya canja alk'ibla, ya janye mata sosai, dukda ta damu amma saita danne zuciyarta darajar mahaifiyarsa dake k'yautata mata, da gudin tsinka igiyar zuminci. Shekarar Sauda biyu takuma samun wani cikin, nanma dai Zakari yakuma k'wallafa rai ga haihuwar d'a Namiji, yakoma ririta Aminatu. Itadai mamakinsa take ainun, amma bata ta6a cewa dashi uffanba har cikinta yakai haihuwa.
        Tab an da6a kenan, inji masu iya magana, dan kuwa wannan karonma Aminatu Mace ta sake haihuwa k'yak'yk'yawa San kowa k'in Wanda bai samuba, itadai murna tai tayi da kuma godema ALLAH da wannan k'yauta. Amma ga zakari ba haka bane, dankuwa jiyay yakuma tsanar Amina, wai danmi zataita cika masa gida da y'ay'a Mata. A wannan Karon koda ya takalota da fitina bata d'aga masa k'afaba, tai masa tatas, wannan shine silar guntulewar aurensu, sai a gidansu aka rad'ama jaririya suna Hannatu, dan kuwa Zakari yace yabar mata bayaso. Ran mahaifiyarsa yakai k'ololuwar 6aci, ta tattara kayanta takoma Adamawa ita da yahaya.
         Shekarar su d'aya da rabuwa da Aminatu yasake aure, Wanda da k'yar mahaifiyarsa ta amince, saida ma Baban Aminatu ya saka baki.
     Saidai wannan karonma auren Zakari da Ai'sha baiyi k'arko ba, dankuwa tun a haihuwar farko suka raba jaha, sakamakon haihuwar d'iya mace mai suna Zulaiha. Itama yace bayaso ya barmata. Ananma sosai mahaifiyarsa ta fusata, amma bisa hak'urin da dangi sukaita batane yasata hak'ura. Zakari yakuma auren Rammah. A haihuwar farko Rammah ta haifi mace itama, tashin hankali kenan, dankuwa Zakari yakai k'arshen fusata da haihuwar Mata da ake masa, a cewarsa haihuwarsu batada wani amfani sai d'orama mutum nauyi (🙁humm).
     Itama dai batakai labariba ya 6alleta tareda bar mata y'arsa mai Suna  Nafisa tace bazata rik'eba. Dole ruk'on Nafisa yakoma hannun mahaifiyarsa dake Adamawa.
       Bayan Aurensa da rammah saida ya shekara hud'u bai k'ara zancen aureba. Sai kuma rana tsaka ALLAH ya had'ashi da Y'ar Shuwa wato Yagana, Zakari ya had'u da Yagana ne a Adamawa, lokacin yazo gaida mahaifiyarsa, yayinda Yagana kuma sunzo biki makwaftansu mahaifiyar Zakarin. Dandanan soyayya ta k'ullu a tsakanin yagana da Zakari, dukda sukarsa Na auri saki da k'in haihuwar y'ay'a Mata da akaita kawo Mata. Ba awani ja lokaciba manya suka shiga magana, akaje har Maiduguri aka d'auro auren Yagana. Saida tayi sati biyu a Adamawa sannan suka taho kano, bisa ga dogon gargad'i da mahaifiyarsa tai masa, takumace inhar ya Saki Yagana ALLAH ya isa bata yafeba koda a bayan rantane...........✍🏻

(Turkashi🙆🏻).




*_ya RABBI ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_Ya rabbi kabani ikon fad'ar abinda zai amfanar da al'ummarka, ka tsare harshena daga fad'ar abinda zai cutar daku da ni baki d'aya._*😭🙏🏻

_Ya ALLAH ka gafartama mahaifina abin alfaharina da dukkan y'an uwa musulmai da suka rigamu kwanta dama🙏🏻😭_

*_Wannan littafi tukuycine a gareku my sweet sisters, ina gidiya da karamcinku gareni, alkairin ALLAH yakai gareku a duk inda kuke._*🥰🥰🤝🏻

_Billy s Fari_
_Ummu Basheer_
_Fareeda Musa sweery_
_Ai'sha Manshat_
_Hafsat writer d'in Hafiz_

   
__________________________________

                   *_[2.....]_*

................ Zakari dai yataho da Yagana kano cikeda farin ciki, sunkumazo sun zauna lafiya har ALLAH yabata ciki itama, a lokacinne kuma yahaya shima yadawo kano suka cigaba da kasuwancin atanfofi da shaddoji shida d'an uwansa Zakari.
    To a wannan Karon dai Yagana ta Haifa masa Namiji, wayyo zokaga murna da tsalle da shirin suna Na bajinta, ragoma biyu aka yanka kuma manya-manya. Ansha shagalin suna yaro yaci suna Nuhu. Sai dai kash bayan suna da kwanaki uku yarasu, wannan Abu yasaka Zakari takaici, harda kukansa rurus, kaikace wani babban mutumne yarasu.
      Babu dad'ewa Yagana takuma samun wani ciki, Zakari ya shiga tattalin ta kamar zai maidata a ciki, dan a ganinsa Namijin za a kuma Haifa masa. Sai dai kuma shi Ubangiji babu mai masa shishshigi a lamarinsa. Koda Yagana ta haihu saiga d'iya mace. Babu kunya Zakari ya nuna tsantsar takaicinsa da haihuwar jaririya, gashi babu damar sakin Yagana. Yarinya taci suna *HAUWA'U (Jiddah)*, ko kad'an Zakari bai damu da Hauwa'u ba, koda ciwo takeyi babu ruwansa balle ya damu, ahaka takai yaye aka yayeta, Yagana takuma samun wani cikin. Nanma Zakari ya saka idon ganin namiji, amma saiga mace, itama kiri-kiri ya nuna bayaso, taci suna Fatima (Zarah), bayan an yayeta saiga wani ciki, a wannan Karo zakari baiwani damuba, hasalima ya maida hankalinsa ga kasuwancinsa ne daketa ha6aka gaba d'aya, ga shirin auren Yahaya da sukeyi kuma.
      Ansha bikin yahaya da matarsa Zulaiha, itama ta tare anan cikin anguwar, amma haya ya kama kafin ALLAH yakawo kud'in gina d'an filinsa daya siya. Bayan auren yahaya da kwana ashirin da uku ALLAH yayma mahaifiyarsu rasuwa, takuma jaddada wasiyarta ga Zakari inhar ya saki Yagana bata yafeba. Sunsha kuka da alhini rasuwarta, kwananta tsara a k'asa Yagana tafara nak'uda, amma sai Zakari ya nuna halin ko inkula akanta, acewarsa bazai wahal da kansa da dukiyarsa ba ahaifa masa wadda bazata iya taimakonsa da komaiba idan ta girma. Haka Yagana tasha matuk'ar wahala kafin ta haihu dak'yar, wahalar da tasha yasaka jinjirin jigata yazo babu rai. Hankalin Zakari yatashi matuk'a, yakumaji haushin kansa ainun, dan aganinsa sakacinsa yasaka su6ucewar Abu mafi daraja da soyuwa a gareshi, ya rungume gawar yaron yayta hawaye da ALLAH wadai ga abinda yayi, daya kai Yagana asibiti da yanzu d'ansa Na nan a raye.
      Baki kawai Yagana ta ta6e ta d'auke kanta, takaici Na kuma cimata a zuciya.
        Saida takusa shekara sannan ALLAH ya kuma bata wani cikin, zakari yadage tuk'uru wajen bata kulawa da addu'ar samun Namiji a wannan karonma.
    Zan iya cewa Yagana ta haihu kusan lokaci d'aya da Zulaiha Matar yahaya, zulaiha ta santalo d'anta Namiji, itako Yagana mace. Takaicifa kamar zai kar mutumin naku. (😆😝).
         Babu wani abun arzik'i dayayi a taron sunan tamkar sauran y'ay'ansa Na baya, ranar suna yarinya taci suna Hadiza (waleeda) saboda sunan mahaifiyar su zakari aka sanya Mata, d'an yahaya kuma Abubakar.
         Bayan haihuwar Waleeda Ruk'on Nafisa yadawo hannun yagana, tunda yanzu babu mahaifiyar su zakari. Tsakani da ALLAH yagana ke ruk'on Nafisa, inma ba fad'a tayiba bazaka ta6a sanin ba d'iyarta baceba. Yanda take bama y'ay'anta tarbiyya haka take bama Nafisa, duk abinda ta siya musu itama zata saya Mata.
   
      Zakari kam babu ruwansa da maganar yaransa, tsakaninsa dasu sai hantara da duka, yak'i sakasu boko balle Arabic,  daga waleeda ma sai haihuwar ta tsayama Yagana baki d'aya, ita murnama tayi sosai, y'an uwantama suka tayata. Da taimakon yayan Yagana aka saka su Jiddah firamari da islamiyya harma Nafisa, yahaya ma yana bada gudunmawa, dukda a tsorace yakeyi saboda a k'ark'ashin Zakari yake har yanzu.
      Matar yahaya kuwa tanata haihuwarta, cikin ikon ALLAH kuma maza taketa haihuwa, shikuma yana masifar son a Haifa masa mace, sai yayta sha'awar su jiddah.
      Shekarar waleeda takwas a duniya Zakari yaje makka, a wajen aikin hajji yahad'u da matar aure mai suna Hajia Hindatu. Hindatu irin gogaggun matan nanne masu Ido a tsakar goshi, ta ta6a aure amma haihuwarta d'aya ta fito, bata dad'e da fitowa ba suka had'u da zakari. Tun a Saudia soyayya ta k'ullu a tsakaninsu, suna dawowa Najeriya babu 6ata lokaci akasha biki.
    Ko kad'an auren bai d'aga hankalin yagana ba, dan damuwarta itace a gabanta, takuma San wanene Zakari, idan baisamu cikar burinsa ba (haihuwar namiji) to itama hindatun ba k'afa zai d'aga mataba.
      A gida d'aya aka had'asu da farko, dukda Zakari yafara ginin wani gida mai k'yau dayafi Wanda suke ciki d'an k'arami mai d'aki uku da kicin d'aya da bayi d'aya a waje.

        Sosai Hindatu kema Yagana Ummansu Jiddah iskanci kala-kala, su Jiddah kuwa basu isa su wala a gidansuba zata makesu. A lokacin kuma Nafisa nada shekara 19 dan tama isa aure, Jiddah kuma 14, Zarah 12, Waleeda 10.
        Tuni Nafisa tabar zuwa boko dan daga firamari itada Jiddah basu cigaba ba, yayan yagana dake taimaka musu ALLAH yayi masa rasuwa, ganin nauyi zaiyima yagana yawa dukda d'an kasuwanci da takeyi saitace Jiddah da Nafisa suyi hak'uri, k'annensu su Zarah suyi su sai suci gaba da islamiyya kawai. Basu musaba suka amince, Zarah da Walida suka cigaba dayin boko da islamiyya, Nafisa da Jiddah kuma islamiyya kawai.
    Zuwan Hindatu saiya kuma harmutsa komai Na gidan, domain kuwa shekararta d'aya ta haihu d'a Namiji, murna da shagalin da Alhaji Zakari yayi 6ata lokacine, bayan shekara biyu takuma tagwaye duk maza. Nanfa likafa taci gaba, dan gidan da Alhaji Zakari ya gina dukda girmansa sai yace Hindatu ce kawai zata koma ciki. Dukda abin ya6ata ran Yagana saita danne, tai masa ALLAH ya sanya alkairi.
     Acanma akayi sunan tagwayen hindatu. Bayan suna babu dad'ewa Nafisa tasamu miji, babu bincike babu komai Alhaji Zakari yace yabashi, takaici Yakama mahaifiyar Nafisa da Yagana (dayake mahaifiyar Nafisan suna mutunci da yagana sosai saboda ruk'on gaskiya da taima y'arta, itama tayi aure tuni ta hayayyafa ma).
      Haka dai akasha biki, Alhaji Zakari baima Nafisa wani abun arzik'iba, a cewarsa baya zuba jari inda bazai kwashi ribaba. Komai sai mahaifiyarta da yagana sukayi iya k'ok'arinsu, saikuma dangi.
        Sosai Alhaji Zakari ke nuna banbanci tsakanin y'ay'ansa maza Na wajen Hindu (wadda suke kira Aunty Amarya) dasu Jiddah.
       Hindu takuma saka haihuwar d'a Namiji, yanzu yaranta hud'u duk maza, kalifa, Hassan, hussen, Najib.
       Alhaji ya sakasu makaranta mai tsada, komai suke buk'ata an tanadar musu, sun taso y'ay'an Hutu, Ana shagwa6asu ainun.
    Yayinda gasu Jiddah ba haka bane, ko Alhaji zakari zai musu Abu saiyayi musu tozarci, bakuma zaiyi yanda ya kamata ba, saiya had'a wata baizo wajen Ummansu Jiddah da sunan sauk'e mata hak'k'i Na aureba, kayan abinci ma saiya gadama, saidai yahaya yakawo, wataran kuma ya hanashi ma.
     Jiddah iyakarta firamare itada Nafisa, yanzu haka shekararta 20 dai-dai, tana makarantar islamiyya, hafizace ta alkur'ani mai girma, tayi zurfi matuk'a a fannin ilimin addini, ta halarci musabak'an alkur'ani kashi-kashi, kuma tayo nasara, amma a boko saidai abinda ba'a rasaba da Wanda k'annenta su Zarah ke koya Mata.
      Da taimakon Uncle yahaya dana Umma, Zarah da walida ke karatu, dukda makarantar gwamnati sukeyi saida ji6in goshi ake iya kare musu buk'atun yau da kullum, dukda ALLAH yayima mahaifinsu arzik'i gwargwadon hali babu ruwansa da su.
     Zarah Na shekara 18, tana aji biyar a makaranta, tasamu Matsala ne a wata shekara aka maidata baya, amma da yanzu tagama secondary, itama babu laifi tana ta6a karatun addini. Walida kuwa tana 16 itako ajinta uku a makaranta, sune zasuyi jsce yanzu. To ankoma Hutu amma gashi uncle yahaya bayanan, yayi tafiya, shine Umma tace Jiddah taje wajen Abbansu kozai taimaka ya bada, amma saita dawo da 6acin ran cin mutuncinsa dana matarsa hindu (aunty amarya).

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

*_MUN DAWO LABARI_*

       Sai yamma lik'is Zarah da Walida suka dawo nik'i-nik'i da ledoji, Jiddah dake tsakar gida tana tuk'in tuwo akan gawayi tai sagade tana kallaonsu, dukda tasan hakan daga aunty Nafisa ne, kullum cikin k'ok'arin k'yautata musu takeyi da abinda ALLAH ya hore Mata.........
      Maganar Zarah ce ta katse ta.
        “Kai Yaya Jiddah, irin wannan sakin baki haka? ALLAH sai sauro ya antaya ciki”.
      Walida dake dariya tace, “gashinan kuwa yana yawo k'umu-k'umu wlhy, aimu gidannan ALLAH yay mana arzik'in sauro kam tamkar d'angwate da kud'i”.
     Dariya sukayi su duka har Jiddah, ta rufe tukunyar tuwon data gama tuk'awa tana d'an yarfama rutsin wutar ruwa danya rage zafi kar tuwon ya k'one. “Y'ammatan Umma ya kuka baro Aunty tamu dasu Affan?”.
        “Lafiya lumi wlhy Yaya Jiddah, tamace ace miki ta gode da cika alk'awari”.
    Murmushi kawai Jiddah tayi, dan tasan laifinta.
      ”Wai ina Umma?”. ‘Cewar Zarah dake k'ok'arin shiga bayi’.
    Jiddah tace, “Taje gidan Uncle yahaya, Maman Sadiq ce k'irjinta ke ciwo, shine taje dubata”.
     Walida da Zarah suka had'a baki wajen fad'in “Ayya ALLAH ya k'ara lafiya to”.
     “Amin”, Jiddah ta amsa.

          Ledojin walida ta d'auka takai cikin d'aki tana fad'in “Yaya Jiddah mi zamu tayaki dashine? Naga yau aikin yamuku dare”.
        “Wlhy kuwa auta, amma nama gama, dan miya na farayi sannan, sai dai idan tsakar gidannan zaki share a kunna maganin sauro musami wajen zaman hira”.
       Walida ta amsa da to tana nufar inda tsintsiyarsu take.
        Zarah ma koda tafito sai tace bara ta kwashe tuwon ita kuma. Haka suka k'arasa dukkan ayyukan suna hirarsu a nutse, dolene su burgeka, dankuwa akwai shak'uwa da k'aunar juna mai yawa tattare dasu, hirar tasuma duk akan Auntynsu ce Nafisa.
   
        Ana kiraye-kirayen Sallar magriba Umma ta shigo, a lokacin su Jiddah sun gama komai, sai k'ok'arin d'aura alwala da sukeyi, amma banda Zarah dake fashin salla.
      Atare suka amsa sallamar Ummansu, yayinda suke mata sannu da zuwa da tambayarta mai jiki.
      “Da sauk'i Alhmdllh, y'an yini sai yanzu muke ganinku?”.
      “Wlhy kuwa Umma, aunty dasu Affan Na gaisheki, yanata kukama saiya biyomu gashi gobe akwai makaranta”.
      Y'ar dariya Umma tayi tana cewa, “Ja'iri yau kuma? Amma ranar dayake yaga babansa ai babu yanda banyi ya zaunaba yak'i. Yaya kuka baromin yarinya ta?”.
      “Lafiya lau take Umma, ammafa ni sai naga aunty Nafisa kamar laulayin ciki take?”.
       Harara Jiddah ta zubama Zarah mai maganar,
      “O ke Zarah, wlhy bakida kunya, yaushe kikai girman gane mai ciki?”.
       “Tab lallai, kaji Yaya Jiddah da wani batu dan ALLAH, cikin saikace wani abu........”
        Hijjab Umma ta cillamà Zarah tana fad'in “Zarah k'aniyanki kinji, Anya kuwa ba aure zansa ayi mikiba?”.
        “Wlhy dama yafi Umma, dan Idonta kullum k'ara fetsarewa yakeyi yarinyar nan”.
      Waleeda dake alwala ta kwashe da dariya, yayinda Zarah ta kwad'a Mata harara.
      “A'a nikam Yaya Zarah karki huce kaina, bani nakar zomanba”.

    Haka kullum suke cikin tsokanar juna da wasa da dariya, hakan kuma baisa raini yashiga tsakaninsu ba, Ummansu ta maidasu tamk'ar k'awayenta, sune abokan hirarta sune shawararta, shiyyasa suma basuda wasu aminai a waje sai ita, saikuma a tsakaninsu su biyar.
    Sune abokan juna, sune aminan juna, sune y'an uwan juna.

*_Dare_*

    Da daddare suna zaune a tsakar gida sunacin tuwo, yayinda Zarah kema Umma bayani akan kayan da sukazo dasu.
     
      “Umma tsarabar Dadyn Affan ce Aunty tace mu kawo, takuma bamu kud'in makaranta tace gobe muje mu biya mukoma makaranta”.
       Umma tace, “ALLAH sarki Nafisa baiwar ALLAH, ALLAH ya saka Mata da alkairi, yamata albarka itada zuri'ar ta daku baki d'aya, ALLAH ya cigaba da had'amin kanku kunji”.
      “Amin Umman mu”.suka had'a baki wajen amsawa. Kayan aka shiga bud'ewa, sabulan wanka da wanki, sai man shafawa da omo, kayan shayi da maltina rabin katon, da biredi manya guda uku da kud'in makarantar su Zarah sai kaji biyu gasassu.
       Addu'a sukaita zubama yayar tasu, Umma ta kirata tai mata godiya da addu'a, tace aima dadyn Affan godiya shima.
      Sund'an ta6a hira zuwa tara na dare suka mik'e domin kwanciya, saboda sauro daya damesu gashi kuma su Zarah zasu makaranta gobe.

✨✨✨✨✨✨✨✨

          Da wuri su Walida sukai shirin makaranta, sannan sukai Karin kumallo da d'umamen tuwon jiya da Jiddah ta tashi da wuri ta d'umama musu.
    Bayan wucewarsu makaranta tagyara gidan duka da taimakon Umma, dukdama gidan bawani babba baneba. Saida tagama komai itama zuwa tara da rabi tai shirin tafiya Islamiyya.
     Tsaf tai shirinta cikin Uniform d'inta kalar ruwan toka, (ash color) yad'au guga sai d'aukar ido yake, turarenta da Aunty Nafisa ke k'ok'arin saya musu ta fesa kad'an, sannan ta d'aura Nikab, saidai bata sakeshiba tafito rataye da jakarta mai d'an tsawo kamar suwaga. 'Dakin Umma tashiga da sallama, tana zaune da alama sallar walha ta idar.
        “Umma naga bakiyi Addu'a ba, gashi nakusa makara, nawuce saina dawo”.
      Kai Umma ta d'aga Mata batare da tayi magana ba, dan batason katse addu'arta.
      Jiddah Na fitowa soro ta Saki nik'ab d'inta tare da gyara hijjab d'inta tai addu'ar fita daga gida sannan tafito. Tafiya take a nutse kuma a sanyaye, kanta a k'asa dukda ta sakaye fuskar tata da nik'af. Kullum haka take cikin suturta jikinta, dayawan y'an anguwar a haka suka Santa, saika Tara mutum goma basu iya siffanta maka kamannin fuskartaba, saidai a tafiya kokuma kwatancen ta da suna mai saka hijjab har k'asa da nik'ab, amma mafi yawancinsu sun manta da kamanninta, dan tunda tafara mallakar hankalinta takoma suturta fuskarta..............✍🏻

*_Yanda kuka kar6i labarin yasakani farinciki matuk'a, ina godiya😄🤝🏻, dan haka kumuje Zuwa my guys⛹‍♀ ⛹‍♀_*



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻
*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[3......]_*

   
..............Malam Abdul-ra'uff Maina babban malami ne da akeji dashi cikin Najeriya da wasu k'asashen k'etare makwaftan k'asar, ALLAH ya azurtashi da tarin ilimi, ga tsage gaskiya komai d'acinta a wa'azinsa, yanada manyan makarantun addini sosai a cikin Najeriya da k'etare, dukda bashine kad'ai ya ginasuba, akwai taimakon attajirai da jama'ar gari masu buk'atar d'aukaka kalmar ALLAH.
     Matan malam Abdul-ra'uff hud'u cif, duk da dai a yanzu uku suka rage, ALLAH yayma matarsa ta biyu rasuwa shekaru kusan 15, ALLAH ya azurtashi da y'ay'an da adadinsu zai iya kaiwa 17 a duniya kuma maza da Mata.
             Huwaila itace uwargidansa, yaran gidan suna kiranta da suna Hajia bah-bah, yaranta shidda, maza uku mata uku, Muhammad, Zainab, Abubakar, Adawiyya, Ni'ima, Mahmud.
     sai ta biyu da ALLAH yay mata rasuwa, Sunanta Hauwa'u, suna kiranta da Annau, yaranta uku, Ruk'ayya, Aliyu, Siyama.
           Ta Uku Habiba, suna kiranta iya habi, yaranta hud'u, Umar, Bilal, Aminatu, Abdul-aziz.
     Sai Amarya Mariya, suna kiranta gwaggo, yaranta hud'u itama, Binta, Usman, Asiya, Na'imah.
    
        Agidan malam bazamu ce ba'a kishiba, anayinsa kam sosai, saida ba kishi Na haukaba, kishi akeyi Na matan da sukeda ilimi.
      Mafi yawa daga cikin y'ay'an malam ALLAH yabasu ilimi sosai, amma Wanda zai iya bugar k'irji yakira magajinsa Kai tsaye shine *ALIYU*.
        *Aliyu* mutumne nutsatstse, ma'abocin zirfafa ilimin addini da yad'ashi, yanada sauk'in Kai sosai, bashida fad'a ko yawan hayaniya, komai nasa zaka gansa a sanyaye akuma nutse, badan bashida k'arfi baneba, a'a sanyi tamkar halittarsace, dan ko maganarsa haka take cikin sanyi da nutsuwa. Tunda ALLAH yayma mahaifiyarsu rasuwa sai suka koma kamar an waresu, bakomai Na gidan zakaga an sakosuba sai dai idan mahaifinsu Na kusa, hakan yasaka Aliyu bai damu da sabgogin gidanba inhar bana y'an uwansa biyu ba Mata, gashi yanzu duk sunyi aure sun barshi.
          Zurfin iliminsa da yawan maida hankali wajen bama addini gudunmawa yasaka mahaifinsu malam Abdul-ra'uff yawan jawosa a jiki, ga tausayin maraicin da suke ciki. Aliyu ya ziyarci wurare daban-daban domin Neman ilimin addini, kullum cikin ziyartar zaurukan malamai yake, ba a Neman ilimin addini ya tsayaba, yana ta6a kasuwanci dai-dai k'arfinsa, dan yanada shago Na saida kowane irin nau'in littafi na Addini da magungunan musulinci, ko kad'an bai yarda yajira daga waniba, koda kuwa mahaifinsane.
      Wannan k'ok'arin nasa da ho66asa yasaka wasu daga cikin y'an uwansa jin haushinsa, dan aganinsu kullum Malam yafison Aliyu fiye da kowa a gidan. Bawai su kad'aiba, hatta da iyayensu suna a kan wannan tunanin.
         Saidai kuma bahaka bane ga malam, dukda dama ko cikin y'ay'anka akwai Wanda zakaji yafi soyuwa a gareka shi duk yanason yaransa, dan mutumne Maison y'ay'a sosai, kawai abinda basu ganeba (zuciya na k'aunar mai k'yautata Mata a koda yaushe) wannan shine kawai sirrin da Aliyu yabi wajen samun matsayi ga mahaifinsu dama wasu jama'ar dake zagaye da mahaifin nasu.
  
         Yanada shekaru 27 a duniya ALLAH ya had'a jininsa da wata yarinya y'ar makwaftansu, sannan kuma d'aliba a makarantar mahaifinsu inda shima yake koyarwa idan yana gida.
        Tunda malam ya fahimci k'aunar dake tsakanin Aliyu da Asma'u saiya nema masa aurenta, dayawan jama'ar gidansu hakan ya 6ata ransu, dan akwai yayunsa da basuyi aure ba kusan su uku. Dayake babu mai damar magana sai basuce komaiba akasha biki cikin tsari Na addinin islama.
        Bayan aure da kamar wata uku matsaloli sukai yawa a gidan Aliyu, dan kuwa tunda akakai Asma'u gidansa yakasa kusantarta, badan bashida sha'awar hakanba, a'a lamarinne kawai ya gagara bisa alamun bashida cikakkiyar lafiya.
       A matsayinsa na mai ilimi zaunar da Asma'u ya farayi ya fahimtar da ita akan tayi hak'uri ya fahimci baida lafiya, baikuma ta6a fahimtar hakanba saida yay aure, dan kafinma yay aure yakanji sha'awa, sai dai a jarabawa ta Ubangiji yakasa biya Mata buk'ata, yana neman alfarmar fara neman magani.
       A wannan zama tayi masa uziri da fahimtarsa, amma yayinda tafiya tafara nisa sai hak'urinta ya nemi gazawa, dukda k'ok'arin neman magani da Aliyu yakeyi ba'a daceba har kusan watanninsu bakwai da aure.
       Yakanyi wasanni da Asma'u, amma idan anzo batun biyan buk'ata sai Abu ya gagara, ita kuma hakan yana tada hankalinta daga k'arshe kuma babu biyan buk'ata.
       Tabi ta saka kanta a matsananciyar damuwa, dukda k'ok'arin kwantar mata da hankali da Aliyu keyi. Ahankali sai y'an gidansu suka fara fahimtar akwai Marsala, mahaifiyarta ta turketa da tambaya itada yayarta, amarya dake murjewa danjin dad'i ita sai bushewa take a tsaye.
           Bata wani tsaya Jan maganaba ta sanar dasu komai.
    Tun daga lokacin komai ya harmutse, sukace sai Aliyu ya sakar musu yarinya. Yanason matarsa, dan haka yayta basu hak'uri da k'arin neman alfarma akan magani dayake nema, amma Sam sai sukak'i saurarensa.
      Ganin abun zai tasarma tozarci dan harsun fara yawo da magana a anguwa sai malam yayma Aliyu nasiha da nuna masa muhimmancin hak'k'in Asma'u, tunda ta nuna bazata jureba ya sawwak'e mata kawai, kar nan gaba wata 6arnar ta biyo baya.
       Cike da damuwa da tashin hankali yabama Asma'u saki d'aya, har hawaye saida yayi, dan yana masifar son Asma'un.
     A ranar dai kam sai a asibiti ya kwana, kwanansa uku ya murmure yadawo gida, lokacin dayaje gidansa saiya iske sun kwashe komai, sai iya kayansa kawai aka bar masa, shima abinda keda muhimmanci ya d'iba ya kulle gidan ya fito zuwa gidansu.
    Ganin yana tare da damuwa malam ya shawarcesa kozai koma karatune?.
    Babu musu ya amsa. Dandanan aka shiga cuku-cukun nema masa gurbin karatu a k'asar Saudia. Cikin sati biyu komai ya kammala, ya cane cikeda kewar ahalinsa da y'an uwansa Mata biyu, Ruk'ayya da Siyama.

      Tafiyar Aliyu Saudia saita zame masa alkairi abin alfahari, dan ya ture komai gefe ya maida hankalinsa ga karatu da addu'oin ALLAH ya bashi lafiya, tunda yakuma jin dad'in zak'in karatu saiya manta da wani batun aure. Ya maida hankalinsa tuk'uru. akan Neman ilimi da zurfafa bincike wajen malamai. Cikar kamala da girman mazantaka irinna nutsatstsun samari ta bayyana a gareshi, yazama cikakken mutum ma'abocin yawan ilimi, dukda shekarunsa kad'an suka haura talatin hakan bai hana masana duniyar ilimi girmamashiba, idan yana zuba maka tafsir da yaren Nasara (English) zaka d'auka baisan komai a yaren Africa ba, hakama idan ya juye Larabci abin ba'a magana, saika d'auka wani cikakken balarabene d'an asalin k'asar Saudia, hakama 6angaren yarensa Na Hausa yana nan daram a harshensa bai manta komaiba, dukda baya cikin Nageriya tafsiransa suncika ko'ina Na k'asar cikin harshe daban-daban, wa'azinsa yana saka zukatan bayin ALLAH nutsuwa ta musamman da k'arajin tsoron ALLAH, idan kaji tafsir nasa dolene ka nutsu wajen saurare da k'arajin tsoron UBANGIJI matuk'ar k'urewa, tsage gaskiya yake komai d'acinta.
        Tunda yabar Najeria bai sake waiwayenta ba, saidai idan mahaifinsa yaje Umara ko wani Abu ya kaishi ya ziyarcesa, amma koda yaushe suna tare a Video call da mahaifinsa da y'an uwansa su Siyama dama sauran jama'ar gidansu.
     Ganin shekaru sunja malam ya shawarcesa akan ya dawo k'asarsa hakanan, kodan ya cigaba da kula dawasu al'amura nasa, saboda shi girma yafara kamashi, sauran yaransa kuma ba kowa keda makamancin halayya ta Aliyu ba, hasalima yafisu indai a fannin ilimine.
     Bisa ga bin Umarnin mahaifinsa ya tattaro ya dawo, kusan shekararsa d'aya kenan, tunda ya dawo malam ke zuba ido yaji kozaiyi batun aure, amma shiru kukeji babu wani motsi, sai harkokinsa Na k'ok'arin yad'a ilimin addinin islama yakeyi ta hanyoyi da dama. Dan ALLAH ya d'aga darajar *_Sheirk Aliyu Abdul-ra'uff Maina_* fiye da zaton mai hasashe a ciki da bai Na Najeria da k'asashe masu mak'waftaka, harma sunansa nason fin Na mahaifinsa dan masu iya magana kance kowa da zamaninsa.
       

   Wannan kenan👌🏻🚶🏻‍♀.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

            K'arfe d'aya dai-dai su Jiddah suka tashi daga islamiyya, kamar yanda ta saba saida tai salla a masallacin makarantar gudun kafin taje gida lokacin salla ya shige, gashi a k'asa zata tafi.
     Bayan sun idar da sallar da d'alibai irinta masu tsayawa ta tako a nutse zuwa wajen makarantar, da d'an sauri-sauri take tafiya akan k'ok'arinta na isa gida da wuri ta taimaki Umma da aiki, tasan tana can tana fama da gawayi danyin girkin rana. A hankali ta furta “Anya Abba kana tsoron gamuwarka da mahaliccinka kuwa? Kana gudun tashi cikin masu shanyayyen jiki a jerin raunana wajen gina adalci akan iyalai? Ya rabbi ka shiryi Abbanmu, ka ganar dashi gaskiya kafin ka kar6i ruhinsa”. hawaye masu d'umi suka gangaro a kumatunta, bata damu da son sharewa ba dan tasan babu mai ganinta, da wannan ta k'arasa gida.
     Kamar yanda ta saba tai addu'ar shiga gida sannan ta shiga da sallama bayan ta tsaya a soro ta goge hawayenta.
         A k'ofar kicin ta iske Umma nata faman fifita wutar gawayin.
    Umma ta amsa Mata tana fad'in “Lale da malama Jiddah, har an dawo?”.
     Jiddah ta yaye nik'ab d'inta tana murmushi saboda jin tsokanar Umman tasu, “kai Umma inafa malama, kodai d'aliba, sannu da gida”.
      Umma dake dariyar amsar Jiddan tace, “yauwa, ai kuke da sannu”.
     Bokitin fenti Jiddah ta jawo ta zauna tareda k'ok'arin kar6ar maficin hannun Umman. Umma ta hanata tana fad'in “A'a baiwar ALLAH daga dawowa, kid'an huta mana ko Uniform ki samu ki cire, nasan dai kinyi salla a can?”.
        “Umma karki damu, wlhy banajin wata gajiya, dama saurin danaketa yi kenan, dan jiya gawayinnan Na fahinci jik'ak'k'ene, yau da safema da k'yar ya kama”.
      “Aifa naga alama wlhy, sauk'inma nagama miya, dan nasamu sund'an kawo wuta shine nayi akan abincan da Nafisa ta sayo mana, ina k'ok'arin d'ora shinkafar suka d'auke wutar”.
        “Ai y'an wutarnan basuda alk'awari, sannu da k'ok'ari Umma, amma ina kika samu kud'in kayan miya harda gatantamu?”.
       Murmushi Umma tayi, sannan ta mik'e zuwa cikin kicin d'in tana bama Jiddah Amsa,
      “Kud'in adashin nanne hajia Lantana ta kawo, ni harma Na fidda ran samunsu, to naga ga kajin da Nafisa ta bamu sai kawai naba Dauda ya yomin cefane”.
      “ALLAH sarki Ummanmu abin alfaharinmu, mai share kukanmu, ALLAH ya saka da alkairi, kingani kuma darajar hak'urin da mukai ga kud'in wajen hajia lantanar sun fito, bayan kowa ya fidda ransa ga samunsu, Umma sai ki koma sana'arki karmu cinye kud'in a ciki mu koma tsugunne-tsugunne”.
        “Nayi wannan tunanin wlhy nima Jiddah, shiyyasa tun d'azun Na Kira Nafisa muka kuma shawartawa kafin kuma ku dawo kuji yanda mukai”.
       “To shikenan Umma, aimu duk abinda kuka yanke dai-daine a garemu, ALLAH yayi mana jagora”.
    “Amin” Umma ta amsa.

          Bayan gawayin ya Kama sosai Jiddah ta d'ora ruwan shinkafa, cikin amincin ALLAH dandanan ta gama, tana cikin kwashewa a kula su Zarah suka shigo da sallama, kowa a galabaice yake saboda rana. Sannu Jiddah tai musu, hakama Umma. Walida ta wuce gaban randarsu da suke zuba ruwan sha saboda k'arancin rashin wutar lantarki ta k'asar tamu Tasha.
       “Ke kuwa walida ki taimaki kanki da wannan ruwan hakanan kafin ya k'ulle miki ciki”,
       Kofin ta ajiye tana had'iye Na bakinta cikin hura hanci, “Umma wlhy k'ishirwa Na kwaso, yau Na manta banje da ruwaba saboda saurin karmu makara, nikuma bana iya shan Na bohol d'innan Na makaranta wlhy”.
      “to miye matsalarsa?”. Cewar Jiddah dake shiga falo da kular abinci..
       Caraf Zarah tace, “Yo iyayi irin nata dai Yaya Jiddah.......”
      “Kai Yaya Zarah kiji tsoron ALLAH, kemafa kinsan baida dad'i wlhy”. ‘ta k'are maganar da turo baki gaba’.
     Umma dai tana jinsu bata sake tankawaba, saida tagama kashe wutar da Jiddah ta sauke abinci sannan tace, “Da wannan gardamar mara amfani dama tashi kukai kuka cire Uniform kuka watsa ruwa, dan sai k'aurin rana kuke”.
          Duk sai suka kumbura baki, wai danmu Umma zatace suna k'aurin Rana.
     Fahimtar hakan ya saka Jiddah da Umma kwashewa da dariya, Umma ta toshe hanci tana ra6awa ta gefensu ta shige d'akinta. Jiddah ma saita shige d'aki tana dariya.
      Zarah da Walida suka kalli juna suna jinjina kai irin zamu rama d'innan. Walida tace, “y'ar uwa barsu sunci bashi indai munai, daga Umma har yaya Jiddah kowa munsan lagonsa. Dariya suka kwashe da ita suna tafawa, sannan duk suka mik'e zuwa d'akinsu inda Jiddah ta shiga.

       Duk d'insu saida kowa ya samu ya watsa ruwa, Walida tayi salla sanna suka hallara a falo domin cin abinci. A babban faranti Jiddah ta zuba musu suka saka miya da namansu a sama, suduka har Umma suka saka hannu bayan walida ta d'ebo musu ruwan tulu mai sanyi. Dama can haka suke cin abinci su Biyar, bayan auren Aunty Nafisa ne suka koma su hud'u, tunda suka taso a wannan tarbiyar suka tsinci Kansu, harma sun Saba, kowa baya iya sakin jiki yaci abinci shi kad'ai saida y'an uwansa. (Iyaye mu kula wlhy, cin abincin yaranmu a waje d'aya yana k'ara musu k'aunar juna a zukata, dan kowa nacin yawun d'an uwansa, shak'uwa da soyayya na sake shiga tsakaninsu, wannan k'yak'yk'yawar d'abi'ar da muka bari tana taka rawar gani wajen raba kayin y'ay'anmu tundaga tushe. ALLAH yasa mugane🙏🏻).
      
      Babu mai magana har suka gama tsaf, suka koma kan nama, kowa yanaci a nutse babu had'ama balle nuna zalama. Bayan sunyi nak walida ta kwashe kwanikan ta gyara wajen, daganan suka baje a falon suna cigaba da hirarsu mai cike da k'arama juna sani ba surutai marasa amfaniba............✍🏻

Wannan kenan👌🏻🚶🏻‍♀.


*_Assalamu alaikum, dan ALLAH Zan d'anyi wani tsokaci a fahimceni. Gameda masu turamin massages ta PC wasu suna ganin tamkar wulak'ancine idan sun tura ban amsasuba a lokacin, Ku gane wani Abu, inada aurefa, sannan inada uzirirrika tamkar kowacce mace, sannan duk lokacin da ka gama typing ko sha'awar ta6a waya bakayi wlhy, ji kake kanka ya d'auki zafi,  sannan fa bake kad'ai bace, mutum yakan samu sak'onni sama da 200 a rana d'aya, banda Na groups, tayaya kuke ganin Zan iya amsasu a lokaci d'aya😄?, shiyyasa nake barin kamar sak'o Na yau Na amsashi da safe kafin Na Fara typing, dana gama nai posting saisu wuce gaba d'aya, to dan ALLAH kuringa mana uziri🙏🏻. Kuma masu Comments a groups wlhy ina kula da kowa, kuma inajin dad'i matuk'a, amma kunyi yawan da bazan iya binku d'aya bayan d'aya Na amsaba wlhy, dan groups ne sama da 30, dan ALLAH kuma kuyi mini afuwa, amma kuna raina kuma ina kula da motsin kowa wlhy, ngd ALLAH yabar zuminci, inajin dad'in addu'oinku gareni da mahaifina😭🙏🏻🥰🥰🥰👌🏻_*

_Naga an bud'e groups d'in MUTUM DA DUNIYARSA kusan 8 kuyi hak'uri sunyi yawa wlhy, dan haka Zan fita a wasu, kafin Ku had'ama wayata zafi😂, inba hakaba nakoma la6e a WhatsApp aradu😫🤣⛹‍♀⛹‍♀._







*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[4......]_*

   
..............Kamar yanda suka saba a kowanne dare bayan sallar isha'i akwai karatun manya magidanta a masallacin k'ofar gidan malam. A da shikeyi, amma dawowar Aliyu sai abun ya rabu biyu, malam Na koyar da dattijai, shikuma Aliyu matasa. Kowacce rana akwai littafin da suke karantawa, yauma kamar kullum Qur'an ne a gabansu, yayinda Sheirk Aliyu Maina ke karanto ayoyi daga suratul An-nisa cikin zak'in muryarsa da sanyin irinna masu nutsuwa. da alama ma yau suka shiga Surar, dan fako yake karantowa cikin kwarewar larabci da taka tsantsan.
        Masallacin yayi tsit kowa yana saurarensa, sai da ya maimaita ayoyin daya karanta sau uku kafin ya d'ago idanunsa yana kallon d'aliban nasa da zasu iya kaiwa 40+, fuskarsa d'auke da murmushi mai sanyi.
      Cikin nutsuwa suka shiga maimaitawa suma, yayinda yake musu gyara a inda yaji kuskure.
       Har k'arfe 9 suna karatu.
      Sheirk Aliyu ya kalli agogon fatar dake d'aure a tsintsiyar hannunsa, ganin har tara da kusan kwata yay d'an gyaran murya alamar su dakata. duk kallonsa sukayi, yad'an murmusa yana fad'in “Masha ALLAH, Inaga yakamata mu dakata haka, domin kowa yaje ya k'arasa Uzirinsa”.
        Duk sun amsa masa da to.
     Addu'a yay musu kafin kowa yatashi ya fito bayan sunbashi hannu duk sunyi musabaha da bankwanar tashi lafiya.
   Bayan fitar kowa ya tattare littatafansa yana zare farin glesses d'in fuskarsa sannan ya mik'e shima ya fito. Cikin gidan ya nufa, inda a zauren farko ya iske mahaifinsu malam Abdul-ra'uff da dattijan d'alibansa. Rissinawa yay ya gaidasu, dan yaga da alama suma sun gama karatun nasu na yau, har zai mik'e Malam yace, “Ali inason ganinka kuwa”.
      Kansa a k'asa ya amsa da “To Babah gani”.
     “A'a ba ciki zaka shigaba? Shiga ka fito zuwa sannan Na kammala nima”.
       “To”. Ya amsa yana mik'ewa.

       Da sallama ya shiga gidan nasu da a yanzu babu yawan hayaniya, saboda mafi yawan yaran gidan sunyi aure, wad'anda suka rage kuma duk sun mallaki hankalinsu, sai dai jikoki da wasu ke rik'o a matan gidan. Babu kowa a tsakar gida, sai wutar lantarki data haske ko ina kasancewar ba'a kashe gen... Ba saboda masu karatun dare. Kai tsaye k'ofar hajia bah-bah ya nufa uwargidan malam. Saida yay sallama a k'ofar d'akin aka bashi izinin Shiga sanna ya shiga da sallama.
    Hajia Bah-bah da wata matashiyar budurwa da yara biyu suka amsa. Yaran suka taso suna masa oyoyo. Hannayensu ya rik'e cikin murmushi yana fad'in “A'a malam k'arami yau anan za'a kwana kaida Ai'shatu?”.
        A tare suka amsa da  e Kawu! Zamu kwana wajen hajia bah-bah ne, Ammin mu taje Kaduna.
       “Masha ALLAH, ALLAH ya dawo da ita lafiya”. ‘ya k'are maganar yana zama a kujerar kusa da k'ofa’
      Budurwar tace, “Yaya ina yini? Wad'annan iyayen maganar sun tsareka da surutu”.
    Murmushi yayi sannan ya amsa da ”lafiya lau Ni'ima, ya makaranta?”.
     “Alhmdllh yaya”.
Murmushi yayi yana maida hankalinsa kan hajia bah-bah dake kishingid'e tana murmushi tun shigowarsa.
             Cike da girmamawa yace, “Hajia ina yini?”.
    “Lafiya lau Aliyu, har an tashi daga makarantar?”.
     “Muntashi hajia, saikuma ALLAH yasa muna cikin masu kaiwa gobe”.
      “To ALLAH ya datar damu”. Hajia bah-bah tafad'a tana tashi zaune sosai. Yayinda Aliyu ya yunk'ura zai tashi, amma sai hajia Bah-bah ta dakatar dashi ta hanyar fad'in “Aliyu abinci fa?”.
        “Alhmdllh hajia, dan yau nagaji barci zanyi da wuri, idan naci abinci yanzu zai takura min”.
      “To shikenan, bandama dai kanason zama babban kwabo ai kawuce cin abincin gidanku saina matarka, yakamata dai a motsa hakanan Aliyu”.
      Murmushi yayi yana mik'ewa da fad'in “Za a duba insha ALLAH hajia”.
                   Bayan fitarsa Ni'ima tace, “Wlhy kuwa hajia yakamata Yaya Aliyu yay aure, yanzufa kaf gidanan shikad'ai ya rage baiyi aureba a maza, gasu yaya Mahmud da Yaya Usman harsun cika wata hud'u da aurensu, shiko ko maganar ma bayayi, yakamata ya cire Asma'u a ransa, tana gidan mijinta hankali kwance harda yara biyu da cikin Na uku shiko ya zauna”.
        Hajia bah-bah batace komaiba, amma fuskarta ya nuna alamun damuwa da tausayin Aliyun.
                Shikam d'akin iya habi ya shiga itama bayan yayi sallama an bashi izinin shiga, ita kad'aice kawai a d'akin, dan dukta aurar da yaranta, sai yarinyar k'anwarta da take rik'o mai suna Maimunatu, itama budurwace, dan zatakai sa'ar Ni'ima.
      Iya Habi ta tareshi da fara'a kamar yanda ta saba, dan ita mace ce mai yawan barkwanci, cikin tsokana tace, “Tuzurun gidanmu har an tashi daga karatun?”.
     Fuskarsa d'auke da murmushi ya zauna, cikeda sanyinsa ya gaidata, shi mutumne da bashida yawan magana, shiyyasa ko Ana tsokanarsa bai iya ramawa.
       Maimuna data fito a d'aki tawani washe baki, a rayuwarta tana k'aunar Aliyu, amma shi yanda ta lura matanma basa gabansa kokuwa duk malantarce oho.
     “Yaya Aliyu barka da dare”.
     Idanunsa yad'an d'ago ya kalleta kad'an ya janye sanann ya amsa da fad'in ”Yauwa Maimunatu, ya makaranta”.
      “Alhamdllh yaya, d'azun a islamiyya nazo dubaka a office amma saina tarar ka fita ma”.
      “ALLAH sarki”. Abinda kawai yafad'a kenan yay shiru da bakinsa, saima ya mik'e yayinda Maimuna ke shirin zama kusa da kujerar da yake zaune.
     “Iya bara naje sai ALLAH ya kaimu”.
     “ALLAH ya tashemu Aliyu kaji”.
    “Amin iya”.
Maimuna da takaici ya isheta kam batama amsaba, tarasa yanda zata shawo kan Aliyu kanta.
     Iya Habi Na kula da ita, murmushi kawai tayi ta d'auke kanta, tuni ta fahimci Maimuna nason Aliyun.
              Aliyu kam yana d'akin gwaggo itama suna gaisawa, itama mace ce mai yawan sakin jiki da mutane, nanma ya gaisa da k'annensa biyu dasuka rage a d'akinta basuyi aureba, Asiya da Fatima, sanan ya fito zuwa kiran malam.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

          Jiddah dake fitowa daga d'aki cikin shirin fita ta kalli Umma dake zaune a tsakar gida tanajin redio, su kad'aine a gidan, su walida sun wuce islamiyya.
     “Umma bara naje Na duba Maman Sadiq daga nan zanje na duba sa'adatu sulaiman ta islamiyyarmu ance batada lafiya yau ko islamiyya batajeba”.
     “To jiddah saikin dawo, amma a dawo dai da wuri”.
    “To Umma insha ALLAH”.
         A k'afa ta taka har zuwa gidan Uncle yahaya, dan basuda wani nisa mai yawa, ta iske gidan shiru, su Sadiq duk sun wuce makaranta, Maman sadiq dake wance a tsakar gida ta d'ago Kai tana murmushi da amsa sallamar Jiddah.
        “Yau malama ce a gidan namu?”.
     Jiddah ta zauna gefen tabarmar tana yaye nik'ab d'inta, fuskarta d'auke da murmushi ta fara gaisheta. Maman sadiq ta mik'e zaune itama tana amsawa.
      “Maman sadiq yanaji gidan shiru?”.
      “k'annen naki duk suna islamiyya Jiddah, yasu Zarah?”.
     “Suna lafiya, suma idan sun dawo islamiyya zasu biyo dubaki”.
     “ALLAH ya dawo dasu lafiya”,
       “Amin mama”. Jiddah tafad'a tana mik'ewa tsaye, hijjab d'inta ta cire ta d'auki tsintsiya ta share tsakar gidan. Duk wani aiki daya dace tayisa, ta dafa musu taliya bisa Umarnin  Maman sadiq d'in. Bayan ta kammala komai taima Maman sadiq daketa kwarara Mata addu'a sallama ta tafi.
     Daga nan napep ta hau zuwa gidansu Sa'adatu sulaiman d'in.
     Bata wani dad'e a canba takuma hawo napep zuwa gida kasancewar yamma tayi lik'is, gab ma ake da kiran magriba.
    
