Breaking News

Tantiriya a Gidan Yari Book 1 Paga 71-75

🏫 TANTIRIYA 🏫

        A GIDAN YARI


BOOK1


                  71-75




Official


By

AsmaBaffa


SADAUKARWA NE GA

AIDA MAMAN TASNIM



PAGE NAKI NE

Baby Ak 


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LAizQA6PofSLoFhQ7XeaQx 


Ina kuke masu burin suga sun kawata gadajensu da hadaddun bedsheets? Ko Kuma blankets kike nema? Masu aurar da yara ko kannai da ke kanki uwargida indai kitchen utensils kike bukata

To kukanki yazo karshe.kuyi joining group din R&U exclusive kitchen and more

Ku more wa idanun ku da kayan kitchen Yan yayi na gayu da  zannuwan gado na kowanne kasa Zaki samu  acikin farashi Mai sauki 

Kuma Maza Bata barku abaya ba idan Kuna bukatar a hada muku lefe nagani na fada na amarya Kona  uwargida wato na fadar kishiya duk Zata hadamuku acikin kwanciyar hankali.idan ma akwatunan kawai kuke bukata duk inkuka tuntubi Rumaisa zaku ganewa idanuwanku

 Tana Kano state Kuma Tana tura Kaya kowanne state afadin nageria harma da kasashen da muke makwagtaka dasu

Zaku iya tuntubarta ta wannan number

07034559202




      Washe gari kuwa Spark ko fadawa Naila baiyi ba ya taho sabo da sai taga dama take daga Masa waya,kawayenta na kauye sunzo da shigar Yan Fulaninsu gasu kyawawa sai kalle kalle suke yi,Rayya, Jidda,Nafee,Dije su hudu Wanda gasu yara ma Naila ta girme su duk an musu auren Fulani sun gudu daga gidan Mijin ma basa auren, yara kanana duk an sake su sabo da ba a basu time sunyi zabin su ba, wasu ma auren hadawa kawai akeyi yarinya ta dinga guje guje,karshe idan ta Saba da namiji tayi ta sheke ayarta.


    Naila duk ta kira me lalle tayi musu,kayanta ma sun musu yawa ta fisu kiba da tsayi sai ta samo kayan Hidaya ta basu kala bibiyu,Hidaya tasan Naila zata basababbi bata ko hana ba ,sannan Kuma ta siya musu anko an Dinka musu su hudun tunda tun a waya tasan zasu zo,sai murna suke yi,ta siya musu Yan takalma haka masu kyau flat da wata ke siyarwa a makwafta,tace ko wacce ta zabi Wanda ya mata har da Yar jarkarsu Naila tayi musu kokari, dama sunyi kitsonsu gasu da gashi,tunda suka zo basa Hausa da Naila fulatancinsu suke ta yi Naila an samu Yan uwa,Umma sai da ta gaji tace Dan Allah kuyi Hausa ai sai ace gulma kuke ba dadi mutane na zaune Kun juya harshe.


   Naila an Sha lalle hannu da kafa ya zuba kyau,sanye take cikin vest me siririn hannu da skert Dan kanti sun mata kyau abinka da me kyau gata Yar bulbul,gashi yasha gyara ya koma baki ta dole,babu ko dankwali a kanta tana zaune ana karasawa Rayya lalle tana cire mata na hannu.


     Ta juya baya tana aikin cire lalle taji Mohsin ya shugo danginsu Yan Fulani sai tsokanarsa suke yi ango ango, kado baya Jin fulatanci,Sallamar Spark Naila taji ashe tare suke da Mohsin,Naila a hankali tace Kai ga mijina nan,Rayya tace wayyo kunya ku miko Hijabi aradu a lullubeta,ango ne zai ganta tsirarar babu sutura,Dije tace shike nan Tantiriya ta gama yawo aradun Allah wai Ina zaki je da abin kunya hoodi jam,aradu ban iyawa cewar Nafee,Naila tace ni an fada muku kunyarsa nake ji,ai dama ke baki Jin kunya ko kado haka ya ganki ya kyaleki Tantiriya,tunda Yan kauyen suka zo ba Wanda ya kirata da Naila sai Tantiriya,Umma tayi tayi su daina fada sunki ji.


    Spark kuwa da ita ya fara tozali Yana ta kokonto ko ba ita bace ne irin wannan chanji haka yayi yawa,ya sake kallonta a ransa yace Janare wannan haske da taka Kara haka,gashinta ya kalla yasan itace sabo da askin da taba yi gefe da gefe da aka kwashe Bai Kai tsakiya yawa ba.

   Naila tana jinsa ma Bata juyo ba sai murmushi take ita kadai.


   Umma suna daki da baki,saitin Inda Naila ke zaune ya yazo ya tsaya kamshinsa duk ya mamaye gidan,Hannu yasa a wuyanta ta baya ya kama sosai kamar me shaketa ta baya a hankali ya girgiza wuyan ya saki ya wuce abinsa,Dariya Naila tayi tace ai nasan kazo Malam,Dije tace kunya ta kamani ta jawo hijab ta dukunkune kanta,Rayya tace Ina zan sa kaina yau da abin kunya ku matsa na buya, Tantiriya tace kwayi Kwa gama me za a fasa mutuwa ko hisabi?  tamike taje ta wanke yatsunta da taba lalle, Umma tana ta faman kiranta,ta tafi palon,Spark a cikin Yan kauyen Daji sai kallonsa suke.