       Tunda ta fito a napep d'in gabanta ya fad'i domin ganin motar Abbansu a k'ofar gida, jiki a sanyaye ta mik'ama mai a daidaita hamsin d'insa tanufi k'ofar gidansu, kamar kullum saida tayi addu'ar shiga gida sannan ta shiga da sallama.
        Tunkan ta k'asara shiga take jiyo sautin muryar Abbansu Na magana a zafafe.... Batada ikon juyawa dan haka ta ida shiga. Umma Na zaune a kujera y'ar tsugunno, yayinda Abba ke bisa tabarma da Umma ta shinfid'a masa. Yaye nik'ab d'inta tayi tak'arasa gabansa ta durk'usa, cikin rawar murya tace, “Abbah ina yini?”.
         Harara yakuma zuba Mata, wadda dama tunda ta shigo yake mata ita. “Daga ina kike k?, nifa bazan d'auki wannan iskancin nakuba, wlhy duk wadda tajawo min magana saidai ya k'arema uwarku, ke ko kunya bak'yaji kiyita yawo gand'an-gand'an cikin anguwa domin kuji dad'in tozartani a dinga nunaku Ana y'ay'an Alhaji zakari ne ko? To lallai bazan lamunta ba, kodai ki fidda Mijin aure kokuma wlhy Na baki duk Wanda yaymin, itama Zarahn tazo ta fidda miji dan banga amfanin wannan karatunba, kuma da kukeyi bazai amfaneku da Komaiba balleni dake wahala daku”.
       Cikin share hawaye Jiddah tace, ”Abbah kayi hak'uri, wlhy ba wani waje najeba, gidan Uncle yahaya naje Na duba Maman Sadiq batada lafiya”.
       “Wannan kuma ke kika sani, nidai nafad'a miki”.
      Umma na zaune tana saurarensu, duk k'ok'arinka baka isa gane yanayin da take cikiba, dan fuskarta gwanace wajen shanye damuwa da 6acin rai. Koda Jiddah ta tashi ta shige d'akinsu tana hawaye da kallo kawai Umma ta bita, bayan shigewarta ta d'auke idonta tana maidawa ga Abba.
      “Alhaji nikam inason na tambayeka wani abu”.
      Banza yay bai tanka mataba, sai dai ya nuna alamun yana saurarenta.
    Bata damuba itama ta cigaba da fad'in “Shin wani yata6a nuna maka illar abinda kakeyi a rayuwarka kuwa? Baka tsoron ranar da zakayi nadama akan wannan ak'idar taka ne? Kokuwa dan kaga dai ina maka shiru akan lamarin yarannan? Lallai Ubangiji adalin sarkine, domin adalcin mulkinsa ne yasa shi fidda rayayye a cikin matacce wlhy, lallai ina jiye maka ranar dana sani”.
     Umma Na gama fad'a ta tashi ta shige d'akinta. Cike da tsantsar takaici Abba ya bita da kallo, sai dai kuma ya had'iye abinsa ya mik'e domin bin bayanta.
    
    Umma dake zaune a bakin gado tayi tagumi ta d'ago idanu ta kallesa kafin ta janye.
    Zama yay kusa da ita a bakin gadon yana fad'in “ke dad'ina dake Yagana rashin fahimta, to miye Na yankamin wannan maganganun?”.
     Murmushi kawai Umma tayi, dan hakan da yayi yakuma tabbatar Mata da zarginta. Ta d'an kallesa a kaikaice, “Halan yau amarya ta murd'a kanbunta na doguwar tafiya? Shiyyasa aka taho ga juji?”......
      Da sauri ya saka hannu ya rufe mata baki. “Nidai karkimin sharri, a  yaushe na ta6a cemiki juji?”.
      Nanma murmishin Umma tai kawai ta d'auke kanta tana had'iye wani Abu mai d'aci. Lallai rayuwar wasu mazan wanan zamanin Na d'aure kanta, mace batada wani kima ko muhimmanci a garesu sai in zasu biya buk'atarsu. Takanyi wata bataga Abba a Idonta ba, badan tayi tsufan da bazata iya amfanar dashi ba, a'a sai dan kawai ita uwace ta y'ay'a Mata wad'anda ba sune tsarinsa ko ra'ayinsa ba, idan harka gansa yana yawan zuwa gidan to lallai yayi fad'ane da hindatu ko tayi wata tafiyar da bazai iya jurewaba shikuma, to lallai a wannan lokacin zai maida gidanta wajen zuwa, abinda ke 6ata ranta da zuwan nashi shine gushewar farin cikin yaranta, dan yata caccakarsu da jifansu da kalamai marasa dad'inji, badan sun masa laifin komaiba, sai dan kawai su ba abin sonsa baneba............
      Katse mata tunani yay da jawota jikinsa, tai firgigit Na dawowa hayyacinta, sannan ta janye jikinta tana mik'ewa.
      Fuskar Abbah a d'aure yace, “Amma kinsan hakan bakomai bane a gareki sai nemawa kai tsunuwar Ubangiji da mala'iku ko? Dan inada ikon nemanki a duk sanda Na gadama kuma nayi buk'ata.
     Wani murmushi. Takaici Umma tayi tana had'iye hawayen dake Neman cika Mata idanu, da k'yar ta iya furta “Salla ake kira”.
      Tsaki yayi ya cire hular kansa ya ajiye a saman gadon sannan ya mik'e, babbar rigarsa ya ajiye itama kusada hular ya fita.
      Umma ta share hawayen fuskarta da bakin zani kafin tabi bayansa zuwa tsakar gidan. Yana zaune gindin rijiya a kujerar da Umma ta tashi, k'arasowa tayi ta  d'auraye butar k'arfe data d'akko a d'aki sannan ta zuba masa ruwa ta rissina gabansa ta ajiye.
      Hakan yayi dai-dai da shigowar Zarah da Walida suna Y'ar dariya, amma ganin Abbansu Na alwala sai kowa tai azamar had'iye dariyarta, ko kad'an basu Lura da motarsa ba a waje su.
    Kallo d'aya yay musu ya d'auke idonsa, yayinda sukuma suka durk'usa suna gaisheshi.
      “Lafiya”. Kawai yace yaci gaba da alwalarsa.
      Jiki a sanyaye suka maida kallonsu ga Ummansu. “Umma barka da gida”.
     Murmushin kwantar da hankali ta sakar musu tana fad'in “y'an makaranta an dawo?”.
      “Eh Umma”. Suka amsa murya na rawa, kafin su mik'e zuwa d'akinsu jiki a sanyaye.

      Jiddah dake kuka tun bayan tasowarta gaban Abbah ta mik'e da sauri jin maganar y'an uwanta, bata buk'atar su isketa tana kukan, dan haka tai azamar share Hawayenta.
    Yayinda suka shigo da sallama saita tarbesu da fara'a, harda tsokanarsu.
        “y'an matan gidanmu yau kun makara, dolene ayi muku bulalar makara gaskiya”.
      Duk yanda taso 6oye musu hakan bai hanasu fahimtar tayi kukaba, sai gani kawai tai Walida ta fad'o kanta ta fashe da kuka, itama zaran saita had'asu ta rungume tana sakin Nata kukan. Daman sunsan zuwan Abbansu gidan tamkar zuwan 6acin rai ne a garesu da Ummansu abar alfaharinsu da sonsu.

     Umma data d'aga labulensu saboda Abba ya fita masallaci tace, “Kukuma minene haka? Nifa kunsan banason wannan shashancin, kufito kuyi alwala, k Zarah tunda ba salla zakiyiba maza fito ki d'aurayemin kulolin Abbanku Na abinci”. Daga haka ta Saki labulen tabar wajen.
      Suma sai suka saki juna kowacce Na share hawayrnta, sunsan ita kanta Umman nasu k'arfin hali kawai takeyi. Umarninta sukabi suka fito waje, walida da Jiddah suka d'auka butocin al'awala, Zarah kuma ta shiga kicin d'akko kulolin.................✍🏻






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻
*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[5......]_*

   
..............Gaba d'aya saisu Jiddah suka kasance cikin rashin sakewa, dan koda suka idar da salla basu fito tsakar gidaba, duk da zafin da ake zubawa yau. Itama Umma bata nemesu ba, dan tana idar da salla ta fito ta had'a abincin Abba takai falo, baiwar ALLAH harda kunna turaren wuta da maganin sauro. Tana kammalawa Ana kiran isha'i, dan haka bata nemesuba tawuce d'aki dan yin salla.
       Ana idar da sallar isha'i Abba ya shigo gidan, babu batun sallama dama a tsarinsa sai gyaran murya, ada dasu Jiddah Na k'anana dasunji gyaran muryarsa suke guduwa su 6uya. (Humm ALLAH ya k'yauta🙁).
     Babu kowa a tsakar gidan, dan haka ya wuce d'akin Umma, kulolin dake a tsakkiyar falon yake bi da kallo, kafin ya maida kallonsa ga Umma dake can wani d'an loko inda ta maida wajen ibadarta a tsakanin kujeru. Addu'a takeyi, dan haka baice komaiba ya zauna a kujera mai zaman mutum biyu.

      Su Jiddaha sunajin Abbansu na gyaran murya amma babu wanda yay koda gigin lek'owa waje.
     Saima tagumi duk da suka rabga, kowa da irin kalar tunanin da yakeyi.
   Jiddah ce tafara d'ago Kai ta kallesu, tausayin y'an uwan nata Yakuma kamata, cikin kauda tata damuwar ta zunguri walida dake kusa da ita. Kallonta Walidan tayi, Jiddah ta sakar Mata murmushi “Haba Autar Umma, irin wannan tagumi haka? Yau kin rik'e karatun islamiyya ko?”.
         Kasa magana Walida tayi, sai hawaye da suka fara zarya a kumatunta. Jiddah tad'an zaro ido waje tana kamo hannunta “Walida miya faru da kuka haka? Ko bakida lafiya ne?”.
             Kafin Walida tayi magana Zarah tace, “Yaya Jiddah kema kinsan Abbane”.
     “Abba kuma? To mi Abban yayi? Naga da kuka shigo baice daku komaiba ai?”.
       Shiru duk sukayi, Walida ta d'ora kanta bisa kafad'ar Jiddah tana cigaba da kukanta.
      Kamata Jiddah tayi ta tayar zaune, “Kinga kukan ya isa haka to, yanzu dai idan anmuku k'ari kuzo muyi, idan kuma ba ai mukuba muci abinci nabaku wani labari, dan wannan kuka bazai canja komaiba y'an uwana, sai k'arin takaici da saka k'unar zuciya, mukasance masu godiyar ALLAH da samunsa a matsayin mahaifi, wani mahaifinma yafishi munin hali ai, amma masushi basu jefarba, to muma addu'a yakamata mu cigaba da masa kunji”.
     A tare suka amsa da to, kowa Na share hawayensa.
       Qur'an suka d'akko suka karanto inda akai musu k'ari, Zarah ta fara karantowa, dan haka Jiddah taimata gyara dakuma maimaita mata har saida taji ya zauna a harshenta sannan takoma kan Walida, itama saida ya zauna sannan sukai Addu'a, Zarah ta fita d'ebo musu abinci.
     Koda suka zauna zaman cin abincin sai duk suka kasa, sai kad'an sukad'an tsakura kowa yace ya k'oshi. Damma kad'an suka zuba.
  
              Daga Umma har Abba suna jiyo sautin karatun su Jiddah daga falo, shi yanacin Abinci ita kuma tana zaune gefensa, dukda dai ba wata hira sukeyiba, garama shi akan kirashi a waya lokaci-lokaci, wani ya amsa wani ya share.
         Itadai Umma ranta cike da farin cikin jin sautikan muryoyin y'ay'an nata Na karatun littafi mai tsarki, saitaji kaso mafi yawa Na damuwarta ma ya ragu.
        (ALLAH sarki Umma😿)

★★★★

     Da asuba Umma da kanta ta fito ta hura gawayi, dan sanda Jiddah ta tashi harya ruru, lokacin anata kiran sallar farko.
        Jiddah Ta fito tana fad'in “Umma kinga yau mun kusan makara wlhy”.
     Kallonta Umma tayi tana d'aura tukunya bisa garwashin, “Ai dama yanzu nake shirin zuwa na tadaku Jiddah, halan baku kwanta da wuribane?”.
        “Kusan haka kam Umma, yanzu mi Zan miki?”.
       “A'a jekiyi alwalanki kawai, suma su Zarah ki tadosu”.
    ”To Umma”.

    Abba ya fito daga d'akin Umma fuska a d'aure, kai kace sak'on mutuwa aka aiko masa, Butar da Umma ta cika da ruwa ya d'auka domin yin alwala.
       Su Zarah da Jiddah ta taso harsun lek'o kai zasu fito suka koma saboda ganin Abba atsakar gida, ciki suka koma, idan yagama ya fita sa fito.
    Shikam baima San sunayi ba, yana kammala alwalarsa batareda yacema Umma komaiba yanufi hanyar soro, k'ofa ya bud'e ya fita.
      Umma ta sauke ajiyar ziciya kafin ta kalli k'ofar d'akin su jiddah tana fad'in “Ku kuma Na la6e saiku fito ko”. Ashe tana kallon su Walida sanda zasu fito suka koma.
       Fitowa sukayi, walida ta d'auki butar alwala, Zarah kuma ta matso wajen Umma.
     ”Umma dan ALLAH nad'an d'iba ruwannan?”.
       Umma ta mik'e tana cewa “Ki d'iba mana, Amma ki k'aramin”.
     “To Umma Na gode”.

Lokacin da Abba ya dawo su Walida duk suna tsakar gida, bayan sun idar da salla suka fito suna kimtsa gidan.
    Umma ta dama kunu, sai Jiddah dake suyar fanke, Walida Na bakin rijiya tana wanke-wanke, Zarah kuma sharan tsakar gidan bayan ta gyaro d'akinsu.
    Umma ma tana gyaro nata d'akin, dan inhar Abba Na gidan bata barin su Jiddah shiga mata d'aki.
         Da gyaran murya ya shigo kamar kullum, dan haka su Walida duk suka nutsu, Dama bawani hira sukeyiba. Kowacce gaisheshi ta shigayi, ya amsa saud'aya yana harare-hararen Neman kuskuren dazai ci zarafinsu. Saidai kuma baiga komaiba, dan haka ya shige yana fad'in Zarah ta goge masa takalmansa.
     Da to ta amsa muryarta Na rawa.
           A d'arare su jiddah sukaita komai tamkar jiya da daddare, su Walida dai suka samu sukai shirin makaranta bayan sun cakuli abinci, dan yauma basuci Na kirkiba.
      Lokacin da sukema Umma sallama Abba yanaji amma bai tankaba, sai Ummace taimusu addu'ar dawowa lafiya.

    Jiddah ma a gaggauce takuma kimtsa gidan tai shirin Islamiyya ta fito, dukda da sauran lokaci ta gwammace tabiya ta gidan Uncle yahaya ta cinye lokacin acan.
    Kodà tazo yima Umma sallama bata hanata ba, dan tasan gudun zama suke a gidan.
      Bayan duk sun fice Abba ya kalli Umma yana wani cika da batsewa yace “Yagana had'amin ruwan wanka”.
      Da “to” ta amsa tana mik'ewa ta fice. Babu dad'ewa ta dawo tace ta had'a.
     Fitar Abba wanka babu jimawa wayarsa tahau ringing, Umma batako kalletaba balle tayi tunanin d'auka harta tsinke aka kuma Kira, nanma sharewa tai, ganin anyi kira Na hud'u ta nufi wayar danta duba.
      *Matata*
Shine abinda taga an rubuta a jiki, dan haka ta maida ta ajiye masa kayarsa takoma wajen zamanta.

   Daga can ba k'aramar harzuk'a hajia Hindu tayiba, dan jikinta ya bata yana gidan matarsa. Shanye damuwarta tayi, saboda tana cikin taron mutanene, k'awarta ce ke aurar da y'a a jigawa shine taje. Dalilin kiran nasa kuwa ta kira kalifa ne taji idan sun wuce makaranta shine yace Mata driver yace babu mai a mota, kuma Abbansu tun jiya da yamma daya fita bai dawoba. Shine ta kirashi taji ina yaje? amma har Kira hud'u babu amsa.
      Tana cikin wannan tunanin Kira ya shigo wayarta. Abba ne daya fito daga wanka Umma ta fad'a masa an kirashi shine ya duba, ganin Hajia hindatu ce yay azamar kiranta yana shigewa bedroom yabar Umma a falo. Sai dai kuma har wayar ta tsinke bata d'agaba. Kuma kiranta yayi.
        Hajia Hindu dake kallon wayar taja guntun tsaki sannan ta d'aga. Ko sallama babu tace, “Alhaji kana inane?”.
      Dukda tambayar tabashi haushi saiya danne, saikace wani yaronta. Amma a fili sai yace, “Haba Maman kalifa ko gaisuwa ma babu?”.
      Dogon tsaki taja, a harzuk'e tace, “Kaga malam nifa ba wannan ya sakani kiranka ba, yara suncemin tun jiya baka gida, gashi yau sun tashi motarsu ta zuwa makaranta babu mai........”
          Cikin nuna damuwa da 6acin rai yace, “Amma driver d'innan d'an iskane,  shine bazai kirani a waya ya sanarminba?, to lallai bazan yarda da wannan iya shegenba......”
      Hajia Hindu ta katse masa magana da fad'in, “Aiba laifinsa bane shi kad'ai, inda jarabarka bata motsaba katafi wani waje ka kwana hakan zai faru? Kamayi duk yanda zakayi kakaimin yara makaranta kafin su makara”.
        Kafin yayi magana ta yanke wayar. Ya dafe kansa saboda takaicin yanda Hindu ke datsa masa magana tamkar boyi-boyinta. Da hanzari yahau shiryawa, dukda ba zaman gidan yakeba yanada kaya a gidan.

         Lokacin daya fito Umma na k'ok'arin had'a masa shayi da kayan tea d'in da Nafisa ta kawo musu.
      Ganin zai fice tayi saurin fad'in “Abban Nafisa ina kuma zakaje ga Karin kumallo ina had'a maka?”.
        “Kinga barshi Yagana, su kalifa zanje nakai makaranta karsu makara, motar da ake kaisu makaranta babu mai”.
      “To”.
Kawai Umma tace masa taja bakinta tayi shiru. Shikuma ya ajiye dubu uku a hannun kujera yay ficewarsa batareda yayi bayaniba.
        Ko motsi Umma kasawa tayi a wajen balle tasamu damar d'aukar kud'in. (Nace, “Humm”🙁).

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

       Lokaci da Aliyu ya fito daga cikin gida malam ya shige falonsa da k'ofar ke a zaure Na biyu.
     Sallama yayi ya amsa masa tare da bashi izinin shiga.
    Malam dake kishingid'e bisa lallausar dardumar dake wani sashe Na falon ya d'ago ido yana kallon Aliyu bayan ya rufe littafin dake hannunsa. Zama Aliyu yayi a gefen dardumar, malam yaymasa alama daya matso kusa dashi. Matsawa yay yana guntun murmushi.
     Saida suka nutsu malam yace, “Aliyu!”.
      Cikin sanyinsa yace, “Na'am baba”.
       “Aliyu ina muka kwana akan batun aure? Nazata a shekara d'aya da dawowarka yaci ace kazomin da zancen samun Matar aure, amma sainaji tsit, mike faruwane?”.
         Kansa a k'asa ya kasa kallon malam, cike da kunya yace, “Baba ai har yanzu......”. Saikuma yay shiru.
      “Har yanzun mi?”. Cewar malam yana kuma tsareshi da idanu.
       Aliyu yakuma k'asa da kansa. “Baba har yanzun banida tabbas akan samun......”. Nanma ya kasa k'arasawa.
      Murmushi malam yay, dan ya fahimci inda Aliyun ya dosa.
      “Ali kenan, to ai a ganina auren shine zai banbance mana hakan ko? Zamanka haka babu aure a matsayinka Na babban mutum mai koyar da ilimi da yad'ashi ko kusa bai daceba, aure shine cikar kamala Na kowanne d'an Adam, duk girmanka da mulkinka da addininka saika saka rigar aure kake kuma daraja a idon jama'a. Yakamata ka nemo Matar aure hakanan, idan kuma ni Na nemo maka to shikenan. Ni dai nabaka watanni uku idan ALLAH ya kaimu, daka dawo daga tafiyar nan da zakayi kafara shirin aure, inason kafin azuminnan mai zuwa ka ajiye iyali, kaje kayi shawara, zaka nemo kona nema maka kafin ka dawo?, idan kuma kanada wadda kakeso saika sanarmin, dan nikam nagaji da ganinka haka kana yawo babu aure”.
         “Amin afuwa baba, insha ALLAH Zan duba, abinda Na yanke zakaji zuwa Safiya idan ALLAH ya kaimu, ALLAH ya huci zuciyarka”.
     “To Alhmdllh, ALLAH ya kaimu lafiya, kenan kanada wadda kakeso?”.
      ”A'a baba”.
“To shikenan, kaje ina saurarenka zuwa safiyar. Akwai wasu littatafai da Malam Salis keso, nace masa Zan tambaya masa ko kana dasu”.
      “To Baba wannene?”.
“Yafa bani a rubuce dama dan karna manta, duba littafincan ko ciki Na saka takardan”.
      Mik'ewa Aliyu yayi zuwa inda kantar buks d'in malam take, ya bud'e littafin dake a jiye a k'asa da malam ya nuna masa.  A shafin farko yaga k'aramar takarda dan haka ya d'akko yana nuna masa.
    Kai malam ya jinjina alamar eh itace.
    Aliyu yay masa sallama sannan yazo ya fice domin zuwa makwancinsa..

           K'aramun gida dake jikin masallacin malam nanne gidan da yaran malam maza duk suka zauna kafin aurensu, ayanzu haka Aliyu ne kawai a ciki sai idan malam yayi bak'i ai musu masauki anan.
     'Dakinsa dake can k'arshe ya bud'e da key ya kunna fitilar wayarsa sannan ya shiga da sallama, d'akine babba dake malale da kafet ruwan makuba (oxblood) sai k'atuwar katifarsa irin wadda ba'a sakawa a gado, sai firij da kantar litatafai da k'aramar wardrobe ta kayansa, d'akin babu wani tarkace dan mazaunin cikinsa ma'abocin tsaftane a koyaushe. Fitilar wayarsa ya kashe ya kunna wadda yake amfani da ita idan babu wuta, dandanan d'akin ya gauraye da haske.
         Wata k'ofa danake k'yautata zaton bayice a d'akin naga ya shiga. Kusan mintuna 30 saigashi ya fito da alama wanka yayi.

       Bayan malam Aliyu ya kammala dukkan uzurorinsa yazo ya zauna a gefen katifarsa yana jawo lap-top d'insa, yanar gizo ya Shiga domin duba sak'wannin jama'a Na neman fatawa da masu gaisuwa.
       Ahankali yake binsu d'ai-d'ai yana dubawa, wata fatawar ta tausayi wata ta mamaki, wanima takaici ne tsantsa a ciki. Wasu yakan basu amsa, wasu kam wucewa kawai yakeyi. Wani sak'o dayaja hankalinsa matuk'a ya nutsu yana kuma dubawa.

*_Assalamu alaikum. Malam barka da warhaka, malam wlhy inada damuwa ne, kuma Na rasa Wanda Zan tunkara da ita. Mu hud'u iyayenmu suka Haifa, mata biyu maza biyu, nice nake bima babban wanmu sai k'anwarmu sai kuma autanmu, to malam yanayin rayuwar da muka tashi ta ak'idar boko saiya zamto ta6a jikin juna irinsu runguma da zama kusa da juna hakan ba komai bane nida y'an uwana, wannan kusancin mai tsanani saiya kaimu ga fara wuce iyaka har yayana yafara kwanciya dani, iyayenmu basu ta6a saniba konace ak'idar data lullu6e zukatanmu bata ta6a kai tunaninsu da zarginmu ba, malam yanzu haka maganar da nake maka inada ciki wata hud'u kuma bansan da shiba sai kwanaki 6 da suka shige, hankalina yatashi na nufi d'akin yayana danna sanar masa saina taddashi yana irin abinda yakeyi da ni da k'anwarmu dake bimin. Malam narasa yazan fassara wannan halin dabbancin namu, sakacin iyayenmu ne? kokuwa d'aukar ak'idar da bata dace da addininmu ba?, wlhy jinake tamkar Na kashe kaina malam, nayi nadamar rayuwata data y'an uwana, malam ka taimakeni da shawara dan ALLAH😭🙏🏻_*

Tagumi kawai malam Aliyu yayi ko yatsansa yakasa motsawa, sai had'iyar yawu yake mai d'aci da k'yar, idonsa ya kad'a yayi jazur, yama rasa yanda zai fassara wannan kwamacalar, anya wannan duniyar kuwa mutane na tunanin barinta?.
     Kansa dayaji yana Sara masa ya dafe tare da ture lap-top d'in gefe ya zame ya kwanta a katifar.         
        Gaba d'aya zuciyarsa ta k'untata, wasu hawaye masu d'umine suka silalo masa a kumatu.
         Yaja tsawon lokaci yana jujjuya abin a ransa, har agogo ya nuna k'arfe 1am bai iya runtsawa ba, mik'ewa yay yashiga toilet ya d'auro alwala ya dawo yafara jero nafilfili, a cikin sujudansa yana kuka da jaddada neman gafarar ubangiji. Sai kusan 3am ya idar, jin idonsa ya cika da barci yakoma saman katifar ya kwanta.
     Amma maimakon barcin yazo saiya fad'a duniyar tunani akan maganar baba kuma, dukda wancan maganar yarinyar nata cin zuciyarsa a gefe. Harga ALLAH a yanzukam baisan kuma ina zai nemo mataba, dan tun tabon da Asma'u tabar masa har yanzu baigama gogewaba, gashima bashida tabbaci akan ingancin lafiyarsa har yanzu.
     Kwanciyarsa yakuma juyawa yana ayyana kodai yabama baba damane kawai, k'ila shi yanada wadda ya hango ta dace dashi, tunda yasan baba bazai ta6a masa za6en tumun dare ba.
     Da wannan tunanin barci ya saceshi bai fargaba............✍🏻






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[6......]_*

   
..............Da k'yar ya iya tashi da asubar farko, dan kansa ciwo yake masa, bayi yashiga ya d'aura alwala kafin ya fito ya canja kayan barcinsa zuwa jallabiya ruwan madara, yad'an fesa turare sannan ya fice.
          Tunda ya dawo shike kiran sallar farko a masallacin, yauma kamar kullum zazzak'ar muryarsa mai cikeda sanyi ta karad'e anguwar. Koda ya kammala kiran salla ba zama yayiba, saida ya gabatar da nafila raka'a biyu kafin yay zaman karanta littafi mai tsarki. Ahankali mutane d'ai-d'ai suka fara fitowa, ciki harda malam.

          Bayan an idar da sallar Asubahi Aliyu bai fitaba, zaman yin azkar na safe yay, saida ya kammala sannan yafito a massalacin. Shiga yay suka gaisa da Malam.
     Kallo d'aya malam yayi masa ya karanci damuwa mai tsanani a fuskar d'an nasa, har zai mik'e ya tsaidashi ta hanyar kiran sunansa,
     “Aliyu!”.
“Na'am baba” ya amsa yana waiwayowa ga malam.
        “Dawo ka zauna”.
Bai musaba ya dawo ya sake zama kansa a k'asa.
       “Mike faruwane? ko bakada lafiya?”. Malam ya tambayeshi cikeda kulawa.
        Ajiyar zuciya M. Aliyu ya sauke, cikin sark'ewar murya yace, “Lafiyata k'yalau baba, kawai dai wani abune da ban ya girgiza dukkan kuzarina”. Shiru yad'anyi yana sauke numfashi da ajiyar zuciya, yayinda malam ya kafeshi da Ido amma baice komaiba. M. Aliyu yaci gaba da fad'in “Wani sak'one ya birkita dukkan hankalina wlhy baba...............” tiryan-tiryan ya shiga karantoma baba sak'on yarinyar jiya. Shi kansa baba maganar ta girgizashi, har gumi yad'an tsatstsafo masa a goshi, yanayinsa dukya sauya. Wata ajiyar zuciya ya sauke k'arfi yafara fad'in “Dolene ka girgiza Aliyu, duniyarnan cike take da curkud'ad'd'un abubuwa masu hargitsa tunani, babu abinda ke kusanto duniya sai alamomin tashinta, inaga kamata yay kanemi gidansu ita yarinyar, dan mahaifinta yakamata mu fara gani”.
       “To shikenan baba insha ALLAHU zanyi k'ok'arin hakan”.
        “ALLAH ya bada nasara, ya maganarmu ka yanke shawaran”.
         “Baba kawai nabar maka za6i”.
       “To Alhmdllh ALLAH yasa mu dace”.
    “Amin” m. Aliyu ya fad'a hannunsa dafe da kansa.

        A k'ofar fita daga Falon malam yaci Karo da yayansa Abubakar, hannu ya bashi sukai musabaha cikin girmama juna, Aliyu ya tambayi iyalansa da aiki kafin suyi sallama, Abubakar ya shige shikuma Aliyu ya fice.
          Cikin gida ya koma ya sake kwanciya, dan kansa ya matsa masa da ciwo ainun.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

        Umma ta dad'e zaune zuciyarta Na suya, ta tsurama tea d'in data had'ama Abba ido, wai ko kunya baijiba a gabanta yake fad'in zaije yakai yaransa makaranta saboda motar da ake kaisu babu mai, bayan a gaban idonsa su Walida suka fita amma ko ALLAH ya kiyaye baice musuba? Sai yaushene Alhaji zai fahimci kuskuren da yake tafkawa a rayuwarsa? Kosai guri ya k'ure masane?. Wani lokaci takanji kamar bazata iya jure wannan zamanba, musamman idan ta kalli halin k'unci da yaranta suke a ciki. Sai dai kuma wani 6angaren tana duba wani Abu, yaranta sunkai girman da gidan mahaifinsu shine adonsu, dan burin kowacce y'a a nema aurenta tana gidan mahaifinta gaban iyayenta biyu. Wasu hawayen takaicine suka ziraro mata, tayi murmushin da iyakarsa hak'oranta tareda mik'ewa tahau tattare kayan shayin da Wanda ta had'ama Abban.
          Sallamar Dauda ta jiyo a tsakar gida, ta amsa masa tana fad'in, “Ina zuwa Dauda”.
      Daga tsakar gida ya amsa da “to”.
      Tea d'in data had'ama Abba ta d'auka ta fito, Dauda ya rissina yana gaisheta, cikin sakin fuska ta amsa masa kamar yanda ta Saba. “Yau naga ka makara, ko Baku tashi a makaranta da wuri bane?”.
        Dauda yace, “A'a muntashi, Na tsaya yin rubutune a allona”.
       “To ALLAH ya taimaka, bara Na kawo maka abincinka ka karya saikai maza ka kaimin 6arzan masarannan dan ALLAH, yau sonake nayi dambu, kowa yagaji da shinkafarnan”.
     “To hajia” dauda ya fad'a cikin girmamawa.
     Kunu da fanke Umma ta kawo masa, ta had'o da shayin data had'ama Abba duk tabama Dauda.
            Wasu y'an aikace-aikacen tafara ragewa kafin Dauda daya fita soro cin abinci yagama yakai mata 6arjin masaran.
       Babu dad'ewa ko saigashi, dama ta had'a masa a wani k'aramin boket, dan haka kud'in 6arjin ta bashi dana abinda zai sayo Mata Na cefane. Sannan ta nuna masa masaran.
      Bayan tafiyarsa bata zauna ba, ta kunna redio tana saurare da rage wasu ayyukan gudun zama tunani ya addabeta.

★★★★★★★★★★★★

          Koda Jiddah ta fita bata zame ko inaba sai gidan Uncle yahaya, ta iske su Sadiq sun tafi makaranta, sai mamansu kawai da Uncle yahaya daya dawo jiya. Sosai ta nuna farincikinta da ganinsa, shima cike da tsokana da k'aunar yaran d'an uwan nasa yake fad'in “Sayyadata mafarkin dawowata kikayine?”.
     Dariya Jiddah da Maman Sadiq sukayi, Jiddah tace, “kamar kasani kuwa Uncle, dukda dai banyi mafarkinba amma tunda asuba dana tashi zuciyata keta kwad'aitamin Abbana ya dawo, ashe da gaskene”.
     Uncle yahaya yace, “ALLAH ya albarkaci wannan zuciya da tarin alkairi yarinyata”.
      “Amin Uncle, kadawo lafiya? Wlhy munyi matuk'ar missing naka, kusanfa watanka biyu kenan?”.
         “Nima ina cike da kewarku, dan banda yanda zanyine, inasu Zarah da Maman Nafisa?”.. 
     “Duk kowa lafiya”.
“To Alhmdllh, nima yanzu nake shirin karyawa naje Na gaida Maman Nafisan ai”.
     “To shikenan Uncle, Abba ma yana gidan, inba dai kafin kaje ya fitaba”.
       “Yau kuma ya tuna da anguwar tamu kenan?”. Uncle yahaya ya fad'a cikin takaici.
      Jiddah ma saida yanayinta ya canja. Maman Sadiq ce tai saurin canja yanayin nasu da fad'in “To Y'ar Uncle tashi ki had'a tea ga doya nan a kula”.
      “Wai, wlhy mama cikina a cike yake, makaranta Zan tafima lokaci yayi”.
       “Haba dai jiddodo ai d'anyar fata bata fashewa, ki k'ara lodawa kawai”.
     Dariya Jiddah tayi tana mik'ewa da fad'in “Lallai Uncle ka tanaji kud'in kaini a d'inke nawa, dan nasan dai zai iya fashewa inhar na k'ara masa wani abu”.
        Nanma dariya Uncle da Maman Sadiq sukayi. Jiddah ta nufi hanyar tafiya tana musu sallama.
     Kiranta uncle yayi yabata d'ari biyu.
      “A'a Uncle basai kabani ko nairaba, naci Na k'oshi mizanyi da kud'i?”.
         “Hawa Napep mana, ko har yanzu dai bakiji fad'ana Na hanaki wannan tafiyar k'asanba?”.
      Shiru kawai tayi tana murmushin yak'e, dan tasan tafiyar k'asa zuwa makaranta yazame mata tamkar dolene, tunda ba kullum Umma ke tashi da kud'iba, bazai yuwu ace kullum kuma zatazo wajensa ta amsaba, inama laifin wahalar da yakeyi dasu akan karatun da buk'atun yau da kullum alhalin mahaifinsu nada ransa bai mutuba................
     Uncle ya katse mata tunani da fad'in “Ina kuma kika tafi Hauwa'u!?”.
     Ajiyar zuciya ta sauke ta risina ta kar6a tana masa godiya, sannan tayi musu sallama ta fita.

      Uncle yahaya ya jinjina Kai kawai yanamai jin takaicin halin d'an uwansa, wai ALLAH yay maka k'yau ka butulce masa saboda shaid'ancin zuciya, ga wasu can suna nema da miliyoyin kud'i basu samuba. Yaja guntun tsaki yana faracin abincin da Maman sadiq ta ajiye masa.
          Batace masa komaiba, dan tasan inda tsakin nasa ya dosa.

        Yau da wuri Jiddah ta Isa makaranta kasancewar ta hau napep da kud'in da Uncle yahaya ya bata.
        Makarantace babba mai d'auke da d'alibai Mata zallah, amma yara da k'anana harma da matan aure.
       Wata musabak'a dasu Jiddah sukaje tazo Na d'aya shine ta burge wani bawan ALLAH, a take a wajen yaymata albishir d'in d'aukar nauyinta zuwa wannan makaranta harta gama, dan da iyakarta islamiyyar anguwarsu, a yanzu haka kuma sune ke a aji shida fanin y'an Mata. Tunda Jiddah ta shigo makarantar take samun nasarori, kwakwalwarta takuma bud'ewa, dan ayanzu haka babu wani Kalmar larabci dazata layance mata, a littatafai kuwa Na fannin Addini tuni tayi babbar zarrah, 6an garan Qur'an tadad'e dayin sauka tana akan hadda. Kai bama itaba dukkan Wanda kagani a ajin su Jiddah to kwarone a makarantar, makarantace daduk Wanda yake cikinta lallai ya kwankwad'i ilimi ya k'oshi, dan ana tatosune daga wasu k'ananun makarantu Ana kawosu nan, babu ruwan wannan makaranta dakai d'an wanene?, duk Wanda kagani kaifin kwakwalwace ta kawoshi.
      Kamar yanda dokar makarantar take duk Wanda ka iske a aji dolene kayi sallama, Na ciki su amsa maka, sannan kabisu d'ai-d'ai kabasu hannu kuyi musabaha🤝🏻.
      Yanzuma hakace ta kasance ga Jiddah, bayan tayi sallama duk suka amsa, ta yaye nik'ab d'inta tanabinsu d'ai-d'ai suna gaisawa cikin musabaha da murmushi shinfid'e akan fuskarta, saida takai har k'arshe sannan tadawo mazauninta Na gaba ta zauna kusa da Madeena Isma'il da kusan itace k'awarta da suke mutunci sosai a makarantar.
       Murmushi sukaima juna bayan sun kuma kama hannun juna suna gaisawa.
       “Ukti yau naga kin iso da wuri?”.
      Jiddah tace,  “ki Bari kawai ukti, yau dai naji fad'anki banyo tafiyar k'asaba”.
        “To Alhamdllh da farajin maganata”.
     Y'ar dariya sukayi a tare, wadda shigowar malam Mustafa ta katsesu. Duk suka mik'e suna gaisheshi kafin yabasu izinin zama.
        Jawabin daya kawoshi ya fara musu, danshi ba koyar dasu yakeba, shine Vice principal na makaranta.
      ”Umm Assalamu alikum, nasan zakuyi mamakin ganina a wannan lokacin, wani uzirine ya tasomana Na gaggawa, an gayyaci wannan makarantar cikin jerin taron k'arama juna sani Na k'asashe goma da aka shiryama d'alibai, taron kuma zai gudana ne a sati mai zuwa, insha ALLAH zamu za6i d'alibai biyarne kacal, wannan ajin shine Na manya idan aka cire ajin matan aure, dan haka mun yanke shawarar d'aukar d'alibai biyu a cikinku, insha ALLAH malam Usman zaizo anjima ya za6i wad'anda zasu jagoranci tafiyar amma ta hanyar rubuta jarabawa, daganan zuwa awa d'aya kunada damar yin nazari, zamu dakatar da malamai yau gaba d'aya daga kowanne darasi”.
       Atare ajin ya d'auki kabbarar *ALLAHU AKBAR!!!*.
         Malam mustafa yay musu sallama ya fita.
        Nanfa kowacce tashiga duba littatafanta da fatan dacewa.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

            Abba kam yana isa katafaren gidansa ya iske su kalifa tsaitsaye a harabar gidan suna jiransa. Babu Wanda ya gaidashi, saima tunzura masa baki da suka shigayi wai sunyi fushi.
     Fuskarsa cike da fara'a ya hau fad'in “O shalelen Abba amin afuwa kunji, maza kushiga mota Na kaiku karku makara, Abba yayi laifi ayi hak'uri”.
       Cikin tura baki Hassan yace, “Amma Abba tunfa d'azu muke jiranka, kabarmu dukmun bushe a tsaye”.
         ”Ai nace ayi hak'uri ko Hassan, Muneer taho kaji”. Yak'are maganar yana Kama hannun autansu Muneer.
       Kalifa kuwa da Hussain uffan basuceba, shi kalifa ma iyafis ya saka a kunne, Hussain kam yayi cid'in-cid'in da fuska yana wani shan k'amshi.
            Ko'a mota Muneer ne kawai ke fira da Abba, amma Hussain da kalifa da Hassan tamkarma babusu a motar.
       Ya diresu a makarantarsu mai tsananin k'yau ta y'ay'an manya y'an gata, ya zaro dubu d'aya yabama Kalifa, babu ko godiya yay wucewarsa aji, Hussain da Hassan kuma d'ari biyar², suma dai babu godiyar, amma sun d'aga masa hannu alamar bye.
        Munner ne aka bama d'ari biyu dukda an shiryo masa abinci a lunch box nashi kuwa.
       Kalifa ajinsa uku 6angaren sakandire, Hussain da Hassan su kuma aji biyu, Munner kuwa yana firamare 5 ne.
         Saida Abba ya raka Munner har sashen y'an firamare sannan yashiga motarsa ya fito daga makarantar................✍🏻

Kuyi manage please😄👌🏻

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[7.....]_*

   
..............Kamar yanda malam Mustafa ya fad'a bayan awa d'aya malamin da zaima su jiddah jarabawa ya shigo, sallama yay suka amsa masa tare da gaisheshi.
      Ajin yayi shiru kowa yana kallon malam Sulaiman, yad'an tura hularsa baya yana shafa gaban goshinsa da nazarinsu, saikuma yay murmushi ganin duk sunyi tsuru-tsuru sun zuba masa idanu. Zama yay inda aka tanada domin zaman malamai kafin ya kuma maida hankalinsa Kansu.
        “Inaga nama canja shawara kawai, zanyi jarabawar da baki”.
     Kallon kallo aka komayi tsakanin su Jiddah, kowanne a sanyaye ya amsa da,
     “Na'am ya mu'allim”.
Fita malam Sulaiman yayi, babu jimawa ya dawo shida Malam Shu'aibu da malam mika'il. Nanma su Jiddah gaidasu sukayi. Malam Sulaiman yabasu izinin fita waje su duka, zuwa wajen wata bishiyar dake gaban aji. Ahaka zasu ringa zuwa d'aya bayan d'aya.
        Da yawansu sun rikice, dan kowa baisan miza'a tambayeshiba, ga malam Sulaiman gwanine wajen iya zak'ulo tambaya.
         Amirar ajin mai suna Shamsiyya jamilu yasaka ta rubuto sunayen kaf y'an ajin tazo saman baranda tana kiransu d'aya bayan d'aya. Hakan kuwa tafaru, bayan tagama rubuta sunan kowa aka Fara, gaba d'ayansu dama su 38 ne a ajin, dan haka aka fara komai a tsanake. Kowa ya fito saikaga yana mazurai, nanfa cikin Jiddah Yakuma d'urar ruwa, (dama ita kwai tsoro) saima Madina ce ked'an k'arfafa Mata gwiwa. Tunda aka kira Bilkisu Ahmad Jiddah takuma tsurewa, dan daga bilkisun sai madina sai ita. Bayan fitowar bilkisu aka kira Madina daga nan sai Jiddah, tamkar wadda k'wai ya fashewa a ciki haka ta shiga ajin, inda kowa ke zama idan ya shigo ta zauna itama.
      Malam Sulaiman dake kallonta ya karanto mata tambaya,
          *“Malama Jiddah ko zaki iya fad'a mana Kalmar shahada da Manarta?”*.
       Dak'yar Jiddah ta iya had'iye yawu, k'asan zuciyarta tana addu'ar Neman nasarar yin bayani cikin nutsuwa, zamanta tad'an gyara cikin sanyinta tace,

       *_“SHAIDAWA BABU ABIN BAUTAWA DA GASKIYA SAI ALLAH , KUMA MUHAMMADU MANZON ALLAH NE”_*
         _Wad'an nan kalmomin shahada guda biyu, sune kofar shiga musulunci, sune kuma rukuninsa mafi girma, kuma ba a yin hukunci da musulusncin mutum, sai da furuci da su, da kuma aiki da abin da suka k'unsa, da wannan ne kuma kafiri yake zama musulmi._
    *_MA'ANAR KALMAR SHAHADA_*

             _Ma’anar shaidawa da cewa babu abin bauta da gaskiya sai ALLAH, shi ne yin furuci da ita tare da sanin ma’anarta, da kuma yin aiki da abin da tak'unsa, zahiri da bad'ini, malamai sun had'u akan cewa furuci da kalmar shahada, ba tare da sanin ma’anarta ko yin aiki da abin da ta k'unsa ba, ba shi da amfani, kai sai dai ma ta zama hujja a kansa, kuma ma’anar (La Ilaha Illallah) shi ne babu abin bautawa da gaskiya sai ALLAH shi kad'ai matsarkaki mad'aukaki._

         Rukunan wannan kalmar (shahada) sune (korewa da tabbatarwa), wato kore hak'k'in bauta daga wanin ALLAH, kuma tabbatar da shi ga ALLAH shi kad'ai ba shi da abokin tarayya. Haka kuma wannan kalmar ta
K'unshi kafircewa d'agutu (shi ne dukkannin abin da ake bauta masa wanda ba ALLAH Mad'aukaki ba, ko da kuwa ya kasance mutum ne (tare da yardarsa da bautar da ake masa), ko dutse, ko bishiya, ko son zuciya, ko sha’awa), da nuna masa k'iyayya da yin kubuta daga gare shi.Wanda ya fad'i wannan kalmar (shahada da bakinsa) amma bai kafircewa abubuwan da ake bauta

musu wanin ALLAH ba (a aikace), to tamkar bai fad'eta
ba.
         ALLAH Mad'aukaki sarki ya ce:

     “Kuma abin bautarku abin bauta ne guda d'aya. Babu wani abin bautawa da gaskiya sai Shi. Mai

rahama Mai jink'ai”.(Bak'ara: 163).
 
     Kuma ALLAH Mad'aukaki ya ce:

       “Babu tilastawa game da (shiga) addinin

(musulunci), hak'ik'a shiriya ta bayyana daga 6ata, saboda haka wanda ya kafirce wa d'agutu kuma ya yi

imani da ALLAH, to hak'ik'a ya rik'i igiya amintacciya, (wadda) ba ta yankewa. ALLAH kuwa Mai ji ne, Masani
ne”. (Bak'ara: 256).

     Kuma kalmar (Ilah) tana nufin abin bautawa da gaskiya, duk wanda ya kudurci cewa abin da ake nufi
da kalmar (Ilah) shi ne: Mai halitta, Mai arzutawa, ko Wanda yake da ikon kirkira, kuma ya kudurci cewa yin imani da wannan kawai zai wadatar, ba tare da kad'aita
ALLAH da ibada ba, to hak'ik'a fad'in kalmar (La Ilaha illallahu) ba za ta amfane shi ba, a nan duniya wajen shiga Musulunci, kuma a Lahira ba zata kubutar da shiba daga azaba madawwamiya.

      ALLAH Mad'aukaki ya ce:

    “Ka ce (da su): “Wane ne yake arzutaku daga

sama da k'asa? ko kuma wane ne yake mallakar ji da gani?, kuma wane ne yake fitar da mai rai daga matacce, ya kuma fitar da matacce daga mai rai? Wanene kuma yake tsara al’amura?” To za su ce: “ALLAH ne”. To ka ce (da su): yanzu ba za ku ji tsoronsa ba?” (Yunus: 31).

       ALLAH Mad'aukaki ya ce:

           “Ko wane ne ya halicci sammai da k'assai, ya kuma saukar muku da ruwa daga sama, sannan (da wannan ruwan) muka tsirar da (shukokin) gonaki masu k'ayatarwa, ba kuwa za ku iya tsirar da bishiyoyinsu ba?, shin akwai wani abin bautawa tare
da ALLAH, A’a, su dai mutane ne da suke kauce wa (gaskiya)”.(Naml: 60).
         Kuma ALLAH Mad'aukaki ya ce:

        “Kuma lallai idan ka tambayesu, “Wane ne ya halicce su?, Lallai za su ce: “ALLAH ne” To, yaya ake juyar da su (daga bauta wa ALLAH)?” (Zukhruf: 87)”. Jiddah ta k'are jawabinta cikin sauke numfashi da ajiyar zuciya.

            “ALLAHU Akbar”. malam uku suka had'a baki wajen ambata. yayinda jiddah keta addu'ar dacewa da tsoron yin kuskure.
     Malam mika'il yace, “zaki iya tafiya”.
     Kamar an bige mata gwiwoyi haka ta mik'e ta fito, a bakin barandar ta zauna kamar yanda su madina sukayi. Murya k'asa-k'asa madina tace, “Ukti mi aka tambayeki?”.
       Jiddah tai murmushi cikin sanyinta tace, “Ma'anar Kalmar shahada. Kefa?”,
         “Ni sharud'd'an Kalmar tauhidi guda biyar. Amma wlhy duk saina rud'e ukti”.
           “Bake kad'aiba ALLAH, har yanzu ni kaina gabana baibar fad'uwaba”. Cewar Jiddah tana kar6ar ruwan da madina ta mik'a mata. Sosai tasha ruwan harta d'an samu nutsuwa. Suna zaune a wajen suna d'an ta6a hira har aka gamawa kowa suka koma aji. Bayan fitar malaman kowa ya shiga k'us-k'us da makwafcinsa a kan tambayar da akai masa. Da wannan suka cinye lokacin tashin.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

            Sai kusan 9:30am Malam Aliyu yasamu tashi, kansa yad'an rage ciwon amma yanayi k'asa-k'asa har yanzu.
    Tashi yay bakinsa d'auke da addu'a, yayi mamakin barcin da yayi, a gaggauce ya mik'e yayo alwala domin gudanar da sallar walha kamar yanda ya Saba, yau barci yasashi zai makara. Koda ya idar d'akin ya kimtsa, ya d'auki filas d'insa Na tea ya fita zuwa cikin gidan dan Neman ruwan zafi. Ta k'ofar cikin gidansu yabi inda Kai tsaye zata kaishi sashen iyalan malam. Shiru gidan babu wata hayaniya, Kai tsaye kicin ya nufa, nanma babu kowa dama baiyu tunanin samun kowanba, yana tsaye zuciyarsa Na tunani d'aura ruwan zafin sai yaji motsi a bayansa.
     Waigawa yay da mamakin wanene?.
    Maimuna dake bayansa tsaye ta saki murmushin basarwa tana fad'in “Yaya Aliyu ina kwana? mikake buk'ata ne?”.
      Batare da yayi magana ba ya nuna mata filas d'in daya ajiye.
      K'arasowa tayi ciki kicin d'in “Kaje Yaya bara Na dafa maka, asaka kayan k'amshi”.
      “Eh ki saka, amma miya hanaki zuwa makaranta?”.
       “Uhm... Uhm wlhy Yaya ciwon.......”
      Saikuma tayi shiru ta kasa k'arawa.
      Kad'an ya kalleta ya d'auke kansa, can k'asan mak'oshi yace, “Ba dole kuyi ciwon maraba kullum kunacin zak'i, yakamata kafin sati d'aya da zuwan jini ku ringa d'agama duk wani Abu mai zak'i k'afa, Ku kuma yawaita amfani da ruwan zafi yayin da yazo....”
     Yana gama fad'a ya wuce abinsa tamkar bashi yayi maganarba. Ita kanta Maimuna da kallo ta bishi baki bud'e, sum-sum dashi sai zaro magana, komai girmanta babu ruwansa shi, to ita yaushema tace masa ciwon mara takeyi? “Kai Yaya Aliyun nan ni wlhy harma yaban kunya, a inama yasan Mata na ciwon Mara dalilin period🙈?”. Ta k'are maganar da rufe ido.
         Shikam gogan naku ko'a jikinsa, hankalinsa kwance ya koma 6angarensu yashiga wanka.
        
     Koda Maimuna tagama dafa ruwan batai gigin d'auka takai masaba, a kicin d'in ta barsa, dan basa Shiga sashen samarin gidan kwata-kwata.
           
     Koda ya fito saiya koma cikin gida ya d'akko filas d'insa, yana shirin fita Maimuna ta shigo kicin d'in hannunta d'auke da kula madaidaiciya.
      Kanta a k'asa tace, “yaya gashi inji iya”..
       Baice komaiba, yadai mik'a hannu ya amsa yay ficewarsa, saida yafita sosai sannan yace, “kice Mata nagode”.
        Maimuna ta girgiza kai tana fad'in “ALLAH ya k'yauta, shidai kullum baki 6am, idan kaji yana dogon bayani sai a tafseer ko k'arin karatu kokuma shida Malam”.   
         bakuma dan baya maganarba, danshi ba miskili baneba, kawai dai fahimtace bataiba, dan itad'ince baya sakewa da ita, dadukma macenda ba muharramarsa ba, muharamman nasama taka tsantsan yake dasu, sannan shi ba'a surutun banza dashi Mara ma'ana.

        Baimasan tanaiba, dan shi tuni yaje d'akinsa. Tea ya had'a babu madara, sai wasu abubuwa daya zuba wad'anda suka saka turirin shayin fita da wani k'amshi mai dad'i da saka kwad'ayin shan shayin. Saida ya bud'e kular da Maimuna ta bashi yaga fankasune sai miya a robar kular tanata tashin k'amshi, maidawa yayi ya rufe, saida ya shanye shayinsa daya had'a sannan yafara cin fankasun a tsanake.
        Bayan kammala cin abincinsa daduk wani uzirinsa yay shiri cikin shadda ruwan makuba mai duhu, d'as taimasa k'yau daka gansa kaga cikakken d'an Arewa, yad'au hularsa Zanna bukar kalar shaddar ya saka. Kafin kace me d'akin ya gauraye da wani mayatacen k'amshi mai sanyaya zuciya da sakata nishad'i.

          Tunda ya fito aketa gaishesa a k'ofar gidan, yayinda shikuma yake gaida dattijan da suka girmesa, tuni wani saurayi yazo ya kar6i littatafan hannunsa, agogonsa ya kalla, dan yanason shiga wajen malam kafin ya wuce inda zaije, ganin sha d'aya saura saiya nufi cikin soron, dan yasan malam ya fito yanzu, a zauren farko ya iskeshi shida wasu mutane guda biyu a rukunin kujerun da'aka shirya tamkar falo acan gefen soron kasancewar babba, annan malam ke karatu da d'alibansa dakuma ganawa da b'aki.
     Sallamar Aliyu ya sakasu amsawa a tare suka juyo suna kallansa, ya cire takalminsa a gefen kafet d'in kafin yak'arasa shiga rukunin kujerun, hannu ya mik'ama bak'in malam sukayi musabaha, sannan yaje gaban malam ya risina yana gaisheshi cikin mik'a masa hannu sukai musabaha (malam bai amince d'ansa yak'i samun ladan musabaha da shiba, shiyyasa kozai gaisa da yaransa suma yakanyi musabaha dasu tamkar kowa, hakama matansa).
      “Ya ciwon kan Ali?”.
“Alhmdllh baba”. Aliyu yafad'a yana d'an murmushi kafin ya kuma fad'in “Babu wani Abu da za'ai maka? Zanje wajen Mustafa ne”.
      “Eh to kaje abinka harma ka dawo, dan akwai bak'in da zasuzo inason ka gana dasu”.
       “To bara kawai nabari  saisunzo d'in, daga baya naje wajen Mustafan”.
     “A'a kaje abinka kawai, dan sai k'arfe hud'u mukai dasu, nikuma akwai inda nakeson zuwa a wannan lokacin, shiyyasa nace musu zasu gana da kai”. Malam ya k'are maganar da mik'ama Aliyu key d'in motarsa.
      Hannu biyu Aliyu yasa ya kar6a yana godiya kafin ya mik'e yay musu sallama. Yana k'aunar mahaifinsa sosai, akoda yaushe cikin kulawa dasu yake, haka yake masa inhar zaifita inda yazama saiya hau abin hawa, saiya d'auki makullin motarsa ya basa, saboda shi yama kasa sayen motar, dukda Alhamdllh gwargwadon hali yanada y'an kud'insa dazai iya sayen koda k'aramace dai-dai k'arfinsa, to amma akwai abinda ya dakatar dashi daga sayen tukunna.
     Da wannan tunanin ya k'arasa inda motar malam take ya bud'e, yayinda Wanda ya kar6a littatafansa sanda ya fito yamatso jikin motar shima ya saka masa a gefen mai zaman banza.
     Cikin murmushi Malam Aliyu yace, “Jazakhallahu khairan kamaludden”.
      “Amin malam”. Kamal ya fad'a yana washe baki da rufema malam Aliyu k'ofar.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

              Tunda Jiddah ta iso k'ofar gidansu bayan mai napep ya ajiyeta taga babu motar Abbansu sai farin ciki ya kamata, ta sauke ajiyar zuciya tana nufar shiga, da sauri ta dawo baya danta manta batayi addu'ar shiga gidabama (Kai jiddo😂).
             A yanda ta shigo cikin farin ciki saiya saka Umma dake kwashe dambu a kula murmushi, “Kuluwa ko anyo mana samune yau?”.
      Dariya Jiddah tayi tana fad'in “Umma mikika gani?”,
       “Naganki cikin farin cikine ai, nasani ko suruki aka samowa yahaya”.
       Da hanzari Jiddah ta shige d'akinsu tana dariya. Umma ma dariyar takeyi tanajin dad'in ganin d'iyar tata cikin farinciki akasin sanda suka fita. Kira ta k'walama Jiddah.
        Jiddah ta ida cire hijjabinta sannan ta fito.
      “Haba yarinya, kinga ina dambu koma kimin sannu”. ‘Umma ta k'are maganar dad'an harar Jiddah.
       Hannu Jiddah tasa a baki tana dariya kafin tace, “O Umman mu kad'ai, ALLAH kece kika bani kunya, amma nasoyin magana, gaskiya yau zamuci dad'inmu, ALLAH ya tsumbula Ummanmu a aljanna”.
         Umma tace, “Amin Jiddah, tare daku gaba d'aya”.
        “Amma Umma wlhy kinmayi saurin aikin”.
          “Kinsan Dauda idan ya saka kansa babu wasa, dandanan saigashi yayomin 6arjin, sandama yahay yazo gidannan harna had'a wuta”.
         “Eh dama yacemin zaizo, dan can naje saida lokacin makaranta yayi na wuce, Humm Umma kinsan yau miya faru a makaranta?”.
        “Inafa Zan sani, sai zubomin zance, amma tsaya Na dawo”.
     Cikin Dariya Jiddah tace, “O Umma bafa wani Abu bane, naga kin d'aukeshi da girma”.
          “Eh naji d'in ba komai”. Umma dake k'ok'arin shiga bayi ta fad'a.
       A hankali Jiddah ta furta “Ina sonki Umma har cikin kowanne numfashina”. (jiddo Abba fa?🤭😝).
           Bayan fitowar Umma itama fitsari taje tayo sannan tazo tabama Umma labarin abinda yafaru a makaranta.
      Umma tace, “to ALLAH ya bama mai rabo sa'a”.
      Cikin shagwa6a Jiddah tace, “Kai Umma, kice ALLAH yabama Jiddanki sa'a saikice mai rabo”.
      Ha6a Umma ta rik'e tana kallonta, “Yo inbanda abinki Jiddah suma sauran ai y'ay'anane, miyasa Zan wareki namiki addu'a ban had'a da suba, kamar yanda idan kinci zanyi farinciki haka suma iyayensu, duk wanda kuma yay nasara a cikinku nasarar musulincice da mu ko”.
      “E gaskiyane Umma, shiyyasa kullum nake k'ara sonki, dan bakida sonkai balle Hassada ko kad'an”.
      Dariya Umma tayi. Tace,
      “Kinga Zubaida tashi ki soya mana mai, yanzu zakiga su auta sun dawo faran-faran da yunwa”.
      “Wlhy kuwa Umma, ballema yau Zarah bawani abin kirki taciba saboda anyi mak'iyinta fanke”.
        “kinga kuwa ni nama manta batason fanke, ai danace tazo ta d'ebi biredin wajen Nafisa”.
       ”Aiko dai wlhy Umma”.

         Jiddah na gama suyar mai sagasu Zarah, duk a d'arare suka shigo, amma ganin Jiddah da Umma Na dariya sai sukaji sanyi, sunsan dai Abba baya gidan kenan.
         Jiddah tai saurin Fad'in “Albishirinku kwailolin Umma”.
      “Goro suka fad'a a tare”.
      “Humm kunsan mi Umma ta dafa mana yau?”.
    Kai suka shiga girgiza Mata.
        A hankali Jiddah tace, “Dambu”.
     Wani ihun murna sukasa suna kwaso rawar shoki. Mi Umma da Jiddah zasuyi inba dariyaba, Zarah da Walida sukaje sukaima Umma kiss a hannu.
        Dak'k'uwa taimusu tana fad'in “k'aniyarku wannan shaid'ancin fa?”.
        Dariya suka hau yima Umma.

     Bayan sun kimtsa aka zauna cin dambu kowa cikin zumud'insa, yayinda Dauda yazo ya kar6a Na Uncle yahaya da Umma ta zuba masa tace yaje yakaimasa gida yazo ya kar6a nasa shima.
     Su Walida anacin dambu Ana santi amma bana surutuba.
        Daka gansu zaka fahimci farincikinsu yadawo sa6anin jiya daya 6ace 6at................✍🏻

🚶🏻‍♀🧳kowa ya shirya gobe zamuje gidan Abba zakari hutun k'arshen mako🤣⛹‍♀😝
   





*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻
*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

_________________________
https://youtu.be/eOU-ju4f6KY

Duk mai buk'atar jin raina Kama a audio zai iya bin wannan link Na Abban dausayi YouTube channel😄🥰🤝🏻.

_________________________

                 *_[8......]_*

   
..............Zancen yarinyarnan data turoma malam Aliyu sak'o yata damunsa a rai da zuciya, dan haka ya buk'aci tabashi address Na inda suke.
     Batayi musuba ta turo masa suna cikin Kaduna ne.
    Washe Gari ya sanarma malam yanda sukayi. Kai tsaye malam yabashi Umarnin shiryawa suje shida Mahmud (kaninsa) da mustafa.
           A washe garin wannan ranar suka shirya domin cika umarnin malam.
      Bayan sun Isa kaduna masauki suka fara samu gidan babban malaminnan Sheirk Haruna bala, sanin zuwansu da yayi yaymusu tarba mai k'yau da mutuntawa, dan malam Abdul-ra'uff amininsane sosai. A ranar kam basu bar malam Aliyu ba, dukda gajiyar daya kwaso da daddare bayan isha'i saida ya gudanar musu da lecture Mai taken *_ILIMI DA RAYUWA ABOKAN TAFIYA_*.
     Washe Gari kusan misalin goma na safe ya nema yarinyar da sukazo dominta, dan yanaso a gobe su juyo Gidane.
         Da taimakonta suka iso gidan nasu, gidane babba badai can sosaiba, amma komai a tsare.
          Afrah yarinyar data turama malam sak'oce ta fito tarbarsu, k'yak'yk'yawace a fuska kam sosai, sannan akwai Fari amma irin na kanti, sanye take da hijjab iya gwiwa dan haka su malam basuda damar tantance shigarta, dukdama kallo d'aya sukai Mata kowa ya d'auke kansa, ita kanta cike take da kunyar ganinsu, dan haka kanta a k'asa tabasu umarnin shiga falon Abbansu da k'ofar take a harabar gidan.
     Bayan duk sun zauna ta fita, shidai malam Aliyu yana mamakin da tsarkake sunan ALLAH akan wannan hargitsatstsen al'amari.
           Kusan mintunanta goma da fita saigata tadawo itada wata dattijuwa d'auke da tirirrika, sudai su malam basuce komaiba, fita ta kumayi kafin mintuna kad'an ta sake dawowa ita kad'ai d'auke da wani tiren, bayan ta ajiye ta gaidasu.
      Duk amsawa sukayi.
Kanta a k'asa tace, “Malam kuyi hak'uri Dady bai dawo aiki baneba, amma yana hanya, dan yasan da zuwanku, dukda dai ban sanar masa ainahin abinda ya kawokuba”.
      “Masha ALLAH”. malam Mustafa ya fad'a.
    Malam Muhmud shima yace, “babu damuwa, ALLAH ya maidoshi lafiya”.
    Malam Aliyu dai baiyi maganaba, dan k'ok'arin amsa kiran da akai masa a waya yakeyi.
      Mik'ewa tayi tana rok'onsu dan ALLAH suci abincin.

     Zaman kusan mintuna talatin saiga Dadynsu Afrah ya shigo falon da sallama, da alama ma yadawo tuni, saida ya kimtsa ma sannan ya fito.
      Daka gansa kaga cikakken d'an boko kam, dan sanye yakema da wando tree quarter da T-shirt Mara nauyi, hannunsa rik'e da wayoyinsa, a hasashe zai iya kaiwa shekaru 60, Afrah Na matuk'ar Kama dashi, kawai dai shi bak'ine, itako tayi fari (amma na kanti😝 ). Tarba ta mutunci yayma su malam Aliyu tankar ya sansu, dan sunkula mutumne Mai yawan fara'a.
      Fuskarsa d'auke da murmushi yake fad'in “Lallai nazama Mai sa'a da farin ciki, yau sheirk Aliyu bin Andul-ra'uff maina ne da kansa a gidan, dukda bansan mike tafe dakuba ina muku lale marhabun, amma tabbas nayi mamaki sosai da wannan zunwan, tun jiya da Afrah ta sanarmin abin yak'i barin raina, harma Na tsareta da tambayar ina ta San babban mutum irinka? Dahar zaizo gidannan?”.
       Murmushi su Aliyu duk sukayi, kafin Aliyu yad'anyi gyaran murya, cikin sanyinsa da nutsuwa irinta masu ilimi yace, “Alhaji inafa manya, har gobe mu d'aliban ilimine, abinda ya kawomu kuwa gaskiya babban al'amarine Dani kaina yahana zuciyata da ayyukana sukuni, ina ganin har saina sauke kayan dake kainane Zan sami nutsuwa. Da farko dai tabbas nayi mamaki da kokwanto akan abindama ya kawonin, saboda ganin karanci da mutuncinka, saidai banida wani hurumi na k'in gaskatawar tunda nasamu zancen ne daga amintacciyarku”.
       Kai Dady ya jinjina, sannan ya gyara zama yana kuma damk'e kofin lemon hannunsa, “malam maganganunka sun sakani a duhu matuk'a, amma Zan kwantar da hankalina domin k'ara fahimtarsu daga gareka”.
         “Masha ALLAH, Alhamdllh Alhaji, mun gode da wannan karamci, da farkodai in babu damuwa ina son ganin dukkan iyalanka anan tare damu, wannan ne zai bamu damar fahimtar abinda ya taramun”.
           “To shikenan babu damuwa, Nawwas ne dama kawai baya gida, amma nasan ya dawo insha ALLAH” duk kiran wayoyinsu yayi d'aya bayan d'aya, acikinsu Afrah ce kawai a tsorace, amma Nawwas da  Namrah duk basusan ma'anar kiranba.
        A yanda Nawwas da Namrah da mahaifiyarsu kawai suka shigo ya isa Fara gaskata zancen Afrah. Gaisuwa ma ta sifirin a kaima su malam🤣.
           Dan Hajia Mansura ma tana taunar cigam ta shigo, dukda dai cin masu aji ake masa bana karuwaiba, Afrah ce kawai a k'asa zaune, amma Nawwas da Namrah duk a kujera suka zauna kusama da juna, hannun Nawwas akan Na Namrah wadda ke sanye da wando da Riga masu bin jiki, sai siririn mayafi data yano, shima saida mamansu Tamata magana, kanta yaci uban kitson gashin doki, daka gantadai kaga wayayyun wannan zamanin. Shiko Nawwas wandone irin Na babansa iya gwiwa, sai singlet ruwan d'orawa, askin kansa abun takaici da kuka ga al'ummar musulmai, dan an saisaye gefe da gefe da k'eya,  anbar gashin iya tsakkiyar kai sannan akai masa k'itso kalba (Dada) daga kasan gashin bak'i, sama kuma k'arshen kitson Brown.
       Duk a cikin mintuna kad'am su Malam Aliyu suka nazarcesu.
      Dady yace, “Malam ga iyalin mawa, d'ayane babu a ciki autansu, yana jami'ar legas yana karatu, kwannan ma yatafi, wannan itace matata mahaifiyar yarana, sai babban Nawwas mai shekaru 27 a duniya, yagama p.h.d d'insa, watansa shidda kenan, yanzu haka yana aikinsa. Sai Afrah, tagama degree d'inta itama kwannan, muna mata shirin zuwa masters, sai Namrah tana jami'a tanan jos L200 yanzu”.
         Masha ALLAH su malam Aliyu suka fad'a a tare, da d'orawa da addu'ar fatan alkairi.
             Daga Nana malam Aliyu ya d'ora da fad'in “Dalilin zuwanmu nan gidan shine yarinyarka Afrah”. Atare suka kalli Afrah da kanta ke a k'asa. Malam Aliyu yacigaba da fad'in “Wani sak'o daya kasa barin zuciyata ta turamin, harma naji nakasa hak'uri saina dangane da wannan family, Afrah indai ban shiga huruminki ba inason ki kuma maimaita abinda kika turamin domin Na tabbatar”.
     Hawayen dake d'iga a kumatunta ta share, kafin tace, “Dady da mah-mah Ku gafarceni, yau Zan bud'e sirrin daku baku saniba, saidai har a yanzu ina tambayar kaina Sakacinku ne kokuwa ak'idar boko ce? Da wautar barin tarbiyyar addinin islama?. Har yanzu zuciyata ta Gaza amsamin tambayar, amma ban saniba ko idan Na fad'a yanzu amsar zata fito”.
     Ba k'aramin fad'uwa gaban Nawwas yayiba, dukda baisan mi Afrah zata fad'aba yaji ya tsargu. Mik'ewa yay niyyar yi amma dad ya tsaidashi da Ido, dole ya koma ya zauna yana wani kumbura baki.
      Afrah takuma fashewa da kuka sannan tafara jawabi dalla-dalla kamar yanda taima malam Aliyu a sak'o, harma ta k'ara da abinda bata sanar masaba.
      Gaba d'aya falon jikin kowa ya mutu murus, Dady da mah-mah ma jikinsu rawa yakeyi, hakama Namrah datayi wani tsalle zuwa k'asa saboda tsorata, bata ta6a zaton wani mahaluki yasan suna tarayya da Nawwas ba, sannan bata ta6a zargin yanayin abinda yakeyi da ita da Afrah ba.
      Gani kawai sukayi Dady ya kifo k'asa, Mah-mah ma data mik'e domin zuwa garesa saita yanke jiki ta fad'i. Nawwas kam dukya rikice, yarasa ina zashi ya 6uya saboda kunya da tsantsar tashin hankali.
        A tsorace su malam Aliyu duk sukayo kan Dady, yayinda Afrah tayi kan mah-mah d'insu.

     *bayan awa biyu* su Dady suka dawo a hayyacinsu, saboda kiran likitansu da Namrah tayi, annan yake sanarda jininsu ne yahau sakamakon jin abinda ya tsoratasu.
     Bayan tafiyar doctor da nitsawar komai, malam Aliyu yafara magana a matuk'ar sanyaye da k'unar zuciya. Ya Fara dajan ayoyin alkur'ani da hadisai, sannan ya d'ora da nasiha Mai girgiza zuciya.
        “Wlhy iyaye Ku farka😭, karku d'auki wancan zancen matsayin labarin littafi kawai, wannan fitinace data shigo acikin wannan al'ummar, Uba kaga yana Neman y'ay'ansa, Uwa ta nemi d'anta ko abokin d'anta, ko abokin mijinta, ko makwafcinsu, Yaya da k'annensa suringa Neman junansu, Yaya da kanwa su ringa aikata mad'igo, ko Matar uba da y'ay'an miji😭, aboki yaringa zina da d'iyar abokinsa, k'anin uwa ya ringa zina da Y'ar k'anwarsa ko yayarsa, k'anin Uba yana zina da y'ay'an d'an uwansa, shin dan ALLAH wad'anne irin al'umma muke son zamane? Anya kuwa muna tsoron mutuwa da kwanciyar kabari da hisabi? Muna tuna duniya tak'aitaciyace? Innalillahi wa inna'ilairaji'un, wlhy kaiconmu da toshewar imani dana zuciya😭, k'iri-k'iri munason barin dokokin addininmu muna aro Na yahudanci da tsantsar tsagwaron kafirci a matsayin wayewa, *MUTUM DA DUNIYAR, y'an uwana YA DACE MU GYARA KANMMU* dai tunkan lokaci ya k'ure mana,  wlhy tunkan muga kayinmu cikin WUTAR JAHANNAMA mu farka daga wannan barcin asarar, duk yanda muke kallon mutuwa a nesa damu saitazo garemu, domin a kullum k'ara kusantomu take a kowacce safiya, mimuka tanada mikuma zamu tarrar?”.
     Malam ya k'are maganar hawaye Na cika idonsa, malam mustafa da malam Mahmud Kansu jikinsu Yakuma yin sanyi lis da maganar malam Aliyu.
             Kafin kacemi kuka ya 6alle a tsakanin wannan ahali, kowannensu yana kaico da koyi da al'adar yahudanci da barin tafarkin addininsu bisaga rud'in duniya da wayewa Mara amfanii a duniya da lahira. Duk Wanda ya kallesu saisun bashi matuk'ar tausayi. Har kusan magrib su malam Aliyu Na gidan, saida sukaga komai ya natsa sannan suka wuce, sukabar wannan ahali cikin tsantsar rud'ani da nadama.

         Gaba d'aya da zazza6i Malam Aliyu ya kwana a ranar, washe garima haka suka tafi kano baida lafiya, koda suka dawo har k'arin ruwa yasha, saboda azababben ciwon kai da damuwa sun kasa barin zuciyarsa, komai kallonsa yake tamkar ba gaske ba ma. Amma dole zuciyarsa ta tilasta masa gaskatawa tunda yaje yaga zahiri.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
              Sai da jarabawar su Jiddah takai kwanaki hud'u sannan sakamako ya fito. Cikin amincin Ubangiji Jiddah taci ita da Mariya Ibrahim wata y'ar ajin, sosai suka shiga farinciki da wannan nasara, nanfa y'an aji suka shiga tayasu, dukda zukatan wasu babu dad'i akan rashin nasarar.

       Da tsantsar farin ciki Jiddah ta iso gida, ta kanand'e Umma dake shanya kayan da take wanki.
         “An dace kenan?”.
Umma tafad'a tana dariya bayan ta juyo ta kalli Jiddah dake mak'ale da ita.
        “Alhmadllh Umman mu naci wlhy, kai ina cikin farin ciki”.
       “Alhmdllh Jiddon Uncle, ALLAH ya sanya albarka da nasara tagaba”.
       “Amin Ummana”.
  Su Zarah na shigowa gida Umma ta taresu da wannan farin ciki suma, tuni sun kaure da murna suna k'ara yima yayar tasu adduar nasara. Itama Aunty Nafisa suka takura saida Umma ta kurata ta gumtsa Mata. Sosai tayi farinciki itama.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

          Yau gaba d'aya Malam Aliyu a busy yake, saboda tafiyar da tazo masa babu shiri, dukda dama yasan da tafiyar, amma bai tsammaceta cikin wannan watanba.
        Muhimmancin abinda zashiyine ya sakashi shiryawa babu wata damuwa da zuwan tafiyar a yanayin rashin shiri. Ko d'alibansa bada kowa ya samu damar yin sallamaba, sai sak'on ban hak'uri daya barmusu, da d'ora malam Mustafa matsayin Wanda zai cigaba da yimusu karatu harya dawo tafiyarsa ta watanni uku zuwa hud'u insha ALLAH.
         Cikin gida ya Shiga yayma matan Malam sallama, y'an uwansa kuma dukya kirasu ta waya musamman Ruk'ayya da Siyama daya dad'e yana waya dasu domin yin sallama, yaso su had'u kafin ya wuce, amma ina lokaci yariga da ya k'ure sosai.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

          “Haba hindu, fushinnan ya isa haka mana, tunda kika dawo kink'i saurarena, minene amfanin dawo da abinda akayi ya wuce, kuma nabaki hak'uri”.
        Shiru tayi tamkar bata jisaba, tacigaba dacin abincinta, shiko ya k'ura Mata ido yana juya nasa cokalin akan filet.
              A haka su Hussain suka fito suka samesu, kowanne kujerar Dani d'in yaja ya zauna, ko sallama basuyima iyayen nasuba.
       Kalifa daya zauna kusada Abba ya kallesa yana fad'in “Abba wai sai yaushe zaka cikamin alk'awarina?, ALLAH wayarnan bana sonta, Su Faisal duk an canja musu ni bandani, harma kunyar zuwa school nake da wayata”.
      Murmushi Abba yayi ya shafa kan kalifa, “Haba babana ka kwantar min da hankalinka mana, aina fad'a maka Zan sake maka, yanzu wasu abubuwane suka d'an tushemin, amma kabani nanda k'arshen watannan insha ALLAH taka wayarma duksai tafi tasu, dan nayima Nabel magana ma ya za6o maka mai k'yau”.
    Washe hak'wara kalifa yayi yana rungume Abba da fad'in “Kana birgrni Abbana......”
       “Abbanmu dai”. Cewar Hassan cikin jin haushi.
    Kallonsa Hajia hindatu da Abba sukayi, yayinda kalifa ke antaya masa harara kafin yaja tsaki da fad'in “Jealousy”.
      Hassan ya ta6e baki shima yana hararar kalifan “Jealaus d'in Ubanmi za'a maka, gaskiya Abba muma ka siya mana phones, nidai nafasa sai munkai js3 d'inma, ai gashi Aisar nan suna dashi”.
         Hajia Hindu dake dariya tace, “Y'an biyun Abba da gaske dai kishin kukeyi da babban Yaya”.
        “ALLAH ya kiyaye wlhy Mom, kibarma hura masa wannan k'aton kan nasa”.
      “Kai dan Uwarka waye mai k'aton kan?”. Kalifa ya fad'a a fusace yana mik'ewa zai kaima Hussain dayay maganar duka. Amma sai Abba yay nasarar tarewa.
        “Haba yaran Abba minene abin fad'a anan, ya Isa haka to abar maganar, kowa za'a saya masa indai wayace. Kai Auta mikake buk'ata?”. ‘Abba ya k'are maganar da kallon Munner daketa kallonsu kawai’.
        “Abba ni sonake ka siyamin motar da muka gani ni da mom ranar, nace ta sayamin saitace kud'inta bazai kaiba”.
        Jinjina kai Abba yayi yana maida kallonsa ga Hajia Hindu. Da ido tai masa alamar anyi haka.
    Murmushi yayi, “To Auta mom zata rakani na saya maka insha ALLAH”.
    Sosai Munner yake murna shima.
       Haka dai suka cigaba dacin abincin kaya-kaya tamkar wasu kaji. Bayan sun gama kowa ya kama gabansa.
        Sayayyar da Abba yay alk'awarin yimasu Munner ce ta saka hajia Hindu sauka daga fishinta Na kwananda Abba yaje yayi a gidan Umma. Dan suna shiga d'aki ta rungumeshi.
    Sosai yaji dad'in, shiyyasa ya kudiri aniyar kokartawa ya siya musu duk abinda ya alk'awarta musu..................✍🏻

      (Humm🚶🏻‍♀😏).





*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[9......]_*

  

  ...........Alhamdulillah komai ya kankama Na shirin tafiya taron su Jiddah, Wanda Abba baimasan anayiba, sai Ana gobe tafiyarne Uncle yahaya ya kirashi ya sanar masa.
      Masifa yaytayi akan shifa bayason gantali, yagaji da yawon da Jiddah take zuwa Ana fakewa da addini, yarinya balaggiya ce zata tafi har wata uwa duniya Abuja, to bai aminceba.
     Banza Uncle yahaya yamasa, daga k'arshema ya yanke wayar, koda yaje gidansu Jiddah da daddare cemusu yay kawai Abban ya amince.
     Sosai Jiddah taji dad'i, dan dama gobene tafiyar tasu, duk abinda yadace Uba yayi Uncle yahaya ne yaje makarantarsu yay Mata, (dama idan irin haka ta taso shine ke musu, bama sabi takan Abba).
      Tun a Daren ranar suka farajin kewar juna itada su Zarah, kad'an-kad'an saisuce gobe iyanzu kuna Abuja Yaya Jiddah, wlhy zamuyi kewarki”.
      Umma da ita kanta takejin babu dad'i tai dariya, “to in banda abinki walida yaune tafara tafiya? Kuma wataranfa gidanma aure duk zaku tafi, baga Nafisa ba kamar bata zaunaba”.
        Duk kasa magana sukai, sai hawaye dake zirara a kumatun kowaccensu, duk sanda Umma zatai musu zancen tafiya gidan aure duk saisu shiga damuwa, tunaninsu tayaya xasu rabu da juna? Tayaya zasu barta ita kad'ai?.
       Umma ta ta6e baki tana fad'in “Tofa, ta6arar tazo? To kunga bara nayi nan ALLAH ya bamu alkairi”.
     Umma ta shige d'aki abunta, tana shiga itama ta share hawayen da suka mak'ale mata cikin ido. (😫aure yak'in Mata).
               Suma bayan sun gama shashshare hawayensu suka tashi daga tabarmar suna kaye-kayen tsakar gida kafin su shige d'akinsu. Acan d'inma babu mai magana, jikinsu duk a sanyaye sukai shirin barci, kowacce ta kwanta da tunanin. (🤣zakuyi bayani indai aurene).
             Abubuwa da yawa ke saka su Jiddah kuka idan suka tuna zasuyi sure. Na farko rabuwa da juna da kuma Ummansu farin cikinsu. Na biyu wane irin miji zasuci karo dashi? Mai irin halin Abbansu ne kokuwa Wanda yafi nashi muni? Na uku tayaya Ummansu zataji dad'in rayuwa babusu a kusa? Tunda suka tashi sune take gani taji dad'i, k'aunar da take musuce tasakata hak'urin zama da mahaifinsu dukda munin halinsa da rashin k'aunar da yake nuna musu da ita kanta, to ta Yaya bazasu damuba a yayin da suka tuna zasu tafi su barta cikin kad'aici bayan ita ta zauna danta gusar da nasu kad'aicin a lokacin da suke matuk'ar buk'atarta.
          Haka kowaccensu taita sak'awa da kwancewa har dare yay nisa, ganin sun kasa barci Jiddah tace su tashi suje suyi alwala suzo suyi salla.
      Wannan shawarar sukabi, suka fito domin d'aura alwala, Umma dake sallar itama duk tana jiyo motsinsu. Godiya taima ALLAH daya bata y'ay'a irinsu Jiddah, dama akance Ubangiji baya had'ama bawa zafi biyu, idan ta k'untata wajen mahaifinsu saitaji sauk'i da farinciki a garesu, itako tayaya zata jahilci ni'imar Ubangiji buwayi gagara misali, shima dayake a cikin duhun kai ALLAH ya ganar dashi gaskiya.
          

★★★★

         Washe gari duk sukuku suka tashi, gashi ranar lahadice babu makaranta, haka dai suka taimakawa jiddah ta shirya kayanta kala biyu sai Uniforms d'inta kala buyi suma (tafiyar ta kwana uku ce kacal, ko hud'u).
     Bayan sun gama Karin kumallo Uncle yahaya ya iso, dan tare zasu tafi, k'a'idar makarantar su Jiddah ce inhar tafiya irin wannan ta Kama saida muharraminka, basu yarda tafiya iya malamai da d'alibaiba, kowacce zatazo da muharraminta ne aje dashi, sauk'insu ma koda tafiya ta Kama ta k'etare to lallai makwaftan Najeriyane irinsu Cameroon, Niger dadai sauransu, mafi yawanci kuma duk tafiyace ta mota balle ace babu kud'in biyan jirgi.
      
        Har makaranta Zarah da Walida saukai mata rakkiya, sun iske malam mustafa da malam Bilal (kanin M. Aliyu) sai malam mika'il da sauran d'aliban da za'ayi tafiyar suma da y'an rakkiyarsu. Basu wani 6ata lokaciba suka shiga motar da za ayi tafiyar.
      Har suka fice su Walida basubar d'agama Jiddah da Uncle yahaya hannuba, itama Jiddah Na d'aga musu, yayinda Uncle yahaya suke k'ara birgeshi da k'arajin k'aunar yaran, dan tarbiyyarsu da zumincinsu Na birgeshi, sosai yayarda da maganar man ta bahaushe dayake cewa mace itace ginshik'in zuminci, dan inhar babu ita saikaga kan y'ay'anka kowanne da inda yayi.
           Wannan shine zuwan Jiddah Abuja Na uku, dan haka bata wani damu da 6ata lokaci wajen kallon hanyaba, hasalima ramuwar barci tashigayi, sa6anin abokan tafiyar tata dake hira a hankali, su Uncle yahaya dasu malam mustafa ma hirarsu sukeyi wadda ta danganci rikicin rayuwa da ta'addancin dake faruwa a duniya kullum Ana cewa musulmaine.

        Sun Isa Abuja k'arfe uku Na Rana, dan kokad'an basuyi guduba, tafiya sukai a tsanake babu wani cida zuci, sun tsaya a Kaduna masunyi salla, sunkuma dad'e kusan Awa d'aya da wani Abu.
     Tuni Jiddah ta tashi, dukda ba hira takeba tana sauraren hirar ta 6angarori biyu, y'an uwanta d'alibai da malamsu da iyayensu.
       Sun Isa Babbar makaranta ta Arabic da akeji da ita a ciki da wajen Nageriya, dan akwai d'alibai cikinta harda Na k'etare, sannan ta had'a k'abilu daban-daban. Makarantace da duniyar ilimin addinin Islam keji da ita matuk'a, dan duk Wanda yaje nan lallai yakai abin kallo da tutiya ga al'ummar musulmai, makarantace tundaga nursery har zuwa University, guda biyuce makarantar, ta mata ce a farkon shiga layin, sai ta maza acan k'arshe wanda nisansu yakai zaka iya hawa mashinma, babu yanda za'ayi namiji ya shigo sashen mata, hakama mata basuda hurumin shiga sashen maza, akwai tsaro sosai a makarantun mai ban sha'awa da tutiya ga al'ummar musulmi. wani taro dasu jiddah sukazo a makarantar suka sauka, amma lokacin anma d'alibai Hutu, sai y'an manyan kawai suka tarar y'an jami'a, amma wannan Karon d'alibai Na nan.
         Bayan y'an wasu abubuwa da suka gudana aka kai su Jiddah masaukinsu a cikin hostel. Tarba suka samu ta mutunci ga d'alibai y'an uwansu, sai kaf-kaf akeyi dasu. Hakama sauran d'aliban da suka halarci taron daga k'asashe daban-daban.
      Dukda wad'annan abubuwan hankalin Jiddah naga tunanin Ummanta da y'an uwanta, kad'an-kad'an saita ayyana “komi sukeyi yanzu?”. a zuciyarta.
        Yawan murmushinta yasaka wata d'aliba Mai suna kemi tambayarta cikin harshen larabci, (dan yoroba ce, bakuma tajin Hausa, ita kuma jiddah bajin turanci takeba sai tsinta-tsinta da ake koya musu a makaranta dakuma Wanda y'an uwanta ke koya mata).
      Murmushi Jiddah tai Mata, kafin tace, “babu komai”.
       Badan kemi ta yardaba tabarta.
       Ranar dai haka suka kwana cikin d'alibai, inda da daddare aka gudanar da lecture mai ta6a zuciya da ruhi, wadda aka sakama suna *_TARBIYYAR MUSULMAI A YAU!!_*.
      sosai wannan lecture ta shigi su jiddah da sauran d'alibai, k'arfe sha d'aya aka tashi kowa ya nufi makwancinsa. Da k'yar jiddah tasamu tayi barci, dan kewar su Zarah ta addabi zuciyarta matuk'a.
       
      Washe garima bayan Sallar Asuba ankuma yimusu lecture, ita kuma Mai taken *_YAYA YAKAMATA MU RAYU A MATSAYIN MUSULMAI?!!_*.
     Itama dai tashigi su jiddah sosai, dan har kuka wasunsu sukasha saboda jin kura kurai da al'umar musulmai suke tafkawa a cikin zaman takewar rayuwa, wadda a yanzu mafi yawancinmu bama kare hak'k'ok'i da dokar da addininmu ya sharad'd'anta mana mu rayu, kowa gaban kansa yakeyi da abinda yay maisa a zuciya. (Ya rabbi ka gyaramu muda halayenmu😭🙏🏻).

       Sosai ake shiryama zuwan manyan bak'i wannan taro, an gyara k'aton fili da akan gudanar da makamanta wannan taron, mazaunin d'alibai, mazaunin manyan bak'i, Na iyaye, da d'alibai irinsu Jiddah daga kasashe 10 na Africa.
      K'arfe kusan 9am su Jiddah suka fito daga hostel, tuni har waje ya d'inke da jama'a, manyan bak'in da aka gayyata duk sun iso.