    Masu wasa da Naila suka fara tsokanar Spark,Suna cewa wannan ma ai namu ne Kai yaro wannan da Fulani yayi kama,Spark yace a'a yanzu ba a alfahari da ku,wato yanzu a kasar Nan kowa ya tsani Fulani sabo da Bata gari sun watsa mu,Spark an daina alfahari da Fulani yanzu bana ciki ni,Naila ce ta shugo suka koma kanta su Tantiriya an dawo Yan birni iya shege ya kare sai dai kiyi a dakin mijinki,Naila tace wlh bai kare ba kawai dan nayi aure sai ace tawa ta kare sai kace wacce ta tsufa ni wlh shi yasa ma bana son auren ai su Yaya ne suka jawo min.


     Mohsin yace kika jawowa kanki dai dama mene amfaninki,Ango Spark in banda kallon Naila ba abinda yake,sabo da iskanci Kuma taga Yana kallonta ta fuske tana surutu tana girgiza,Spark sai ya susuce,Umma sunga yayi shuru sun zaci kunya yake ji,Umma tace ki kaishi Daya dakin ga key can,Naila ta dakko Key tace muje,Mohsin yace dama gidana kuka kaishi ba mutane can,Naila tace a'a tasan halin Spark,yace Hanan fa tana tsohon gidan har yanzu bata koma sabo ba ta dai kwashe kaya ko Ina yanzu  ba komai wai sai ranar da za a Kai amarya itama kawayenta zasu sake rakata dakin miji,Spark yace ko Maza ne suka kaita ana farko,kara'i zatayi kenan ko babanta ne ya kawota ne farkon aure yanzu take so kawaye su Kai ta,Mohsin yace iskanci ne kawai ya fice.

   Dakin Naila ta bude ba komai ciki sai katifa ta Sha gyara da bedsheet, Spark yace Alhmdllh sa key,Naila tace ban gane ba.

   Key din ya kalla yace bani key din idan wani ya shugo fa.


    Wai me zaka yi? hanashi key tayi ta fice daga dakin tare da Maida key din wajen Umma ta saka bra ta saka riga me dogon hannu sannan ta zuro hijab ta dawo dauke da ruwa da lemo a tire,wai security kika saka kenan? Naila tace ba dole ba ka bari mana a kawoni ko mene sai kayi,shike nan ba abinda zan taba? Naila tace ae,zaki zo ne ai zan fanshe,komawa tayi ta kawo Masa sandwich da Samosa duk ita tayi abarta Kuma sabo da shi tayi,Naila an dage da koyon girki sabo da a birge miji,ganin tana so yaci, sai ce Masa take yi Kaci kaji,yace bazan ci komai ba sai kin koma kin cire rigar Nan da kika saka,kina yi zan ci,Naila ana so aci girkinta,tace yaushe zan koma cire riga a cikin mutane,cire a Nan yanda kika saka ki cire, sai na ci abincin, ta cikin hijab ta cire ta zauna da vest dinta ko bra din ya ce ta cire.

 Yace hijab fa a'a cire,Sai dai idan baza Kaci ba ta furta,fisgo hannunta yayi ta fado Saman katifa.


    Tsaya nifa ba abinda zan miki hugging naki kawai zanyi,rungumeta yayi a jikinsa,tasa hannaye tayi hugging nasa back,Naila da anji Jikin Spark sai jikinta ya mutu murus,abinka da shakuwa an Shaku,kasa katabus tayi sai ma sake kankame shi da yi,a hankali ya dago fuskarta tare da tallafar fuskarta ya fara aika mata da kiss,Naila Idanuwa ta lumshe tsayawa yayi Yana karewa fuskarta kallo Yana dariya kasa kasa yace bude idon to,suna a rufe tace baza su budu ba yanzu, ci gaba yayi da tsotse bakinta,tun tana Dan sharewa har ta kasa ta fara Maida Masa martani , tana juya bakinta cikin nasa kamar zasu cinye juna,Spark yace kaga Yar gari,kin gama wayewa,Naila taji kanta ya Kara girma an yabeta har da sake bada himma zata nuna wayewar,Batasan Wato yake mata ba.


     Juyata yayi tare da zaunar da ita tsakanin kafafunsa bayanta Yana Saman kirjinta,A hankali yana shafa wuyanta har ya gangara tare da sa hannunsa ta cikin vest Abu ko bra,Naila zama ta gyara tana Jin dadi,harda ajiyar zuciyar bata sake magana ba sai dai tayi ta faman Sosa idonta, tana tsoro kar tayi Nishi sauti ya fita, yace bata da kunya,yace Ko ba Tantiriya bace ne? Naji tayi mukus,Ido ta Sosa tace itace mana,ya naji kinyi shuru ke da zanji kalamai na tashi,Naila tace nayi hankali tare da dawo da hannayenta ta bayansa ta rike shi Kam,Spark yace au baza kice komai? Haka kawai nayi ihu ka dinga min dariya daga baya, na daure abina,kiyi abinki ni ba abinda zan miki Kinga a musulunci ba a so duk abinda kayiwa matarka idan tayi ihu ta nuna taji dadi daga baya ka dawo kana mata dariya ko kana tsokanarta to zata dinga Jin kunya ta daina shi yasa akace ba kyau,nima Kuma idan nayi ihuna kika min dariya daga baya ba kyau,Naila tace ni dai wlh sai na Maka dariya sai na tsokaneka,dariya suka yi.