          Malam Abdul-ra'uff Adam Maina yana d'aya daga cikin manya-manyan malamai da akeji dasu a wannan wajen, tun kusan k'arfe takwas na safe ya iso shida tawagarsa, dan haka komai dake gudana a wajen akan idonsune, tundaga fitowar d'alibai da isowar sauran jama'a bak'i.
          K'arfe 10 waje ya nutsa, dan mafi yawan wad'anda ake jira sun iso,  acikin d'aliban makarantar aka tada wata tafara karatun alkur'ani cikin nutsuwa, tsitt kakeji wajen yayi kowa Na sauraren zazzak'ar muryarta. Bayan itama wata takuma zuwa tayi, daganan wani malami ya kar6a yana jan doguwar addu'a da fatan alkairi ga kowa tareda mik'a gaisuwar barka da zuwa ga manyan bak'i irinsu malam Abdul-ra'uff Wanda shine farkonma ambata.
             Komai yana gudanane da harshen larabci. (Da banaji Nima danaga idi, rahoton da bai d'aukuba. 😝😂)
      Malam Andul-ra'uff shine Wanda ya fara gufanar da jawabi awajen taron, tareda yima kowa fatan alkairi Na musamman, daganan sauran manyan bak'in daya kamata su tofa nasu suma suka tofa.
      Taro yafara gudana bisa jagorancin lectures daga malamai daban-daban da suka fito a sassan k'asashe, kowa da taken tasa lecture d'in mai shiga 6argon jiki.
     Su Jiddah dai sunata saurare da d'aukar darussa, lallai wannan taro ya cancanci a kirashi Na *k'arama juna sani* .
      Zuwa k'arfe d'aya aka tafi gudanar da sallah dakuma bama bak'i filin cin abinci da hutawa.
     Su Jiddah duksun koma hostel domin gudanar da sallar zuhur suma.
     Zuwa k'arfe 2 aka daddawo aka d'ora daga inda aka tsaya, akuma wannan lokacinne aka bama su Jiddah dama suma, an Fara kiransune makarantu-makarantu suna gudanar da karatun alkur'ni Mai girma, sannan kowacce abata damar yin bayani akan wani Abu cikin mintuna biyar.
     Koda akazo makarantar su Jiddah sai malam mustafa yace Jiddah ta tashi.
      Gaba d'aya jikinta rawa yakeyi, dukda ba yaune Karon farko data Fara halartar taro irin wannanba, saidai wannan ya banbanta saboda yawan jama'a, gashi kowa ya zubo mata ido, cikin takunta Na sanyi da nutsuwa ta isa inda ake buk'atar ganinta, kanta a k'asa bata iya kallon kowa saboda ta Saba ko yaushe fuskarta sanye da nikab. Koda ta tsaya agaban microphone d'inma kanta Na a k'asa, tad'anyi shiru Na wasu seconds kafin tayi gyaran murya, ahankali muryarta tafara ratsa lasifikan da ambaton bismillah tashiga karanto suratul Al-anfal.
      Bawai dan Jiddah tafi kowacce d'aliba iya karatu bane zata burgeka, a'a nutsuwa wajen karatun da yanda zak'in sautin muryarta ke fita wajen fidda kowanne harafine yasaka zukatan bayin ALLAH nutsuwa, masana Na fassara kowacce aya daki-daki idan ta karanto a zukatansu.
      UBANGIJI yaba jiddah matuk'ar murya mai sanyi wajen jan k'ira'ar alkur'ani Mai girma, idan tazo ayar dake gargad'i,  saikaji muryarta Na rawa alamar tahowar kuka, har sai tasaka handkerchief d'in hannunta ta share idonta. Dad'in sautin muryar tama ya hana a dakatar da ita, saida takai aya ta 68 sannan malam yasamu damar dakatar da ita, yayinda hawaye masu d'umi suka wanke fudakarta, handkerchief tasa tana tsanewa kanta a k'asa, yayinda shashshekar kukanta ke fita a hankali daga cikin lasifikan.
     Guri fa yayi tsit babu Mai kwakwkwaran motsi, dan kukan Jiddah ya raunana zukatan jama'a da yawa, ita kanta batasan miya k'arfafa kukan nataba ma, bayaninma da kowa keyi Na mintuna biyar ita sai hak'ura akai aka barta.
        Malam Abdul-ra'uff Kama sai ajiyar zuciya yake saukewa yana k'arabin Jiddah da kallo, yayinda ransa ke hamdala da samun irin wad'annan y'ay'a acikin al'ummar musulmai.

         Malamin dake kiran sunayensu yay gyaran murya yana fad'in,
ماشا ، الله ، المعلم ، جدة ، هي الطائفة المسلمة التي يحتاجها المسلمون ، لقد بارك الله حياتك.
     أهنئ والديك على الحصول على الوضع الراهن ، وهذا بالنسبة لنا ، في كل مرة تقرأ فيها القرآن وتقرأه بدمك ومعناه وما يتحدث عنه ، بكل طرق الخوف من الله و قوة الإيمان ستكثر أيضا في قلوبنا. كان الأمر كما لو كنا قد سلمنا طفل جدة في رحم طفلها.
“Masha ALLAH malama Jiddah, irinku sune al'ummar musulmi da musulinci ke buk'ata, ALLAH ya albarkaci rayuwarki. ina taya iyayenki farin ciki da samunki matsayin d'iya, wannan wa'azine a garemu, yanada k'yau idan kana karanta alk'ur'ani karingajinsa har cikin jininka, ma'anarsa da abinda yake magana akai, ta wannan hanyarne tsoron ALLAH da k'arfin imani zai kuma yalwatuwa a zukatanmu. kamar dai yanda mukaga malama Jiddah zakari yaro ta tsinci kanta a ciki yanzu”.
         “Kuma sauran d'alibanmu ALLAH ya albarkaci rayuwarku gaba d'aya”.
      A take wajen ya d'auki kabbara ta d'alibai da ambaton Amin.
      Dad'i ya kama Uncle yahaya sosai, sai nanata godiyar ALLAH yake a zuciyarsa, da takaicin d'an uwansa daya gaza fahimtar baiwa da ni'imar da ALLAH yay masa ta samun wad'anan yara.
       Jiddah kam wajen zamanta takoma ta zauna tana cigaba da sauke ajiyar zuciya.
      Abubuwa masu muhimmanci sun cigaba da gudana har zuwa k'arfe 3:40pm, lokacinne kuma taro ya tashi lafiya, cikeda addu'oi ga d'alibai da iyayensu.

*washe Gari*
           Washe gari kam an gudanar da lecture ne, wadda gaba d'ayanta malam Abdul-ra'uff maina ne yayita, sosai tsohon ya birge Jiddah, jitake inama ita jininsace. Bayan kammala lecture d'in malam aka bada k'yauta gasu Jiddah, wadda cikin amincin Ubangiji tasamu babbar k'yauta da saka sunanata a jerin d'alibai uku da za'a tantance su wakilci Nageria musabak'a dazata gudana a k'asar saudia ta y'an shekaru 20 zuwa k'asa.
       Wannan Abu bak'aramin farin ciki yasaka malam Abdul-ra'uff maina ba, ganin d'aya daga cikin d'aliban yankinsa kuma yarensa tasamu wannan dama.
     Yayinda Jiddah ke gudanar da godiyarta ga ALLAH da jigogin wannan taro sai kuka ya sark'e.
    Malam Abdul-ra'uff yay murmushi yana ambatar “sarkin kuka kenan” akan la66ansa, shi kansa malam mustafa murmushi yayi, yayinda uncle yahaya idonsa yacika da hawaye, dan shikam ya fahimci kukan Jiddah da biyune.
          Yau kam antashi karfe 1pm, yayinda manyan bak'i sukayi haramar tafiya.
   Sukuma su Jiddah sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu da rai..............✍🏻

https://youtu.be/eOU-ju4f6KY

  Zaku iya samun Raina Kama a audio ta wannan link d'in Na sama, Abban dausayi YouTube channel😄👌🏻.

*_Larabawa Idan kunga kuskure alarabcina please azo amin gyara, kar a sakamin Ido nacigaba da tafka kuskure, kai adukama littafin, dan maganar addini tawuce gaban wasa, bilyn taku ajizace tana kuskure, dan Allah Da anga Na sauka alayi ayi azamar tunatar dani🙏🏻😿._*


*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[10...]_*

   
..............Baje suke a falo su Kalil Na homework, yayinda Abba ke kallon labarai, hajia Hindu kam Ana zaune gefe ankashe kan d'auri Ana latsa waya da d'ora lemo.
          “Lah Abba wannan tana Kama da Jiddahn gidan Umman gwammaja”. Hussain yafad'a idonsa a TV shima.
      Ware ido sosai Abba ya kumayi, itama hajia hindu dasu kalifa duk suka kalli TV.
     Wata Y'ar zabura Abba yayi dan mamaki, tabbas wannan Jiddah ce y'arsa, wato dayace kartaje saida taje kenan?. Baikai k'arshen tunaninsaba aka wuce rahoton taron dasu Jiddah sukayi.
     Hajia Hindu cikin ta6e baki tace, “Itace kuwa Hussain, anje nunamana su masu addinine ko, ai tsoron ALLAH a zuci yake dai”.
        Dariya Kalifa yay suna tafawa da Hassan tareda fad'in “Tab d'i, su ustaziya kenan”.
    Dariya duk yaran sukayi har hajia Hindu, amma banda Abba da Munner dayay barci. Abba kam ransane a 6ace wai jiddah batabi Umarninsa ba, da ace dare baiyiba da yanzu sai yaje ya saukema Umma ta cikinsa kafin jiddah ta dawo yaci Ubanta.

Humm🚶🏻‍♀😏.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

            Su Umma dai basusan wainar da ake toyawa ba, dansu ba kayan kallon ke garesuba, sai yau da yamma saiga Sadiq da majeed sunzo gidan (yaran uncle yahaya).
     Da fara'a Umma ta taresu, hakama su Jiddah, walida da Sadiq Kansu d'aya, dan shekarunsu kusan d'ayane, dan haka take kiransa Hussain, shikuma yace bai yardaba itace Hussaina shine hassan.
     Yauma tanajin sallamarsu da gaida Umma tafito daga d'akinsu tana fad'in “Oyoyo Hussain d'ina”,
     Hararta yayi cikin wasa shima yana fad'in “Hassan dai, Umma dan ALLAH ni da ita wanene babba?”.
       Dariya Zarah dake wankin Uniforms d'insu ta saka musu, “Umma dan ALLAH yaudai kiraba gardamar gayunnan, kokuma abari sai Yaya Jiddah tadawo sannan”.
      Da sauri majeed shima yace, “Eh abari sai Yaya Jiddah tadawo, dan karsu musama, kunga anyi gaban kowa kenan”.
     Umma dake dariyarta har yanzu tace, “ALLAH ya shiryaku dai”.
     A tare suka amsa da amin Ummanmu.
       “Kunsan wane albishirma mukazo fad'a wannan k'anwar tawa ta katse mana hanzari?”.
      Umma da Zarah sukace, a'a saika fad'a. Yayinda Walida ta antayama Sadiq harara shima ya rama yana Mata gwalo.
     Da sauri Majeed yace, “Umma wlhy an nuna Yaya Jiddah a TV jiya”.
         “Dan ALLAH da gaske?”. ‘Zarah tafad'a tana saurin ajiye kayan datake cud'awa a hannunta’.
    Umma da walida ma a d'okance sukace da gaske majeed?.
       “Wlhy kuwa Umma...........”
    Zama sukayi suna basu labari, farin ciki duk ya cika su Umma, harda hawayen dad'i suka cika mata idanu.
       Anan su Majeed sukakai har dare, basu tafi gidaba har saida sukaci abinci.

         Daga Umma harsu Walida kwana sukai mik'a godiyarsu ga Ubangiji ga wannan nasara da Jiddah tasamu. Fatansu ALLAH ya dawo musu da ita lafiya.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

              Tunda malam suka baro Abuja sai yarinya Mai kuka keta masa Kai kawo a zuciya, haka kawai yakejin farinciki da kasantuwarta Y'ar yankinsa kuma yarensa, dad'in dad'awa kuma gashi a makarantarsa take karatu, yana mamakin yama akai bai Santantaba, lallai dolene yayi bincike akan yarinyarnan, dan yana ganin zata dace da tunaninsa.....
      Yad'anyi murmushi saboda hangota tana kuka, kokad'an ya Lura kuka baya Mata wahala saikace Aliyunsa. Shima abu kad'an ke tada masa hankali Yakama kuka tamkar wani mace, mutumne shi Mai yawan tausayi.
         Malam Yakuma murmushi saboda jin k'arin k'aunar Aliyun Wanda jama'a ke kira magajinsa.
        Har suka iso gida da tunanin Jiddah a ransa.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

         A yau k'arfe 12 su Jiddah suka baro cikin Abuja cikeda kewar k'awayensu d'alibai, dakuma murnar nasarar da suka dace da ita acan.
       Gaba d'aya Jiddah cikin zumud'in son ganin y'an Uwanta take da Ummanta, saikace wadda ta shekara bata gida.
      Sai kusan biyar Na yamma suka iso cikin kano, kaf d'aliban da iyayensu kowanne har gida aka kaishi, su Jiddah sune Na ukun saukewa a k'ofar gidansu.
     Yau ko Addu'ar shiga gida bata tsaya yiba ta shiga gida da murna tana kwala kiran sunansu Zarah.
       Ummace kawai a gidan, dan haka tafito daga d'aki itama cike da murna.
    Jiddah ta ajiye kayan hannunta ta mak'alk'ale Ummansu tana sakin kukan farin ciki. Umma ma cikeda murna taimata kwakkwaran rik'o, a haka Uncle yahaya yashigo ya samesu yana waya. Murmushi kawai yayi yacigaba da amsa wayarsa.
       Jiddah da suka saki juna da Umma tafara tambayar “Umma ina y'an uwana?”.
     “Yanzu zasu dawo, gidan indo sukaje siyo awara. Yanzu zaki gansunan, d'akkoma babanku tabarma mana ambarsa a tsaye.
         'Dakin Umma Jiddah ta shiga ta d'akko tabarma ta shimfid'ama Uncle yahaya da har yanzu yake waya.
         Walida da Zarah ne suka shigo da sallama, ganin Jiddah yasakadu ajiye kayan hannunsu suka mak'alk'aleta suna ihun murna. Tuni sun haukata gidan da hayaniya. Umma da Uncle daya gama waya sai dariya suke musu da mamakin wannan soyayya. Saida suka gama murnarsu kafin Umma da Uncle yahya su sami damar gaisawa, suma sukazo suna gaisheshi da masa sannu da zuwa.
        Yayinda su Jiddah ke murnarsu Uncle yasami damar yima Umma bayanin komai daya faru, farincikine sosai ya kamata, tama rasa yanda zata musalta, video d'in dayayma Jiddah da waya ya kunna Mata tana gani, tuni hawaye sun wanke fuskarta, suma su Zarah suka amsa suka gani, jisuke tamkar su lashe Y'ar uwar tasu dan dad'i.
      Da k'yar Uncle ya tsaya aka bud'e k'yautar da Jiddah ta samo, litattafaine da kud'i naira dubu Hamsin. Atake duk suka zaro idanu dan mamaki, Umma ta ajiyema Uncle kud'in duka a gabansa tace ya d'auka ita Jiddah tunda ga littatafai.
     Murmushi yayi yana mamakin kawaici irinna yagana, ya mik'e yana fad'in “Lallai Maman Nafisa, to wannan tsarin naki kam baiyiba, jiddodo ALLAH ya huta gajiya ni nayi nan”.
     Duk magiyar da Umma kemasa bai sauraretaba ya fice abinsa.
     Sabon shafin murna suka k'ara bud'ewa bayan fitar Uncle. Walida Na had'a wutar gawayin da zasu soya awara, Zarah kuma Na yankan su albasa da kabeji, Jiddah dake kusa da Umma zaune tanata basu labarin komai daya faru a wajen.
          Haka suka kasance a wannan dare cikin firar yaushe gamo, yayinda sukaci awaransu sukayi nak.

    😋😋😫nima zanci awara dan ALLAH.

           Washe Gari tunda safe saiga Abba a gidan, Walida da Zarah na shirin tafiya makaranta, yayinda Jiddah ke gaban rijiya zaune zatayi wankin kayansu.
         Duk tsit sukayi daga dariyar da sukeyi saboda shogowarsa, hakan yasaka Umma dake falo fad'in “Su auta suntafine naji gidan tsit?”.
       “A'a Umma”. ‘Zarah tafad'a a hankali kamar munafuka’.
         Fitowa Umma tayi, saitaci karo da Abba dake tsaye tamkar tsohon soja, sai harare-harare yakeyi. Tuni Umma ta had'e fuska itama sannan tace, “Zarah kuwuce ku tafi karku makara”.
     Sum-sum suka fice daga gidan.
     Cikin tsantsar masifa Abba yace, “Idanma sun zauna Uwarmi zasumin? K dan Ubanki bance karkije Abuja ba?”.
     Ya kare maganar yana nuna Jiddah da kanta ke a kasa tana hawaye.
    Jikinta Na rawa ta d'ago ta kalleshi, “Abba wlhy bansan ka hanaba da.......”
     Katseta Umma tayi da sauri.
      ”Jiddah tashi kiwuce gidan Sa'adatu” (makwafciyarsu).
    Ai tunkan Umma takai k'arshe Jiddah ta zari hijjab tafice da hanzari tamkar zata kifa dan har tuntu6e tayi da k'ofar zaure babban yatsanta ya fashe, amma bata kula da zafi da jinin da yakeba tafita abinta.
    
        “To tafita, saiki nemo iccen dukana Yagana”.
     Murmushin takaici Umma tayi, cikin fushin dabai ta6a sanin tanada shiba tace, “Ka kwantar da hankalinka Alhaji, yagana batada k'arfin dukanka, amma lallai akwai babbar kotu Mai hukuntaka, yanzu dan ALLAH bakaji kunyar d'akko k'afa kazo cin zarafin yarinya akan taje taron addini ba? Anya kuwa Alhaji kana tsoron rad'ad'in d'aukar rai da kwanciyar kabari kuwa? Wlhy kaji Na rantse a wannan Karon kace zakayima yarinyata wani Abu akan zuwa taro namasu k'yak'yk'yawar manufa ALLAH saimun gurfana kotun musulinci dakai. Idan kuma kaji k'arya bismillah gata ga kanan ai”.
    Tana gama fad'a tayi shigewarta d'aki tabarsa tsaye zororo a waje. Takaici ya kumeshi yakasa koda motsi, sai huci da hura hanci yakeyi. Kusan mintuna biyar Umma taji fitarsa cikin buga murfin gidan da k'arfin tsiya.
    Ta6e baki Umma tayi tana fad'in “Oho dai, wannan shashancin ya isheni, ka tsaya a rashinson nasu, amma bazan lamunci a zugoka kazo kana cimin zarafin yara akan hanyarsu ta aikata dai-dai da alfaharin kowad'anne iyayen kwaraiba wlhy”.

      Jiddah kam saida taga lokaci yaja sannan tadawo gidan tacigaba da wankinta, bata tambayi Umma Abba ba, itama Umma batace Mata komai akan Saba, saima d'akko Mata hirar zuwa Barno datayi wajen bikin Y'ar kaninta autansu.
     Nanfa Jiddah tashiga murna sosai, dan tanason zuwa danginsu saboda tarbar mutunci da koyaushe ake musu, ga dad'in zama da kakarsu dasukeji over. (Mahaifiyar  Umma💃🏻).

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

           Tsawon kwanaki goma kenan da dawowarsu daga taron Abuja, amma gaba d'aya tunanin yarinyar yakasa barin malam, dan haka yau ya buk'aci ganin malam mistafa.
      Bayan la'asar lis malam Mustafa ya iso, lokacin malam yana waya da Aliyu.
       Malam Mustafa na zaune har suka kammala sannan ya gaidashi cikin girmamawa. Malam ya amsa yana tambayarsa ya k'ok'ari da d'alibai?.
     “Alhamdllh malam”.
“To Masha ALLAH mustafa. Niko wata tambaya biyu Zan maka”.
      “To malam ALLAH yasa inada ilimin sani”.
        Murmushi malam yayi yana gyara zamansa, “Abokinka bashida wata wadda yake so ne?”.
           “Gaskiya malam babu, dan nidai tun Asma'u ban sakejin zancen wata mace a bakinsa ba, koda yadawo ma banji yanama maganarba, nakan tsokaneshi akan maganar Aure lokaci-lokaci amma amsata dashi shine (ba yanzuba), har Maimuna danaga kamar tana nuna alamar sonshi nabashi shawarar aurenta amma baima tankaminba a lokacin”.
       Nanma murmushi malam yayi yana girgiza kansa kafin yace, “Maimunatu tanan gidana?”.
       “Eh ita malam”.
  “To Masha ALLAH. tambaya ta biyu akan yarinyar datai karatu awajen taron ranar ce, d'iyar wanene? Konace mizaka d'an fad'amin game da ita?”.
       Gaban malam mustafa ne, Yay mugun fad'uwa a ransa yace wayyo ALLAH badai Jiddah taba? Yarinyar da kullum nake kaffa-kaffa da duk wani motsinta. Amma a fili saiya had'iye abinda ya toshe mak'oshinsa, cikin danne abinda ke ransa yace, “Malam itama d'alibarmuce, maikuma tsananin hazak'a da rik'o da addini, duk yanda kake zatonta ta zarce hakan, tarbiyya da duk k'yak'yk'yawan hali Na *MACE TA GARI* za'a iya samunshi gareta. Mahaifinta kam da wuya idan zaka sanshi, sunansa Alhaji Zakari yaro, ni kaina sau d'aya nata6a ganinsa, dan komai Nata k'anin mahaifinta kezuwa makaranta yay Mata a koyaushe aka buk'aci ganin iyaye”.
      Kai malam ya jinjina cikin gamsuwa, “Mustafa kana ganin zata iya dacewa da tsarin abokinka kuwa?”.
       Bak'aramin wuntsilawa cikin malam mustafa yayiba, harya d'ago yad'an kalli malam d'in, amma sai yay saurin maida kansa k'asa ya duk'ar, muryarsa nad'an shak'ewa yace, “Insha ALLAH malam zasu dace, dan dukkan abinda zai iya buk'ata Na tarbiyya daga gareta zai iya samu insha ALLAH”.
         Malam dayaso fahimtar wani Abu yay d'an shiru yana kallon Mustafan, kafin yace, “To Alhmdllh, amma kana ganin babu maganar auren wani kanta? Kokuma Mai neman aurenta?”.
       Da Sauri malam Mustafa ya dai-daita kansa, danya kula kamar malam yafara harbo jirginsane. Cikin sabuwar natsuwa yace, “Banajin hakan gaskiya malam, amma insha ALLAH zanyi binciken daduk yadace akanta”.
         “Nagode sosai mustafa, ALLAH yayima rayuwa albarka, ya raya maka yaranka”.
       “Amin malam”. ‘malam mustafa ya amsa cike da kunya.

    (Malam mustafa shike auren Siyama k'anwar Aliyu dasuke Uwa d'aya Uba d'aya, to shifa da burinsa Jiddah nagama makarantarsu yayi ta biyu da ita, amma sai baita6a koda nuna mataba saboda wani dalilinsa, gashi malam yamasa shigar sauri😂).

               ★★★★

       Dukda son da malam mustafa kema Jiddah haka ya danne da rok'on ALLAH ya cire masashi yahau bincike sosai akanta. Lallai yana taya abokinsa kuma d'an uwansa murna da samun Jiddah matsayin matar aure.

     Jiddah kam dabatasan mi akeba tanata harkokinta, hutunsuma Na kwanaki hud'u Na k'arewa takoma zuwa makaranta abunta. Yayinda a gefe suke cikin k'yak'yk'yawar zaman takewa itada ahalinta.
    Abba ne kawai kansa yay kudu, lokaci-lokaci idan yaga dama ya lek'osu, wani lokacinma da Rana yake zuwa idan bukatarsa ta tsunkuloshi sannan su jiddah basa gida, dayazo yasamu kuma yak'ara gaba. Hakan kuma bazai hana idan gobe ya dawo Umma tasake bashi kantaba.
         A wannan yanayinne su Zarah suka sami hutun makaranta, yayinda gefe kuma Umma keta musu shirin tafiya Barno biki Wanda zasu tafi har aunty Nafisa da yaranta.
          Yau lahadi takama babu makaranta gasu Zarah, Jiddah kuma take suka taso da wuri saboda suna jarabawa, Jiddah ta fita sayo abu a shago dan almajirinsu dauda bai zoba bashida lafiya tun shekaran jiya, Walida da Zarah kuma suna wanki.
       Da sallama Jiddah ta shigo shagon, Mai shago sama'ila ya amsa yana tsokanarta da “Malama Jiddah mikike buk'ata?”.
    Murmushi tayi tacikin nik'ab d'inta kafin tafara lissafo masa a nutse da sanyinta. Juyawa yay cikin shagon yana had'o mata, itakuma takoma gefe jikin k'ofar ta tsaya tana jiransa dan tabama masu zuwa sayyaya hanya.
         Hirar samarin dake d'an gefen shagonce kad'an taja hankalinta, saboda maganarta kamar akeyi. Wani taji yana fad'in,
      “Tab, wlhy ban kwarar kaina Na auri Matar dabata wayeba, kullumfa tana cikin hijjabi kamar Matar liman, yanzu haka inza'a kasheni bazan iya fad'ar kamanninta ba ma”.
      “Aiba kaikad'aiba wlhy Labaran, nikaina inason wayayyar mace wadda zata fiddani kunya aduk inda muka saka k'afa, amma irin wad'ancan mizasu iya banda suyita jawo maka aya da hadisi a kowanne minti”.
    Gaba d'aya suka kece da dariya. Wani yakuma fad'in,
      “Nikam dukma ba wannan bace matsalata deeni, kaje aimaka ta ubansu aita Haifa maka y'ay'a mata su karya maka tattalin arzik'i, ka ciyar dasu suna gabanka suyi aure kakoma shari'ar matsalolinsu, babu ribar daka samu na wahala dasu sai k'arin wata wahalar”.
     “Tab Ashe kagane Ishaq, wlhy koni bana ra'ayin a cikamin gida da y'ay'a Mata, guda d'aya ta isheni sauran su zama duk maza, rayuwar yarancan tama isheka ishara, nifa ban ta6a ganin wani saurayi a k'ofar gidansu Neman aurensuba, hakafa yayarsu Nafisa tayi bandaro a anguwarnan, to nama lura wannan ustaziyar saita fita tsufa a gida”.
      Nanma dariyar suka shigayi, jiddah da takaici yasakata hawaye tayi wucewarta gida batareda ta kar6a abinda tazo sayenba.
     Sai sama'ila ne yabama wani yaro yabita dashi.
          A zaure ta tsaya ta share hawayenta sannan ta kar6a ledan kayan da Sama'ila yasa abiyota dasu.
      Da sallama ta shigo gidan, ta ajiye kayan tashige d'aki batareda ta cire Nikab d'inba.
    Umma Na bayi, su Walida kam sun duk'ufa wanki shiyyasa basu Lura da halin da jiddah ke cikiba.
     Sosai tasha kukanta, saida taji Umma Na kwala Mata Kira sannan ta share hawayen tafito.
    Kallo d'aya Umma tayi Mata tafahimci tana cikin damuwa.
      ”Omon dake hannunta da jiddah ta sayo yanxun dan suyi  tsaraba ta ajiye tana fad'in “Lafiyarki kuwa?”.
       Murmushin yak'e Jiddah tayi, “Umma babu komai, k'asace ta shigarmin Ido saboda iskar da akeyi, alamu zubar ruwa Nata kuma bayyana”.
    Badan Umma ta yardaba tabarta, saima ta d'akko wani zancen.
     “Walida ku gama wankinnan kije gidan zainabar bashari ki amsomin dakan kuka da ku6ewarnan da Sauda (babbar yar su jiddah)  tace aimata, Gurasar Hannatu (yayarsu ta biyu, y'ay'an matarsa Na farko Amina) dai sai a bari gobe idan ALLAH ya kaimu da yamma sai'a a amso gidan y'an gurasa dan karta bushe”.
       “To Umma bara mugama sainaje d'in”.
      
         Zarah ta mik'e tsaye tana rik'e kugu da sauke numfashin gajiyar wanki, “Umma waikuwa aunty Zulaiha (yayarsu, y'ar matar abba ta biyu) zataje d'in?”.
        “Wlhy Zarah ban saniba, tadai cemin yau zata Kira da daddare akan yanda sukai da Mijin Nata, idan ya amince gobe zata baro huntuwa tazo nan kano ta kwana saimu wuce jibin”.
       “To ALLAH dai yasa ya barta, wannan Mijin Na aunty Zulai bayason yaga tamatsa ko nan da can”. ‘Cewar Jiddah dake kulle omo a leda’.
     Dariya su walida sukayi suna fad'in wayaga Yaya Adam cigam d'in aunty zulai.
      “Kunci gidanku”. ‘cewar Umma tana musu dak'k'uwa’.
    Dariya sukayi har Jiddah..............✍🏻

https://youtu.be/eOU-ju4f6KY

_Zaku iyabin wannan link d'in na sama domin sauraren littafin RAINA KAMA a audio, Abban dausayi YouTube channel😄🤝🏻_

*_Abba zakari Na gaisheku🤭, jiya gidansa Na yini tunda duk kunki zuwa gaisheshi ku😆😆😝⛹‍♀_*




*_ALLAH ka gafaiyayenmu😭🙏🏻_*

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[11...]_*

   
..............Yau su Jiddah da murna biyu suka tashi, Na tafiyarsu barno gobe da zuwan yayarsu Zulaihat dake aure a huntuwa Katsina state kenan.
     Tsaf kowa yagama had'a kayansa, Zarah da walida suka fito cikin shirin zuwa kunshi Wanda Jiddah tace bazatajeba, ko kitso tak'iyi tace saitaje barno za'ai mata irin nasu.
        “Umma dan ALLAH kibamu aron dubu d'aya inji aunty Nafisa, tace idan tazo zata baki”.
       “Wa? Kunga idan zaku kubar tsayani, idan kuma kunje kubar tunoni, sisi ban badawa, yanzunan zamu Shiga kasuwa nida Maman Sadiq da Jiddah ”.
          “Haba Umman mu ta mutunci, ALLAH ya k'ara miki Nisan kwana”. ‘Walida tafad'a tana salute d'in Umma’.
     Cikin dariya Jiddah dake janyo ruwa a rijiya tace, “Kumace ta tsiyace mana”.
       “Kai Yaya Jiddah dan ALLAH karki 6ata mana tsari mana.........".
       “kujimin yarinya, yoni minace? Umma nace karki basune?”.
           “Ai koma bakiceba ba bayarwa zanba, kuje taimuku bashi, idan Nafisar tazo Ku k'arata, ai Rashidar zata muku lamuni”.
         cikin shagwa6a Zarah tace, “ALLAH Umma sokike kawai girmanmu ya fad'i a wajenta, ga sabon d'inkinmu ki rik'e matsayin jingina, idan munbaki saiki bamu”.
          Jiddah ta kwashe da dariya tana mik'ewa, “Umma Na rantse ki kar6a, idan ba a biyakiba kibar gayu susa tsoffin kaya a wajen biki”.
       “Gaskiya Jiddah kin kawo shawara Mai k'yau, y'ammata aje a d'akko ga dubu bugun Abuja”. ‘Umma tak'are maganar tana dariya da ciro dubu a jaka’.
       Walida data kwaso sabbin kayansu itada Zarah ta mik'ama Umma tana tura baki irin munji haushinan.
      Kar6a Umma tayi tabada dubu, suka fuce suna musu sallama ciki-ciki. Dariya sosai Umma da Jiddah keyi harsu Zarah suka fice.
       Cikin dariya Jiddah tace,  “Umma y'ay'ankifa sun shak'a”.
          “Ai gara da suka shak'a, nima Na rama kiramin innata dasukaitayi d'azun da farar safiya”.
        Jiddah ta had'iye dariyarta tana zaro ido waje, “Tofa Umma ashe nima ba tsira zanyiba”.
        “Oh kinzata kema kinsha banzane? Inanan zuwa kanyi ai”.
        “Haba Ummanmu yi hak'uri, kingafa har kud'in saya mata goro na tanada ALLAH kuwa”.
        “Ban yarda dakeba Jiddah..........”
     Kafin Jiddah tabama Umma amsa Maman Sadiq ta shigo da sallama. Amsawa sukai Umma namata lale. Yayinda Jiddah ke fad'in “Mama ina Rudwan d'in?”.
        “Nayi cinikinsa a hanya yanzunan”.
        “Haba dai mama, aiko dabaki k'arasoba”.
      Mama tai dariya, “Mizai hanani k'arasowa kuwa? Na gamu dasu Zarah ne suka amsheshi”.
       “Yanzu naji batu mama, yama huta dashan wanan ranar da turnitsin kasuwa”.

         Babu 6ata lokaci suka shirya suka fito domin tafiya kasuwa, sai da Jiddah ta lek'a gidan Rashida tabama su Walida key d'in gidan sannan ta fito suka tari napep zuwa kasuwa.


✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

               Tsaf malam mustafa yagama binciken da malam ya sakashi akan Jiddah, dan haka yau bayan idar da sallar zuhur yasameshi da bayanin komai daya danganci Jiddah da ahalinta.
      Malam yayi farin ciki sosai da tarbiyyar yarinyar, saima yaji takuma Shiga ransa fiye da lokacin daya ganta, dukda ya jinjina mamakinsa akan lamarin mahaifinsu na jahilci, inba jahilciba babu wani bawa dazai guji Ni'imar ALLAH saboda tsarinsa na banza, indai kana numfashi kaji Abu iri-iri a duniya, na ban haushi dana ban al'ajabi..

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

               “Da gaske kana sonta Alhaji Garba?”. ‘Abba yay maganar yana kallon abokinsa Alhaji Garba mai tabarma’.
         “Wlhy da gaske nake maka wannan zancen Alhaji Zakari, inason Jiddah y'arka, danni dai bak'aramin birgrni tayiba wajen taronnan da akayi”.
       Abba yay murmushi kafin ya muskuta zamansa ya jingina da bango, “Alhaji Garba daga yau nabaka Jiddah, ko gobe kake buk'atar ganinta a gidanka kazo a d'aura muku aure”.. 
       “Kai amma naji dad'i sosai abokina, ALLAH ya k'ara girma, tabbas inason auren ya kasance kusa, saboda matsalar hajia deluwa ta isheni ainun, ina buk'atar Matar da zata kwantar da hankalina nima, sai dai ba wai gobeba, idan babu damuwa yakai k'arshen watanan”.
      “Hakan mai sauk'ine, dama zasuje Barno biki gobe, nima jibi zanje a d'auro auren Dani, saboda k'anin mahaifiyar tasune zai aurar da yarinya, insha ALLAH zan sanar da danginta kai”.
        “Ai to indai hakane kawai bara Na shirya muje tare, kaga saisu ganni dak'yau nayi gaisuwar surukai ma”.
     Dariya sukad'anyi suna tafawa.
     Abba yace, “Lallai kakawo shawara mutumina”.

Turk'ashi🙆🏻, yau munga idi abba zai 6aro mana ai😱.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

               Sai kusan k'arfe 5 su jiddah suka dawo gidan, sun iske ko ina ya kacame da hayaniya, dan kuwa aunty Zulai ta iso da y'ay'anta biyu, tabar manyan guda uku acan gida wajen kakarsu, nanfa aka kuma kacamewa murnar ganin juna, dan kusan shekara kenan batazo kano ba, sukuma inba haihuwa tayiba Abba ba barinsu zuwa yakeba, garama Jiddah wani lokacin Umma kan aiketa tayi kwana biyu ta dawo.
       Ana cikin Murnar ganin Aunty Zulai saiga Aunty Nafisa itama takasa hak'uri tataho nan ta kwana tunda da sassafe zasu wuce. Gidafa ya kacame tamkar ana biki, babu maijin maganar wani, ga y'ay'ansu Aunty Nafisa dama bajin magana sukeba, Umma dai tasamu ta rufe rijiya 6am saboda tsaro. Ganin k'unshin su Zarah yayi k'yau Jiddah tace dama itama tasani taje.
     Dariya sosai suke Mata hardasu Aunty Nafisa.
     Yaukam sunsha hira, dan kusan raba dare sukayi ana hirar zuminci.
     Washe gari tunda asubar farko suka tashi, ALLAH ya sosu aka kawo wuta, dan haka sukasa ruwan zafi Mai yawa a hita, har suka samu ya tafasa akwai wuta.
     Kaf yaran Zarah ce tai musu wanka, yayinda Walida ke shiryasu. Jiddah da aunty Nafisa kuwa sunata k'ok'arin had'a abin Karin kumallo.
           Sunsami gudanar da komai akan lokaci har sallah, karfe 6 saura motar bos da Uncle yahaya ya tanadar musu ta iso, dan haka akaita fidda kayansu ana lodawa amotar, bayan angama tsaf, saikuma ga Maman Sadiq da tata gayyar y'ay'an itama. Tuni suka shishshiga mota aka rufe gidan suka shilla Barno.

      Saina karaso nima🚗, dan bazan had'a mota da kowaba🥺.

          ★★★★★

          Sun isa barno lafiya, yayinda dangi suka kacame da murnar isowarsu, bazaka ta6a cewa aunty Zulai da aunty Nafisa ba tsatsonsu bane, dan yanda akema su Zarah suma haka ake musu babu wani banbanci. Dan danan aka shiga hidima dasu, bayan sunci abinci sunyi nak kowa yanemi Mai fisheshi, tuni Zarah da Walida sunbar gidan bayan sungama tsokanar Inna hajia (kakarsu mahaifiyar Umma), ta tsufa kam, saidai bazamuce irin tukuf d'inan ba, daka ganta kaga cikakkiyar kanuri, dan harda 6ular hancinta ras, Hausa kam kad'an-kad'an takejinta ma.
     Fitar su walida babu dad'ewa saigasu Fannah amare, tuni suma suka janye Jiddah bayan sun gaisa dasu Umma.
          
     Washe gari da Hantsi saiga Aunty Sauda babbar yar su Jiddah tazo itama daga Yola, dan can take aure. Zokaga murna wajen Umma dasu Aunty Nafisa anga y'ar uwa, su Zarah kam basusan tazoba saida sukazo d'aukar kayansu, nanfa suma suka kadandaneta suna nuna murnar ganinta, tare damata tsogumin batazo da yaraba sai wadda take goyo kawai Hanan.
        Wajen karfe 3 itama Hannatu ta iso tare da Mamansu (Amina Matar Abba ta farko) dakuma wasu daga dangin Abba da sukazo yima Umma Baici, y'ay'an Ummafa sun had'u, Amina da Umma kam idan kagansu abin sha'awa, tamkar wasu Yaya da k'anwa, dukda basu zauna gidan Abba a tareba hakan bai hana kulluwar zuminci mai k'arfi a tsakaninsu ba, dan sunajin dad'in yanda Umman ta had'a y'ay'an dukta rik'e, (itako aunty Zulai mahaifiyarta ALLAH yamata rasuwa dama) dan haka batada Uwa irin Umma, Abbanma daya haifesu ba damuwa sukai dashiba, dukda suna bashi girmansa kamar yanda koyaushe Umma ke nuna musu muhummancin hakan.
     Biki yacigaba da gudana yanda yakamata, yayinda aketa zuba al'adun biki irinna kanuri, Su Jiddah dai anshige ko ganinsu ba'ayi, kuma duk wannan shagali bai hanata saka hijjab d'intaba duk inda zataje, nik'ab ne dai data d'akko zatasaka sai a kwace a hanata, babu yanda zatayi dole ta hak'ura, amma duk saitake jinta a takure, shiyyasa ko yaushe kanta a k'asa batason kallon kowa.
     Washe garin d'aurin aure saiga Abba da abokinsa Alhaji Garba, kasancewar tafiyar wuri sukayi wajen k'arfe d'aya suka iso.
      Basu sami ganin Umma ba saida aka d'aura aure, amma sun sami tarba ta mutunci daga y'an uwan Umma maza.
           Bayan gama d'aurin Aure Umma tasamu da k'yar tafito cikin mutane ta samesu a gidan makwafta da aka saukesu a d'akin soro, ganin dukkan tarbar da zata iya musu an musu sai suka gaisa takoma kiran su Aunty Sauda.
     Amina kan duk yanda Umma ta rok'eta tazo su gaisa k'i tayi.
        Daga Sauda, hannatu, Zulaihat, har Nafisa haka suka shigo fuskoki babu walwala, kowacce kuma cikin kamalarta, dan duk ALLAH ya kaisu gidan hutawa, babu maishan wahala a gidan aure.
         Abba yayi mamakin ganinsu amma saiya 6oye ya amsa musu gaisuwarsu babu yabo babu fallasa, ko tambayar ya yaransu baiyiba, amma su da suka tambayi yasu kalifa saiya hau washe baki da fad'in duk sun a lafiya.
     Takaici ya cika zuciyarsu aunty Sauda da Umma, basubi takansaba sukai masa sallama suka fito.
      Umma ma sama-sama taimasa sallama ta fito tabarsu, dan anan zasu kwana sai gobe zasu wuce. Aiko bata sake bi takansuba saida daddare data kawo musu abinci, anan ta iskesu da y'an Uwanta maza, haka kawai tasha jinin jikinta da zaman hirar tasu, saidai batace dasu komaiba ta juya tana fatan ALLAH yasa alkairine.
                 
            Washe gari Abba yasamu gaisawa da Inna hajia, itama yaymata dukkan bayanin da yama y'an uwan Umma, ta jinjina wannan lamari sosai, saidai batada hurumin hanashi yin yanda yaso da y'ay'ansa, dan haka tabishi da addu'ar ALLAH ya za6a abinda yafi alkairi.
     A ransa yace, “ai yama za6a, dan auren Jiddah da Alhaji Garba babu fashi”.
        A ranar suka koma shida Alhaji garban bayan angama nunasa cikin dangin Umma da sunan Mijin da Jiddah zata aura.
      Kowa dai wannan za6i bai masaba, amma basuda hurumin hanawa saboda dai shikeda iko da y'arsa. Umma da Jiddah da su Aunty Sauda dai basusan abinda ke faruwaba, duk da sunji anad'an maganar sama-sama, saidai basu fahimci wacce Jiddarba.
      
       Kammala biki da kwana biyu suma sukayi azamar tafiya, dama tun jiya aunty Sauda da mama Amina da aunty Hannatu sun koma da sauran dangin Abba.
            
        Abba dai daga Barno Ashe Adamawa ya wuce da Alhaji garba, inda yasanar dasu shine zai auri Jiddah, babu mai hurumin hanashi iko da d'iyarsa, amma wasu sun nuna masa illar hakan, dan Alhaji garba yayma Jiddah Tsufa sosai. Amma ganin ya dage sai suka bishi da fatan alkairi kawai, dan kowa yasan halinsa na kafiyar tsiya.

      Da daddare Inna hajia ta kira Umma gefe, cikin tausasa harshe taimata dukkan bayani akan auren Jiddah da Alhaji Garba da Abba ya sanar musu. Take hankalin Umma ya tashe, tace wlhy Sam bazata aminceba, sai dai a wannan karonkam su rabu dashi.
     Murmishi Inna Hajia tayi tana jinjina kai, kafin ta nisa cikin dattako tace, “Uhm-uhm Yagana karmu soma haka dake, wannan baikai abinda za'a tashi hankaliba, ALLAH dai shine maiyi, sannan komai da kowa a hannunsa yake, karnaji karna gani ance daga 6angarenki matsala take, kibarshi yayi yanda yaso da d'iyarsa, ALLAH dai maijine kuma Mai ganine, sannan yana tare da masu hak'uri”.
      “Hakane Inna, amma ita yarinyar lamarinta za'a duba, wlhy koshi kansa Alhaji ya girmesa, manyanfa y'ay'ane dashi zagada-zagada, dan ko autansa saidai suyi sa'anni da Jiddar, amma dan zalunci irina zakari shine zai had'ata aure dashi? Lallai yanzu nakuma aminta da baya k'aunar yarannan da gaske........”
        “Koma dai Miye yagana nidai nace kiyi hak'uri ki saka masa ido, itako mucigaba da Mata addu'a, kokun koma karnaji wani tashin hankali tsakaninki dashi”.
      “Shikenan Inna”. ‘Umma tafad'a wasu hawaye masu rad'ad'i Na kwararo mata’.
       Washe Gari haka suka baro barno ranta a 6ace, su Jiddah duksun damu da halin da sukaga ta shiga daga daren jiya zuwa yau, amma sunyi tambayar duniya tace babu komai.
     Haka dai suka iso kano.
    Tamkar Jira Abba yake dama da dawowar tasu saigashi a gidan bayan magriba, aunty Zulai da aunty Nafisa duk suna gidan, Maman Sadiq ce kawai suka wuce gida itada yaranta.
     Babu wani 6oye-6oye ko lallashi cikin gadara ya sanarma Umma zancen Auren Alhaji Garba da Jiddah, harma da jadada mata zancen kawo kud'i da zaiyi gobe idan ALLAH ya kaimu.
     Uffan batace dashiba harya k'araci hargowarsa ya fice.
     Yayida tuni tashin hankali ya dabaibaye su Aunty Nafisa wad'anda Jiddah ta sume musu saboda abinda sukaji daga bakin Abba.
      Wannan dare dai yazo musu cikeda k'unci da damuwa.
    Washe gari Aunty Nafisa takoma gidanta cikin damuwa da tausayin Y'ar uwar tasu.
     Itama aunty zulai kwanata hud'u tak'ara ta koma gidan mijinta.

           Gaba d'aya gidan Umma ya canja daga yanda kuka sanshi, babu wani farin ciki ko walwala tartare da ahalin gidan a yanzu, komai ya canja musu, kwata-kwata Jiddah tabar zuwa makaranta saboda damuwa.
          Tuni Alhaji garba yakawo kud'i, Wanda Uncle yahaya yayta zabga masifa akan hakan. amma sai Abba ya yayyanka masa magana wadda tai masifar 6ata ransa ya janye hannunsa daga maganar Auren Jiddah.
    Kwata-kwata sati hud'u aka saka bikin, koma tunanin Yaya batun karatunta baiyiba.
      Su Zarah Kansu duksun fita hayyacinsu tamkar sune Jiddahn.
    Ahaka aka cinye sati biyu, ana saura kwanaki 10 cif lefe ya iso, saboda Abba yabama Umma haushi saiyasa y'an kawo lefe suka Kai gidansa da Hindu ke ciki, Aunty Nafisa da Maman Sadiq ne kawai sukaje, sauran kam duk k'awayen hajia Hindu ne. Sai shak'iyanci sukeyi wai tsoho ya iya had'o kayan lefe.
    Sosai lefen kam aka kashe kud'i dan komai yaji d'am, kaikace na saurayi d'an shekara 26 ne😑.............✍🏻

https://youtu.be/eOU-ju4f6KY

*_Zaku iya samun RAINA KAMA a audio ta wancan link d'in Na sama, Abban dausayi YouTube channel tv😄🤝🏻._*

Yau babu magana🤫🤐


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[12.....]_*

   
..............Malam Mustafa yadamu kwarai da rashin ganin Jiddah a makaranta, dan da wahala kaga tayi fashi, inhar kuwa tayi washe gari sai kaga k'annenta sunzo sun fad'i dalili, kokuma idan itace tazo tafad'i abinda ya hanata zuwa.
      Madina ma ta damu da rashin zuwan Jiddah, gashi ko gidansu bata saniba, dan duk iyakar shakuwarsu k'awancen iya makaranta ya tsaya, sai a yaumane takejin takaicin hakan.
      Da aka tashi Malam mustafa yaso zuwa gidansu Jiddah, amma sai wani uziri ya rik'eshi, dole ya hak'ura akan sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu.
      Saikuma da yamma malam yay kiranshi a waya akan yazo yana nemansa.
        Bai samu ganin malam ba sai bayan sallar isha'i, dan ya iskeshi yana da bak'i. Bayan tafiyarsu yasamu gaisawa da malam.
        “Mustafa dama akan yarinyarnanne, inaso asamo mana inda mahaifinta yake, dan inason ganawa dashi kafin musan abinyi”.
      “To malam, insha ALLAH zuwa gobe zanzo na sanar maka”.
      “To ALLAH ya kaimu da rai”.