    Sandwich din ta dakko ta fara ci sai ta yi wayo wai tana cewa sandwich dadi,a ranta tace karya nake Kaine me dadin bari na fake da dadin sandwich nake ji,Ido ta lumshe tana taunawa tace dadi kashe ni wlh dadi,Spark ya ganeta shi dai yace ko dai nine Sandwich din? Naila dariya tayi tace na rasa me yasa motsi nayi sai ka gane,Spark shi Kam boobs yake aikin sarrafawa sai mutsu mutsu Naila take yi.

  Ta bayanta ta miko Masa Samosa, kansa ya duko da shi saitin hannunta Yana gutsira,Naila tace Kwalbewa duniya ce,kwanciya yayi ya dawo da ita samansa,Naila ta Kalli Hallare harda dagawa Spark riga ta ganta kuwa a wando duk tana fitar da ni'ima,Naila ta rufe da sauri tace Allah ya baki hakuri,Bai San ma ta daga masa rigar ba,yace me? tace to Hallare ce take dalalar da yawu fa,ke fa? tace bado wai? Tace ae me yake ciki? tace aradu Hawaye ne yake ta zubowa,Spark dariya yayi yace Bado na hawaye,ya dauki lokaci Yana murzata sai da taga duk ya fara fita hayyacinsa ta kwaci kanta da kyar tace a bari sai an kawo Amarya please,yace ni da nazo yau daga dinner sai hotel zamu kwana, Naila tace Bada ni ba wlh haka kawai aje na samu ribar Hotel,ni kwana nan gaba daya ban yarda da Kai ba,da a baya wani Dan Salihi da Kai yanzu Ina abin naka kullum shahara yake.


    Snacks dinsa ya zauna Yana ci yace ah yanzu an fara iya abubuwa,ai dagewa nayi naga za a barni a baya kullum girki nake koya,yace good girl ga Indomie da bishiyar salat ai kina kokari,kwana nan zaka yi tumbi,sun dade suna hira kafin yace zan wuce hotel naje nayi baccina kafin lokacin dinner,tace to shike nan abincin fa? Kadan Kaci,kafin na fito naci a gidane ai naci snacks dinki da yawa abincin ne ban ci da yawa ba,mikewa yayi yace yau hannuna albarkar da take jikinsa tayi yawa,dariya tayi yace you are so sweet,komai naki me kyau Allah ya miki baiwa,Naila tace Alhmdllh bari na kira kawayena na kauye ku gaisa,yace alright ya koma tare da kwanciya a katifar.


    Fita Naila tayi bayan ta Maida hijab dinta tace Rayya tunda an gama lalle Kun wanke ku zo zaku gaisa,Rayya tace wayyo ni Allah kunya,Dan birni haka,Dije ita gwana tace ku fa baku waye ba aradu ku taho mana,suka tashi a kunyace suka shiga dakin,Spark Yana kwance abinsa Saman katifa suka durkusa har kasa tare da gaida shi Ina yini,yace lfy Yana fara'a a fuskarsa, Yana dariya a ransa kuma irin daurin da suka coka goshi kwal,ya musu irin gaisuwar su,yace ya gida? Suka ce lafiya Lau mun sameku lafiya? Spark yace lafiya Lau..lafiya Lau,ya manyan? Sukace lafiya kalau kalau wallahi,ya sake cewa ya shanu ya masu gidan naku? Rayya tace nidai Dan marakina Daya bashi da lafiya ciwon hanta ta kamashi,Spark yace to a yanka shi mana a Sha dadi, suka ce kaiiiiii hodi jam suna dariya Rayya tace ai Affana sai ya kusa kasheni,sanuwar fa wacce ta haifi Dan marakin gadonta nayi wajen kakana,Spark Yana jinsu,Dije tace nidai tsakani da Allah mijina ya sake ni dukkan mu auren mu ya mutu,gwara ma Nafee ita ta samu ciki ya zube mu kuwa shuru,Spark ya kallesu wannan tsigi tsigin yaran ma me za a tsinta a jikinsu,Jidda tace mudai Allah ya kiyaye mu musamman ni Iro Allah Bai bashi sa'ar iskanci Dani ba da tuni na boni la lalashe ,Spark Yana ta dariya a ransa yace a ransa Iro anyi dakiki marar rabo,Rayya tace kaga ni dai Ina son Sagiru na wlh amma iskancin Sagiru bazan iya ba nace ni da Sagiru kaadii fau fau aradu,Spark yace uhm Sagiru ya cuci kansa, Rayya tace Tantiriya ta dawo birni kowa a riga Yana ta kewarta.


   Spark yace na manta ban tayaku jimami ba ya akaji da rashin Tantiriya? Suka ce ohh Tantiriya ta barmu sai hakuri muke ta yi Allah yasa hannun na gari ta fada? Spark yace na gari ne mana tunda gashi ta hadu da Tantirinta,dariya suka yi suna Jin kunya suna rufe Baki suka ce to mun tafi,yace na gode ya mika musu kudi suka ki karba sai Naila ce ta karbar musu.


   Suna fita suka dinga labari wlh kirki ne da shi Ashe suna ta bawa Umma labari ai har Hira suka yi dama Yana da magana,har wasa ya dinga yi mana wlh akwai kirki, a farko mun zaci bashi da mutunci mun ga Yana gadara da takama Ashe shima Tantiri ne a nutse yake magana baza kice shi ya fada ba,Spark fitowa yayi zai tafi Naila tazo zata raka shi ya Dan matsa nesa da ita kadan yace kar ace bani da kunya a gidan surukai,suna zuwa kofar gida yace koma gida,karki min make up lokacin dinner kuma na tsani wannan kwalliyar da mata keyi,duk kyanta Bata birgeni Sam,kiyi da kanki kawai ni bana son make up duk ta canjawa mutum kamanni,Naila tace to na huta nima.


     Ana ta Shirin Dinner da yamma Chikar gayu itace babbar kawar Beauty an dauki wanka kamar me,Amarya kuwa tana wajen make Up tare da wasu kawayen ta Sha farin bride material me tsadar gaske an mata wata gown me kyan gaske ta zaratan amare,an nada mata dauri da silver gogoro, takalmi Silver jaka ma haka,make up din tayi kyau an dora mata mayafin amare a Kanta sharashara sai walwali take ta ko Ina,Ango Yasa Shadda Yar ubansu Silver kalar takalmi da jakarta da gogoro.


     Su Chika duk anci ankon Leshi me kyan gaske Blue and white,kawaye an Sha wanka sunyi gayya kamar me, Yan mata tamfatsa tamfatsa sunzo duk kawayensu ne yawanci daga gidan yari suka fito,Kamal ne zaizo shima sabo da abokinsa Spark ai kuwa Rafeeq yace akwai dinner? akace ae yace ko banza na Kalli mata mu tafi Kamaluddeen,Kamal yace Allah ya shiryeka Kai ba Dan iska ba sai son kallon mata? Rafeeq yace ko banza ai na kashe kwarkwatar idona muje,Da yamma suka dira,Rafeeq lokaci nayi yafi uban kowa saurin shiryawa yace Kano sai da shadda ya fito cikin shadda me kyau wata ita ba milk ba ita Kuma ba ruwan kasa ba,suna dakin Spark shi da Kamal,Kamal yace gaskiya kayi kyau Rafeeq Allah kawo babban rabo,yayi shuru kamar Salihi,Mayen mata Misam ne Allah yayi ya kira wayar Rafeeq,kana Ina? Rafeeq yace dinner Yan mata ne iya kallonka,Misam yace amma baku da mutunci shine ko ku fada min ni shugaban mata guda,Ba komai ai gobe ma matan zasu taru ko? Rafeeq yace ai ance akwai walima mata da Maza za ayi wa'azin zama da iyali lafiya,Misam yace tab zanzo naji Ina jin wa'azi Ina zabar nawa ya nawa.


      Ana ta tafiya wurin dinner dangin ango dana Amarya,Abba ya shugo gidan Yana tarkata kan Yan mata danginsu ku fita ku tafi aje ayi rayuwa Allah ya sanya Alkhairi,Wata babbar mace me suna Tani tace zanje nima nayi kallo, Abba yace Tani gidan uban wa zaki? ki batawa yara show sunyi gayu aga irinki kamar wata Tsohuwar mota hayis ba Inda zaki ai zubar da girma ne,Kubra ta cakare taci wani material an mata make up,kyan da tayi ya Isa,Dake Kubra ce sai Abba yace Yar Inna an fito? Ko ranar bikinmu baki kyau haka ba,idan an girma asan an girma,Kuma wallahi sai kika yi kyau kamar kiyi ta zama a haka,ai da bazan sake fita wajen sana'a ba gwara kullum na dinga kallonki.


    Umma tace wai baza kaje bane? Abba yace a'a haka kawai naje na zubarwa da yarana mutunci wlh tsab naji kida zan taka, Kinga ai girma ya Fadi kuje ku dai kawo Basma nayi miki rainonta,tace madararta tana dakina Jikin bed,yace to ya karbi Basma Umma ta fita ta tafi tare dasu Hajiya Tagwadas ansha gayu.


    Naila ta Sha anko itama ta cakare ta zuba kyau kamar a saceta kawai Spark take jira,ba a dade ba yazo a mota ana tuka shi ya hakimce a baya sai kace shine angon,shadda sky ya saka shigen color din ankon da Naila ta saka,baya ta bude ta shiga gefensa,Yana ta kallonta yace kinyi kyau sosai,Amarya da ango sun karasa wajen Event  suna waje ana ta musu ruwan pics sannan aka Bada sanarwa Amarya da Ango zasu shugo,salon kida aka canja.

   Amarya da Ango ana rakosu ana wata musu buzzer suka shiga tar da zauna,Rafeeq tuni suna ciki shi da Kamal,Spark ne ya karaso tare da Naila rike da hannunta suka nemi wuri tare da zama,ko wanne table da abinci da kayan Sha gasu Nan.

   Babbar Kawa aka Kira Suhailat Chikar gayu,Chikar gayu ta fito wannan fili ana nemanta,tun daga Jin sunan kowa ya baza Ido yaga wace Chikar gayu,Chikar gayu mikewa tayi akayi harrrrr ana kallonta,ta isa gaban Mc ta karbi Speaker tace Alhmdllh sabo da farin ciki a bani kidan Chika,aka saki sauti Chika tayi rawa iya rawa kamar me ita kadai kwal ta iya chashewa,Naila ce taje da Dan takunta kadan tana mata liki,Su Hanan ne suka shugo da kawayenta suna cin magani.