         Washe garima malam mustafa bai samu zuwa wajen Jiddah ba, sai dai binciko Alhaji Zakari dayayi, gidansa da  wajen kasuwancinsa.
     Duk yanda akai malam mustafa yazo ya sanarma malam.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

            Jiddah dukta fige a tsaye, da kaganta kasan tana tare da damuwa, Umma takan danne tata damuwar tayita lallashinta da nuna Mata muhimmancin yadda da k'addara Mai k'yau ko sa6anin hakan, tareda tunatar da ita amfanin biyayya ga iyaye.
       Da wannan shawawar warin ne Na Umma take d'an rage nauyin damuwarta, har yau take d'an ta6a aikin gyaran gidan saboda su Zarah suna makaranta.
      Gaba d'aya bikin saura kwana shidda ne ya rage, amma bazaka ta6a cewa za'ayi wani biki bane agidan, dama Abba yace Umma karta sai komai, dan Alhaji Garba yace amarya kawai yake buk'ata, komai ya tanadar mata.
      Wannan dalilinne yakuma saka Umma banzatar da zancen auren, tacigaba da yima d'iyarta addu'ar nema za6in ALLAH.

★★★★★

       Biki ya rage saura kwana hud'u dangin Umma suka fara isowa, hakama su Aunty Sauda da aunty Zulai, kowa dai kagani babu wani d'okin auren a tattare dashi. Kowa dandai babu yanda zaiyine da lamarin Abba kawai.

✨✨✨✨✨✨.

       Yayinda shirin biki keta kankama a gidan su Jiddah ga malam Abdul-ra'uff kam shirin zuwa Neman auren Jiddah suke ga Alhaji Zakari. Alhmdllhi sun sami isowa yana gida bisa jagorancin malam Mustafa.
     Dukda Alhaji Zakari baisan mike tafe dasuba yaymusu tarba ta mutuntawa saboda ganin manyan malamai a gabansa, dukda gefen zuciyarsa Na zargin Jiddah ce takai k'ararsa garesu, shiko ya k'udiri aniyar mutuwar Jiddah ce kawai zata Hana ya aura mata Alhaji Garba. Amma duk saiya danne wannan zancen zucin nasa ya fuskanci su malam.
         A nutse malam Salis yayma Abba bayanin abinda ke tafe dasu.
      Abba dake masifa a zuciyarsa hace, “Ahaf zargina yazama gaskiya, to lallai dagaku har ita zanyi maganinku ne”.
      Kwantar da murya yayi a fili tamkar mutumin kwarai yafara magana, “ALLAH sarki malam gaskiya banji dad'in zuwan wannan magana Mai dad'i a k'uarraren lokaciba, dan abin farin cikine ga kowanne Uba yahad'a jini da malam, danasan da wannan kudiri naku daban amshi za6in Jiddah ba, yanzu haka maganar danake muku ranar asabar d'innance d'aurin aurenta wlhy”.
      Gaba d'aya jikinsu malam yayi sanyi, amma babu yanda suka iya, dan Neman aure akan nema bashida kyau, balle wannanma da aski yazo Gaban goshi.
     Sallama sukaima Abba suka tafi, saidai gefen zuciyar malam mustafa bata aminta da maganar Abba ba. Shima Abban kuma ya tsargu da kallon da malam mustafa ke masa.
       Dan haka suna tafiya yanufi gidan Umma, kiran Jiddah yay ya Kora Mata gargad'i akan wlhy idan wani malami a makarantarsu ya aiko koda kiranta taje saiya matuk'ar 6ata ranta sosai.
       Da to ta amsa, takoma cikin gida tana hawaye. Umma kallo d'aya taimata ta d'auke kanta, bakuma ta tambayeta miya faruba.
        Ana saura kwana biyu hajia Hindu ta maido  lefen Jiddah gidan Umma, duk da ta kwashi abinda take so aciki babu Wanda ya gane sai aunty Nafisa da maman Sadiq da sukaga lefen. Amma koda sukai magana sai Umma tace subar zancen, ita ta sani, inma dai dai tayi inma sa6anin hakan kanta taimawa.
        Aranar y'an Adamawa suka Iso, hakama y'an Barno, tuni gidan ya kacame da yaren Fulatanci da Hausa da kanuri, dolema sai kusan rabuwa akayi, dan gidan yamusu kad'an, wasu suna gidan Uncle yahaya wasu gidan Umma.
        Gaba d'aya Uncle yahya ya kauda idonsa akan bikin dukda takaicin auren da tausayin Jiddah Na damunsa ainun.
           Wannan biki dai ana yinsane kawai, amarya ma da k'yar tayarda akai mata k'unshi da kitso, gyaran jiki kam komai akace xa'ayi saita saka musu kuka tace bataso.
    Tausayinta ke sakasu barinta. Duk wani shagali irinsu kamu babu Wanda akayi, dama ita bawasu k'awayene da itaba, y'an uwanta sune k'awayrnta da Ummanta.
        Ranar d'aurin aure gida yagama d'inkewa tab, Amarya kam nacan karshen d'aki kudundune babu lafiya itadasu walida, kowanne zazza6i yamasa rijib, ko wanka basuyiba balle ai batun kwalliya.
     Karfe 12 aka d'aura auren Alhaji Garba da Hauwa'u Jiddah akan sadaki naira dubu d'ari biyu.
     Abin mamaki saiga Malam Abdul-ra'uff dasu malam mustafa sunzo d'aurin auren suma, saboda koba komai dai d'alibarsu ce, wadda sukeji da ita da alfahari da ita.
      Tunda zancen d'aurin auren ya shigo cikin gida jikin Jiddah yakuma rikicewa, dole aka fita da ita zuwa asibiti.
    Amma Kiri da muzu Abba yace wlhy ko suma take yau saita kwana gidan mijinta, shi yagaji da wannan iskancin.
    Umma duk tana jinsa amma uffan bata ceba, dan itama tunda aka fara hidimar bikinnan cikin ciwon k'irji take, dannewa kawai take tana daurewa.

     A asibiti sai da Jiddah tasha ledar ruwa uku, barcin data samune yasaka sauran y'an uwanta zabga tagumi sukai jigum-jigum, kowa shikad'ai yasan minene damuwarsa.
     Anayin Sallar magriba Abba yazo asibitin yace a sallami Jiddah, dukda bayani da likita kemasa nason abarta tasami hutu yace Sam yanzunan yakeso, dan gidan miji za'a kaita.
    Badan likita yasoba aka basu sallama suka dawo gida akahauma Jiddah shiri.
        Koda akazo batun yimata fad'a Umma ficewartama tayi daga d'akin tana hawaye, amma bata bari kowa ya gantaba.
      Dangi dai sun tofa albarkacin bakinsu nayima Jiddah nasiha akan abokiyar xamanta da mijinta harma da y'ay'ansa da danginsa.
     Tuni Jiddah tabar kuka masu hawaye sai dai kukan zuci, a haka aka fiddota wajen motocin d'aukar amarya da akalla sunkai 25, dan haka kowa yasamu waje aka shilla da amarya.
      Y'an anguwa wasu Na sambarka wasu Na tausayin Jiddah.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

           *Gidan Alhaji Garba mai tabarma* babban gidane sosai Wanda kallo d'aya zakai masa ka tabbatar da maishi ya tara.
      Bayan an wangale musu k'aton gate d'in gidan kusan motoci goma suka sami wajen shigewa ciki harda ta amarya.
     Tarba suka samu mai k'yau daga dangin Alhaji Garba, wad'anda suketa fatan ALLAH yasa wannan karon an dace Jiddah tazo kenan.
       6angaren Jiddah aka kaita, Wanda ya k'awatu da kayan alatu tamkar suyi magana, komai yaji zam, duk had'uwar gidan Alhaji Garba da dukiyar cikinta hakan baisa dangin Jiddah jin zasu tayata murnaba.
      Basu wani jimaba suka juya, akabar Jiddah ita kad'ai kudundune cikin hijjabi daboda zazza6i Mai tsanani daya sake rufeta.
     Kusan mintuna ashirin da tafiyar y'an kawo amarya Jiddah tafara jin hayaniya sama-sama, abinda ya dameta shine matsalarta, dan haka bata damu kanta dasonjin mike faruwaba. Zuwa wani lokacima sai taji gidan tsitt tamkar babu kowa a cikinsa.
        Tun tana sauraren k'arar AC har barci 6arawo ya saceta a haka,  dama Allurar bata gama sakintaba.

*Ango*

       Kusan k'arfe sha biyu da rabi ango yashigo gidan, lokacin gidan yay tsit kowa yakama gabansa, Daga y'ay'ansa sai matarsa hajiya deluwa.
      Fakin motar yay yafito hannunsa d'auke da k'atuwar leda, Kai tsaye sashen Uwargida ya nufa Wanda yafi kowanne sashe girma a gidan.
      Tsit babu motsin kowa sai AC da TV daketa faman aiki, ko ina tsaf tamkar ba taron biki akayiba, koda yake yasan babu wani Wanda ya Isa taka mata sashe da sunan zuwa biki. Ledar hannunsa ya ajiye yanufi corridor d'in dazai sadashi da d'akunan barcinta.
    Na farko yafara lek'awa babu kowa, Na biyu ma haka, sai a Na uku ya hangota zaune a saman gado, hamshak'iyar macece wadda ta amsa sunanta Hajia, daka ganta kasan tagama jik'uwa cikin nera, ta girma sosai sanan tanada k'iba dai-dai gwargwado, dan bawata k'atuwa baceba can, Ammafa babu k'arya Y'ar gayuce, dan ko shirin barcin Nata kad'ai ya Isa tabbaatar maka hakan, gata Fara tas masha ALLAH.
     Manyan idanunta ta sauke akansa, kafin tasaki wani murmushi cikin kissa tafara fad'in “Kaga ango Mijin Amarya Hauwa'u”.
        'Dan Murmushin yak'e Alhaji garba yayi, ya zauna kusa da ita k'asan zuciyarsa Na mamakin canjawarta akan wannan auren nasa, Ada inhar zaiyi aure zata d'aga hankalinta, randama aka kawo amarya bata Barin kowa yayi barci Mai dad'i a gidan, amma tunda yafara maganar auren Jiddah ko kad'an bata ta6a nuna damuwartaba, hasalima lefen Jiddah itace ta had'oshi matsayin gudun mawarta.
     Fuskarsa d'auke da murmushi yad'an shafa kumatunta.
    “Uwargida ran gida!”.
  Fari tayi masa da fararen idanunta, kafin ta furta “Fad'I kanka tsaye alhajina”.
     Yad'an dara, “Kinyi k'yau gimbiya ta, sai nakejima tamkar ked'in aka kawomin a yau”.
      Wani shegen murmushi ta Saki, “Alhajina rufamin asiri, kaga tashi katafi wajen matarka, kar zumud'in son ganinta yasaka juyemin kalaman daka tanada dominta anan wajen”.
      “Haba gimbiyata, aike kin wuce aimiki jirwaye da zancen wani, duk abinda yafito zuciyar Abubakar a kanki to lallai nakine, babu Mai kamanceceniya dake balle kamoki”.
     Murmushi takuma Saki tana kamo hannunsa ta sumbaci tsakkiya, kafin yagama dai-daita da shiga sak'on Nata ta haye saman gadon sosai taja bargo da fad'in ”Ango mukwana lafiya, kadai bimusu yarinya a hankali karkai mata irinna hajarah, nasanka yanzu haka kaje ka d'irko magunguna”.
        Wata Y'ar dariyar mugunta yasaki yana mik'ewa, “Hajjaju akwaiki da tsokana wlhy, ni sharri kikemin babu wani magani danake sha, Na barki lafiya”.
     Cikin watsama bayansa harara da murmushin mugunta tace “A gaida amarya”.
      Fita yay yana fad'in “zataji”.
                Daga nan sashensa ya nufa Wanda shima ya had'u, sai dai baikai girman Na hajiya deluwa ba ko kad'an, had'uwa kawai zai iya nuna masa.
     Sai faman zabga murmushi yake yana cire kaya. Wanka ya shiga kusan mintuna talatin sannan ya fito, ya saka jallabiya bayan ya goge jikinsa, yakawo turare ya fesa. Ledar daya shigo da ita ya bud'e yaciro wata karamar leda aciki, saida ya bud'e firij ya Ciro gorar ruwa sanan yakoma bakin gado ya zauna yana zazzage abinda ke ledar saman gadon, magungunane masu d'an yawa, ya 6alli kusan kala shida ya shanye yana zabga murmushi, sai shafar gemunsa dayasha aski yakeyi, tashi ya kumayi ya d'auki wata gorar da aka had'a tsumin magungunan gargajiya a ciki nanma yasha sosai sanan ya d'auki babbar ledar ya fito zuwa sashen amarya Jiddah.
           Lokacin daya shigo sashen Jiddah tsit nanma, dan ita koma TV babu a kashe komai yake, sai k'amshi irin wanda akasan d'akin amarya dashi.
     Bakinsa har k'arshen kunne ya Isa bedroom d'in Jiddah, sai wani lasar la66a yake tamkar tsohon maye😏😣............✍🏻

Kuyi manage please, yau banajin typing🤒

Yau dai nasan Naga idi😑🥺⛹‍♀





*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[13....]_*

   
..............Tunda ya shigo idonsa nakan Jiddah k'yam, duk da a kudundune take da hijjab hakan bai hanashi jin wani farin cikiba, haryay tuntu6e da gado kad'an yarage ya fad'i, yadai samu ya dafa gadon.😂😝
         Ledar hannunsa ya ajiye saman dirowan gefen gadon kafin ya zauna a bakin gadon shima yana fad'in “Amarsu ta ango mai dad'in tuwo! Nidai abud'e fuska indai bakine nasayi abuna dubu d'ari kash”.
    Jin Jiddah tayi shiru bata amsaba yakai hannu ya janye hijjabin, wani hucin zafine ya bigesa, yayinda sanyin AC kuma ya shigi Jiddah tahau kankame jikinta. 'Dan canjawa fuskarsa tayi, yace, “K Jiddah tashi”.. 
      Jiddah dake jinsa sama-sama tad'an bud'e idonta kad'an ta kalleshi, saikuma ta maida ta lumshe tare da k'ok'arin jan hijjabinta daya janye......
      Tsawa ya daka mata, wadda tasata mik'e babu shiri, dama Jiddah akwai d'an banzan tsoro, dan haka jikinta keta k'yarma tana hawaye da karanto duk addu'ar datazo bakinta.
          'Dan sassauta fushinsa yayi ganin ta rud'e, ya kwantar da murya yana fad'in “Bakida lafiyane?”.
     Kai ta d'aga masa alamar eh.
       Shiru yay yana kallonta, danshifa gaskiya bazai iya hak'uri ba, yanda yay savise d'innan ace yatashi a banza ai akwai babbar matsala. Gyaran murya yad'anyi yakai hannu zai Kama nata, amma sai tayi saurin janyewa, yad'an murmusa da ta6e baki, “Kinga da safe likita idan yazo dubaki zai had'a yabaki magani, dan nikamdai yau babu fashi saina more sadakina. Maza tashi kicire kaya, koda yake kefa malamace yo alwala mufara salla”.
      Kan Jiddah a k'asa ga hawaye na zirara da Uban tsoro fal ranta tamkar zuciyarta zata faso k'irji ta fito.
     Harara ya zabga Mata, kafin yay Mata magana ad'an tsawace. Ai babu shiri ta rikito daga gadon, dukta rikice tarasa ina zata dosa, wannan yasaka dukkan illahirin jikinta motsawa saboda babu hijjab, sanye take da riga da zani nawani yadi ruwan goro, kayan sunmata d'as a jiki, dan dai-dai gwargwado ALLAH yayma Jiddah cikakken jiki da sura, danma damuwa da ta sakata ramewane yanzu.
       Gaba d'aya sai jikin Alhaji Garba Yakama rawar jaraba, sai faman lasar la66a yake saboda yakai makurar buk'atarta, maganin daya loda sha yanzu magani yanzu ne, sune karfinsa ga mace, inbabusu babu uwar dazai iya daboda shekaru sunja garesa sosai, dak'yar ya iya Mata nuni da hanyar band'aki dake cikin d'akin, ta shiga.
       Bata damuba da kallon band'akin, fitsarin da dama ya matseta tun d'azun shita samu ta tsugunna yi cikin kwamin wankan dake bayin. Wata muguwar fad'uwa gabanta yayi lokaci d'aya, ta waro idanu waje tanabin jan abun da ke gudu cikin kwamin Wanda da alama jinine.
        A fili ta furta “Jini! Kuma?, ni Jiddah mike faruwa dani haka?”. Ido takuma sakawa sosai dan sake tabbatarwa, lallai da gaske jinine wannan, to amma ai yau kwananta uku kacal dagama period, ina kuma tasamo jini..........”
        Bata ankaraba kawai taji maganar mutum a kanta. Alhaji garba daya gaji da jiran fitowarta ya biyota, harya shigo bata saniba, shima bin jinin yay da kallo kafin ya furta “K minene hakan?”.
       A rikice ta juyo tana kallonsa, in banda iskanci mizaisa ya biyota band'aki, saurin mik'ewa tayi tana sakin zaninta, dukda jinin dake bin k'afafunta bata damuba. Shiko ya k'urama jinin data zubar ido, sosai ransa yakai matuk'ar 6aci, dan wannan jinin ko kad'an bai masa adalciba, batareda ya tanka mataba yafita fuuuu. Da kallo tabisa harya 6acema ganinta sannan ta lumshe idanu tana sauke ajiyar zuciya. Bata kawo komai a rantaba tahau gyaran jikinta, dan ita duk zatonta ko jinintane kemata wasa, sai dai yanda yake zuba da yawa yabata mamaki. Tsaf ta gyara jikinta da wajen sannan ta fito, dan komai da mace zata iya buk'ata akwaishi a bayin, ganinma an ajiye always da fants abin har mamaki ya bata, saikace ansan da zuwan jinin Nata.
       Koda ta fito babu Alhaji babu dalilinsa, bata wani damuba tayi kwanciyarta bayan ta canja zaninta kawai, amma rigar da d'an Kwali duk da abinta ta kwanta. Taja bargo ta lullu6e saboda sanyin ac ya addabeta, itakuma batasan yanda ake kashewaba, har kanta ta saka a bargo. Sai dai yanzu takasa barci sa6anin d'azun, tunanin y'an uwarta da kewarsu tadawoma zugiyarta sabuwa, tuni tafara zirar da hawaye. Ta dad'e tana kuka, dan harkusan karfe uku kafin barci 6arawo ya saceta bayan tasamu tayi addu'a da k'yar.

★★★★★★

          Alhaii Garba dai daga k'arshe sai wajen Hajia deluwa Yakoma ya sauke kayan wahalarsa, inda Sam tak'i saurarensa daga farko, dak'yar ya iya shawo kanta bayan sunyi cinikin zai bata dubu d'ari biyar. Atake kuwa yaymata transper d'insu dan hakan shine k'a'idarta Dama, saitaji dumus a hannu ko a asusun banki ( wannan bawai sabon Abu baneba).
      Aiko ranar tagane kuranta, dan saida takoma yimasa kuka rurus sannan ya hak'ura ya barta badan yasamu yanda yakeso ba, a zuciyarsa kam sai kuma tsinema jinin Jiddah yakeyi, dayanzu yanacan yana morewarsa, sai sanda yaso barinta, amma ita wannan ta ishesa da shegen raki badan yagama nutsuwaba. (😆😝⛹‍♀)

*Wanene Alhaji garba?*

          Alhaji Garba Mai tabarba kowa ya sanshi dashi, haifaffen cikin birnin kano kuma girman nan, sana'ar tabarma dayakeyi tun yana matashi shine sunan ya bishi, Wanda sanadin tabarmar ALLAH yay masa arzik'in da harya bud'e kamfanin da akeyinta, ahankali arzik'insa yacigaba da bunk'asa.
     Matarsa ta farko (ladan noma) itace Yahanasu, wadda tun tana k'arama ake kiranta da suna Deluwa, tuni sunan yagama binta harma an manta da yahanasu gaba d'aya.
    Yaransu bakwai da ita, maza hud'u Mata uku. Y'ay'ansa Mata biyu sunyi aure shekara d'aya kenan, mazan kam babban ne yahuza kawai yayi, amma sauran ukun duk sunanan suna ruwan ido, iyayansu kuma babu maicewa basu k'yautaba, duk d'insu sunyi katunema a k'asashen k'etare, yanzu haka autarsu Zaliha wadda zasuyi sa'anni da Jiddah tana Niger karatu.
       Tun zamanin kuruciya akaima hajia deluwa shaidar batason zama da kishiya, Dan Alhaji Garba yayi aure-aure bayan ita amma babu mai rufa shekara biyu take barin gidan saboda masifar hajia uwargidansa. Sannan koda ciki kika samu to dawuya ki haifeshi, kodai kiyi 6arinsa kokuwa ma ki haifeshi babu rai, mace d'ayace tahaihu dashi bayan hajia deluwa, yaran yana shekara d'aya da haihuwa ya rasu Alhaji Garba kuma ya saketa.
     Dangin Alhaji Garba basu isa su ra6eshiba, wannan yasaka duk sanda zai sake aure cikin d'oki suke, saidai auren baya wani Kai labari.
       Hajara itace mace ta k'arshe daya sake aure, wadda a k'alla takai shekara uku a gidan, kowa yafara murna da fad'in Hajarah ta gagari Hajia deluwa sai kwatsam ranar ya dank'ara mata Saki. Tundaga nan kuma bai sake zancen aureba kusan shekara hud'u kenan, yay hak'urin cigaban  zama da matarsa wadda tun zamanin kuruciya bata yarda yay kwanciyar aure da ita saiya biya, (wanna daliline yake sakashi yawan aure-aure, harga abin Na binsa har tsufa) ahaka ALLAH ya albarkacesu da haihuwar y'ay'anan bakwai.
     Kwatsam ranar sai yaga Jiddah kusan shekara biyu data wuce, to amma kuma yarasa ta inda zai tunkari Alhaji Zakari yaro da zancen, dan shima yasan ba kanwar lasa bane, sannan yasan mafi yawa daga sirrkan gidansa, abokinsane shekaru masu yawa wadda sanadin kasuwanci suka kulle, saidai Alhaji Garba yafi Alhaji Zakari kud'i nesa ba kusaba, dan ko a kwatancema bazasu had'uba. To rana tsaka kuma saiga Alhaji Zakari yazoma Alhaji Garba da buk'ata, wadda itace sanadin daya samu damar sako zancen Jiddah a tsakkiyar hark'allarsu. Shiko Abba domin biyan buk'atarsa saiya amince, yakuma dage saboda Neman biyan buk'atarsa.
       Sosai Hajia Hindu ke k'awance da Hajia Deluwa tuni.

★★★★★

            Sai k'arfe kusan takwas ALLAH yabama Jiddah ikon tashi, dan barcin dabata samu tayiba shiya janyo mata doguwar makara, da addu'a d'auke a bakinta ta farka, idanunta duk sunmata nauyi luhu-luhu saboda kuka, hakama kanta jingim take jinsa, dak'yar ta iya sakkowa a gadon tanufi bayi tana hawayen kewar ahalinta da bak'incikin wannan auren.
     Wani mugun mamakine ya kamata sosai dankuwa k'amas babu ko d'igon jini a jikin always d'in data saka, hakama jikinta normal yake, to kodai jiya ta iske jinin a wajen ne itakuma ta tsugunna? To amma kuma ai tagansa har a jikinta ajiyan kuma? Kai wannan lamari da mamaki, itadai dukma takasa fassara lamarin, dan haka tahad'a ruwa Mai d'umi tayi wanka, irin wad'annan ta6e-ta6en kayan y'an gayun dukta iyasu gidan aunty Nafisa, shiyyasa anan basu zame mata sabon abuba, itadai wankan tsarki tayi saboda kore kokwanton ko jinintane yaymata wasa, koda ta fito saita rama sallarta kamar yanda shai'a tabamu damaryi.
       Koda ta idar saman gadon ta koma ta sake kwanciya tana cigaba da kukanta, har kusan k'arfe d'aya bataji motsin kowaba a gidan, ga yunwa tafara addabarta dan batasan iya lokacin data d'aukaba rabonda taci abinci mai nauyi. Da k'yar yanzuma tatashi tayi salla, bayan ta idar ne tasamu zarafin bud'e ledar da Alhaji yashigo da ita jiya, dan itadai har jiri-jiri take gani.
     “Alhmdllh” tafad'a saboda ganin kaji dasu ice-creem da sauran kayan kwad'ayi irinsu chocolate mai dad'i dawasu kalolin biscuits dadai tarkacen kayan kwad'ayi. Kazar kawai ta d'auka taci kusan rabi, saida taji tafara zufar k'oshi sannan ta mik'e taje ta wanko hannunta da bakinta.
      Handbag d'in datazo da ita gidan ta bud'e tazaro Qur'ani madaidaici a girma tazauna tafara karatu cikin suratul Bak'ara da muryarnan tata mai saka zukata nutsuwa. Har aka kira sallar la'asar tana karatunta, saida taji za'a shiga salla sannan tayi addu'ar ta mik'e ta gabatar da salla.
      Yanzu dai ta daure ta gyara bedroom d'in musamman ma gadon. Amma koda wasa batayi tunanin lek'a koda falonba, tana gamawa takoma ta zauna tana tunanin su Ummanta ko misukeyi yanzu oho. Hawaye taji suna kwararo Mata, jin kanta zai Fara ciwo saita maida akalar tunaninta zuwa yin Azkar Na yamma.

★★★★★

         Ango Alhaji Garba kam fitace ta gaggawa ta sameshi tunda sassafe, dan haka yafita batareda ya lek'o Jiddah ba, har dare kuma bai dawoba.

     Hajia deluwa kam dak'yar yau ta iya tashi tana tsinema Alhaji garba a zuciyarta, tareda zubama likitocin da sukawo maganin dayakesha ALLAH ya isa fiyeda cikin buhu, tasamu nasarar aikinta amma wuyar tadawo kanta....
       Tana cikin wanna tunanin Kira ya shigo wayarta, kallon wayar tayi a yatsine, amma ganin Mai kiran saita d'auka har jikinta Na 6ari.
       “Malam lafiya dai kuwa?”.
     Daga can malam na barewa yace, “Dadai sauk'i, amma hajia haka mukayi dake? banace idan an daceba ki kirani tun a daren nasan abunyi? Kinsanfa wannan yarinyar nafad'a miki tanada tsari sosai a jikinta, dan bata wasa da addu'a ko kad'an, wannanma munsami damartane saboda taimakon batada lafiya”.
      “Malam kayi hak'uri dan ALLAH, wlhy anyi nasara, nima wahalar daya maido kaina wadda yayma amaryar shiri shine yahanani sukuni, yanzudai zance maka an dace, dan jiya a sashina yadawo ya kwana yana masifa, Dana tambayesa kuma ya sanarmin komai akan jini takeyi wai”.
        ”Ni dama nasan za'a dace, ammafa aikin tun a daren jiyama ya warware, dan tanayin addu'ar barci aljanin yakasa matsarta, hasalima kasa zaman gidan yayi gaba d'aya saida ya dawomin, ayanzu danake miki magana lafiyarta lau, hasalima babu sallar dabatayiba a yau”.
    Sosai hankalin Hajiya Deluwa ya tashi, jikinta Na rawa tace, “Malam yanzu minene mafita?”.
       “Mafita kam a yanzu dai babu ita daga gareni, dan saina sake sabon shiri akanta da Neman lagonta, ammafa gaskiya komai zai iya faruwa tsakaninta da mijinki, dan naga hakan a istaharar danayi”.
     Rud'ewa sosai hajia deluwa tayi, bata kuma sauraren malam ba ta yanke wayar tana zagaye-zagayen Neman mafita. ta nufi k'ofa yafi sau biyar da nufin tafiya sashen Jiddah saikuma zuciyarta ta gargad'eta ta dawo baya, daga k'arshe dai Kira ta kwalawa bilki Mai aikinta.
     Bilki tazo da sauri tana fad'in “hajia gani”.
      Kallonta Hajia deluwa tayi tana d'an Huci, “Balki kunbama amarya abincine?”.
      “A'a Hajia ai baki bada Umarnin hakanba”.
      “Jeki sashenta yanzunan ki kiramin ita”.
    Da to bilki ta amsa tana mik'ewa zuwa sashen Jiddah.

         A zaune ta isketa tazuba tagumi, sai dai ba tunani takeba Azkar takeyi.
        Sallamar Bilki ta sakata d'agowa ta kalleta. Bilki tad'an risina ta gaidata, amsawa Jiddah tayi cikin Y'ar fara'ar yak'e. Bilki tace, “Amarya kizo hajia Na kiranki”.
    Ba k'aramin fad'uwa gaban Jiddah yayiba, ta had'iye wasu yawu masu kauri kafin ta d'agama bilki Kai da k'yar.
    Fita Bilki tayi domin ta jirata a falo.
            Gaba d'aya Jiddah ta rikice a tsorace take, jikinta sai rawa yake ta d'auki hijjab d'inta ta tasaka ta fito, a falo ta iske bilki, dan haka taimata jagora zuwa 6angaren hajiya deluwa.....

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

              Malam kam ganin burinsa Na farko bai cikaba saiya yanke shawarar aurama malam Aliyu Maimunatu, dan haka babu 6ata lokaci yadsamu Iya habi da maganar.
     Shiru tad'anyi tana nazarinsa, kafin zuwa can ta sauke nannauyan numfashi “Malam bank'i wannan had'inba, amma kana ganin Aliyu ya warke daga lalurarsa?”.
      Murmushi kawai malam yay yad'an girgiza kansa da mamakin furucinta, “Habiba kenan, wannan shine matsalarki kenan? to gaskiya bamuda tabbas akan hakan, sai dai munada yak'ini da addu'ar samun nasara, duba da yanda yay amfani da magunguna da dama akan lalurar domain Neman waraka”.
       “To ALLAH ya datar damu, aishi lamari na aure ba'ai masa shishshigi, Zan Kira Sani muyi magana (kaninta Baban mamuna)”.
        Malam yace, “To shiken sainaji daga gareku, dan inason ayi auren kusa, daya dawo da sati biyu, tunda yanzu saura sati biyu ya dawo, kinga nanda wata d'aya kenan”.
       “Hakane, insha ALLAH zakaji”.

     Bayan kwanaki uku dayin wannan magana iya Habi taima malam maganar sukai kud'i ga mahaifin maimunatun, danshi yayi farinciki kwarai da gaske da wannan had'in.
     Sosai malam yayi murna, dan haka babu 6ata lokaci akayi komai aka gama. Koda malam ya sanarma Aliyu cayay ALLAH yasa haka shiyafi alkairi kawai. Dama malam baya hangen matsala daga gareshi, saboda yasan biyayyar Aliyu akan mahaifa.

             Kwana goma dayin wannan magana Aliyu ya dawo, d'alibansa da malam sunyi matuk'ar farinciki da dawowarsa dakuma nasarar daya samo.
     Kwana biyu da dawowarsa y'an uwansa sukazo yimasa sannu da zuwa, aunty Ruk'ayya da Siyama.
    Yana k'aunar y'an uwansa haka suma suna k'aunarsa, hira sosai ta 6arke a tsakaninsu har akazo kan maganar aurensa da Maimunatu, a yanda ya lura duk basuso had'inba, dan haka yashiga kwantar da hankalinsu cikin nasiha da nuna musu muhimmancin yin k'ysk'yk'yawan zato ga musulmi. Hakan ne yad'an saka kwanciyar hankali agaresu, har suka fara jefa kalmar fatan alkairi ga auren nasa, dan koba komai suma sungaji da zamansa haka, kowa yana girmamashi matsayin babban mutum amma kuma bashida cikon rigar kamala Na aure, idan har yay auren koyaya mutuncinsa da k'imarsa zasu kuma bayyana ga jama'a.
      Duk abinda yadace su tsara Na al'ada Wanda baishiga hurumin addiniba sun tsarashi aranar, tareda had'a k'arfi da k'arfe wajen burin fita kunya, dukda auren gidane bazai hana ai kananun maganaba idan sun gaza.
      A 6angaren malam ma sunata k'ok'arin gyara gidan Aliyu, Wanda tunbayan rabuwar aurensa da Asma'u ya saida wancan gidan ya cika yasai fili, yana Saudia yayta aiko da kud'i a hankali aka gine filin da madaidaicin gida Wanda akai masallaci Mai d'an girma a jikinsa da islamiyya Mai ajujuwa da bazasu gaza shida ba. Iya gwargwado gidan yayi k'yau, sannan duk Wanda yagani yasan ba tsarin zaman mace d'aya baneba, kusan komai angama sai abinda ba'a rasaba, dan haka a yanzu malam ya tsaida malam mustafa akan k'ok'arin kammala komai.
          Ahaka aka shiga hidimar biki, ango kuwa kosau d'aya bai ta6a ke6ewa da amarya ba da sunan zance, yace ai gidansa zata, minene abin 6ata lokaci a waje.
        Shagali biki yafara gudana tamkar yanda Shari'a ta tanadar, babuwani hayaniyar shed'anci Mara amfani, ranar juma'a bayan sakkowa masallaci aka d'aura auren Aliyu da Maimunatu acan gidansu dake anguwar d'orayi. Taron d'aurin aurene daya samu halattar mutane daban-daban a sassan Nageria, burin kowa ya nuna halacci ga Sheikh Aliyu Abdul-ra'uff Maina, Alhmdllh anyi cikin nasara an k'are lafiya, bayan d'aurin aure aka gudanar da gagarumar walima wadda malamai suka zazzaga wa'azi akan aure da rayuwar ma'aurata, tareda jan doguwar Addu'a ga wad'annan ma'aurata.
     Amarya Maimunatu tana cikin farin cikin mallakar cikar burinta, yayinda ango baka gane nasa yanayin.
    Bayan kammala walima aka mik'a amarya d'akinta tareda fatan alkairin ALLAH yasa bad'i adawo suna...............✍🏻

https://youtu.be/eOU-ju4f6KY

_Zaku iya samun RAINA KAMA a audio ta wanann link d'in Na sama, Abban Dausayi YouTube channel tv😄🤝🏻_

*_Bazan 6oye mukuba jiya bak'aramar dariya naci akan Comments nakuba gaskiya, lallai nalura kund'auki aurennan da zafi, Abba zakari da Alhaji garba sun zagu babu k'arya🤣🤣, ALLAH ya taimakeni ba a had'a daniba nima😂⛹‍♀._*





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[14➖15]_*

   
..............Sosai Jiddah ke yaba k'yawun tsarin sashen hajia deluwa, dan bak'aramin kud'i aka narkaba gaskiya, gabanta ya fad'i saboda hango Hajia deluwa dake hamshak'e cikin kujera, taci kwalliya cikin wani ubansun leshi ruwan ganye, ga wani kamshi Mai kwantar da hankali datake zabgawa.
          Tunda Jiddah ta shigo itama Hajia deluwa kemata kallon k'asan ido daga k'asa har sama, sosai Jiddah taimata k'yau fiye da yanda hajia Hindu ta nuna Mata ita a hoto, dukda a yanzu cikin hijjab take kuwa.
         Gabanta Jiddah taje ta zauna a k'asa, cike da girmamawa muryarta a matuk'ar sanyaye tace, “Hajia ina yini”.
       Cike da yatsina hajia deluwa ta amsa da “lafiya amarya ya kwanan amarci?”.
      Shiru Jiddah tayi takasa amsawa, yayinda hajia deluwa keta wani ta6e baki tana gyara zamanta, cikin dakewar murya tace, “To amarya inason muyi magana ta fahimta dake, dan banason biyo miki ta hanyar da zaki gaza 6illewa, da farko dai kisani ina matuk'ar son mijina da dukiyarsa, babukuma wata danake k'aunar tazo ta haihu dashi bayan nawa y'ay'an, kullum burina dagani sai y'ay'ana mu mallaki komansa, a girme Na girmi Mamanki ma balle ke nasani, Alhaji kam inda su Yahuza auren wuri sukayi sun Isa Haifa masa kamarki matsayin jika, inason nabaki shawarar kibar gidannan tunda arzik'inki, Zan baki ko nawa kikeso domin kibarmin mijina, dan tabbas nasan dukiyarsa tasaki aurensa, dan Ku y'an matan yanzu duk inda naira take kuna a nanik'e, abinda yasa duk nake miki wannan jawabin cikin lalama saboda nakula kamar zakiyi hankali, sannan kece mafi k'ank'anta a matan da Alhaji yata6a aura adukkan aure-aurensa. Kifita kisamu saurayi dai-daike ki aure, inma baida kud'in aurenki Zan iya masa komai, ke nama tak'aita miki zance koda cikin su Ashir kikeso ki za6a (yayanta fa🙆🏻).
      Duk wannan maganganu da Hajia deluwa keyi kan Jiddah Na k'asa tana mamaki da al'ajabinta, gaba d'aya takasa fahimtar inda surutanta suka dosa, wannan wace irin macece?........
      Kafin Jiddah tasamu zarafin amsawa sallamar matashin saurayi dazai iya kaiwa shekaru 29 ta karad'e falon.
      Cikeda washe hakora Hajia Deluwa ta amsa masa tana fad'in “Wai ina kashigene haka Ashir?”.
      Idonsa akan Jiddah yace, “Mami wlhy ina d'aki kwance abuna, wannanfa?”. ‘Yak'are maganar yana lasar la66a da nuna Jiddah’.
        Baki hajia deluwa tad'an ta6e, ”Amaryar gidance”.
        Sosai Ashir ya zaro ido waje yana kuma lek'a fuskar Jiddah, “wai mami dama wannan karon karamar kaza Dad ya d'akko mana? Kai dad yana yarfamu wlhy, inma auren zaiyi ya d'akko wadda kowa yagani zai yaba mana”.
      Harara Hajia deluwa ta watsa masa, amma batace komaiba.
      Jiddah kam gabanta saikuma fad'uwa yake, ga maganganun Ashir na sukar zuciyarta amma batako motsaba.........
       “Kinga tashi ki tafi, kije kiyi nazari akan maganata”.  Maganar Hajia deluwa ta katsema Jiddah tunani.
      Dak'yar ta iya mik'ewa ta fice jikinta Na rawa, yayinda Ashir kebinta da kallo tamkar tsohon maye..

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

         Ango Ali baisamu damar shiga gidan nasaba sai wajen sha d'aya, Malam Mustafa ne ya kaishi har gida, batare daya shigaba ya juya yana tsokanarsa wai asha angwanci lafiya.
     Murmushi kawai yay bai iya bama malam mustafa amsaba, danshi ba mutumne Mai yawan maganaba inhar baisoba, idan kuma yaso zakaji yanayi sosai mussaman ma idan tashafi addini.
       Cikin sanyin nan nasa tamkar mara laka a jiki ya k'arasa cikin gidan,  a hankali ya furta “Masha ALLAH” akan la66ansa saboda k'yawun da falon yayi, komai yayi cikin tsari dai-dai gwargwado, bai zaunaba ya nufi bedroom d'in Maimunatu.
     Cikin sassanyar muryarsa yay cikakkiyar sallama.
      Maimunatu dake kwance tad'ago idanu tana kallonsa da amsa sallamarsa akan la66a, sanye yake cikin wani lallausan yadi kalar madara, sai hularsa kube ruwan makuba dad'an ratsin kalar madarar, jikinsa Na fidda wani sassanyan kamshi maisaka zuciya nutsuwa.
       Shikam kallo d'aya yaymata ya janye idonsa tareda ajiye ledar hannunsa saman madubi sannan ya zauna a bakin gadon d'an nesa da ita. Tashi tayi zaune tana fad'in “Yaya Aliyu ina yini”.
        A sanyaye yace, “Lafiya lau Maimunatu, ya gajiyar hidima?”.
        Murmushi tayi kawai amma bata iya bashi amsaba sai wasa da gefen gyalenta da takeyi.
      Kuma kallonta yad'anyi kafin yakuma d'auke idonsa, “Ga abinci nan nasan kina buk'atarsa, danku Mata idan kuna hidima nakula bakuda lokacin cikinku”.
       Murmushi tayi idonta  akan bakinsa dake motsawa a hankali tamkar bashi ke maganarba....
    Jin tayi shiru saiya juyo ya kalleta, saurin janye idonta tayi akansa ta amsa da “to, nagode”.
       Karan farko daya d'an murmusa, ya mik'e yana fad'in “Bara nad'an watsa ruwa, kafin Na dawo kici abinci kiyi alwala...”. Kafin tabashi amsa tuni ya fice.
     Ajiyar zuciya ta sauke a hankali, tajawo ledar daya ajiye ta bud'e, gasashshen namane sai kayan fruits da abinda ba'a rasaba. Bata wani kwari kantaba taci abinta tayi nak sannan taje tayo brosh tadawo ta zauna.
         Kusan mintuna Arba'in saiga malam Aliyu ya dawo, sanye yake da kananun kaya wando dogo fari da riga t-shirt ruwan hanta, abinda tunda maimuna take bata ta6a gani daga gareshiba kenan, saka kananun kaya, gaba d'aya ta shagala da kallonsa saboda wani mugun k'yau dayay Mata, Yakuma komawa yaro d'anye sharaf, a ranta tana ayyana dama yana saka k'ananun kaya haka?......
      Malam Aliyu da yaga ta shagala da kallonsa ne yay murmushi yana zama kusa da ita gab tareda kai yatsansa tamkar zai tsokale Mata ido.
      Da sauri ta sauke ajiyar zuciya tana rufe fuskarta saboda taji kunya sosai.
     Murmushi yad'anyi, yana cewa, “Na canja mikine?”.
      “Sosaima”. ‘Ta fad'a har yanzu Idonta a rufe’.
      “Humm dama can kallon tsoro kikemin shiyyasa kike ganin Na canja yanzu. Ina fata kinyi Alwalan?”.
        Batare data bud'e fuskartaba tace, “Nifa Yaya ina up”.
      Baice komaiba sai d'auke kai dayay daga dubanta yana d'an sauke numfashi, kusan mintuna biyu yana mulmula maganar dazai mata a ransa kafin ya gyara zama yakuma fuskantarta.
        “Yaushe yazo?”.
    Tamkar zata nutse dan kunya haka taji, gyalenta taja takuma rufe fuskarta sosai kafin ta iya bashi amsa, “Yau”.
       “Babu k'yau k'arya, yau kwannansa biyu, nanda kwana hud'u zaki samu tsarki”.
    Babu shiri ta bud'e fuskarta tana ware idonta a kansa, “Yaya ya akai kasani?”. ‘maganar ta su6uce Mata batare da ta saniba’.
         Jikinsa kawai ya jawota batareda ya bata amsaba, cikin kunnenta ya rad'a Mata “Kinason sani?”.
       Gaba d'aya kunya ta rufeta, ga jikinta sai tsuma yake saboda jinta a jikinsa, shikansa hakance ke faruwa daga gareshi, amma ya daure kamar bayajin komai.
    Kusan mintuna biyu suna a haka kafin ya d'agota zaune sosai. “Tashi muyi magana”.
      Gyara zamanta tayi, taja gyalenta takuma rufe fuskarta sosai.
        “Maimunatu da farko dai nasan kinada ilimin addini dana zamani, kinkai shekarun da zaki iya banbance dai-dai da sa6anin haka, inaso kisaka a ranki zamuyi tsaftataccen zaman aure tamkar yanda Manzon ALLAH (s.a.w) ya koyar damu, insha ALLAH Zan sauke dukkan hak'k'ok'inki a kaina iya iyawata, kema ina fatan hakan daga gareki. Nasan tunkan ki shigo gidana kinsan inada lalura wadda itace sanadin rabuwata da matata ta farko, to kisanifa har yanzu banida tabbacin samun waraka, sai dai muna fatan dacewa, wannan kuma saikin samu tsarikine zamu tabbatar, idan babu wani canji game da lafiyata to lallai bazan cutar dakeba Zan sallameki insha ALLAH, idan kuma an dace Alhmdllh, zaki zama Aliyu, Aliyu zai zama ke, mallakar Aliyu gaba d'ayansa kuma saikin zama jaruma wajen fahimtar abinda yakeso da Wanda bayaso. Nabaki satar amsa”. ‘ya k'are maganar da yaye gyalen data lulllu6a’.
      Saurin kife kanta tayi a cinyarsa saboda kunya, yayinda shikuma yay murmushi.