     Naila ce ta radawa Chika maganganu sannan Chika tace a tsaya da kida zata Dan Bada tarihin Amarya a takaice,Sai dariya Chika take bawa mutane domin rawar tata ma ta iya shege ce,Speaker ta karba tace na tabbata kowa yana Jin Hausa a Nan sabo da haka ba ruwan mu da turanci America ma uwata,aka yi dariya.


    Tarihin Amarya ta bayar a takaice a nutse Kuma, aka tafa mata,sannan tace Alhmdllh Alhmdllh nasan Amarya baki gaji siyar da dankunne da tozalin tsofaffi ba,Baki gaji siyar da mazari da Alli ba wannan sai Dan koli,Naila tace gaskiya ne wannan, sannan uwarta Bata kulla omo dan awo cewar Naila,bata da kanne ma bare ayi mata fitsarin kwance a mayafi ko Ango ya taba Jin zarnin a Jikin Amarya sanda Yana zuwa zance? Idan ya taba ji ya fada,Naila tace sai dai kamshi wlh,yeeeeee yan mata suka saki shewa.


   Hanan ranta ya baci ita da kawayenta masu zugata,tun a wajen ta fara kwalla,tace ba Wanda yasan sirrina sai Naila,wallahi wallahi sai sun San sun min habaici,sai na lakadawa Amarya duka bari a kawota a ranar a gaban mijin nata shege munafuki ai shine ya Fadi sirrina.


  Naila tace sabuwar Miya sabon tuwo,me za ayi da tsohon tuwo sai dai almajiri wlh ko a jefa a bola,Chikar gayu tace Kainuwa dashen Allah Amarya Beauty an gaji arziki gaba da baya, fara me farar aniya babu Mai ba sabulu natural daga Allah ce,hakora reras ango ka dace,Naila tace da gani ba yunwa a jikinta Kai da Ganinta kasan ta Sha Madara ta koshi tayi brush da Naman kaza,yayana yayi dace,yanzu nasan yayana ya auri mace, na tabbata ango kayi dace domin ka samu mace ta gari wacce zaka samu nutsuwa a cikin gidanka,wacce zata kula da Kai da danginka da duk wani Wanda ya shafeka.


   Duk kawayen su Chikar yawanci daga gidan yari suka fito babu na gari sai dai dai kowa shegiyar kanta ce shi yasa basa Jin kunya ana fada zasu saki shewa,Chika tace jama'a a gurguje bamu iya tashin hankali ba duk da cewa Kawata Nawwara wato Beauty tana da abokiyar zama

  

  Sabo da haka zan danyi nasiha ga Amarya,Beauty idan kika shiga ciki kika tashi hankalin ango to kinci amanata ni babbar Kawa,ko da abokiyar zamanki ta tsokaneki ki to ki nuna mata zaren ba kalar yadin bane, ki mata fatan shiriya idan Kuma anyi rashin sa'a tana da motsi a kanta to karki sa kishi a ranki ki tsaya iyakar iyawarki na ganin cewa an sadata da asibitin masu rangwamen hankali,Bamu ce idan an tabaki ki kyale ba,a'a bamu gaji haka ba,ba ruwanki da tsokana amma ana cewa kule kice chass amma a wajen me gida,yeeeeee ayiririri sai Chika lallai a nuna mata gidan kaso ba karya ba cewar Yan matan,Chika cikin nutsuwa taci gaba yanzu kishin fada da hauka jahilci ne da rashin sanin darajar Kai,a wajen me gida ake nuna kishi, Idan ta bashi Sadine ki bashi sukumbiya,aka kwashe da dariya a wajen,Rafeeq Yana dariya yace wannan yarinyar ban taba ganin Yar iska irinta ba,wai Sukumbiya,Kamal yana ta dariya yace ai dole suyi Yan gidan yari ne fa kaf kawayen maybe,waccen matar Spark din itace key na iskancin ita take musu rada.


   Sabo da haka Amarya a zauna lafiya da miji,mudai Munji dadi da iyayenmu basu gaji siyar da tozalin mata da Alli ba,Mun gode Jama'a Allah ya Maida kowa gidansa lafiya ta mikawa MC waya,Hanan ta kumbura iya kumbura ta fusata,Mohsin ango Yana jinsu ba yanda ya iya da su yaso dai ya hanasu amma sun shammace shi,Bai zaci haka zasu yi ba,yace maganin Hanan kenan da ta taba Naila ita zata dinga sasu suna mata rashin mutunci,bata San Naila ba,da ace bata kula Naila ba da lafiya za ayi bikin a gama,Naila ta koma ta zauna kusa da Rafeeq tace baka gaishe ni ba Ina Auntynka,Rafeeq yace ni kawar Nan taki badan Yar duniya bace da na sota ma,Chika? Yace ae ita amma duk danginmu mu kare a Yan gidan yari fisabilillahi,Naila tace gobe za a dakko malamar mu me yin wa'azi a gidan yari ta bangaren Mata,Matashiya ce irinmu amma akwai ilimin addini da hankali wlh ga wa'azi da koya zamantakewar aure,yanzu ku Dan masifa ma malamar me wa'azi yan gidan yari takewa wa'azi duk malaman duniya,Naila tace gwara irin tamu,shekarata ashirin a gidan yari a can aka haifeta yanzu an fitar da ita shekaru biyu da suka wuce Bata fi 22yrs ba wlh sai baiwar wa'azi,Rafeeq yace Allah ya kaimu ai harda Maza maji wa'azin,su Chikar ne suka gayyato mana malama Ikram,wlh indai kana son Chika zan Maka hanyarta,sai nayi shawara cewar Rafeeq,Kamal yace Amarya ango Yana harararmu ki koma wajensa kishin masifa ne da shi,Naila ta mike ta koma wajen Spark.