😂ta gidan Sheikh Ali ina tayaki murna🤭⛹‍♀.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

               A gidan Umma kam bayan biki da kwanaki uku kowa ya Kama gabansa, aka barsu su kad'ai, daga ita harsu Walida babu Mai isashshiyar lafiya, kowa damuwa da tausayin Jiddah da kewarsa ta isheshi.
     Washe Gari dole Uncle yahaya yanemo likita yazo har gida ya sakama Umma k'arin ruwa saboda batajin dadi sosai.
      Bayan la'asar Zarah ta cire Mata saboda ya k'are, ruwa Mai d'umi suka had'a Mata tai wanka, suna tsaka da gyaran gidan saiga Abba.
      Kowacce kai a k'asa ta gaidashi.
       Bakinsa ya ta6e ya wuce d'akin Umma, dan ya lura yau su Zarah awani yanayin jin haushi suka gaidashi.
     Umma na zaune tana cin faten waken da Maman Sadiq ta aiko Mata Abba ya shigo, kallo d'aya taimasa ta d'auke kanta.
     Zama yay shima yana wani kumbura. Umma tace, “Ina yini”.
    Bai amsaba, sai tambaya daya jefoma Umma.
     “Yagana waike aurar da y'arne yasaki maida kanki haka? Lallai aiki ya sameki ashe”.
      Wani murmushin takaici Umma tayi kafin ta d'ago ta kalleshi ido cikin ido, “Koma minene ya maidani haka wannan ba matsalarka baceba, saidai inason maka tambaya d'aya. Shin nawa Alhaji Garba yabaka kabashi Jiddah?”.
      Gaban Abba ne ya fad'i, bakinsa Na rawa yace, “Yagana ban gane wannna maganar banzar takiba? Dan Zan bada auren y'ay'ana sai an biyani kud'i?”.
       “Humm Alhaji kenan, bar ganin ka fini shekaru wlhy kar nake kallonka, a ina kasamu kud'in biyan banki bashin da kaci musu?”.
      Harara ya watsa mata yana huci, “Shak'eni Na fad'a miki mana yagana?”.
         “Aiba saina shak'eka bama, zaka fad'ane cikin kwanciyar hankali. Wlhy Alhaji ka farka daga nannauyan barcin daya d'aukeka, wato ka ciwo bashin kud'i a banki lokacin da suka baka Na kar6a yayi bakadashi ko? Saboda kakashe kud'in akan matarka da y'ay'an Sonka yanzu anema kabada kud'in ko kaddarorinka hankalinka ya tashi ko? Karasa ina zaka nufa matarka tabaka shawarar Neman bashi wajen Alhaji Garba. Shikuma dayake tsohon banzane kaje da buk'atar kud'i yabuk'aci musanyarsu da yarinyata saboda ta tsole idonsa, wlhy danasan auren manufa kayi da Jiddah ko sama da k'asa zata had'e baza'ayi aurennanba. Amma ko yan.............”
      Wata razananniyar tsawa ya daka Mata yana mik'ewa a zabure, “Daga bakin wane mak'aryaci wannan zancen ya fito? Ko rantsuwa nayi babu kaffara nasan yahaya ne........”
          “Kwarai kuwa nine?”. ‘Cewar Uncle yahya dayake shigowa yanzu’.
    Daga Umma har Abba juyawa sukai suna kallonsa, fuskar Uncle yahya a matuk'ar d'aure yacigaba da fad'in “Wlhy ko'a mafarkina ban ta6a zaton rashin son gaskiyarka yakai hakaba Yaya, yanzu dan ALLAH har nawa Jiddah take da zakayi wannan kulla-kullar akanta? Ashe har mutane masu mutunci sukazo Neman aurenta amma ka shirya musu k'arya? Namaka magana ka gaggayamin son ranka, Anya Yaya kana tsoron gamuwarka da ubangiji kuwa?”.
        “A'a bana tsoro dan Ubanka, shin komadai kaine Ubansu Jiddah ban saniba?”.
     Daga Uncle yahya har Umma a tsorace suke kallon Abba.
      Muryar Umma Na rawa alamar tahowar kuka tace, “Alhaji kana cikin hankalinka kuwa? Mu kake jifa da wad'annan munanan kalamin?”.
      Shiru yay yakasa bata amsa saboda ya fahimci 6acin rai ya sakashi yin kato6ara.....
     Uncle yahya yay murmushin takaici yana fad'in “Karki wani damu kanji da kalamansa Yagana, idan yamana sharri wannan yarage tsakaninsa da Ubangijinsa, dan shine zaimana hisabi, wannan kuma ni bazaisa naji komaiba saboda ban ta6a kwatanta aikatawaba koda a zuciya balle zahiri, ka saka a ranka kuma alhakin wad'annan bayin ALLAH kawai ya isheka ishara inhar baka rok'i gafararsu ba ka gyara mu'amularka dasu. Maman Nafisa ga magungunanki nan, ni nawuce gida”.
       Uncle yahya nagama fad'a ya fice abinsa.
     Umma ma tashi tai ta shige uwar d'aka abinta. Da sauri Abba ya bita.
          Da sauri tace, “kaga fitarmin a d'aki zakari, idan kuma ni kake buk'atar nafita to lallai yanzu Zan barmaka gidanka tafiyarda har abada bazan dawoba koda hakan yana nufin Zan mutu da igiyar aurenka a kaina”.
     Baki ya bud'e zaiyi magana tai saurin janyo hijjab d'inta “ALLAH ya baki hak'uri nizan fita”.
      Bai jira amsartaba ya fice.

       Duk abinda ke faruwa su walida naji, dan haka suka had'e kai a tsakar gida suna dirzar kuka.
    Itama Umma yana fita tafad'a kan gado ta fashe da kuka maiban tausayi.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

       Tunda Jiddah ta koma sashenta taketa juya maganar hajia deluwa a zuciyarta, da mamakin kalamun saurayi da hajia ta Kira da Ashir Wanda take kyautata zaton d'ansune kenan. Lallai ita taga takanta, mutanan gidan kowanne da nashi matsalar....
     Motsin dataji a bayantane ya sakata saurin juyowa, gabanta yay mummunar fad'uwa saboda ganin Ashir. Murmushi ya sakar mata yana matsowa gab da ita, “Auntyn mu gaisuwar bangirma nazo kawowa”. Yay maganar yana d'aga Mata gira d'aya.
       Baya Jiddah ta matsa sosai jikinta harya Fara tsumar tsoro, Ashir ya kuma kwantar da murya tamkar yana gaban matarsa ko budurwa yace, “Wani ya ta6a fad'a miki kinada k'yau kuwa babie? Da sabon jini kika dace babie ba dad ragowar basirba, kizo nabaki dukkan farin ciki dan nine dai-daike nasan dad babu abinda zai iya miki wlhy, shegen aure-aurensane kawai da basa k'arewa......”.
      Duk maganarnan da Ashir yake jikin Jiddah 6ari kawai yake, dan tsaf tagama fahim manufar Ashir a kanta, babu abinda takeyi sai Addu'ar Neman tsarin ALLAH daga shed'ancinsa, yayinda tuni hawaye sun cika Mata idanu. Ganin Ashir yamatso zai kamata yasata afkawa d'aki a guje Ashir ya take Mata baya..............✍🏻 

🙆🏻turk'ashi, Uban ko d'an?.

*_Ammafa kun iya buk'ulu, irin wannan addu'a da kuke jama Maimuna kar Sheikh Ali ya angwance_*🤣🤣🤭



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻
*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[16➖17]_*

   
..............Hannunsa daya kai zai rik'e k'ofar Jiddah ta had'a ta datse, take yasaki wata azababbiyar k'ara, yayinda zufa tafara keta dukkan sassan jikinsa.
    Jiki Na rawa Jiddah tasaki k'ofar kafin ta lek'oshi, ganin ya zube k'asan kafet yana sakin wahalallen kuka da yarfe hannu sai hankalinta yay matuk'ar tashi, kamar zata fito saikuma taji tsoro takoma da baya da sauri ta rufo k'ofar....
     Hakan yayi dai-dai da shigowar Hajia deluwa da gudu, wadda tundaga sashenta tajiyo ihun Ashir.
      “Mami ta kasheni, ta tsinkemin yatsu mami..”
    Abinda Ashir keta fad'a kenan yana birgima a k'asa da mik'ama hajia deluwa hannunsa.
     Hannun nasa takama ta rik'e jiki Na rawa da fad'in “Ashir! Kai Ashir mitaimaka?”.
          “Hannuna ta had'a da k'ofa mami! Mami kikaini Asibiti Karna mutu”.
     Gaba d'aya hajiya deluwa tarud'e, da Sauri tafita tana kwala kiran direbansu, da taimakonsa suka fiddo Ashir daga sashen Jiddah zuwa harabar gidan.
     
         Sosai hankalin Jiddah itama yake a tashe, sai faman tsiyayar da hawaye takeyi, jin fitar mota yasata bud'e k'ofarta, tasan kila suntafi asibitin, jinin daduk Ashir ya d'igar takebi da kallo wasu hawayen tausayinsa masu zafi sunabin kumatunta, data sani dabata guduba da waje ta fita, “Amma dakin tsaya ai zai tozartakine” wani gefe Na zuciyarta ya fad'a.
    Zubewa tayi saman kafet d'in wajen tana kuma sakin marayan kuka da godiya ga ubangijin daya jarabceta da wannan rayuwa....
       Ahaka Alhaji Garba ya shigo ya sameta, daganima sashenta yafara shigowa, dan rik'e yake da babbar rigarsa dawasu tarkace a hannu.
         “Jiddah lafiya kuwa?”. Ya fad'a yana ajiye kayan hannunsa a kujerar dake kusa da ita.
     A tsorace ta d'ago ta kallesa tana girgiza masa kanta, “Alhaji wlhy ba laifina baneba, bada gangan nayi masa hakaba ka yarda Dani...”
      “Ban gane maganar da kike ba Jiddah? Mike faruwa? Jinin menene wanan?........
     “Alhaji wlhy Ashir ne ya......”
     “Yayi Ubanmi munafuka?”.
    Maganar Hajia deluwa ta katse Jiddah, gaba d'aya suka maida kallonsu gareta. K'arasowa tai tana cigaba da fad'in “Wai Alhaji munafukar yarinyarnan dan kawai Ashir yazo gaisheta shine ta had'e hannunsa da k'ofa ta murje”.
      “Ta murje kuma? Ke Jiddah akanmi?”.
      “Akan mugunta mana da mugun hali”. ‘Hajia deluwa takatse Jiddah dake yink'urin yin bayani’.
     Duk yanda Alhaji garba yaso jin ainahin zancen hajia deluwa ta hana hakan, dan Kiri da muzu tahana Jiddah yin bayani. Daga k'arshe sai fita sukayi zuwa sashensa akabar Jiddah Na hawaye. Acan hajia deluwa ta shiryama Alhaji garba karyar datakeso saida taga ya aminta sannan tabaro sashensa.

     Tana dawowa sashenta malam Na marwa takira, a k'ufule tace, “Malam bazan iyaba, maza kasan yanda zakai da yarinyarnan wlhy, ni dama tuni Hindu ta tsoratani akan uwarsu datace ta nacema Ubansu dukda wulak'antatan da yakeyi, koma miye yazo kanka ka aikata Mata tabarmin gidana, yanzu haka harta gwada nakasamin yaro tunkan aje ko inama kenan”.........
         “Kinga kwantar da hankalinki hajia, yinin yau gaba d'aya a aikinki nake, dama kobaki kiraniba ni Zan kiraki, gobe idan ALLAH ya kaimu ki aiko a kar6ar miki sak'o”.
           Cike da d'oki Hajia deluwa tace, “Nagode sosai malam, harka saka zuciyata tayi Fari wlhy”.
         Dariya yayi shima daga can.
   
        Ashir dai ya bugu kam, dan hardasu karaya a yatsunsa biyu Na tsakkiya, farce d'aya ya fita gaba d'aya. bayan an d'orashi aka nad'e hannun da bandeji aka bashi magunguna da sallama.
       Tunda suka shigo gidan yake Harar sashen Jiddah yana kunkuni, kai tsaye sashen hajia deluwa driver ya rakashi.
             Sai wani sannu da tarairayarsa takeyi, “Sannu kaji Ashir, amma dai yarinyarnan muguwace wlhy, muna ganinta salaf-salaf kamar bazata iyaba”.
        “Wlhy mami bazan hak'uraba saina rama, haka kawai kinsakani aikata Abu naje a banza an nakasani, to ayanzu naratse miki saina aikata Na gaske a kanta, naje da nufin Mata barazana tamin haka, to ta shirya Na gaskiyar kuwa w........”
    ”Kai wai bakada hankali Ashir! Ba Matar Ubanka baceba, banason halin dabbancifa”.
     “To amma mami ai duk kece kikaja ko, dabaki turani mata barazanarba tayaya hakan zata faru? Ni koma kallo da zata ishenine? ALLAH kinji Na rantse saina fatattaka yatinyarnan kuma a cikin gidannan saidai dad ya koreni bayan nayi”.
       Dafe kai hajia deluwa tayi, dama tasan Ashir akwai bak'ar zuciyar tsiya, duk maganar da take masa bai sauraretaba yafice fuuuu zuwa sashensu.
  
      Jiddah kam bayan taci kukanta ta more tashitai ta koma d'aki abinta.
     Bata sakejin motsin kowaba Na gidan har ta kwanta, sai a cikin barcine tad'anji motsi a d'akin, idonta ta bud'e kad'an saitaga Alhaji zaune yana latsa lap-top.
      A tsorace ta tashi zaune, yad'an kalleta yana wani had'e fuska.
       “Dama kin kwantar da hankalinki kin kwanta abinki, ni idanma mace Na jini a tsarina ko ta6ata banayi balle tunanin ra6arta”.
        Badan Jiddah ta yardaba tazame ta kwanta, saidai dukta takura takasa barci, har kusan karfe d'aya taga yazo gefenta ya kwanta tareda juya mata baya, tun tana fargaba harta farajin saukar numfashinsa cikin gurnani.
       A hankali ta sakko k'asa ta kwanta itama barci 6arawo yayta fusgarta har yay galaba a kanta.

*_Bayan kwanaki hud'u_*

          Jiddah dukta kuma figewa saboda tunanin su Umma da fargabar halin datake ciki, bata sake had'uwa da Ashir ba balle hajia deluwa, Alhaji Garba kam yakan shigo mata da safe, da daddare kuma anan yake kwana, amma zai raba dare yana latse-latse a laptop, tarasa ubanda yakeyi, zamansa a d'akin yake sakata barci rabi da rabi saboda tsoro, shiyyasa dasafe saitaita zabga barci, ALLAH dai ya taimaketa yau yagama kwana bakwai ya koma wajen uwargidansa itama tasami sukuni.
     Da wannan barcin hajia deluwa tasamu damar shigowa sashenta ta saka wani Abu a k'ark'ashin gadon Jiddah tun a randa tacika kwana uku a gidan.
        Jiddah dai batasan mike faruwaba, yau bayan tayi sallar azahar tad'an fito falonta ta zauna, gaba d'aya batajin kwarin jikinta, saboda tunda tazo gidan bataci abinciba, kullum sai kayan kwad'ayin da Alhaji garba ya kawo Mata na sayen baki, a kullum kuma Alhaji garba Na tambayarta Ana kawo mata abinci? Itakuma saitace eh kawai. Bai ta6a sanin ba'a kawowaba shidai, dan itama hajia deluwa daya tambayeta haka takecewa ankai Mata. da wannan ya d'auke hankalinsa bai saka idoba. Yau kuma gashi a lissafi sashenta zai kwana, duk fargaba ta isheta
          Sallamar Alhaji garba tajiyo cikin nishad'i, dan muryarsa a matuk'ar sake, tasan farin cikin nasa baya rasa nasaba da rutsata tana sallar walha d'azun, dan sai kusan 9 ya fita daga gida yau, yashigo mata sallama ne ya isketa tana sallah, tun sannan yaringa farinciki da tambayarta Ashe tasamu tsarki? Itadai kasama bashi amsa tayi a d'azun......
      Tunanintane ya katse jin yace, “hummmmmm!” Yana toshe hanci. Da mamaki ta kallesa, ganin zai juya da sauri tace, “Alhaji sannu da dawowa”.
      Hannu kawai ya d'aga Mata ya fice da sassarfa. Yana fita ya sauke numfashi da fad'in “Kai wannan wane irin warine a sashen yarinyarnan?”. Babu Mai bashi amsa dan haka yay gaba zuwa sashen hajia deluwa.

★★★★★

     Wasa-wasa dai sashen Jiddah ya gagari Alhaji garba harma da Ashir dake fakon Jiddah yay ramuwar gayya.
    Ita kuma Jiddah haka kawai takejin wani masifar tsoron maza, ko maganar namiji taji a TV saita rikice, cikin kwana uku kuma saiya koma ma tana tsorata da ganinsu koda a TV ne, dan dama ananne kawai take ganin nasu, tunda ba fita take konan da canba.
    Tashin hankali Na biyu abinda take samu taci komai ya k'are, yauma duk a jigace ta wuni saboda yunwa, sallama ta magrib sai a zaune tayita saboda rashin karfin jiki, babu abinda take d'urama kanta sai ruwa.
    Zuwa washe gari ko ruwa tasha sai amai, saboda babu komai a cikinta, ga wani Uban jiri dake d'ibarta.
      Cikin ikon ALLAH saiga bilki mai aikin hajia tazo kawo Mata waya inji Alhaji, dan yakai kararta wajen Abba shine abban yace ya had'asu, shikuma bazai iya zuwa sashenba shiyyasa ya aiko bilki.
    Ganin halin da jiddah take ciki sai hankalinta ya tashi, dan jiddah da k'yar ta iya fad'a mata yunwa takeji, da hanzari ta ajiye wayar takoma sashen hajia deluwa a sace ta had'o tea da abinci takawo sashen Jiddah. Itace ta taimaka Mata tad'ansha tea d'in cikinta ya warware, sannan tabata abincin shima kad'an taci saboda cikinta ya cinkushe, tanama gamaci sai amai.
     Sosai bilki taji tausayinta, itace ta taimaka Mata ta gyara jikinta sannan ta gyara wajen, koda Abba ya Kira sai bilki ta d'aga a matsayin Jiddah, yagama bambaminsa harya yanke wayar bilki dake mamaki da al'ajabi bata tankaba, aiko ko fad'a ma Jiddah yanda akayi batayiba. Tadai koma sashen Alhaji tace masa Jiddah batada lafiya.
     “ALLAH yabata lafiya”. Yafad'a a k'ufule yana amsar wayarsa.
    
    Tundaga ranar sai bilki takoma kaiwa jiddah abinci a sace, dukda Jiddah nasamun abinci sai ciwo ya zame Mata jinya, kullum tana a kwance babu lafiya, ciwon baya da k'irji ga wani tsoron maza dake kuma shigarta babu gaira babu sabar.
    A haka tacika sati uku a gidan, ranardai Alhaji garba yakasa hak'uri, dan  haka ya aika bilki da yamma dayake yadawo da wuri saboda juma'ace ta kirawo masa Jiddah.
    Tunda Jiddah taji Mai kiranta saita birkice tahau kuka da rokon bilki taje tace tayi barci.
        Bilki tace, “Hajia karama dan ALLAH kizo muje Karna rasa aikina”.
       Jin wannan furici Na bilki ya saka jiddah Binta, dan bata fatan bilki ta rasa aikinta ta sanadinta. Sai dai kumafa suna yin ido biyu da Alhaji garba jikinta ya Kama rawa tafara kuka da Neman kofar fita, da sauri yazo ya rufe kofar yana matsota cikin toshe hanci, yayi alkawarin yau ba wariba kominene saiya more dubu d'ari biyunsa Na sadaki.
     Yana kai hannu zai ta6a jiddah ta kwala Kara da lalumar filawa dake kusa dashi ta kwala masa akai.
       Take anan ya zube a sume, jiddah kuma tayi waje da gudu tana kuka.
     A k'ofa sukaci Karo da hajia deluwa zata shigo, ram ta rike jiddah tana tambayarta miya faru? Ina jiddah takasa magana, jikinta sai kuma 6ari yakeyi saboda hango Ashir da Bala dake nufosu saboda jin kururuwar jiddah.
       Da k'arfi ta hankad'a hajiya ta nufi fita da gudu, Ashir da bala sukai tara-tarana kamata, Bala Na rik'e hannunta shima ta hankad'eshi da karfin tsiya yafad'i kasa da fasashshen kai ta fice a guje saboda Mai gadi da Ashir da direba da suma ke tara-taran kamata.
     Haka jiddah taita gudu,  mahaukaciya zam a titi, babu inda take dosa sai hanyar gida kuma, saikace wadda ake control da remote. Mutane da yawa sunyi yinkurin kamata abu ya gagara saboda mazane.

      A gidan Alhaji garba kam tashin hankali biyu, Alhaji da bala duk sun sume, hakanne yasa Ashir kiran y'an sanda ya sanar musu su Kama jiddah, yayinda mai gadi da driver ke kokarin saka su Alhaji mota za'a kaisu asibiti.
    Hajia deluwa kuwa sai shar6ar majina take tana kuka da tsinema jiddah, ita bazata yardaba inhar mijinta da d'anta suka rasa ransu wlhy saita kashe jiddah itama, shi bala daga dawowarsa kwana biyu kenan Jiddah ta kashe matashi. Haka taita sambatu har sukaje asibiti dasu.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨.

        Su Zarah na zaune a tsakar gida kowa nad'an wiki cikin rashin kuzari, dan tunda Jiddah tabar gidan dukkan farin cikin gidan ya gushe, Ga Umma kuma ta hanasu zuwa gidan Jiddah su ganta kwata-kwata, sai Maman Sadiq ce da aunty Nafisa suka shirya zuwa gobe su dubota, shiyyasa Umma tace Subari idan sunje sunga hankalinta kwance suma saisuje.
      Da gudu Jiddah ta shigo musu, dan haka suma duk sai suka kwasa da gudu zuwa cikin d'aki, amma k'arar da jiddah ta kwala tana zubewa a k'asa yasakasu lekowa a rikice, ganin jiddarsu ce duksai suka yo waje hankali a tashe, gaba d'aya kanta sukai suna kiran sunanta, amma ina fisge-fisge kawai take tana kwalla gigitattar k'ara......
      A haka Uncle yahya yashigo a rikice shima, dan tuni sama'ila Mai shago dasukaga shigowar jiddah anguwar Ana shirin sallar magriba sukaje suka kirashi.
    Yana kai hannu zai ta6a Jiddah takuma sakin wata k'arar datafi ta farko.
     Kowa saiya kuma birkicewa, ga kofar gida yacika da y'an anguwa, kowa yana tambayar miya sami Jiddah?. Isowar motar y'an sandane yasa kallo komawa Kansu, kutsawa sukai zuwa cikin gida babu ko tsayawa Neman iso.
         Babbar magana, y'an sanda dai sunga abinfa yawuce tunaninsu, dan shigowarsma saita kuma kid'ima Jiddah tacigaba da sakin wani ihu Mai fita da gurnani maiban tsoro, sai wata irin fisga takeyi nason guduwa daga rikon da sukai Mata........

Tashin hankali ba'a saka maka rana😿, wayyo jiddah.😣

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

         A 6angaren Aliyu kam Maimunatu na samun tsarki a ranar yay shirin gwajin lafiyarsa cike da fargaba.
       Da farkoma shareta yay kusan kwana goma da samun tsakinta, saida yau yaji yakasa jurewa saboda sha'awar kasancewa da mace yakeji ainun. Dan haka yaymata shiri Na musamman irinna masu ililin da sukasan sirrin yanda ya kamata a tunkari mace, musamman ma budurwa.
          Cike da tsoro yayta driving Nata akan abinda yakamata tayi kafin akai ga kwanciya, sunyi salla da tambayoyi dayay Mata akan addini Wanda baisamu Matsala da itaba sai kad'an-kad'an.
      Daganan kuma sukai shirin barci.
     A farkon Fari da fargaba yake sarrafata, da lamura sukai nisa kuma sai komai ya tafi dai-dai fiyema da yanda yay zato.
     A ranar yasamu nasarar Fara bin hanyar cikar burinsa, dan baiyarda yazo Mata kaitsayeba.
      Haka yayta Binta a hankali har tsawon kwanaki hud'u kafin yayi Mai gaba d'aya.
    Maimuna dai kam tazama Aliyu, Aliyu kuma yazama maimuna. Saidai muce ALLAH yabada zaman lafiya Na har Abadan.
       A kwanakin da suka biyo baya sosai yake Nuna Mata kulawa Mai cike da martaba ta, dukda tasan baya sonta bài ta6a Nuna mataba koda a fukane kuwa.
     Saima mamaki da yake bata yanda ya iya sarrafa mace a zaman takewa Na yau da kullum da shinfid'arsu. Abin ba'a cewa komai sai sambarka.
    Tuni kaunarsa takuma mamaye jini da ruhinta, suk hanyar dazata k'yautata masa ita takebi.
         A haka sheikh Aliyu yafara gudanar da al'amuran addini a anguwar, masallacinsa da makarantarsa suka Fara aiki, da dare maza magidanta ke d'aukar karatu, wataran kuma ya gudanar da tafseer.
    Da safe kuma matan aure, da yamma yara da y'ammata.
       Kafin kacemi makaranta tafara cikewa, dan kowa yaji babban malami sheikh Aliyu maina ne, to baya sanya saiya kawo iyalansa dashi kansa.
        Angwanci yayi matuk'ar kar6ar Aliyu, danya murje yayi wani 6ul-6ul dashi, sai wani k'yalli da cikar kamala yake k'arawa.
   Kullum yaje gaida malam kuwa saiya tsokanesa akan mirjewar da yayi, hakama malam mustafa.
     A yanzukam bashida wata Matsala, komai yana tafiya masa dai-dai saidai abinda ba'a rasaba Na kalubalen rayuwa Wanda ba'a taba raba Bawa dashi musamman ma irinsu dake d'auke da nauyin al'umma.............✍🏻

https://youtu.be/eOU-ju4f6KY

*_Zaku iya sauraren RAINA KAMA a audio ta wannan link d'in Na sama, Abban dausayi YouTube channel tv😄👍🏻_*

*_Humm yau dai nasan ba sauk'i a wajen fans🤭⛹‍♀⛹‍♀⛹‍♀⛹‍♀⛹‍♀🥰🥰🥰😂_*



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[18➖19]_*

   
..............Duk yanda akaso nutsuwar Jiddah abin ya gagara, sai da y'an sanda suka kira Uncle yahaya waje dansuyi magana sai akaga Jiddah ta lafa daga fisge-fisge da k'arar da takeyi. Hakanne yasaka Umma dake kuka son fahimtar wani Abu, amma batace komaiba tajigaba da tofama Jiddah Addu'a.
    Bayan kamar mintuna goma Uncle yahaya ya dawo, yana shigowa Jiddah ta tashi aguje zata bar wajen, rik'eta Zarah da walida sukayi da k'yar da taimakon Uncle yahaya suka kaita k'asa.
    Cikin kuka Umma tace, “Uncle d'insu ka fahimci abinda Na fahimta kuwa akan yarinyarnan?”.
     Kansa ya jinjina alamar eh, idonsa jajur shima saboda damuwa yace, “Maman Nafisa Jiddah batason maza su ra6i inda take, lallai akwai abinda ke faruwa dabamu saniba, dan dak'afa fa tazo gidannan tundaga can gidan. Kuma yanzu y'an sandarnan waifa anturosune su kamata saboda Alhaji garba da d'ansa suna asibiti sanadin kwala musu abu datayi. Amma halin da sukaganta a ciki yasakasu komawa”.
      Daga Umma harsu walida kuka suka kuma fashewa dashi, Uncle yahya yace, “Ba kuka zamuyiba Maman Nafisa, bara naje nayi sallah nazo da malam Alfah”.
         Da to suka amsa.
Uncle yahya yafice zuciyarsa cikeda tausayin Jiddah. Tunda ya fita sai Jiddah takuma samun nutsuwa, dan haka su Umma suka kamata zuwa d'aki saboda mutane makwafta dasuke shigowa jajanta abin, wasuko gulmace ta kawosu.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

            A asibiti kam da k'yar aka samu jinin dake zuba a kan Alhaji Garba ya tsaya, shiko bala sunama zuwa ya farfad'o, dan baiwani buguba sosai, allurar barci sukai masa danya samu Hutu.
            Ran Hajia Deluwa da Ashir kam yakai k'ololuwar 6aci, musamman ma da y'an sandan sukazo suna Kora musu bayanin wai ai Jiddah ta haukace, suko tayaya zasu Kama Mara hankali. Tamkar Ashir ya makesu haka yaji, hajia deluwa kuwa datasan abinda ya faru komawa tai gefe takira malaminta tace ya warware asirin dayay ma Jiddah, amma yayi wani Abu akan Alhaji garba danya Saki Jiddah, tanason akama Jiddah aimata hukunci.
      Da to kawai ya amsa mata, danshifa akwai abin tsoroma dayake hangowa gameda wannan abin da suka aikata, shiyyasama tunkan ta kirashi ya warware Na warin ja6a da jiddah keyi, saurama d'ayan.
        Shima Alhaji garba wajen karfe tara aka samu ya farfad'o, alurar barci suka sake masa danya samu nutsuwa.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

       Bayan an idar da sallar magriba Uncle yahya sukazo shida malam alfah, kallo d'aya yayma Jiddah yafahimci akwai sihiri a jikinta, dan indai daga ita saisu Umma ne zakajita luf, da namiji yashigo gidan zata hau ihu da fisge-fisge. Addu'oi yabada kafin safiya asan abinyi.

         Tunda aka bata ruwan addu'ar sai barci ya kwasheta, bata kuma sanin inda kanta yakeba har asubahi. Yayinda su Umma suka kusan kwana a tsaye suna Kai kukansu ga ALLAH.
          Washe gari Alhamdllh jikin nata, dan dakanta tai alwala tagabatar da salla.
    Bayan ta idar ne Umma tabata Qur'an, babu musu ta amsa tana karatu, har wajen awa d'aya kafin ta ajiye tahau yin azkar. Duk wannan abun dake faruwa y'an uwanta na zagaye da ita, saida ta kammala sannan ta gaida Umma, su Zarah suka gaidata suma suna rungumeta danjin dad'in ganinta normal.
    Babu Wanda yay Mata magana akan matsalarta, saima itace ke cewa “wai Umma ya akai nadawo gidane?”.
     Murmushi Umma tayi tana Kama hannunta, murya a tausashe tace, “Uncle d'inkine ya d'akkoki Jiddah”.
     Murmushi ta d'anyi amma batace komaiba. Ana cikin haka sukaji sallamar Uncle yahya, atake jikin Jiddah yafara rawa tashiga matsawa baya.
     Uncle yahya yad'an murmushi kawai, cikin k'arfin hali yace, “Haba jiddodona ninefa, ko baki ganeniba?”.
       “Na ganeka Uncle”. ‘tai maganar murya a raunane tana cigaba da matsawa’.
       “Kinga yi hak'uri karkiyi kuka, amma fad'amin tsorona kikeji?”.
       Fashewa tai da kuka jikinta Na kuma tsananta rawa, “Uncle kayi hak'uri, wlhy banason ganin maza ko muryarsu banason jiiiiii!!!!!!!”. ‘Ta k'are magar cikin razananniyar tsawar data gigitasu’.
      Dole sai fita Uncle yahya yayi, yana fita kuma tafara dai-daita, a hankali saita dawo normal, jikin Zarah dake kusa da ita tafad'a tana kuka, suma su Zarah kukan sukeyi.
         A waje Uncle yahya da Umma suna magana ne akan ya Kira Abba ya sanar masa halinda Jiddah take ciki amma yace wai k'arya takeyi, dan haka shikuma ya faffad'a masa magana akan wlhy koda zasuyi yak'i Jiddah bazata koma gidan Alhaji garba ba, dolene ya saketa koyanaso ko bayaso.
      “Kamin dai-dai Uncle d'insu, wlhy a shirye nake da igiyar aurena ta tsinke akan komawar Jiddah gidancan, acikin sati uku kacal an maidata haka inaga nan gaba kuma?”.
      “Ki kwantar da hankalinki Maman Nafisa, nima ina dai-dai dashi ai, dan yace gobe zai dawo daga legas d'in”.
        “ALLAH ya kawoshi lafiya”. Cewar Umma a zafafe.

*_HARGITSI_*.

           Dolene mukira wannan tsakani da suna hargitsi, dan kuwa komai ya rikice, ga jikin Jiddah da yak'i dad'i, dan koda maganar Abba daya dawo washe garin dawowarta gidan Alhaji Garba taji to zata fara fisge-fisge da k'ara.
     Tsakanin Umma da Abba da Uncle yahya kuwa anyi barank'an-barank'an, dan Abba yaje ya duba Alhaji Garba a asibiti ya shirys masa k'arya da gaskiya akan Jiddah, yayinda hajia deluwa ke tunzurashi a gefe.
     Umma da Uncle yahya sun dage sai Alhaji Garba ya saki Jiddah. Alhaji garba ya kafe akan wlhy bazai ta6a sakintaba. Abba ma yadage sai Jiddah ta koma, dan shima akwai nasa dalilin Mai tada hankaki.
     Lamari yayi tsamari sosai, yau kusan kwanaki takwas da Fara badak'alar amma babu wani sassauci, hakanne ya saka Uncle yahya shigar da Alhaji Garba kotu domin raba auren Jiddah.
      Alhaji Garba yasamu sauk'i harya koma gida, dan haka gidansa akakai masa sammaci.
     Sosai hajia dealuwa ke zubar masa tijara akan ya Saki Jiddah mana, aiba girmansa bane ace yashiga kotu akan wannan banzan maganar.
     A zafafe yace, “ke Yahanasu, nifa ba auren wannan yarinyar bane matsalata, kud'ina da Ubanta yaci sune matsalata, kinsan nawa ya amsa a wajena kuwa? To naira miliyan Hamsin, ya amsa yabiya banki bashin da yaci, bisaga wannan ne yabani aurenta akan zai biyani rabi nanda shekara biyu, nikuma nace Na hafe masa rabi, dan haka saiya biyani kud'ina Zan saketa”.
         “Humm wlhy Alhaji ban ta6a sanin Kai mayen Mata baneba sai yau, akan mace ka d'auki wannan uwar dukiyar ka bashi? To bara Na fad'a maka, rashin sakin y'arsa ba shine mafitaba, dan dama can bason Y'ar yakeba, kobakaga damuwarsama ta dawoba a kullu? To ka saketa, nikuma Zan baka dabarar da zakayi kud'inka su fito cikin sauk'i a hannun Alhaji zakari yaro”.
     Jimmm Alhaji Garba yay yana kallonta, saikuma ya gyara xamansa yana fad'in “kamar kuma Na yarda da shawararki, ke nama yarda, samomin takarda da alk'alami”.
    Da hanzari hajia deluwa taje ta d'akko masa, dandanan ya zana Saki a takarda yabata yace tabama driver yakaima Alhaji Zakari.

*_SANADI_*
    
      Wannan shine sanadin rabuwar Alhaji Garba da Jiddah.
    Su Umma Na tsakar gida zazzaune, Zarah da Walida na wanke-wanke, Umma Na girki yayinda Jiddah ke kwance akan tabarma tayi shiru tana tunanin rayuwa da yanda al'amura suka sauya cikin wata biyu kacal. Sallamar Abba ce ta sanyata mik'ewa zumbur, da gudu ta afka d'aki tajecan karshen gini ta 6uya. Yanzu haka take, ko Uncle yahya ne ya shigo saita gudu ta 6uya, addu'oin da malam alfah ke bata tanasha yasa aka samu rangwame tabar yawan k'ara, amma idan Namiji yacika kusantota tana wannan fisge-fisgen harma ta suma.
         Cikin hargowa Abba ya jefama Umma takardar sakin Jiddah yana fad'in “Hankalinki ya kwanta yagana, kin kashema Jiddah aure, saiki zuba ruwa a k'asa kisha kinji ko, itakuma daga yau dan Ubanta saita dainama mutane haukan k'arya, kuma wlhy kinji Na rantse Na zare hannuna daga duk wani lamarin Jiddah, ta nemi wani uban baniba d........”
       Cikin katseshi Umma ta d'aga masa hannu ”Ya Isa haka Alhaji, dama baka a lamarinsu, dankuma ka fita yanzu bazanji komaiba, amma ina Mai tabbatar maka, ko watan watarana katina wannan maganar taka, sannan ka fad'ama Alhaji Garba, ina godiya matuk'a ni yagana akan sakarmin yarinya da yayi, kaikuma ka gane TUBALIN TOKA baya k'arko, duk abinda ba'a ginashi domin ALLAH ba to baya k'arko, abinda kuma akaima yarinyata nabar wannan ga ALLAH, shine zai Mata hisabi da koma wanene”.
     Umma nagama fad'a tai shigewarta tabi Jiddah, sukam su Walida dama tuni sun shige ai, daga d'aki suke jiyo abinda ke faruwa.
    Kwafa kawai Abba yay batareda ya iya cewa k'alaba, sai yanaji a ransa badan ALLAH ya Isar da mamansa taimasa akan yagana ba da wlhy yau itama Saki Uku zai Mata, to amma anriga an saka masa Kara da hakan.

      Duk wani masoyin Jiddah ya tayata farin ciki da wannan Saki, washe Gari da aunty Nafisa tazo itakam harda rawarta tasha su Zarah na tayata, Jiddah da Umma sai dariya suke musu.
    Tuni maganar sakin Jiddah ya karad'e dangi, kowa yaji dalili saiya tayata murna da hakan, tareda nemawa abba shiriya wajen ubangiji.
     A yanzu matsalar Jiddah ta tsoron mazace kawai matsalarsu, dan har yanzu bata shan inuwa da koda sautin muryar mazane, iya kokari kuma ana maganin akan warware sihirin jikinta, amma lamarin ba'a cewa komai sai sambarka.
     Abba dai ko sisinsa babu balle tambayar Yaya Jiddah hasalima yabar zuwa gidan gaba d'aya, shi a dole fushi yake, sannan ciwon Jiddah yace k'aryane. Kokad'an hakan baya damun Umma, dan a cewarta wannan matsalarsace.
       Alhamdllh jikin jiddah yad'an murmure daga ramar da tayi, saidai kulum tana gida bata fita ko ina, zuciyarta nason komawa makaranta, amma tanajin tsoron yanda zata fiti taci Karo da abokan gabarta maza.
      Ahankali kuma farin cikin gidansu ya dawo, sunkoma tamkar da, saima ka d'auka wani tashin hankali bai ta6a ziyartarsuba a kwanakin baya, yanzu fatansu kawai ALLAH yabama Jiddah lafiya ta koma normal.
       
*_A KWANA A TASHI_*

      babu wahala wajen Ubangiji, yau ga Jiddah tagama iddah, har wani d'an walima su Zarah da aunty Nafisa suka shirya Na murnar Jiddah tarabu da alak'ak'ai.
     Umma dai dariya kawai suke bata, Uncle yahya harda taya 6era 6ari kuwa shida maman Sadiq.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

           “Mustafa yanzu ya kake ganin zamuyi akan maganar wadda zataje musabak'arnan ta Saudia tunda yanzu babu yarinyarnan? Kagafa wasu kwanakine kawai ya rage Wanda bazasu gaza ashirin da biyu ba, a ko yaushe kuma za'a iya buk'atar ganinta ma”.
       “Wlhy malam nima abun Na damuna, shiyyasa nake kuma takaicin rashin Jiddah, amma yanzu inaga zamu samu wata d'alibar mukuma horata kawai”.
      “Eh to shawararka tayi sosai, ALLAH yasa mu dace”.
       Ameen Malam mustafa da Sheikh Aliyu dake zaune yana saurarensu suka fad'a.
    Daga nan wani zancen suka d'akko, mafi yawa akan gudunmawar da Jiddah tabama makarantarne Na ciwo musabuk'ok'i kashi-kashi da tayi. Shidai Aliyu na zaune yana nazarin wani littafi yana saurarensu, amma k'ala bai tofa ba, dan ba huruminsa baneba. Sai dai k'ok'arin yarinyar ya burgeshi kamar yanda su malam suke fad'a dukda bai santaba.
   

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

         Yau  Su Zarah duk suna makaranta, gashi Umma nason yin aike shago, Dauda kuma baikai ga zuwaba, rasa yanda zatayi tai, ta lek'a kozata samu yaro amma layin fetal yara duk suna makaranta. Dawowa tayi ta kalli Jiddah daketa hidimar d'aura abincin rana.
      “Jiddah koda kanki zaki fita dai siyen yis d'innan, kinga nariga nafara kwa6a fulawar alkubus d'inan, ki lek'a konan shagon sama'ilane, idan kuma kingamu da wani yaron saiki bashi ya sayo”.
      “To Umma kawo naje d'in”. ‘Jiddah tafad'a tana d'auraye hannunta data ta6a gawayi'. Tana gamawa ta kar6a naira d'arin hannun Umma taja hijjab a igiya ta fita bayan ta d'aura Nik'ab tamkar yanda ta Saba.
      Dukda tsoron dake addabarta da tsumar da jikinta yafara haka ta k'arasa shagon sama'ila, da k'yar ta iya mik'a masa kud'in tana fad'a masa abinda takeso, lokacin daya mik'o mata hannunsa yad'an ta6a Nata kad'an sai kawai tai baya jiki Na rawa, bai ankaraba kawai yaga ta zuba da gudu tabarsa rik'e da yis.
     Mamaki da al'ajab suka kamashi, dan haka yabiyota yana kwala Mata Kira, amma ina gudu take iya karfinta.
     Umma Na gyara mata wutar sai kawai gani tai ta shigo a guje, tana tambayarta lafiya amma bata sauraretaba ta afka d'aki. Umma na shirin binta Sama'ila mai shago ya rabga sallama daga soro.
     Wata razananninayar k'ara jiddah ta fasa tana toshe kunnenta. Tuni hankalin Umma ya tashi, dan ita tashagala Jiddah ta samu sauk'i sosai, dan tadad'e batai irin wannan firgitar mai karfi hakaba.
        Jikin Umma na rawa ta lek'a dantaga wake sallama, ganin sama'ila saitake tambayarsa komi yafaru da jiddah?, iya abinda ya sani ya sanar mata, sannan yabata yis d'in ya juya.
     Dole Umma ta kira Uncle yahya a waya, babu shiri yabaro kasuwa, tsayawa yay suka taho da malam alfah.
     Tunda suka shigo gidan malam Alfah yaga halin da Jiddah take ya girgiza Kai kawai.
       “yahaya inaga yakamata mukai Jiddah wani waje, bak'in aljanin da suka had'ata dashi yanada matuk'ar naci, tunda munyi namu ba'asamu warakaba yakamata mu gwada wani wajen kuma nakega”.
       “Malam duk yanda kace haka za'ayi, mu mun aminta dakai d'ari bisa d'ari, Kai Ubane a garemu, ko bama kusa zaka iya zartar da komai akan jiddah”.
       “Nagode da wannan karamci, yanzu ita mahaifiyar tata saitai k'ok'arin fidda mana ita zuwa mota”.
      Da k'yar Umma ta iya fidda Jiddah, daga k'arshema saida taimakon Uncle yahya, aiko Jiddah sank'ame musuma tayi amota.
         Tafiya sukayi sukabar Umma a gida............✍🏻




*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[20]_*

   
..............Tunda suka tafi Uncle yahya keta tofama Jiddah addu'a saboda fisge-fisgen da takeyi da wata Y'ar siririyar k'ara maikama da muryarta ta dishe. a cikin wannan halin malam Alfah ya faka motarsa k'ofar wata cibiyar magungunan musulunci. Shikad'ai ya fita yana fad'ama Uncle yahya yana zuwa.
    Kai kawai Uncle yahya ya iya d'aga masa, idonsa yay jajir yana rik'e da Jiddah daketa fiffisgewa har yanzun.
        Bud'e motar da a kai ya saka Uncle yahya d'ago kansa ya kalli malam Alfah dake k'ok'arin zama a mazauninsa.
      “Baba Malam miya faru?”.
     “An samu matsalane yahaya, malam tajudden baya nan, amma anmana kwatancen wani wajen a Gadon k'aya, dukda shi bawai yana bada magunguna bane, yana taimakawa dai idan yaga abun ya tsananta ne, sai dai na rok'i alfarmar d'aya daga cikin almajiran malam tajudden wani ya rakamu, ga shinan zuwa”.
     “To baba malam muje cand'in, ALLAH ya saka da alkairi”.
     Gosulon da suka fuskanta a hanya yahanasu damar isowa da wuri, Ana sallar la'asar suka iso dai-dai masallacin bisa jagorancin kwatancen Zubairu Almajirin malam tajudden.
      Malam Alfan ne kawai da zubairu suka fito, massalacine babba dake jingine da wani babban gida shima, anguwar tayi tsitt sai sautin karatun salla dake tashi cikin wata sassanyar murya. Alwala su malam Alfah sukayi suma suka shiga sallar, amma Uncle yahaya yana wajen Jiddah dan ba'a barta ita kaid'aiba..
     Bayan an idar mutane suka fara fitowa d'ai-d'ai, sai da kowa ya fito, aka bar malam kawai da wasu tsirarun mutane a masallacin, su malam alfah suka k'arasa ga malam dake shirin fita shima.
        Cikin mutunta juna malam da malam alfah suka gaisa, sosai malam zai iya girmar malam alfah a shekaru, shima zubairu ya gaisheshi kafin ya masa bayanin abinda ya kawosu.
    Cikin jinjina kai malan ya amsa sannan suka fito.
        Ana k'ok'arin fiddo Jiddah amota za'a shiga da ita ciki malam mustafa ya iso wajen, da mamaki yake kallon Uncle yahaya dake share zufa daya had'a saboda rik'e Jiddah.
      “Uh uhm malam yahaya kaine yau a anguwarmu? Injidai lafiya?”.
      Juyowa Uncle yahaya yayi damson ganin Mai maganar, shima cikin mamaki yace, “A malam Mustafa dama nan anguwar kake? Amma Alhamdllh nayi farin cikin ganinka, wlhy Jiddah ce babu lafiya muka kawota”.
         “ALLAH Sarki, jiddah dai dana sani? Wadda akai biki watannin baya?”.
       “Wlhy kuwa malam Mustafa itace”.
     “Subahanallahi, ina mijin nata? mike faruwa haka?”.
     Murmushin takaici Uncle yahaya yayi, yana gyara tsaiwarsa, “Malam Mustafa labarin maid'an tsawone, amma bara mushiga da ita dan malam Na jiranmu”.
       “To ba laifi, amma inaga ad'an matsar da motar gaba saboda idanun jama'a”.
    Shawarar malam mustafa sukabi, aka matsar da motar kusada k'ofa sosai ta yanda ko an fito da Jiddah babu mai ganinta.