     Anci an Sha anyi liki,su Hanan anyi kyau anci Leshi harda zuwa fili ta rike hannayen Mohsin tana rawa duk cikin kishi,tana ta uban tikar rawa harda Karin haushi take tikar rawar tana yi da sauri da sauri kamar mahaukaciya,duk ta zauce,Mohsin yaga abin yayi yawa yace karfa ki sumar da kanki,kida slow music ki dinga uban rawa haka kowa na kallonki a mahaukaciya,Hanan ko kulashi bata yi ba kawai ta hada zufa tana haki tana tikar rawa a firgice harda dukawa,tana cewa uban kowa ya Gani bana kishi,Ta fada da karfi kowa Yana ji, Spark ya dinga dariya yace Kai jama'a Dan Allah ga kudi na dauki nauyi a Kai waccen asibitin mahaukata,Rass da Kwass fa ta haukace Baby,Ni na taba ganin kishi haka.


    Umma ce ta gaji taje ta fisgo Hannun Hanan ta fito da ita tace baki da hankali ne,Allah ya isa duk munafukan surukan da suka zuga aka min kishiya ai munafunci ne,surukai su dinga munafunci suna zuga dansu Yana aure sabo da an tsaneka wallahi Allah ya isa,su an barsu sun zageni sun zagi iyayena sai ni yanzu sabo da Ina rawa za'a hanani ta fisge hannunta ta fice daga wurin dinner din gaba daya sai gida.

   Can ta iske da ginta tsirari tana zage zage tace wallahi sai nayiwa amaryar duka za a kawota ne,sai na cinnawa gida wuta idan na tare,suma dangin sai wani bata hakuri suke suna Kara zugata a nutse.


    Bayan an gama Dinner Spark yayi hanyar Hotel da Naila ta fashe Masa da kuka tace nice babba a gidanmu mace komai Dani ake shawara Idan Umma suka ji ni wlh bazan je ba ka sauke ni,Spark yace ko Abba bazai ce min komai ba wlh Dan na daukeki nifa ba abinda zan miki nayi alkawari sai an kawoki gidana,Naila tace aje wajen Abban indai ya yarda zanje,Ta Manda Abba Dolo ne.

    Suna zuwa suka same shi a kofar gidan Yana jiran Naila zai mata kaca kaca,dama yace yau sai yayiwa Naila kaca kaca a gidan da fada, yace naji abinda kuka yiwa Hanan a wajen party ke Naila ki kiyayeni ke Naila ki dinga saukakawa ranki ato magana ta gaskiya, shike nan fadan wai ya gama,Spark yace Abba nima Kara na kawo, akan nace ta rakani unguwa wai baza taje ba, Abba yace ke Naila ki kiyayi fushin ubangiji,kibi mijinki sau da kafa da kika dawo gida mu me zaki yi mana? Banda ku cika mu da surutu da kawaye,Naila tace Abba fa hotel yace hotel fa tana hawaye,Abba yace Yar banza ni da Kubra zata kaini Hotel dinma ai San barka,so nake na samu kudi nima na dauki Kubra muje picnic.

 

     Spark kasa rike dariyarsa yayi,Naila tace Abba Umma fa sai ta sake haihuwa wlh,Spark ya sake shekewa da dariya yace Dole dai a yara a samu DNA na gado ko Yaya ne Naila itama doluwarce,Abba yace ki daina ja da ikon Allah,da ba a haihuwar za a haifeku ne,gashi muna ta yawa a arewa sai cinye zabe muke na shugaban kasa,namu ne  suke ta mulki,Abba da suke cin zaben ai wuya muke Sha munfi kowa Shan wahala,Abba yace ba abinda ya dameni da haihuwar Kubra,Allah in ya bamu muna so wani ma Yana kuka yake bashi da yaro.


    Naila ce ta tsorata Abba tace Yan hisba kame suke yi yanzu a hotel,Abba yace yo Karuwa na dauka da za a kama mutum,jiya naji wa'azi ance a dinga fita da mace yawo idan matarka ce,yanzu ance za a tafi dake kinki kina karyata malamai kamar marar Ilimi,Abba kawayena su Rayya fa, in banda hirar shanu me suka iya,Naila yaja gefe Yana mata kus Kus wai nasiha yace baki da hankali ke bakya koyi da uwarki,a gaban suruki kike jayayya da ubanki wallahi watarana idan kuka yi fada zai miki gori namiji ba Dan goyo bane,inja ki ja a gabansa Yana kallonki a marar tarbiyya,ki wuce ki tafi idan Kuma baza ki je ba wallah baza ki kwana a gidana ba sai dai ki kwana a waje ko ki tafi masallaci,Naila juyawa tayi tana fushi ta shiga mota,Spark da gulma sai da ya tabbatar Naila sai ta je, yace Abba a hakura tunda bata so da an barta.