              Tunda Aka shigo da Jiddah cikin falon malam Abdul-ra'uff maina take wata k'ara da jijjiga da fisge-fisgen guduwa.
        Tausayin Jiddah da tunanin yaushe tagamu da wannan lalurar ya ishi malam mustafa. Sai dai bashida zarafin neman k'arin bayani a halin da ake yanzu......
     Maganar Malam Abdul-ra'uff ta katse masa tunani ya maida hankalinsa gareshi.
       Kallon Uncle yahaya dake rik'e da Jiddah malam Abdul-ra'uff yayi yana fad'in “kaga inkaso sakarta kawai”.
        “Malam da an saketa guduwa zatayi”. ‘Uncle yahaya yafad'a tamkar zai saka ihu’.
     Murmushi malam Abdul'ra'uff yayi yana gyara zamansa, “Karka damu sakarta, babu inda zataje insha ALLAH”,
     Sakinta Uncle yahaya yayi ya matsa gefe, yayinda Jiddah keta bige-bige tana wani irin gunji, ga uwar zufa da takeyi tamkar fanka bata aiki a falon.
         “mustafa jonamin abin turarennan na gefenka”.
      “To Malam”. Malam mustafa ya amsa cike da girmamawa..
      Tunda Malam Abdul-ra'uff yafara zuba garin magani Na turare hayak'i ya fara tashi sai bige-bigen Jiddah ya k'aru, hakama gunjin da takeyi, sai dai kuma tak'i magana, kamar yanda malam yake buk'ata. Kusan mintuna goma sha biyar ana Abu d'aya lamari Na Neman cin tura, gadai alamun shaid'anin dake tare da ita yana jigatuwa, amma taurinkai ya hana yayi magana.
      Malam ya tsaya daga tofama Jiddah Addu'a mik'ewa yay ya fito yana fad'in su Uncle yahaya su biyosa.
        A zaurensa bisa rukunin kujerun ya zauna yana kallon su Uncle yahaya cikin yarce gumi.
         “Wato maganar gaskiya yarinyarnan akwai sihiri mai k'arfi a jikinta, bisa alamu kuma anyi ne cikeda makirci mai wahalar fassara, dan shaid'anin dake jikinta ma kunga yak'i nuna kansa, alhalin kuma alamu sun nuna yana jigata da addu'oin dake ratsashi, shin kozaku bani wani haske akan al'amarin?”.
      Kafin Uncle yahaya yay magana malam mustafa ya sanarma malama wacece Jiddah. Sosai malam Abdul-ra'uff yay mamaki, danshi ko kad'an bai ganetaba, dandanan hankalinsa Yakuma tashi, ya shiga tambayar Uncle yahaya Yaya akai haka? Miya faru da Jiddah bayan gaba d'aya dayin aurenta bata wuce watanni biyarba.
        Kan Uncle yahaya a duk'e yana tsiyayar da hawaye yayma su Malam bayani dalla-dalla akan auren Jiddah da sanadinsa harma k'arewarsa sanadin matsalar da ayanzu Jiddah ke ciki.
       Ran Malam Abdul-ra'uff ya6aci sosai, ga tsananin tausayin Jiddah da k'aunarta ke k'ara ratsashi, nawa yarinyar take da mahaifinta zai za6i sakata a gararin rayuwa irin wannan saboda cikar burinsa? Lallai alokacin dayasan irin auren da za'ama Jiddah kenan koda nuna k'arfine dasai ya aurama Aliyu ita. Amma babu komai, ya d'auki hakan a matsarin *RUBUTACCIYAR K'ADDARA* a gareta, babu wani mahaluki daya isa gogeta kuma...........
             Malam nacikin tattaunawa da zuciyarsa sukaji sassanyar Muryar Sheikh Aliyu cikin sallama. Gaba d'ayansu amsa masa sukayi suna d'agowa da kallonsa. Sanye yake cikin shadda boyal ruwan k'asa mai haske, sai hularsa itama ruwan k'asa amma tad'anyi duhu kad'an, hanunsa rik'e da waya da key d'in mota daya saya tun bayan aurensa da Maimunatu. Kallo d'aya zakai masa ka fahimci hankalinsa a kwance yake, yad'anyi k'iba kuma yay fayau dashi alamun akwai kwanciyar hankali da nutsuwa a duniyarsa.
    'Daya bayan d'aya ya basu hannu suka gaisa bayan ya gaida malam dake kallonsa tamkar zaiga maganin warakar Jiddah a jikinsa.
    Kallon malam Mustafa yay yana fad'in “Ashe kana nan?”.
       “Eh wlhy, tun bayan sallar la'asar nazo dama Na sanarma malam yarinyar da muka za6a”.
       “Masha ALLAH, to bara na shiga cikin gida Na gaidasu, idan kun gama Na dawo”.
     Harya mik'e malam ya dakatar dashi ta hanyar kiran sunansa.
      “Aliyu!”.
“Na'am baba” ya amsa yana maida kallonsa garesa.
      “Ku shiga kaida mustafa Falona akwai yarinya Mai lalura ka dubamin ita”.
      A sanyaye yace, “To Baba”.
         Malam Mustafa na gaba shi yana baya suka shiga, Jiddah Na kwance tayi ligif kamar matacciya, dan tunda su malam suka fita saita bar abinda takeyi ta nutsu, dama matsalarta maza ne kuma sun fita, amma su Malam Mustafa na shiga tahau fisge-fisge da kwalla k'arar datafi wadda takeyi a d'azun.
     Hannu Aliyu yasa ya toshe kunnensa yana lumshe idanu danjin k'arar har cikin kwanyar kansa.
      Ganin zata fice malam Mustafa yay saurin zungurinsa, idanunsa ya bud'e yana janye hannunsa daga kunnen, taku d'aya ya fisgo hijjabinta ya maidota baya ta fad'in yaraf tana wata irin jijjiga.
     Tuni idonsa yayi jajur da 6acin rai (karku manta tunkan Aliyu yaje saudia yanada wajen saida magungunan musulinci dama), kallon Jiddah daketa faman takurewa a jikin bango tana k'yarma yayi, sai duk'unk'une fuskarta take a cikin hijjab. Yaja kujera ta roba dake gefe ya zauna d'an nesa da ita. Nuni yayma malam mustafa dake tsaye yana kallonsu da yabashi ruwa.
        Malam mustafa ya mik'a masa ruwan daya d'ebo a Kofi, kar6a yay yafara tofa addu'a a ciki yana kallon Jiddah dahar yanzu take mutsu-mutsu, sai dai takasa yin k'arar sosai, dan ta k'udundune kanta a hijjab.
      Ruwan Addu'ar daya watsa mata a jikine ya sakata zabura tana fasa wani kuka, bai sauraretaba ya cigaba, sai kuma mamuk'e bango take tamkar xata koma cikinsa.
     Ransa a 6ace, amma hakan bai hana muryarsa fita da sanyiba yace, “Kai wane irin shaid'anine Mai taurin kai? Kana azabtuwa amma bazaka nunaba?”.
     Shiru Jiddah ko nace aljani bai maganaba, k'yalesa Aliyu yayi, ya d'auki Qur'an malam Mustafa ma haka suka Fara karatu cikin suratul bak'ara.
    Karkarwa jikin jiddah ya cigaba dayi tana wata irin zufa maiban mamaki. “Babu inda zanje, bazan fitaba, nace bazan fitaba, ni kubar k'onani bazan fitaba.......” wad'annan sune kalamun dake fitowa a bakin Jiddah tana kuka. Hakan kuma baisa su Aliyu dakatawaba, kusan mintuna talatin suna janyo ayoyin Ubangiji cikin surori daban-daban, sosai Jiddah ta jigata matuk'a, muryartama ko fita batayi, daga k'arshe kuma tama kwanta k'asa tamkar wata matacciya, cigaba da karatu su Aliyu sukayi, sai bayan kamar mintuna goma suka dakata saboda jin numfashin Jiddah ya daidaita.
       Sassanyar ajiyar zuciya Sheikh Aly ya sauke yana rufe Qur'anin, ya kalli malam mustafa shima dake rufe nasa, “Mustafa wacece wannan d'in wai? Minene kuma matsalarta?”.
      Nisawa malam mustafa yayi fuskarsa da tsantsar damuwa yake fad'ama Aliyu komai game da Jiddah, harma yunk'urin had'ashi aure da malam yay da ita tun farko, amma suka iske mahaifinta yamata miji”.
       Shiru kawai Aliyu yayi yana kallon wani waje daban, shi mutumne mai tsananin tausayi da shiga damuwa akan damuwar wani, tuni hawaye harsun cika masa idanu, ya zari handkerchief daga aljihunsa yay saurin tsanesu. Batare daya yima malam mustafa maganaba yatashi ya fice.
       Inda su malam suke zaune yad'an kalla kafin ya kauda idonsa gefe dan kar malam ya fahimci yayi kuka, “Baba ina zuwa su jirani”.
       “To saika dawo Ali” ‘malam yafad'a cikin murmushi’.
    Yana fita malam Mustafa ya fito, kallonsa malam yay “Mustafa miya farune?”.
       “Malam tasamu barcine, inaga zai had'o magungunane”.
     “To Alhamdllh, ALLAH kai mana maganin abinda yafi k'arfinmu, harma wanda muke gani munfi karfinsa”.
     Amin malam, suka fad'a gaba d'aya falon harsu Uncle.
     cikin zolaya malam yakuma kallon mustafa yana cewa, “Halan abokinka yauma halin ya ta6a?”.
     Malam mustafa yay murmushi yana bama malam amsa, “Malam ai wannan wajib ne ga Aliyu, sai dai in Abu bai raunana zuciyarsa baneba”.
      “To ALLAH ya kiyaye, Yaro ya maida kansa kamar wani mace, Abu kad'an yafara zubda hawaye”.
    Duk murmusawa sukayi har su Uncle yahaya dake zaune suna saurarensu. Sosai Uncle yahaya yakumajin k'aunar Aliyu da samun nutsuwa akan maganar da suka gama da malam yanzu.

*********

  Kusan mintuna talatin da fitar Sheikh Ali saigashi ya dawo d'auke da farar Leda madaidaiciya, zama yay yana bud'e ledar, dalla-dalla yayma Uncle yahaya bayanin yanda Jiddah zatayi amfani da magungunan, kafin ya d'ora da fad'in, “Ko kunada damar tura wani can gidan data baro yad'an mana wani bincike? Dan ina zargin kamar akwai abinda aka ajiye ko aka binne dake saka aljanin koda yatafi yake dawowa jikinta, abinda na lura dashi kuma kamar shine ke tsoratata inhar tasamu kusanci da namiji, alamun shine tushen sihirin jikinta, sai kuma mun samu rusa wancan kullin nasu da izinin ALLAH koda komai zai dai-daita, sadai insha ALLAH indai tacigaba da amfani da wad'annan magungunan sannan ta tsare yin azkar da salla akan lokaci, ta kiyaye yawo babu d'ankwali da yawo babu takalmi a tsakar gida, ta kiyaye sauraren wak'a ko shiga bayi batareda tayi addu'a ba, da yawaita kusanta kanta da Qur'ani, to muna fatan dacewa wajen samun sauk'i insha ALLAH”.
       Alhmdllh kowa ya shiga maimaitawa da fatan dacewa. Uncle yahaya ya d'ora da fad'in ”Zamuga yanda za'ayi a bincika d'in insha ALLAH, mungode sosai ALLAH yak'ara girma da hak'urin taimakon bayin ALLAH”.. 
      Amin duk suka amsa dashi, Aliyu daya amsa a la66ansa ya mik'e yana fad'in “Zaku iya tafiya da ita”.
      Sun amsa da to, shikuma yay yunk'urin shigewa cikin gida.
       Da sauri Uncle yahaya yace, “Malam bakai maganar kud'i ba ai”.
      Murmushi Aliyu yayi, batare daya juyoba yace, “ALLAH yabata lafiya” kawai ya ida shigewa.
     Uncle yahaya ya maido kallonsa ga Malam zaiyi magana. Murmushi malam yayi shima, “Malam yahaya wane maganar kud'i kuma? Tunda kaji yace haka bazai amsaba, kuma ai yima kainema, ALLAH yabata lafiya dai mu shine fatanmu”.
      “Amin malam, ALLAH ya saka da alkairi, ya albarkaci zuri'a, ALLAH ya k'ara girma”.
      Kowa ya amsa da amin.

     Uncle yahaya yakai Jiddah dabatasan mi akeba mota, har k'ofar gidan malam da Malam Mustafa suka rakosu, suna niyyar tafiya Aliyu ya fito, hannu kawai ya d'aga musu ya wuce domin haramar d'aura alwalar magriba dake gabatowa.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

        Su Umma na zaune zugum-zugum itadasu walida da Maman Sadiq da Aunty Nafisa wadda tazo sake duba jikin Jiddah ta iske kuma basanan saita tsaya.
     Alkubus d'inma da Jiddah ke k'ok'arin d'aurawa sai Aunty Nafisar ce ta k'arasa, dan Umma ma takasa ta6uka komai tunda aka fita da Jiddah.
      Su Zarah kam tunda suka dawo makaranta sukaji halinda Y'ar uwarsu ke ciki sai suka hau kuka, alkubus d'inma tunda aka gamashi babu Wanda yako kallesa.
    Jin tsayuwar mota ya sakasu mik'ewa a tare suka lek'a.
     Sune suka shigo da jiddah wadda take barci har yanzu. Uncle yahaya ya biyo bayansu da ledar maganin bayan yayima malam alfah godiya sosai.
     Shima yana ajiye ledar fita yay massalaci, dan ankira sallar magriba.
     Jiddah kam d'akin Umma aka kaita aka kwantar da ita, suma suka fito dan suyi haramar sallar magriba, koba komai hankalinsu yad'an kwanta..............✍🏻

*_🤭jiya kwace kodai Abba zakarine ya biya bashin da ake binsa dani😂😝, wani uzirine ya tasomin batareda Na shirya masaba😄, messages d'in PC ma sai yanzu zanje Na amsa mukusu tun kusan Na kwana uku⛹‍♀, wad'anda suka turo kumin afuwa yanzu Zan amsa insha ALLAH.🤐_*

Ina fata duk kuna lafiya?.





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu._*😭🙏🏻
*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[21➖22]_*

   
..............Bayan Uncle yahaya yadawo daga salla suka zauna tattauna maganar Jiddah, bayani yay musu akan dukkan abinda ya faru, kafin ya d'ora da batun malam Aliyu na bincike a gidan Alhaji Garba.
    Kowa ya jinjina maganar, domin wannan abune mai matuk'ar wahala agaresu, dama can babu wata alak'ar dangantaka a tsakaninsu, gakuma wannan batun na Jiddah daya gitta, Abba kam sunsan bama zai basu had'in kaiba, k'ilama idan sun masa bayani ya rusa komai, Hindu kam da ace abokiyar zamace ta kwarai dasai ta taimakesu tunda ita gidan zuwantane.
     Sunta tattauna mafita amma basu samuba, duk hanyar da suka k'ulla saisuga bazata 6illeba. Dole dai suka ajiye zancen akan sai sunyi tunani.
        Sund'an samu kowa yaci abinci, amma zukatansu dank'are da neman mafita suke.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

           Tunda suka idar da Sallar Magriba sai yayma malam sallama yanufi gida, dan yasan d'alibai nacan na jiransa, fatansa sallar isha'i ta riskesa acan.
      Kamar yanda yay fata kam saiya dace, duk da bawani nisabane tsakanin gidansa dana malam d'in, ya iske ana kiran sallar isha'i.
      Alwala ya sake ya shiga masallaci. Bayan an idar sukai zaman karatu. Bai samu shiga gidaba sai kusan goma saura.
        Cikin Sassanyar muryarsa yay sallama, Maimuna dake kwance cikin kujera tana kallon Sunna tv ta amsa tana tashi zaune, tsaf take cikin kwalliya tanata k'amshi, murmushi suka sakarma juna, yayinda Aliyu ya bud'e mata hannayensa alamar tazo.
       Ahankali tataso ta shige jikinsa tana fad'in “Nayi kewarka Annur”.
      “Nima haka habibati”. Malam Aliyu yafad'a a hankali cikin kunnenta.
    Fuskarta d'auke da murmushi har yanzu ta d'ago ta kallesa, goshinta ya sumbata da la66anta, kafin a hankali yace, “Mikika tanadarmin sarauniya?”.
     Cikin kashe ido da murya tace, “Komaima Na tanada maka harda abinda malam ya hana fad'a”.
      Dariya sukayi a tare, Aliyu yaja hannunta yana fad'in “Zomuje ki fad'amin, ai bazan fad'ama malam kin fad'aba”.
         “Yaya Ali kacika wayo wlhy”.
      “Aunty Maimoon kin cika wayo kema al”. ‘Aliyu  yay mahanar suna ida shigewa’.
                 Da taimakonta yay wanka sannan suka dawo falon, kullum dare fruits sune abincin Aliyu, gab da zai kwanta kuma yasha had'ad'd'en shayi irin Na larabawa Kofi d'aya, dan haka Maimunatu take k'ok'arin ganin tamusu nutsatstsan yanka.
        Sosai ya maida hankalinsa ga Tafseer d'in da akeyi a Sunnah tv Wanda ya tarar Maimuna na kallo, harta gama ajiye dukkan abinda zai buk'ata hankalinsa naga tv.
         “Yaya Aliyu”. ‘Maimuna tafad'a ashagwa6e’.
       Juyowa yay ya kalleta batare da ya amsaba, da ido ta nuna masa kayan gabansa. Ajiyar zuciya yad'an sauke kafin ya sauka k'asa saman kafet ya zauna, itama zama tayi, sunashan kayan marmarinsu suna kallon tafseer, lokaci-lokaci sukan jefi junansu da murmushi dakuma magana idan ta kama.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
  
            Jiddah bata farkaba sai kusan k'arfe goma, lokacin Mijin Aunty Nafisa yazo ya d'auketa, su Uncle yahaya ma suna shirin tafiya, amma farkawar tata saita dakatar dasu.
      Alhmdllh normal ta farka, dukda tanata ra6e-ra6e saboda ganin Uncle yahaya.
     Zarah ce data had'a Mata ruwan wanka ta taimaka Mata zuwa ban d'aki, bayan ta shiga ta dawo waje zaman jiranta, bata wani dad'eba ta fito ta d'aura alwala sannan ta koma d'aki, bata shafa maiba sai kayan da Walida ta ajiye mata ta canja tahau ramuwar sallolin da bata samu yiba.
         Su Uncle yahaya basubar gidanba saida sukaga taci abinci da fara amfani da wasu magungunan ta koma ta kwanta saboda jikinta duk babu k'wari.
     Sallama sukaima su Umma suka wuce gida.

★★★

      Washe gari normal Jiddah ta tashi, wandama bai saniba bazaice tashiga wani haliba jiya, koda Uncle yahaya yazo dubata d'aki ta shige ta 6uya, bai damuba shidai, dan yasan bawai yin kanta baneba. Sallama yay musu ya wuce kasuwa.
      Da d'an k'arfin gwiwa su Zarama sukai shirin makaranta suka tafi.
 
         Tundaga wannan lokaci abubuwa sukaima Jiddah sassauci, dukda har yanzu batasan namiji a kusa da ita, amma bata firgita ko fita hayyacinta danta samu kusanci dasu, magani kuma da ruwan addu'oi daya k'are ake aiko mata wani daga gidan malam, malam mustafa da kansa yazo yaymata maganar komawa makaranta saboda sunason sudai taje Saudia d'in, dan tunda sukaji batada aure sai suka ajiye batun waccen da suka za6a suka maida burunsu akan Jiddahn.
     Y'an ajinsu sunyi farin cikin dawowarta, musamman ma Madina.
      Kuma himma sukai wajen Trining d'in Jiddah yanda zata kuma samun gogewar ilimi sosai dabin k'a'idojin gasar, kuma tana k'ok'arin maida hankalinta sosai, dukda duk lokacin da malami zai shigo musu karatu Jiddah batada sauran nutsuwa harya fice, amma haka take dakewa da yawan Addu'ar samun kwarin gwiwa harya fice.
     Duk dokokin da Aliyu yace ta kiyaye Alhmdllh tana iyakar k'ok'arinta, dama can ita bamai wasa da irin abubuwan nan baceba, zaman sihiri jikinta kawai k'addarace daga ubangji Mai jarabtar Bawa aduk sanda yaso, akuma lokacin fayaso.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

       Shirye-shiryen tafiya gasarsu ya kankama, dukda duk wannan hidimar da akeyi Abba bai saniba, rabonshi da zuwa gidan kusan watanni hud'u kenan, kuma yana zaune a garin babu inda yaje.
      Ganin yarage saura kwana biyu su Jiddah su tafi Uncle yahaya yaje har gida ya sameshi da maganar.
       A harabar gidan ya iske su kalifa na ball, kallo d'aya sukai masa suka d'auke Kansu tareda cigaba da kwallonsu.
     Murmushi Uncle yahaya yayi kawai shi yana k'arasawa garesu da fad'in “yarana kuna lafiya?”.
        Cike da rashin kulawa suka  amsa suna cigaba da harkar gabansu. “To ALLAH ya k'yauta” uncle yahaya yafad'a yana kamo hannun kalifa domin tambayarsa. Amma sai yaron yay azamar janye hannunsa yana wani 6ata fuska. Uncle yahaya baice komaiba sai tambayarsu Abba nanan da yay. Muneer kawai ya amsa da eh, amma Hassan da Hussain da kalifa tunima sun koma kan hayaniya akan cin Ball.
       Haka Uncle yahaya ya k'arasa ciki yana tausayin yayansa akan wad'annan yaran marasa tarbiyya, acikinma Hajia Hindu yatsine-yatsine taita masa, tana shirin cewa Abba baya gida saigashi ya fito saboda jin muryar d'an uwansa.
       Zama yay suka gaisa  Uncle Yahaya ya fad'a masa abinda ya kawoshi.
     Kallonsa Abba yay rai a 6ace, “Yahaya kace min dama wannan shine dalilin dayasa kuka kashe Mata aure?”.
         Uncle yahaya yay murmushin takaici yana gyara zamansa. “Yaya ba wannan maganar bace ta kawoni please, nidai yanzu amincewarka kawai da addu'arka muke buk'ata”.
        “Yo inda amincewarsa ake buk'ata Aida tini amfad'a masa basaida lokaci ya k'ureba”. ‘Hajia Hindu tai maganar tana gatsine-gatsine’.
     Murtike fuska Uncle yahaya yayi yana watsa mata wata muguwar harara, “Kinji na sakoki a cikin zancena Maman kalifa? To ki Kama kanki wannan ba huruminki baneba, kibari idan mungama Na wuce saikiyi keda shi”.
    Harara ta watsa masa tabar falon tana jan tsaki. Shima Uncle yahaya tsakin yayi ya mik'e.
     Abba yace, “Ni wlhy ina mamakin yanda kokad'an kaida Hindu bakwa zama inuwa d'aya, nasan dai yagana ce kawai ke rura wutar k'iyayya a tsakaninku kullum tamkar kuna ganin hanjin juna”.
       Baki Uncle yahaya ya ta6e kawai, “Yaya nawuce ni”.

         Uncle yahaya bai sakebi takan Abba ba tundaga ranar har yau dasu Jiddah ke shirin tafiya k'asa mai tsarki, jirginsu zai tashi k'arfe tara Na darene.

★★★*

       “ALLAH Yaya Jiddah harna Fara kewarki tunma da rana”.
       Harara Zarah ta zubama Walida Mai maganar, ta d'auki kwandon wanke-wanke data gama tana nufar kicin, “To Uwar iya, kema kad'ai kike kewarta kenan?”.
     Dariya Umma da Jiddah dake zaune kan tabarma sukayi, Jiddah ta janye albasar datake yanka wadda zasuci awara tana fad'in “Oni Hauwa, wlhy Zarah yanzu kinzama jarababbiya, wannan harar da kike Mata ai saikisa ta rud'e ta tsulma cikin rijiyar”.
     Daga kicin Zarah tace, “Yo Yaya Jiddah abunne da haushi, inama laifin tace munfara kewarki, amma saita wani ware kanta”.
     “Kishi kike da autata kenan Zarah?”. ‘Cewar Umma tana dariya’.
       “Umma barta ai Zan rama wlhy”.
      Zarah da Jiddah suka sanya dariya, yayinda Walida ta kwa6e fuska tana dangwarar da gugan hannunta tadawo kusada Umma ta zauna tana kumbura baki.
        Jawota Umma tayi jikinta itama tan danne dariyarta dak'yar saboda baki da Walida ta kumburo. “Kinga auta barsu kinji, saina rama miki nima bazan bar saita kwanaba”.
     “Yauwa Ummana shiyasa nake sonki”.
     Ha6a Jiddah ta rik'e tana fad'in “To a'a mu tsintomu akai madam, wato Ummanki ma ke kad'ai”.
     Gwalo Walida tai musu, yayinda Zarah takai Mata dundu Umma ta tare. “ALLAH Zarah kika dokarmin yarinya saina rama mata”.
        Jiddah tace, “Umma harda fad'in ALLAH?”.
      “To tadaketa tagani”.
“Yaya Jiddah barsu, badai an waremu ba, yau kina tafiya gidan Uncle yahaya Zan koma nima”.
       “Haba dai y'ammatan Umma wasa muke muku”. ‘Umma da walida suka had'a baki wajen fad'a’.
     Dariya suka sanya suduka.

        Haka suka cigaba da hirarsu har bayan isha'i bayan sungama cin Awara, daga nan Jiddah tahau shiri dan Uncle yahaya yakura Umma yace ta shirya malam mustafa yace zaizo d'aukarsu.
      Karfe takwas da rabi kuwa sai gashi shida Uncle yahaya, alokacin kuma kuka yatashi a tsakanin su Jiddah, Umma ma dai tana dannewa ne kawai, suduka gidan sukai mata rakkiya har airport.
     Wannan dai shine Karon farko na zuwan Jiddah da ahalinta airport, dan haka sukaita zuba k'auyanci, Jiddah dai tanata kalle-kalle amma bata cewa komai sai dariya da take musu itada Uncle yahaya da malam mustafa.
          Saida kuma aka fara shelar matafiyan jirgin Saudia sannan jikinsu yay sanyi, su Zarah aka fara matse hawaye. Sunaji suna gani aka kira sunan Jiddah a bayan Na Uncle yahaya da malam mustafa. A d'arare ta shiga jirgin ga wani tsoro daketa kuma mamaye zuciyarta, Addu'a tafara karantowa a zuciyarta, indama ALLAH ya taimaketa kusada wata Mata malam mustafa ya nuna Mata ta zauna.
           Cikin k'ank'anin lokaci sabo ya shiga tsakanin Jiddah da Matar Mai yawan fara'a, da taimakonta Jiddah ta dake kewar y'an uwanta ta ragu Mata a zuciya.
           Ubangiji ya saukesu lafiya, inda Jirginsu ya sauka a Jidda, itadai Jiddah tanata tsarkake sunan ALLAH a zuciyarta, lallai duniya akwai abubuwan kallo, gaba d'aya saita koma cikakkiyar bak'auya zam, shi kansa Uncle yahaya sai tsarkake sunan ALLAH yakeyi, yau gashi sanadin d'iyar zumu yazo inda baiyi tunaniba (danshi baita6a zuwa makka ba) jiyay yana k'ara k'aunar Jiddah har k'asan ransa, wato zuminci babban abune da mutane ke wofantar dashi bisaga son zuciya, da mutane zasu nutsu su fahimci muhimman zuminci da sun rik'e, shidai babu abinda zai cema ALLAH sai godiya...............✍🏻




Kuyi maleji da wanga🤐🚶🏻‍♀
*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[23➖24]_*

..............Abinda yabama Jiddah mamaki ashe Matar da suka had'u a jirgi tafiyarsu d'aya, sai da suka shiga motar datazo d'aukarsu sannan Jiddah itama taga ta shiga.
     Cikin Murmushi matar tace, “Kinyi mamaki ko? Na 6oye mikine dama danna baki mamaki”.
     Fuskar juddah ma d'auke da murmushin take fad'in “Aiko aunty kinbani, nakuma gode”.
     Y'ar dariya sukayi, wadda tasaka su Malam mustafa kallonsu. Jiddah datun d'azun dauriya take da zamansu kusa da ita tai k'asa da kanta, tana karanto sunayen ALLAH domin Neman sassauci da k'arfin zuciya.
        “Kufa Mata inda kuke birgeni akwai saurin sabo”. ‘cewar malam mustafa idonsa akan matar’.
     Matar tai murmushi cikin wani salo Mai nuna tsantsar so da k'auna tace, “Shiyyasa kuma zumincinmu keda k'arko”.
     Jiddah dai dasu Uncle yahaya suna jinsu.
     A haka suka k'arasa Makkah.
     Sun isa wani k'ayataccen waje Wanda Jiddah ke k'autata zaton Hotel ne, dan yanada matuk'ar girma, Wanda ya d'akkosune yay musu rakkiya har ciki inda aka tanada musu masauki tunkan su Iso. Abun yak'ara birge Jiddah sosai.
      Itada matarnan d'akinsu d'aya, Uncle yahaya da malam Mustafa ma d'akinsu d'aya.
     Gaba d'aya Jiddah tama kasa cewa komai gameda had'uwar d'akin, sai kalle-kalle take. Matar tai murmushi tana kallonta “Dukda nima wannan ne zuwana Saudiyya na farko, na Lura kinfini k'auyanci k'anwata”.
     Hannu Jiddah ya saka tana rufe fuskarta dan taji kunya, a haka tace “Aunty abunne akwai k'ayatarwa, gaskiya mahaifar Manzon ALLAH ta had'u, duk iya hasashenka saidai kayi amma tabbatarwa saikazo ciki”.
       “Wannan gaskiyane k'anwata, ALLAH dai yasa mudace. Yanzu jeki fara shiga wanka dai”.
       “To aunty”.

Sosai Jiddah kejin dad'in kasancewa da Matar, dukda kasancewarta Y'ar gayu hakan baisa ta nuna ta fitaba, gashima ta girmeta, dan ko aunty Nafisarsu ma zata iya girma, amma aunty Zulai itama zata iya girmarta.
     “K'anwata Muna tare awanni masu yawa amma bamusan sunan junaba, ni sunana Siyama, Matar malaminku Mustafa”.
     Sosai Jiddah tad'an waro ido waje, “Lah Aunty dama ina tare da Matar malam ce? Amma kinada kirki wlhy”.
      Dariya sosai Siyama tayi (ina fata kun gane, k'anwar Aliyu) kafin tace, “Kanwata kinada abin dariya wlhy, k ya sunanki?”.
      “Sunana Jiddah Aunty”.
       “Masha ALLAH, ashema mamanace ni”.
     Murmushi Jiddah tai kawai batace komaiba.
      Kasancewar Siyama da Jiddah sai ya d'auke Mata kewar y'an uwanta da Ummanta, dukda k'asan zuciyarta Na begensu, dandanan suka Saki jiki da juna, harma hakan yabama Malam Mustafa da Uncle yahaya mamaki.
              
           Washe Gari Malam Mustafa da wasu manyan malamai y'an Najeriya suka zauna da Jiddah, abin yabata mamaki dan tazatafa sukad'aine sukazo, Ashe harda malamin nan data ta6a gani a taron k'arama juna sani Na Abuja (Malam Abdul-ra'uff), tsuma jikinta yaytayi ganinsu duk maza a wajen, amma haka ta dake tana karanto duk addu'ar datazo gareta, sauk'intama d'an nesa dasu ta zauna, dukda AC dake wajen sai zufa takeyi, Malam Abdul-ra'uff ne kawai yalura da halin da Jiddah ke a ciki, dan haka saita bashi tausayi sosai.
     Tambayoyi sukaita Mata domin k'ara tabbatar da nagartarta, inda tai kuskure suyi Mata gyara da fad'ad'a Mata bayani akan abun, duk kuma yanda abun zai iya kasancewa sun Mata bayani, tareda Addu'ar Neman dacewa.
      Jiddah ta nutsu sosai domin kuma fahimta, Alhmdllh kuma ta fahimci kaso mafi yawa a ciki, inda kuma bata fahimtaba sosai takan kuma tambaya. Sunyi zama kusan Na awa biyu da Jiddah, Wanda ikon ALLAH ne kawai yabata damar kasancewa zuwa wannan lokacin batareda samun matsalaba, danma Malam Abdul-ra'uff dayaga sosai take a takure yay Mata addu'a cikin ruwa yabata Tasha, shinema takuma samun nutsuwar zaman wajen, bayan sun kamala zaman akad'anyi hotuna kafin su fito suka rankaya Massalaci.
           Ai tuni Jiddah tafara hawaye ganinta gaban ka'aba, tashin farko Addu'ar shiriya ta farama mahaifinta, sai Ummanta da Uncle yahaya, kafin nan y'an Uwanta, ta d'ora da addu'ar fatan ALLAH yabasu mazaje nagari itada y'an uwanta da dukkan al'ummar musulmi.
       Basubar massalaci ba sai la'asar, dan acan suka had'u da Siyama da Uncle yahaya.

*_Ranar Musabaqa_*

          Yau dasu Jiddah suka cika kwana biyu a saudiyya ne ta kasance ranar musabaqar data kawosu, tunda safe suka tafi *Riyadh* inda taron zai gudana, duk yanda Zan fasalta muku abin bazaku fahimtaba, amma kowa ya k'iyasta a ransa.
     Tarone Na taurarin al'ummar musulmai, dolene kaganka a wajen kaji kwalla ya cika idonka, Addinin isalama addini Mai nagarta da aminci, duk Wanda ya tsinci kansa a ciki ya godema ALLAH.
       Sai Jiddah taga mu bak'ak'e y'an tsirarine a wajen, saima kayi duba na tsanaki zaka iya zazzak'ulomu, babu yaran da kakeji a wajen yana tashi sai larabci, Su Jiddah Matan an killacesune awani glass da zasu iya kallon komi ke gudana a wajen, ankuma kaimusu abinda zasu rimgajin magana shima, babu ruwansu da mazan. Hakan ba k'aramin farin ciki ya saka Jiddah ba, dukda dai tsorone fal ranta, dan ita yaran larabawannan sun tsoratata, tana tunanin Anya kuwa zata iya Kai labari a gasarnan?.
      A k'asashen Africa gaba d'aya k'asa kusan biyarce ta halacci taron, sauran duk yankin fararen larabawane dawasu d'aid'aikun kasashen turawa..
        Tun Jiddah Na d'ari-d'ari da y'ammatan kusa da ita har suka janye ra'ayinta tafara tanka musu, dukda larabcinta baikai nasu kwarewaba tana k'ok'ari itama. tuni hirar ilimi ta 6arke tsakainta dasu Ummusulaim. Sai hotuna suke musu, Jiddah bata ta6a damuwa da rashin wayaba sai yau, saitaji inama itama tanada ita ta d'auki hotunan domin tarihi........
    Tunanintane ya katse jin an Kira sunanta, d'ago kanta tayi ta kalli Aunty Siyama, Aunty siyama ta mik'a Mata wayarta.
      “Aunty miya faru? Ajiye miki zanyi?”.
      “A'a kema ki d'auki hotunan kodan tarihi”.
    Godiya Jiddah taimata sosai, yayinda tuni Aunty Siyama ta juya ta fita wajen da suma aka tanadar musu kusada su Jiddah.
        Suna tsaka da hotunansu wata sassanyar murya data fara jan k'ira'ar Al-Quran ta daki kunnuwansu. Kusan duk a tare suka kalli wajen, dan da hankalinsu duk baya wajen, shiyyasa basusan hidimar da akeba.
     Mamaki al'ajabi mai girma ya Kama Jiddah, ganin mamalakkin wannan murya ya fitone cikin jinsin bak'ak'e irinta,  sosai ta shagala da kallonsa karatunsa Na ratsata da k'ara Mata nutsuwa, batama San sanda tafara masa video recording ba kamar yanda sauran mutane ketayi, ga wajen yayi tsit bakajin sautin komai saina fitar muryar *Sheikh Aliyu Abdul-ra'uff Maina*, abin birgewa da alfaharin duk wani Mai alak'a da wannan *TAURARO*.
     Saida ya kai har k'arshen Suratul Al-Ahazab sannan ya dakata yana share kwallar data cika idonsa saboda yana karantawa zuciyarsa Na fassara abinda Surar ta kunsa, hakama masana aduniyar ilimi suna saurarensa da fashin bak'i a zukatansu.
     Saida yaja doguwar Addu'a kafin yakoma ma zauninsa, Mutane dayawa ya birgesu dajin k'aunarsa, mahaifinsa kam shikad'ai yasan yanda yakejin d'unbin k'aunar Aliyu a ransa, dukkannin burinsa akan ilimin y'ay'ansa Aliyu ya cika masashi.
    Taro yacigaba da gudana bisa bigiren abinda ya tara mutane, dan anfara gudanar da gasa cikin nutsuwa. Wajen tsit yake bakajin komai sai sautun karatu dakuma gyara dasu Aliyu keyima yaran dan sune alk'alan Musabaqar.
     Lokacin da aka ambaci Nigeria sosai cikin Jiddah ya juya, dak'yar ta iya janyo numfashi da karanto addu'a sannan tasamu mik'ewa zuwa inda kowa ke zuwa ya zauna.
       Tunda ta fito ya kafeta da kallo ta k'asan ido, tashin farko yabata maki d'ari bisa d'ari a 6angaren tafiyar Nutsuwa, harta k'araso wajen yana kallonta, amma bazaka ta6a fahimtar hakanba saishi da yakeyi.
       Cikin hashen larabci balaraben malamin yafara Mata tambayoyi kafin yabata izinin tsunduma ga abinda ya ajiyesu.
      Sura kawai ya za6omata a cikin Al-Qurani tunda tace ta sauke a hadda ma sai abinda ba'a rasaba.
      Aliyu daya d'auke kansa kamar bashine kemata kallon k'asan idoba d'azun yana saurarensu, jin Surar da Sheikh Mohammed Ali ya cafko mata saida yad'an d'ago kai ya kallesu, aransa kuwa yana ayyana shikenan sun fad'i, danshifa bai tabbatar da yarinyarnan zata iya wani abun kwarai ba, dan sanyinta yayi yawa..........
      Tunaninsa ya katse lokacin da nutsatstsiyar muryarta mai zak'i da sanyi tafara karatu cikin Suratul Al-Furqan kamar yanda aka bata Umarni.
    Wani irin sanyi da nutsuwa suka ratsa zuciyar Aliyu, ya lumshe idanunsa yana mai fassara Ayoyin daki-daki.
    Gurin yay tsit ita kawai ake saurare.
     Itadai Jiddah kanta na a k'asa bata kallon kowa a cikinsu, karatunta kawai take idanunta na zurarar da hawaye. Bata tsayaba sai da aka dakatar da ita, aka kuma d'akko mata wata surar.
    Hawayenta ta share jikinta Na cigaba da tsuma tafara karanto suratul Al-Hujurat, nanma tayi nisa sosai aka kuma tsaidata takoma Suratul Al-Mutaffifin, aka sake maida Suratul Al-Ma'arij, ayanzukam sosai Jiddah take kuka a wannan sura ta al-ma'arij, saboda abinda take magana akai Na azaba ga wad'anda suka bijirema gaskiya da Ni'ima ga masu ruk'o da gaskiya, tsoratarwa da ranar hisabi da sakamakon kowa, saida takai har k'arshenta sannan aka maidata suratul Al-Zumar, nanma tayi nisa aka tsaidata aka dawo da ita Suratul Al-Ibrahim, tanayidai tana shartar kwallanta aka kuma maidata Suratul Al-'Imran.
     Daganan aka tsaidata, Handkerchief d'in gabansa ya mik'a Mata ta Y'ar k'ofar gilas d'in data raba tsakaninsu, ta kar6a yayinda idonsu ya shiga cikin Na juna, cikin fad'uwar gaba tai saurin janye nata tana jawo numfashi dak'yar, wani k'amshi mai dad'i yadaki hancinta lokacin datakai handkerchief d'in kusada fuskarta, idanu ta lumshe ahankali ta furta “Masha ALLAH”. saida ta goge fuskarta fes dukda hawayen nacigaba da zubowa kafin ta mik'a masa. Kansa ya girgiza mata yana d'auke kansa, a kan la66anta ta furta “Jazakallahu khairan”, ya amsa da “Amin” shima a saman la66ansa, dan yana kallonta ta gefen idonsa.
       Anfara Mata tambayoyin daduk suka kamata, harma acikin wasu littatafan daban, cikin amincin ALLAH tana bada amsa yanda ya kamata. Duk sanda Sheikh Aliyu zaima Jiddah tambaya sai idonsu yashiga na juna, saidai kowanne yay saurin janyewa.

      Dad'i sosai yacika wakilan Nageria irinsu Malam Abdul-ra'uff da manyan malamai, Sarkin Musulmai da sauransu, saboda jin yanda Jiddah ke amsa komai daki-daki, kurakuran da ake samu daga gareta k'alilanne wad'anda ba'a rasaba.
         Bayan an gama da Jiddah aka cigaba da kiran d'alibai.
         Saida kowa yayi sannan aka tashi saikuma an tantance wad'anda suka tsallake.

★★★★

         Washe Gari Jiddah tasamu nasarar shiga cikin k'asashe bakwai wad'anda suka tsallake, a ranarma Jiddah tasha kuka wajen yin nata.
      Washe gari again nanma aka kuma fafatawa da k'asashe uku da suka tsallake, ciki harda Jiddah mai wakiltar Najeriya.
     Randa akai Na k'arshe ba k'aramar cika wajen yayiba, dan harda Sarkin Saudia da wasu manya-manyan mutane da duniyar Musulinci ke ji dasu, wad'anda mukeji sunayensu a bakunan malamanmu da litatafai Na Addini da suka riskemu.
     A yau kam bak'aramin rud'u Jiddah ta shigaba, saboda tambayoyi su Aliyu ke zak'ulo musu masu wahala da tsunduma kwakwalwa cikin dogon nazari. Kasancewar an Fara da wuri kuma kasashe Uku ne kawai suka fafata sai aka gama da wuri, Nageria ita kad'aice takai wannan mataki a yankin Africa.
     Bayan kammalawar su Jiddah manyan malamai suka koma bayan fage domin tantancewa, yayinda a wajen taro aka cigaba da gudanar da lectures masu ratsa jikkuna da duniya gaba d'aya.
       Ba'a samu nutsuwar sanar da sakamako ba sai bayan salar zuhur.
            Kowa dai kunnensa a bud'e yake da fatan k'asarsa tazo Na farko.
     Wajen yay tsit an zubama Manyan wajen idanu dake Magana k'asa-k'asa.
       An Kira *Azra Asen* Mai wakiltar k'asar *Turkiyya* wadda itace tazo Na uku.
     Gaba d'aya wajen yad'auki kabbara, Azra ta fita inda ake buk'atar ganinta, bayan jinjina da yaba Mata da addu'ar fatan alkairi agareta aka bata k'yautar data samu da k'yautar Nasarar datasamoma k'asarta.
    Gaban Jiddah nata fad'uwa da wasiwasin ta farkoce ita kota biyu....
    Tunanintane ya katse lokacin da ake shelanta kiran sunan *Arwa Saiyyad* Mai wakiltar k'asar Saudiyya, wadda itace ta biyu. Itama dai tasamu k'aututtukan dasukafi Na Azra tareda fatan alkairi, inda y'an saudia sukai murna, dukda sunyi burin zuwa Na d'aya suma.
      Jikin Jiddah duk yay sanyi, azatonta ko ancire sunantane, sai tajiyo Ana kwala kiran sunan *Jiddah Zakari Yaro* *Najeriya* sosai jikinta yahau rawa, saida taimakon Ummusulaim dasuka zama k'awaye ta iya mik'ewa, tafiya take tamkar zata fad'i saboda sassarfa da idanun mutane, ga lalurarta ta tsoron kasancewa muhali d'aya da maza, danma Ubangiji ya sauk'ak'a lamarin.. 
      Dak'yar ta iya k'arasawa garesu. Doguwar Addu'a da jinjina ga Jiddah da iyayenta da malamanta da k'asarta sosai akayi, kafin a damk'a Mata k'autar nasararta dakuma k'yaututtuka da malamai daban-daban wad'an suka fito a k'asashe daban-daban, da manyan attajiran da suka halarci wannan gagarumar Mubabaqa. Kuka kawai Jiddah ta sakamusu harda sheshsheka, inda mutane dayawa suke tayata musamman ma mu y'an Najeriya damuke cikin farinciki.
       Aliyu dake murmushi yasaka handkerchief ya d'auke hawayen da suka cika masa idanu, hakama Uncle yahya, su malam mustafa malam Abdul-ra'uff, Sarkin musulmai da sauran malamai dasuka halarci taron y'an Nigeriya duk suna tare da tsantsar farinciki, Aunty Siyama jitake tamkar k'anwarta ciki d'aya, dad'i dukya lullu6eta.
     Abubuwa sunciga da gudana kafin taro ya tashi lafiya, masu murna nayi masu kuka nayi.
     A ranar su Jiddah suka baro birnin Riyadh zuwa Makkah.
     Kowa saiji yake da Jiddah, sai nan-nan su malam Abdul-ra'uff sukeyo da Jiddah, yayinda dad'i ya cikata, gata ga Sarkin musulmai da manyan malamai Na k'asarta da takejin labarinsu kojin wa'azinsu a redio ko TV.
       Saidai abinda yabata mamaki bataga malam Aliyu ba tun barowarsu Riyadh, dan badashi suka taho Makkah ba, batadai tambayi kowaba tayi shiru da bakinta, amma haka kawai taji tana kwad'ayin ganinsa kodan tamasa godiyar Handky daya bata ranar, dan dataji d'an Najeriya ne kuma d'an mutumin da zuciyarta take kauna da girmamawa sai dad'i ya kamata, ashema tana sauraren tafseer nasa sosai batasan shi baneba sai yanzu.
      Uncle yahya kam fad'a muku irin farin cikin daya tsinci kansa ai 6ata lokacine ma.
     Labari kuwa yakai Najeriya tuni, sai hotunan Jiddah ke yawo a jaridu da televisions.
     Lokacin da zance yakai kunnen su Umma ai kuka kawai ta sanya Na dad'i, tuni labari yagama zagaye dangi, kowa burinsa Jiddah tadawo ya k'ara ganinta. (Saikace sun manta fuskarta🤣), sundake sai sayen jarida suke suk'ara ganinta, su Zarah ma har Umma suka sayomawa, aiko tasaka k'asan gado ta 6oye bayan sungama Karantawa, wai zata adana tarihi😂🤭. Zumud'in dawowar Jiddah garesu dukya cikasu.
      Lokacin da aka nuna Jiddah a labarai Abba da Hajia Hindu suka gani Hajia Hindu rud'ewa tayi, shikansa Abba yau saiyaji wani iri, yarinyarsace a tsakkiyar manyan mutàne da duniyar musulinci ke ji dasu, duk surutan da Hajia Hindu kemasa baibi takantaba yatashi yashige d'akinsa saboda wani jiri dayakeji yana Neman kwasarsa.

      hakance takuma kasancewa a gidan Alhaji Garba, dan gaddama suka kwaso suka dire akan ba Jiddah data zauna a gidan baceba, yayinda Ashir keta rantsuwa da ALLAH itace. Alhaji garba yace bai yardaba saiya bincika.