  Abba yace a'a kuje kuje tafi da ita ai ba a biyewa mata haka suke da yanga ai idan bata yi haka ba ai bata cika mace ba yaro,ai macen kenan,Spark yayi godiya Yace Abba Allah ya Kara  sutura,Abba yace Alhmdllh sutura Kam Ina da ita ma ta isheni haka, Spark yayi dariya a ransa yace wlh Abba Ina ga bokaye ba mutum suka sawa mamansa a ciki ba kawai aka haifo shi.

  

    Naila mota ta shiga tana hawaye tace ko Kaka bamu gaisa ba da shi,Gani yayi bilhakki take Masa kukan,yace ai ke dama ba a abin arziki Dake,yace driver juya ka kaita gida kar ace satota nayi ,fushi yayi,Naila ta kalleshi kadan tayi shuru ya Maidata gida,ko sallama bai mata ba yasa driver ya ja mota suka Kara gaba,Yana mota sai cewa yake hmmm ya ja Kwafa yace yarinyar nan zata gane kurenta bari a kawota.


    Naila bata samu Abba a waje ba tayi sauri ta shige dakin da suke zaune da su Rayya,suma an dawo dasu daga wajen Dinner har sun kwanta,Naila ta shugo tare da cire kayanta ta canja marasa nauyi ta sa Hijab ta wuce dakin da kaka yake tare da wasu dattijan,Yace Naila,tace na'am Kaka,yace shugo Maza ki karbi sakonki,Shiga tayi ya Bata magunguna yace ai duk kin San yanda ake amfani dasu,tace ae Kaka,yace to zauna mana,wuri ta samu gefe ta zauna ya fara mata nasiha sosai,Naila tana ji tana to.. to.. to.. ko Dan kuka babu,ya Dade Yana mata nasiha dattijan ma da suke daki daya, suka tayashi sannan yace idan an kaiki watarana sai kuzo min ziyara ko? Naila tace zamu zo Kaka,yace to gasu an dai kaya an nuna miki ko? Naila tace ae Kaka na gode duk ance ango yayi komai sai da ka kawo min kayan kitchen masu kyau harda tv plasma katuwa da fridge.


 Yace ai sa na siyar muka tafi birni da goggo muka siyo miki na Yan birni,da ace ma ango baiyi komai ba ai ni zan miki kayan dakin,goggonki ta baki naki magungunan ko? Naila tace,yawwa wannan naki ne karki wasa dasu yanda tace ki Sha haka,Naila tace to tayi musu sallama ta tafi dakinsu tayi kwanciyarta.


    Washe gari karfe 11am ne daurin aure,wanka duk suka yi ko wacce taci gayu,Umma Shadda ta saka maroon,Naila da kannensa duka shadda ce pink,Ango kuwa Fara ce Kal ta Sha aiki,Abba yau yasha kyau kamar ba shi ba,Shadda Gezna Mohsin ya Dinka Masa Arsh,gidan Amarya aka dunguma daurin aure, Baban Amarya yayi gayya masu kudi ne kawai suke zuwa,11:30am aka daura auren Beauty Nawwara da Angonta Mohsin Hashim kan sadaki dubu Hamsim.


   Hanan tana Jin labarin tace ai bata yi tsada ba wlh,dubu Hamsim duk kudin Ubanta Sadakin yarsa dubu Hamsim ai sai a saka mata million Daya Muji,kawayen Hanan da danginta suka ce munje gidan surukanki wlh ana ta Shan lemuka mu lemo an kawo mana kadan har ya kare,wlh karki yarda kije a karo mana namu ko da bala'i.

  

    Hanan gidan ta tafi lokacin an dawo daga daurin aure ansha pics da Amarya Ango yazo gida Yana ta dauka da Yan uwa,Abba ana yin pics ya fita sallamar masu zuwa Masa Allah sanya Alkhairi,Hanan tasan babu me saurarenta sai Abba wajensa taje sanye cikin Leshi taci takalmi da jaka,tayi kyau matuka,Abba Yana Ganinta yasan matsala ce wajenta ya nufa kar ta kunyata shi a cikin mutane,tana zuwa ba gaisuwa ba komai Abba lemo nazo a karo mana namu kadan aka bamu ni da kawayena sabo da ni ba'a kaunata sai ta fashe da kuka.

  Abba yace karki bata mana shagali ke wai bakya son zaman lafiya ne,Lemo carton nawa aka Kai miki sabo da Allah,ai yayi mana kadan ni dama nasan an tsaneni ba a kaunata,Mohsin ya daina so na yaga wacce ta fini kyau,Abba yace ai kema ba mummuna bane ki kwantar da hankalinki Hanan bazai wulakantaki ba,karki ga Amarya ta fiku kyau ki tsorata, duk mun San Amaryar nan tana da kyau amma kar wannan ya dameki,

   Abba yace kin San Kubra baza ta Kara miki ba domin an baku da yawa, sabo da korafinki fa abinci da lemo da ruwa da kaina na ebar miki nasa aka Kai miki,jama'ar taki nawa ce? ko Kasuwar singa kika tara ne,Hanan tace ba komai to amma wlh sai an Kara min ko na shiga ciki ayi wacce za ayi dani,kawai sabo da an rainani sai a dinga nuna min kiri kiri ba a kaunata,Abba yace ko kinje Kubra baza ta Kara miki ba,cikin gudunmuwarsa yace lemon duk carton daya nawa ne? tace dubu daya da wani Abu da manya Kuma ya kusa dubu biyu,dubu biyar ya zaro ya mika mata yace gashi jeki ku siya,kudin ta karbe ta juya ta tafi a Hakan ma korafi take yayi kadan.