      Yayinda wancan cakwakiyar ke faruwa a Najeriya Su Jiddah suna can suna gudar da Umrah a Makkah, tareda zagayen guraren tarihi domin k'arin ilimi, yayin da daga baya kuma suka tattarasukak nufi Birnin Madina.
     Kwanansu bakwai a Madina Gari Mai tarin Ni'ima da dad'in zama, Wanda duk muminin daya shiga baya fatan yaga ya fita, kuka dai Jiddah ta shashi yayinda taganta gaban kabarin MANZON ALLAH (S.A.W) da ahalin gidansa.
     Ranar jinta take wata iri daban tamkar ba itaba.
     Duk inda yakamata suje wajen tarihi malam Abdul-ra'uff shine jagoransu, itadai Jiddah tana k'ara mamaki Ina Aliyu ya shiga?.
         Gaba d'aya kwanakin su Jiddah ashirin Cif da tafiya suka juyo k'asarsu ta haihuwa Najeriya cikeda farin cikin d'umbin nasaarorin da suka k'unso.............✍🏻


*_Barkanmu da Juma'a sweet sister's😄😄🤝🏻🥰_*










*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[25➖26]_*

   
............Saukar dare su Jiddah sukayi, hakanne yasaka masu tarbarsu suka kasance k'alilan, tana farin cikin dawowa ga ahalinta gefe kuma na  zuciyarta na kewar k'asa mai tsarki, jin hawaye kawai tai suna gangarowa a kumatunta, wanda harga ALLAH batasan yaushene suka fara saukaba. Muryarsa Mai sanyin nan ta daki kunnenta.
         “Yakamata a nad'aki sarauniyar kuka ta k'asarnan”.
     Gabantane ya fad'i, har abadan bazata mance wannan sassanyar muryarba, da sauri ta d'ago idanunta ta saukesu a kansa.
         Janye idonsa yayi daga gareta tareda d'ora Mata handky d'in hannunsa saman trolley d'in gabanta ya wuce.
       Da kallo kawai ta bisa tana sauke wani kasalallen numfashi a hankali, sanye yake cikin shadda ruwan gwaiduwar kwai, yazuba dukkan hanayensa a aljihu, dukda darene hakan bai hanata shaida k'yawun haibarsa ba, mamaki take dama ashe ya dawo Najeriya shiyyasa bata sake ganinsaba a can.........
        “ALLAH ya tabbatar”. ‘Muryar aunty Siyama ta katsema Jiddah tunaninta’.
     Janye idanunta tayi daga kan Sheikh Aliyu daya k'arasa suna gaisawa da Uncle yahya.
       Jiddah ta share hawayenta tana murmushin yak'e, “Aunty addu'ar mi kikeyi?”.
       “Ta abin alkairin danaga yana Neman k'ulluwa mana Jiddah”.
     Jiddah bata fahimci inda Aunty Siyama ta dosaba, dan haka sai tai shiru. Itama Aunty Siyamar bata ja zancenba daga nan, saima haramar tafiya da sukeyi, dan dama sun tsaya jiran Malam ne dake gaisawa da mutane.
         Har gida sukaima su Jiddah rakiya.

         Su Umma suna zaune jiran isowar su Jiddah, dan Uncle yahya ya sanar musu ta waya, dan haka sunajin tsayuwar motoci suka fito cikeda d'oki.
        Tuni farincikin ganin juna yasa sun manta da kowa, murmushi Aliyu yayi yana lumshe idonsa, ba k'aramin birgeshi wannan family sukaiba, hakama Malam sun matuk'ar birgeshi, Aunty Siyama kam tuni taji kewar mahaifiyarsu ta mamayeta.
       Sai Uncle yahaya ne ya tsaya sukayi sallama da mutane, amma su Jiddah tuni sunyi ciki.

★★★★

      Barci dai yau sai 6arawone ya d'auki wannan ahali, washe garima da wannan farin ciki suka tashi, kafin kace mi gida ya d'inke da y'an taya murna, aunty Nafisa kam ai tunda farar safiya ta iso.
         Haka wannan yini Yakuma kasance musu cikin kar6ar bak'i, ita Jiddah ma sai kunya takeji.
      Dangin Umma ma sunata kiran waya, kawu Bunami (yayan Umma) yace Jiddah tafad'i komi take so indai baifi k'arfintaba zai Mata, dan d'ansa Banu da autar su Umman Balu suna nan zuwa Kano.
    Rasama abinda Jiddah zata za6a tayi, dan haka tabashi za6in ya saya Mata komi yaga yamasa. Albarka dai tashata wajen wajen kakarsu.
      Rana ta uku da dawowar su Jiddah saiga Abbah suna tsakar gida suna hira da innarsu Balu ya shigo, duk shiru sukai sai Balu d'ince dake murmushi. Shima saiya Saki fuskarsa yana fad'in “Ah ah yau Balu ce a kanonmu haka?”.
       “Aiko nice yayanmu, ai tunda nazo nake cigiyarka akace kayi tafiyane”.
       Cikin in ina yake  fad'in “E...eh...eh ta..fiya nayi wlhy, jiya na dawo da daddare shiyyasa”.
      Su Zarah dake zaune kawunansu a k'asa duk saida suka d'ago suka d'an kallesa saboda jin k'aryar da ya sharo babba dashi.
      Yayinda shikuma yad'an hararesu yacigaba da gaisawa da Balu.
     Duk abinnan dake faruwa Umma na cikin kicin tana jinsu, amma ko tarima batayiba, saida taji shigarsa d'aki sannan ta fito tabi bayansa da ruwa d'auke a hannunta.
       Kallo d'aya taimasa ta d'auke kanta gefe tana gaisheshi, jin a yanda ya amsa saita kuma kallonsa, harma ta kasa hak'uri saida tace, “Lafiya kuwa?”.
        “Lafiya lau, mi kika gani ne?”.
      “Babu komai”. ‘Umma ta fad'a tana mik'a masa ruwan’.
          Soyake yay Mata murnar nasarar da Jiddah ta samu amma ya kasa, sai mulmula maganar yake a zuciyarsa. Tsaf Umma na lura dashi, amma sai tayi tamkar bata ganshiba. Daga k'arshe daya rasa ta inda zai kamo zance saiya maida akalar maganar kan zuwan Balu. Itadai Umma eh a'a shine amsarta dashi, harya k'araci zamansa yay mata sallama ya tafi.
        Sosai hakan yayma Umma da Jiddah ciwo a zuciya, koba komai yakamata ya nuna murnarsa ga nasarar data samo, kodan ma darajar Addininta data samo nasarar a dalilinsa, amma saiyay k'ememe.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

             “Aliyu kasan miyasa na kiraka kuwa?”.
       “A'a baba”.
Zama malam ya gyara sosai yana murmushi, “Wato Aliyu abari ya wuce shike kawo da rabon wani Na hango maka”.
     Kallon malam, Aliyu yayi dan bai fahimci inda zancen ya dosaba.
       Malam yakumayin murmushi “Zancen yarinya Jiddah nake magana wadda mukaje saudia, wannanfa damace akaro Na biyu tazo mana, Na fahimci tun a saudia akwai wani Abu a ranka game da ita, amma sakaci irin naku da wautar k'uruciya yasaka yima lamarin rik'on talala Wanda lallai idan kayi wasa zaka ciji yatsa a daga baya. Zancen danake maka yanzu haka tun muna saudia naji Sarkin Musulmi yana waya da Mai d'akinsa akan sha'awar naimawa d'ansa auren Jiddar”.
       Da sauri Sheikh Aliyu ya kalli malam cikin waro fararen idanunsa.
      “Ba ido zaka zarominba, kana sontane? Kokuwa hasashenane kawai nakeyi?”.
       K'asa Sheikh Aliyu ya maida kansa yana susar k'eya, fuskarsa d'auke da murmushi yace, ”Inason na cika maka burinka natun farko Baba, sannan harga ALLAH yarinyar ta kwantamin arai”.
         “Alhamdllh Aliy, lallai nayi farin ciki, ALLAH yaymaka albarka. Tofa a wannan karon bazamuyi sanyaba, dan insha ALLAH gobe idan ALLAH ya kaimu zanje musami mahaifinta da zancen, sonake ana gudanar da taronan da za'ayi washe gari a d'aura auranku”..  
            Acikin Zuciyaryarsa yace, “ALLAH dai ya tabbatar Baba”.
      
★★★★

       Tun a ranar malam baiyi sanyaba ya Kira Uncle Yahya sukayi maganar.
       Wannan zance ba k'aramin farin ciki ya saka Uncle yahya ba, dan haka shima baiyi sanyaba ya doka waya zuwa Adamawa domin gayyato kawunansu guda uku suzo ayi dasu, dan baya son Abba ya sake basu Matsala a wannan karon. Sannan yakira Abba ya Sanar masa shima, da to kawai ya amsa saboda a time d'in suna tare da Hajia Hindu.
 
      Washe Gari tunda asubahi su Kawu Safiyanu suka baro Adamawa kuwa, cikin amincin ALLAH saigasu sun iso da wuri, sun huta sannan sukaje suka gaida Umma da tayata murna, Albarka dai Jiddah dasu Zarah sunshata. Uncle Yahya dai bai fad'a Mata abinda ya kawosuba, dan yafison a kammala komai sannan.
       Daga nan gidan ABBA suka d'unguma, dukkan Abinda za'a iya buk'ata Na tarbar bak'i saida Uncle yahya ya tanada daga gidansa suka tafi dashi, dan baya buk'atar abinda zai 6ata ransa a gidan Abba.
          Abba yayi mamakin ganin su Kawu Surajo sosai, dan haka yayta bin Uncle yahya da kallon tuhuma, yayinda shikuma yay biris tamkar bai gansaba. Sunyi kusan zaman mintuna talatin kafin hajia Hindu ta shigo gaishesu tana wani yatsine-yatsine, babu Wanda yabi takanta, dan Uncle yahya ma ko kallo bata isheshiba.
       Tunda ta fita take masifa wai Uncle yahya yakawo su Kawu Bliya maula, duk sunzo sun cika Mata gida da warin talauci.
      Tun Uncle yahya da Abba na zuba idon ganin hajia Hindu ta kawo ruwa har suka fidda ransu, dan haka Uncle yahya yamik'e ya fita, mintuna kad'an yafara shigowa da kulolin abinci, dandanan ya cika tsakiyyar falon da kayan arzik'i, ko zama baiyiba daga ajiye Na k'arshe sukaji shigowar mota. Hakanne ya saka Abba had'iye tambayar dake ransa suka mik'e suka fita domin tarbo su malam.

           Gaisuwa sukai cikin mutunta juna, kafin Kai tsaye malam da kansa yafara fad'in abinda ya kawosu, dan a ganinsa da zafi-zafi akan daki k'arfe.
     Kafinma Abba ya tofa nashi tuni su Kawu Safiyanu sun bada Jiddah tareda addu'ar sanya alkairi.
      Dad'i ya cika zuciyar malam, cikin fad'ad'a murmushinsa yace, “Muda mukazo Neman izinin Fara Neman so Kuma sai ace amma bamu?”.
     Kawu Surajo yay Y'ar dariyarsu ta manya, “Ai malam Kai ubane, kimarka tawuce kazo Neman izinin zance kawai ka tafi, dan kaima mai iya aurar da Hauwa'u ne ko bama a wajen, to balle kuma babban mutum irin Sheikh Aliyu yaga yarinyarmu yace yanaso harma a tsaya jan dogon zance, badan badan bama mu saimuce ama d'aura ka tafi da amaryar kawai”.
       Dariya suka sanya gaba d'aya suna musabaha, Malam yace, “Wlhy da hakan zata kasance danayi murna kuwa. Amm to indai hakane mizai hana indai bamuyi gaggawaba ranar juma'a ta sama kawai a d'aura”.
         “Malam indai hakan yamaka tomu bamuda ja wlhy, tunda dai yarinyarnan ta ta6a aure, banga wani abun jan jikiba ma”. Uncle yahya ne Mai maganar’.
      Atake kowa yayi na'am da wannan magana, ganin haka shima Abba saiyabi ayarin masu amsawa cikin yak'en dariya. Take annan malam ya ajiye sadaki naira dubu d'ari biyu, amma sai su Kawu Bilya suka nemi a rage.
     Malam yace, “Lah-lah bazamu rage ko sisiba, k'arawama yakamata muyi, wato abinda muka kasa fahimta da 6al6alcewar aurarrakinmu na wannan zamanin da sakaci Na yawan sakin aure to k'arancin Sadaki yana ciki, inda za'a ajiye dukkan bidi'oi dake gudana yanzu a shagalin bukukuwa aringa tsawwala sadaki ga masu aure to lallai sai ansamu sauk'i sake-saken aure. Yaro ya biya dubu hamsin ko talatin sadaki, da anyi aure taimasa ba dai-daiba saiya sauta, idan anyi magana yace ga matanan ledar ruwa tafisu wahala, to yasan daya samo y'ar dubunsa d'ari biyu ta Isa masa wani auren, inda ace ana saka musu sadakin Mai tsauri mahaifin yarinya yace baya buk'atar kowacce bidi'a amma sadakin y'arsa dubu d'ari biyu ko uku ko hud'u to wlhy saisunji shakkar sakin, dan sunsan kafin su tara wani sadakin sun jigata, sannan za'a canja tunaninsu ga wanann shaid'ancin Na fati-fati dasukeyi, kunga mutum da kud'in sadaki zaiji kokuwa da kud'in bidi'ar aure?. To ni yarinyata jiddah ma ta girmi sadaki dubu d'ari  biyu wlhy, kaf yarana ban yarda abani k'arancin sadaki a kansuba, bankuma yarda mazan sukai mafi k'aranci ba suma, sannan bana biyama yaro sadakinsa, zandai taimakeka da wani abun, amma kud'in sadaki ka nemo kayanka. Wannanma Aliyun da kansa ya bada abinsa”.
      Kai  su Kawu duk suka shiga jinjinawa cikeda gamsuwa da maganar malam d'ari bisa d'ari, dajin a ransu suma zasuyi aiki da wannan shawara Mai k'yau da nagarta gamai hankali.
       Fita sukayi sukabar su malam suci abinci, Wanda saida uncle yahya yayta rok'onsu sannan suka amince.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

          Bayan tafiyarsu Malam su Kawu Surajo tasa Abba gaba sukayi zuwa gidan Umma, lokaci Zarah da Jiddah basannan sunje gidan Aunty Nafisa, walida da Umma ne kawai a gidan.
       Mamaki sosai Umma tayi, ita tunaninta ma ko dama Abba ne yakai k'ararta itada Uncle yahya wajen su Kawu Safiyanu akan barin Jiddah taje Saudia. Amma da suka zauna sai taji jawabin nasu bai doshi canba, tuni farinciki ya lullu6eta, dan ita wlhy d'ari bisa d'ari ta amince da wannan zance, saidai tabisu da addu'ar ALLAH ya sanya alkairi kawai.
       Abba dai tunda aka zauna baice Uffanba, hakan kuma bai damu Umma ba, Ana cikin maganarma saiga su Jiddah sun dawo. Da hanzari tayi niyyar komawa cikin rawar jiki, Uncle yahya yace, “Daure ki shigo kinji Jidodona, k'arfafa zuciyarki kinji Y'ar albarka duk iyayenkine”.
        Jikinta na tsuma Zarah ta kamo hannunta suka ida shigowa, tuni harta had'a zufa, muryarta na rawa ta gaishesu.
          Kawu Surajo yace, “ALLAH ya yaye miki kinji Hauwa'u, ALLAH ya warware wannan k'ulli cikin hikimarsa da rahamarsa, Yakuma gaggauta saka miki”.
     Da amin duk suka amsa, sai dai banda Abba dayay shiru yana saurarensu dajin haushin su Kawu surajo, kenan suma sun amince da k'aryar ciwon Jiddah Na shirme?, babu Mai bashi amsa dan da zuciyarsa yakeyi.
        Kawu Bilya ne yaymata bayani akan abinda ya faru, sosai mamaki ya kamata, wannan babban malamin da duniyar musulinci ke alfaharine zaice yana sonta da aure? Halan kallon tsoro yaymata? Ina ita ina shi?.
        “Kinyi shiru Hauwa'u, ko bak'ya sonsane? Kinsanfa yanzu ke bazawarace, kinada damar za6en miji da kanki, wannanma munyi miki katsalandan ne saboda ganin nagartarsa, kuma tunkan aurenki Na farko yanemi aurenki ALLAH ne kawai ya k'addara saikin aurin wancan da kika fito, ammafa idan baimikiba lokaci bai k'ureba, ki fad'a mana tunda ba d'aurawa akayiba”.
     Idon Jiddah Na kwarar da hawayen da batasan daliliba tace, “Kawu duk yanda kukayi wlhy ni Mai biyayyace a gareku, zankuma kar6i dukkan abinda kukazomin dashi hannu biyu, dan nasan bazaku cutaminba”.
      Ajiyar zuciya duk suka sauke, kowa yashiga saka Mata albarka sannan aka sallamesu. Dad'i tamkar zai kar Zarah da Walida, tunda suka shiga d'aki sai kwasar rawa suke, harda rairama Jiddah wak'ar amaryar ya sheikh.
      Itadai shiru tai musu, saima kanta data kife a filo tana cigaba da hawaye marasa dalili.

           Tuni zancen auren Jiddah yagama karad'e dangi, kowa yaji saiya tayata murna da wannan canjin alkairi.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
     
               Su malam suna dawowa yakira Aliyu ya shaida masa yanda akayi, dad'i sosai yaji a ransa, Wanda har kamilallaiyar fuskarsa saida ta nuna, ayayyanawa yake aransa nanda kwanaki sha uku zai zama ango a Karo Na biyu kenan, wannan hikimace ta ubangiji kawai, dan baima ta6a hasashen aurenba a kusa balle Mata biyu a lokacin da bashida tazarar nisa.
      Sosai malam yaymasa nasiha akan adalcin had'a Mata biyu da shawarwari, dukda yasan shimad'in yasani.
        Sheikh Aliyu yay godiya da kar6ar nasihar malam hannu biyu. Shi duk saima yaji shakkar tunkarar Maimunatu da batun, gashi dama batada lafiya a y'an tsakaninnan, kuma yana k'yautata zaton cikine da ita, dan dukkan alamun mace Mai yaron ciki sun bayyana a gareta, shiyyasama datak'i yarda yakaita asibiti bai matsa mataba yadai samo Mata magungunan da bazasu cutar da itaba.

      Haka ya d'auki hanyar gida sukuku bayan yashiga ya gaida su hajia bah-bah ya fito.
      Tun a yanayin tsaftar gidan yaji aransa mai gidan babu lafiya, dan Maimunatu akwai tsafta, ko yaushe gidan k'al yake cikin k'ok'arinta na gyarawa.
      Bedroom yanufa bayan ya lek'a kicin yaga babu kowa a ciki.
      Kwance ya iske Maimuna a kan gado k'udundune a bargo.
      “Subahanallah” ya fad'a yana zama kusada kanta, kafin ya janye bargon yakai hannunsa saman goshinta da wuyanta, “Ya salam” yakuma ambata saboda jin jikinta zafi rau.
     Da k'yar ta bud'e idanunta da sukai jaa ta kallesa tareda sakar masa murmushin k'arfin hali, “Yaya sannu da dawowa”.
       ”Yauwa Maimoon, zazza6inne ya dawo?”.
      Hannunta ta d'ara saman nashi dake kan goshinta, tad'an yatsina fusaka alamun rashin jin dad'i, “Yaya shine ya dawo, amma karka damu nafasha magani”.
        “Ai tama shan magani tak'are, tashi muje asibitin can, tunda Na kud'ine nasan za'a iya samun likita, kuma banason musu”.
       Bata iya cewa komaiba ya taimaka Mata ta sakko, da kansa ya canja Mata kaya zuwa doguwar Riga ya saka Mata hijjab sannan ya kamota suka fito.
          Cikin amincin ALLAH kuwa sai suka samu likita, dukda kuwa k'aramin asibitine.
       Sosai doctor yay Mata tambayoyi kafin yasaka wata nurse tazo ta d'iba jininta.
       Karin ruwa suka saka Mata saboda jikinta babu k'arfi sosai, malam Na zaune a kusa da ita hannunsu sark'e da Na juna ake Mata k'arin ruwan, kirane ya shigo wayarsa, dan haka yay k'ok'arin janye hannunsa dan ya amsa, amma sai ta sake damk'ewa, kallon hannun nasu yayi yana murmushi, saiya d'aga wayar da d'auyan hannun saboda Aunty Ruk'ayya ce.
      Bayan sun gaisa ta tayasa murna akan k'arin  NASA, Wanda malam yakirata ya sanar Mata.
       Da amin ya amsa saboda addu'ar fatan zaman lafiya da take musu, kafin daga bisani ya sanar mata sunama asibiti Maimunatu babu lafiya, amma bai sanarma kowaba.
      “Subahanallahi, muke damunta Aliyu?”.
       “To gadaimunan ana mata k'arin ruwa, sunkuma d'iba jininta zasu gwada”.
     “to yanzu ya jikin Nata?”.
     “A alhamdllh, barci takeyima”.
      “Ganinan zuwa yanzu insha ALLAH, yimin kwatancen asibitin”.
    Kwatance yay Mata kafin su katse kiran.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

            Alhaji garba da Abba ne ke gaisuwa a kasuwa, Wanda rabon da hakan ta faru tun bayan rabuwar aurensu da Jiddah, hasalima had'uwa tamusu wahala gaba d'aya, dan Alhaji Garba dainabin hanyarma dazaiga Abba yakeyi, shima Abban hakanne a garesa.
     Yaukuma abin mamaki saiga Alhaji Garba har shagon Abba. Bayan sun gaisa Abba yasaka yaronsa Jabiru ya kar6oma Alhaji garba fura Mai sanyi.
       Alhaji garba nashan fura suna hira har suka gangaro kan zancen Jiddah Wanda shine mak'asudin zuwan Alhaji garba.
      “Wai nikam abokina da gaske Jiddah matata nagani a taronnan da akayi Na saudia?”.
       Cikin danne takaici Abba yace, “Eh itace wlhy Alhaji, ashe kaima ka gani?”.
      “Nagani dagani har iyalaina, harma mukaita gardama akan itace koba ita baceba”.
     “Aikuwa dai itace”.
  Alhaji garba ya washe hak'ora yana kur6ar fura, “Humm nikuwa abokina wlhy ganin yarinyarnan da abin arzik'in da tayi a k'asa mai tsarki ba k'aramin sake sha'awar komawarta a gareni nayiba, kasan kowa yanason yasama ma y'ay'ansa uwa tagari, inda hakan zata kasance kabani koman yarinyarnan da nikuwa wlhy Na barmaka dukkan kud'ad'ennan danake binka”.
       Abba ya washe baki yana fad'in “Alhaji da gaske kake wannan maganar?”.
     “Wlhy da gaske nake alhaji zakari, kuma a wannan Karon namaka alk'awarin bazan had'a Jiddah da Hajia deluwa ba, sakinma danai Mata sharrin shaid'anne, amma tun bayan barinta gidana da ita nake kwana a raina nake tashi”.
       Abba da k'asan zuciyarsa ke tunanin auren Jiddah da sukabama su malam Abdul-ra'uff yad'an sauke ajiyar azuciya a fili kafin yace, “To dukda ga magar wani auren nata ya shigo, dama kamin maganane da wuri? To amma wlhy tunda har kace ka yafemin kud'innan insha ALLAH zanyi iya k'ok'arina naga Na rusa wancan, dama k'arfina akafi, kawunnaina ne suka kar6i auren bisaga jagorancin munafincin k'anina yahya, to amma kabarni dasu, ai dai d'iyar tawace ko? To ka saka a ranka kasamu”.
     “A to lallai zankoyi farinciki, ammafa kasake bska dawomin da itaba to nanda kwana kad'an ka tanadarmin kud'ina gaskiya”.
      “Haba alhaji, ai insha ALLAHU bama za'ayi hakaba, indai nine Na haifi Jiddah to ka d'aukama ta sake zama matarka ta gama, sunsa aurenta sati biyu, Toni Zan saka sati d'aya kaida ita”.
      Baki Alhaji garba yashiga washewa yana k'ara gidiya da fatan sake tabbatar wannan lamari, a wannan Karon kuma yayi alk'awarin ba wariba da hauka komi Jiddah zatayi babu sanya Randa taje zai mallaki kayarsa...........✍🏻

*_😱🙆🏻Alhaji Garba ya dawo, Sheikh Aliyu Maina Yaya kenan?😫🚶🏻‍♀._*







*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻

*_Typing📲_*

  *_💡HASKE WRITER'S ASSO...._*

   *_💧MUTUM DA DUNIYARSA....!!💧_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_

                 *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

                   *_[27➖28]_*

   
..............Babu dad'ewa Aunty Ruk'ayya ta iso asibitin, bisa kwatancen da Aliyu yay Mata ta iso d'akin.
     Har yanzu yana zaune kusada Maimuna dake barci, hannunsu Na sark'e dana juna har yanzun, shigowar aunty Ruk'ayya da sallama ya sakashi zame hannunsa a hankaki dukdama tarigada ta gansu.
       Hannu ya mik'a ya kamo hannun yaronta Najib fuskarsa d'auke da murmushi. “Najibullah kaine ka k'ara girma haka?”.
      Najib dako magana bai gama iyawaba ya lafe a jikinsa, yayinda Aunty Ruk'ayya ta zauna saman kujera tana dariyar maganarsa.
      Yaranta Sadiya da Naja'atu suka shigo da sallama hannunsu d'auke da ledoji.
        “A'a Aunty kice harda y'ammatana kike tafe?”.
        Sadiya da Naja'atu suka durkusa suna gaishesshi da tambayar ya Mai jiki?, fuskarsu washe da murmushi, shima cikin sakin fuska ya amsa yana tambayarsu makaranta.
    Suka had'a baki wajen fad'in Alhmdllh Kawu.
       “Naga gida gaba d'aya amma banga Ameer ba?”.
       “Kawu ai yana tare da Abba sunje anguwa”. ‘Naja'atu tai maganar cikeda ladabi irin Na y'ay'an da suka samu tarbiyya’.
      Aliyu yace, “ALLAH Sarki, to ALLAH ya dawo dasu lafiya”.
    Da amin suka amsa, kafin ya maida hankalinsa ga aunty Ruk'ayya suka gaisa tana tambayarsa Mai jiki.
      “Aliyu maimuna dukta rame fa, sai haske data k'ara, kodai munsamu k'aruwane?”.
      Murmushi kawai yayi, kafin yabata amsa doctor yashigo da sallama, bayan yabama Aliyu hannu sunyi musabaha ya mik'a masa takardar result d'in yana masa murnar cikin dake jikin Maimuna Na watanni biyu da wasu kwanaki.
      Tuni murna ta kacame tsakanin Aliyu da aunty Ruk'ayya dasu Sadiya, wasu kwallan farin ciki suka taruma Aliyu a gefen ido Na dad'i, Aunty Ruk'ayya kam ai saida suka zubo a kumatunta, koba komai samun lafiyar Aliyu ta tabbata, dama tana tunanin kar aita tsogumi akan wannan auren nasa dazai k'ara, Dama taji anfara k'ananun magana a gidansu akan Maimuna, amma yanzukam hankalinta kwance.
         
★★★★
     
       Lokacin Salla na gabatowa Aliyu yatafi gida yabar auty Ruk'ayya da aunty Siyama datazo daga baya.
      Bai koma asibitinba sai kusan tara Na dare, danma yau bai xauna karatuba, yanema uziri akan Mai d'akinsa batada lafiya.
      Mutane sunta mata addu'a da fatan samun lafiya.
     Lokacin daya dawo ya iske harda malam da matan gidansu suma sunzo duba Maimunatu data farka tuni, baiyi zaton ganin su malam ba, dukda dai shine yakira ya sanar masa batada lafiya, amma bai fad'i maganar cikinba saida sukazo sukeji a bakin su Aunty Siyama.
     Maimuna nata duk'ar dakai tak'i yarda su had'a ido da kowa, koda Aliyu ya dawoma kasa kallonsa tayi, saicin abincin da aunty siyama takawo take a hankali. Duk yanda yaso su had'a ido tak'i bashi damar hakan, murmushi yayi yana k'arajin k'aunarta harcikin ransa. Yanason Maimunatu saboda k'yawawan halayenta Wanda Ada kafin aurensu baiyi zaton tana dasuba. Shiyyasa babu k'yau yakema mutum hukunci akan abinda baka tabbatarba, kakuma k'yautata zato ga kowa shine nagarta da cikar kimar d'an Adam.
     Basu bar asibitinba sai kusan sha d'aya Na dare. Kowa gidansa ya nufa, shima ya d'auki matarsa sukai gida bayan yad'an Mata sayayya a hanya.
    Yanata janta da hira amma takasa amsashi da k'yau saboda barcin dake cike da idonta.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

         Tunda Abba yabar kasuwa babu abinda ke caccakar zuciyarsa sai maganarsa da Alhaji Garba, sai k'ullawa yake da kwancewa, yana hangen k'urar da zata iya tasowa tsakaninsa da Umma da Uncle yahya, gefe kuma yana kallon d'unbin kud'in da Alhaji garba hace ya barmasa inhar Jiddah ta dawo garesa, yasan ko k'asa da sama zata had'e bashida kud'in biyan Alhaji garba, koda kuwa za'a saida gidansane da kayan kasuwarsa da komai daya malakka, dan kud'in daya ranta a banki a shekarun baya dasune ya ida ginin gidansa, ya kuma k'ara jari sosai a kasuwa, suka kuma hau kan sauran kud'in shida Hajia Hindu da y'ay'ansa sunaci hankalinsu kwance, da kud'in kasuwa yad'an fara bama banki miliyan goma, daga baya kuma saiya daina biya, lokacin da suka ajiye shida banki na cika suka nemi kud'insu, amma sai suka iske babu wani abun arzik'i a k'asa sai kayan kasuwarsa, kwanaki goma suka bashi ya maido kud'in kokuma komaima yafaru shi ya sani, wannan ne ya tashi hankalinsa sosai har hajia Hindu ta fahimta, tashin farko tabashi shawarar Neman bashi wajen Alhaji garba. Baiwani dogon tunaninaba ya amince saboda mafita yake nema a lokacin, da taimakon Hindu hajia deluwa ta lalla6a musu Alhaji garba yabada kud'in, sai dai a lokacin shi Alhaji garba saiya 6oyema Hajia deluwa adadin kud'in da Abba ya nema saboda wani dalilinsa, cemata yayi kawai miliyan gomane. Shikuma Abba maimakon dayazo kar6ar bashi ya kar6i miliyan arba'in tunda yabama banki miliyan goma tuni, saiya kar6i hamsin d'in, ya biya banki arba'i ya ajiye goma a hannunsa da zummar ya k'ara jari danya samu ya gama biyan Alhaji garba da wuri. Bayan faruwar haka babu jimawa Alhaji garba yaga Jiddah, d'uwawunsa Na rawa yace yabarma Abba rabin kud'in inhar yabashi auren Jiddah, yakuma lamunce masa ahankali ya biyasa sauran rabin. To dagabaya da auren Jiddah da Alhaji ya rabu sai Alhaji garba ya aikoma Abba cewa ya janye k'yautar dayaymasa ta Rabin kud'i, a yanzukam yanemi miliyan hamsin d'insa ya basa cif. To yanzu kuma Alhaji garba yadawo ruwa saboda ganin Jiddah daya k'arayi ya rud'e, a wannan karonma gaba d'aya ya barma Abba kud'in inhar an maido masa Jiddah, idan ank'i kuma abashi kud'insa da wuri. kunga kuwa dolene Abba yashiga cakwakiyar tunanin son wargaza auren Jiddah da malam Aliyu yakuma k'ullawa da Alhaji garba a Karo Na biyu.

   Tofa masu karatu, Yaya wannan cakwakiya zata kasance? Minene makomar Abba zakari idan baisamu cikar burinsaba?.

    Nidai bilyn Ku nace yasaka yan MASARAUTAR BILYN ABDULL DA MUTUM DA DUNIYARSA GROUPS a kasuwa yabiya bashinsa hankali kwance😝😂😂😂⛹‍♀⛹‍♀⛹‍♀⛹‍♀.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

      Baki hajia deluwa ta ta6e saboda sauraren zancen Alhaji garba da takeyi akan Jiddah. “Wai kana nufin da gaske itace kenan Alhaji?”.
       “Minene ribata idan namiki k'arya Yahanasu, to yanzuma haka maganar da nake miki mun k'ark'are magana da mahaifinta zai dawomin da ita”.
            A zabure hajia deluwa tace, “Ban gane zai dawo maka da itaba, dama ba Saki uku kai mataba?”.
      “A'a k'arya haramun, wlhy Saki biyune, da bama tagama iddah ba datun yau zance na maidata a gabansa, to amma babu komai, nanma da sati d'aya za'a sake d'aura mana aure”.
      Wata makirar dariya Mai had'e da shewa hajia deluwa tayi, kafin ta callara bud'a akan Alhaji garba tana fad'in ALLAH ya nuna mana ango”.
      Da wani kallo tuhuma ya bita harta bar falon amma baice komaiba.
          Hajia Deluwa na shiga d'aki wayarta ta d'auka ta dokama malam Na marwa Kira, yana d'agawa ko gaisuwa bata tsaya sunyiba tafara magana, “Malam Alhaji zai kuma maido shegiyar yarinyarnan, wannan Karon sonake ka haukata min ita kawai tabi duniya”.
    Numfashi Malam Na marwa ya sauke, kafin yace, “Hajia hakan bazata yuwuba gaskiya, dan a yanzu haka zancen da nake miki wandama yake kanta zai iya zame miki babban Matsala, dan aljanin dana had'ata dashi yana shan wahala a hajenta, Sam yarinyar bata sakaci da ibadar ALLAH, danma aljanin yanada nacine, amma wlhy yafara nunamin gazawarsa, kibi tawata hanyar kawai kidai dakatar da auren inaga zaifi”.
       Tsaki taja tana yanke wayar, “Dak'ik'i kawai, ashema bakomai zaka iyayiminba”. (Hummm)
     Maida akalar kiranta tayi ga hajia Hindu bayan sun gaisa tace, “Hindu wani aikin zakimin akan Y'ar mijinki, amma kafin sannan idan kinada wani malami kimin rakiya gunsa koki bani lambarsa”.
      “To Hajia kinsanfa ni indai harkar malamai ce ba'a yinta Dani, akullum bakina shike kwatata a hannun miji da kishiya, dan shine malamina shine bokana, amma bazan bama k'aton banza kud'ina yaci ya had'omin k'aryaba”.
          “Kinga ya isa haka, idan bak'ya wannan ai saikimin aiki da bakin naki, sonake kiyi duk yanda zakiyi kar auren Y'ar mijinki yakuma k'ulluwa da mijina, idan har kikayi haka Zan baki miliyan d'aya”.
      A rikice hajia Hindu tace, “Miliyan d'aya fa? Akan hana aure kawai? To kibani nanda kwana uku kacal zakisha mamaki”.
      “Nabaki, amma karya wuce haka”.

       Gaba d'aya Hajia Hindu ta rikice, batayi sanyaba wajen nufar d'akin Abba, tashin hankalin data iskeshi a ciki naneman mafitar k'ulla auren Jiddah da alhaji garba ne ya sakata samun damar bugar cikinsa, nanko yashiga Mata bayani dalla-dalla akan k'udirinsa Na sake aurama Jiddah Alhaji garba.
    Tana gamajin komai tai saving d'in recording d'in datayi.
     Abba dai baisan anayiba🤣.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

           Washe Gari Abba Na fita kasuwa hajia Hindu tai shiri tatafi gidan uncle yahya, abinda batayi a rayuwarta, dan inba Maman Sadiq ce ta haihuba bazaka ta6a ganinta a gidanba, shima barka take zuwa, minti talatin kuma yayi yawa zata baro gidan.
     Maman Sadiq ma tayi mamakin zuwan Nata, tadai kawo Mata ruwa sannan suka gaisa. Suna cikin gaisawa Uncle yahya dayay shirin kasuwa ya fito, shikansa yayi mamakin ganin Hajia Hindu, amma saiya zauna suka gaisa danyaji dami tazo. Batawani ja musu ajiba tabashi recording d'in yaji. Sosai mamakin Abba da d'unbin wautarsa ta Kama Uncle yahya amma sai baice komaiba ya mik'ama hajia Hindu wayar yana fad'in “ALLAH ya k'yauta” kawai. Dan itama bata isa ya tattauna komai da itaba akan lamarin. Sallama ma yaymusu ya fita abinsa.

      Uncle yahya bai zame ko inaba sai gidan Umma, ya iske ita kad'aicema a gidan, tana falo zaune tana sauraren redio.
     Zama yay suka gaisa kafin yaymata bayanin komai kamar yanda yaji.
     Umma zata birkice masa yace, “Kinga kwantar da hankalinki Maman Nafisa, ni nasan matakin dazan d'auka akan Yaya wannan karon, bayace kafin sati biyun da mukasa zai d'aura Mata aure ba, toni kafin sati d'ayan dayasa nima Zan d'aura mata”.
        “Oni Yagana, wai Alhaji kuwa yasan miyakeyi? A ina yata6a ganin nema akan nema? Balle wannan da harma an biya sadaki? Anya kuwa lokaci baiyiba dazan raba jaha dashi?”.
     “A'a dan ALLAH kibar fad'ar haka Maman Nafisa, ki duba yarannan dake suke kallo suji sanyi a ransu harsu Nafisa dabake kika haifesuba, mucigaba da masa Addu'a, dan son zuciyane kawai ke d'awainiya dashi, ita kanta hindun nasan akwai dalilinta nayin hakan, amma mu insha ALLAHU a garemu alkairi zai zama”.
       “To ALLAH ya rufa mana asiri, wlhy ni sam Uncle d'insu bana ganin laifin Hindu, dan tunkan zuwanta gidannan yake fama da mugun halinsa, ita idan kagama ta aikata d'orata akayi a layi”.
      “Wannan gaskiyane Maman Nafisa, ALLAH dai ya rufa mana asiri, ni bara naje wajen malam d'in mu tattauna, daga nan zan wuce kasuwa”.
     “To ALLAH ya tsare, ya raya mana su Sadiq yabiyaka da mafificin alkairi kaima”.
     Da amin ya amsa yana ficewa.

★★★★★★★

       Kai tsaye gidan Malam Uncle yahya yanufa, dukda ya iskeshi da bak'i haka yasaka aka kai Uncle yahya falonsa ya taso ya saurareshi.
    Bayanin dazai gamsu shima yay masa, shikansa malam ya girgiza da lamarin Abba, amma saiya bishi da addu'ar fatan shiriya kawai.
     Sun k'ark'are magana akan zasu d'aura auren ranar juma'a bayan sakkowa masallaci, nanda kwana 4 kenan, kuma Abba zakari bazai saniba sai a wajen d'aurin auren.
     Daga baya idan an kimtsa Jiddar saita tare.

★★★★★★★

      Koda Aliyu ma yazo da yamma haka malam ya sanar dashi sun dawo da d'aurin aure Juma'a.
     Kansa a k'asa ya amsa da “ALLAH ya kaimu baba, ALLAH yasa haka shiyafi alkairi, duk yanda kuka yanke yayi”.
    Malam ya jinjina kai yana saka masa albarka.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

      Yau dai kam malam Aliyu yasan dolene ya danne zuciyarsa yayma Maimunatu bayani yanda zata fahimta, dan yanason saiya gama da matsalarta kafin yaje ga waccan sarkin kukan (Jiddah😂).
     Yau jikinta dad'an sauk'i, saidai abinda ba'a rasaba irin Na Mai laulayi.
      Kamar yanda ya saba ya bud'e Mata hannayensa ta shige sunamai begen juna.
     Bayan ya watsa ruwa sun dawo fallo takawo masa kayan marmarinsa, gefe takoma ta zauna, dan yanzu bata iya sha ita, ganin yayi shiru yakasa sha yanata kallon fruits d'in saita taso tadawo kusa dashi.
     'Dago fararen idanunsa yayi yana kallonta amma baiyi maganaba.
     Tad'an langa6e kanta gefe cikin salon kwantar da hankali tace, “Wai mike damunkane Annur? Kwana biyunnan nalura Abu Na damunka amma kana 6oyewa”.
      Ajiyar zuciya ya sauke yana juyowa sosai gareta, “Maimoon ba 6oyewa nakeba, kawai dai ina tunanin ta yadda Zan fidda maganar ne gareki, dan bansan Yaya zaki d'auketa ba, kinsan Ku Mata duk dad'in zamanku da miji akazo wannan ga6ar idonku rufewa yakeyi”.
     Cikin d'an nazartar maganarsa tace, “Indai nice bazaka fuskanci hakan daga gareniba insha ALLAH Yaya Aliyu, akoda taushe Zan kasance Mai biyayya a gareka da girmama buk'atarka, kodan nasamu rabauta a wajen ubangijina da gamawa da wannan rayuwar Mai tak'aitaccen kwanaki lafiya”.
       Jawota yay jikinsa ya rungume sabodajin dad'in kalamanta, “Nagode gimbiyata, ALLAH yaymiki albarka, ina sonki da k'aunarki fiye da tunanin Mai hankaki”.
       Maimuna dai Na saurarensa, yayinda a gefe d'aya zuciyarta ke tunanin mike faruwa? Kodai rabuwa zaiyi da itane?.......
    Tunaninta ya katse lokacin da Aliyu ya d'agota daga jikinsa.
      Hannayenta ya rik'e cikin NASA, idanunsa a k'asa dan kimarta tawuce ya kalli cikin idonta yafad'a Mata zai k'ara aure. “Maimoon Zan k'ara aurene”.
     Wata zabura tayi tana cire hannunta daga cikin nasa, yayinda tuni wasu hawaye masu zafi sun Fara bin kumatunta, tana niyyar mik'ewa yakai hannu zai ruk'ota, amma saita kauce tashige d'akin baccinta da gudu.
    Kansa ya dafe a hankali ya furta “Ya salam”.
      Kasa tashi yay a wajen kusan minti talatin, saida ya tabbatar inma kukane take, tayi Wanda zai rage nauyin da zuciyarta tayi, kafin yamik'e ya bita.
      Zaune ya isketa saman stool d'in mirror ta kifa kanta akan Mirror d'in tana shashshekar kuka..
    Yad'an dad'e tsaye a bayanta yana kallonta, kafin yasaka hannu ya d'agota zaune sosai. Yanda fuskarta tai jajur sai tausayinta ya kamashi, kafad'unta ya Kama ya mik'ar da ita tsaye, yaja hannunta zuwa saman gado, koda suka zuna saiya sakata a jikinsa, ya saka hannayensa yana share Mata hawayen.
         “Haba Maimunatu, mumini Na k'warai shike kar6ar dukkan abinda yazo a shari'ance garesa koda yana kallonsa k'untata a rayuwarsa, kefa Mai ilimice, iliminma Na addini, sannan ALLAH yayiki cikin Mata masu hankaki da Nisan tunani, nasan kishi abune Mai zafi, amma idan muka gaurayashi da hak'uri da k'yautata zaton Alkairi a junanmu saimu sameshi da sauk'i, kisaka a rankin mijinki Na matuk'ar sonki, kuma insha ALLAH zaiyi adalci agareku, itama wadda zata shigo matsayin k'anwa a gareki ki k'yautata Mata zaton samunta Mai k'yawun hali da fatan zamu zauna lafiya, dan ALLAH ki kwantar da hankalinki kodan babiena dake tare dake, badan bana sonki bane zanyi aurennan, bakuma dankin gazamin a komai baneba, kawai dai kisaka a ranki San k'ara aure ga kowanne namiji tamkar an haliccemu dashine, dan ALLAH kiyi koyi da halin matayen MANZON ALLAH (S.A.W), hakan shine zaikuma girmama k'aunarki a raina, dan abinda Mata basu ganeba, shirme da sukeyi yayinda mazajensu zasu k'ara aure shike janye k'aunarsu da tausayinsu a zukatan mazanma gaba d'aya, amma idan kika kwantar da hankalinki saikiga Mijin Nata k'ok'ari danya faranata miki Yakuma kare martabarki ga wadda zata shigo, dukda dai nasan akwai azzaluman maza da inhar zasu k'ara aure burunsu shine su wulak'anta matayensu Na gida, suyita tozartasu gaban yarinyar da zasu aura, wannan kuma ba daidai baneba zaluncine, kuma sai ALLAH ya sakama Matar, shiyyasa saikiga yarinya kanta shigo babban burinta shine data shigo ta kori Matar gidan, kinga tunkan tazo cikin gidansa ya gama wargaza farin cikin gidansa gaba d'aya. Nidai insha ALLAH bazan kasance irin wad'annanba Maimoon, dakinga kuma Zan kauce kiyi azamar maidoni, dan kinada kima da daraja Mai yawa a zuciyar Aliyunki wlhy”.
     Tashi zaune maimuna tayi sosai tana k'ara share hawayenta, ”Kayi hak'uri Yaya Na fahimceka, ka yafemin tasowar danai Na barka d'azun, wlhy Yaya kishi Nada zafi, dama Ashe haka duk wadda za'aima kishiya takeji Yaya?, Yaya kamin Addu'a ALLAH yabani ikon jurewa, wlhy ina sonka sosai, amma hakan bazai sakani bijirema ubangiji naba, domin yayimin dukkan ni'imarsa.....”. Tak'are maganar da k'ara fashewa da kuka.
    Jikinsa ya jawota ya rungumeta tsam, tsantsar tausayinta da k'aunarta na ratsashi, sun dad'e a haka kafin ya d'agota ya mik'e, ruwa ya d'ebo a Kofi ya dawo ya isketa zaune inda ya barta tana cigaba da zirarar da hawaye, alkur'ani ya d'akko ya bata sannan yakoma ya zauna yana Mata nuni data karanta, batayi musuba tabud'e tafara karantawa a zuciyarta tana cigaba da hawaye, yayinda shikuma yake tofa Mata addu'oi a ruwa yana kallonta.
        Yadad'e yanayi, yana kammalawa ya kar6i alkur'anin yabata ruwan addu'ar, kar6a tayi ta shanye tana masa murmushi, dan tad'anji nauyin zuciyarta ya ragu.
     Koda ta shanye ruwan addu'ar saiya jawo kayarsa jikinsa yashiga nuna Mata tsaftatacciyar soyayya. (daganan naji bulum😂⛹‍♀).
      Saida yakuma bata nutsuwa da kuma jaddada Mata k'aunarta dake ransa sannan suka dawo falo yasha fruits d'in...............✍🏻


⛹‍♀⛹‍♀duk Wanda naji ya zagi Maimunatu yau dashi za'a biya bashin Abba zakari🥺👯🏻.

_Maman Salma sak'onki ya iso ga bilyn Abdull, ina godiya kwarai da gaske da addu'arki, alkairin ALLA YAKAI gareki aduk inda kike a fad'in duniya🥰🥰🥰🥰🥰🥰❤🤝🏻👍🏻_.





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*🙏🏻😭

No comments