     Tana zuwa suka hau shewa da kawaye tace ai wallahi sai da aka bani kudina chass, ai basu gaji da ganin tashin hankali ba wlh baza su huta ba indai nice har sai an gaji an saki Amaryar.

   Ganin Hanan da haka zata kori Amarya.

   

      Spark kuwa ba zuciya akan Naila duk da yaji haushinta jiya amma Allah Allah yake yazo ya ganta,gidan suka shiga tare da su Rafeeq suka gaida iyaye tare da yi musu Allah sanya Alkhairi,Naila dai sai pics suke da Mohsin my love yau an zama ango yau za a kawo Maka Amarya fa,Mohsin Yana dariya yace yau zan karbi sabon kaya,ta dafa kafadarsa suna ta surutu,Spark ya kalleta yace da nine ai da tuni ta fara korafi,Mohsin yace kema nan da 3days ai za a kaiki,Naila tace ae mana munyi anko,tana ganin Spark tace takawarka Lafiya na Naila,anyi fushin anyi fushin zuciya amma zuciyar ta kasa hakura da ni,ya zaka yi da Jamilu,dariya yayi ba shiri,da ya shugo yace bazai kulata ba sai ya nuna mata fushi yake da ita amma gashi ta sashi dariya a banza.


    Rafeeq Yana ta kallo dama abinda ya kawo shi kenan,Su Dije suna ganin Rafeeq sun zaci irin Spark ne,shima Spark din basu San sabo da Naila ya saurare su ba,Kanin mijin Tantiriya ga kanin mijin Tantiriya, Rafeeq ya wani bata rai wai kar wata ma ta so shi,ya tsani mace tace tana sonsa shi,Spark yace Kai kawayen mu ne na kauye wlh karka Raina mana kawaye zan karbe jarin Dana baka,Rafeeq dariya yayi kadan yace ai Kai yanzu Yaya sai an Maka uzuri,gaishe da su suka yi,Rafeeq ya Kalli Rayya Dake ta kallonsu tace wannan shi dai Yana da da talatu ne fura,ta nuna Rafeeq,Spark murmushi ya saki,to naga Yana ta wani yanga kamar mace,Rafeeq ya daure fuska tam, Spark shi Naila ta dauke Masa hankali tazo tana Masa rada kayi kyau ko Jin abinda Rayya kewa Rafeeq baya yi.

 

     Rafeeq kuwa Naila ya tambaya yaushe za ayi walimar ne taku? Naila tace 3pm to 5pm sai a wuce Kai amarya,Kamal yace na taba Jin walima mata da Maza a hade,Rafeeq yace haka tafi dadi.


     Bayan sun tafi zuwa karfe uku Rafeeq harda canja Jallabiya da carbi a hannu na tafiya walima,Spark ya dinga dariya yace ai Kai ka fi Angon ma,idan iskancin Nan kake sha'awa kayi mana kaima,wannan masifar son mata haka Kuma kace Kai kar wacce ta soka,Rafeeq yace ai ni Yaya nafi so na kallesu daga nesa sunfi birgeni,3pm mutane suka cika a Inda aka kama za ayi wa'azi,Misam maye sai da yazo,Rafeeq ya ganshi yace Misam kana birgeni Kai kawai mata kaji dadinka,baka da control ba komai,zanci uwarka wlh sa'anka ne ni,kaima idan kana so ka fara mana sai son mata a baki da Ido, Malama ce ta shugo.


   Bata fi Naila ba Yar kyakyawa da ita me Dan haske amma ba can ba,ta Sha hijab har kasa,idonta tar a kan kowa,Spark baki ya tabe yace wannan ce zata min wa'azi naji Allah bazan batawa kaina time ba ya mike ya fice, dake a ciki bangaren mata daban na Maza ma daban.

   Matan su Naila duk an Sha Abaya,Maza yawanci da jallabiya,Amarya da Ango ana zaune a high table anyi shigar larabawa ta Amarya da Ango.


   Malama Speaker ta dauka suka hada Ido da Misam ya kashe mata Ido daya tayi sauri ta dauke kanta dama shi da Rafeeq duk suna gaba gaba,Kuskure Malama ta sake yi na kallon Misam ya daga mata gira tare da kashe mata Ido,ya radawa Rafeeq na samu Daya yanzu Malama,Rafeeq yace cikin rada ga Chikar Gayu nan ta shugo,Misam ya basar sai bayan Dan seconds ya kalleta,Chika ta kalle shi suka hada Ido gwalo ta Masa ta zaro harshe,dariya yayi ya sake kallonta ta turo kirji gaba tayi girgiza kadan,dariya yayi a boye yace ta sake yi wai,kanta ta dauke,yace Ina Amaryar Yaya Spark ne? ,Rafeeq yace gata can mana ai wannan tafi karfin kanka sai dai Spark na sallama mata,gata can a gaba Inda Chika take.


   Malama ce tayi gyaran Murya tare da sallama,sannan ta bude da adduoi,Misam Allahu Akbar ya furta sai da kowa yaji,Malama Ikhram ta gaji da iskanci su Misam magana daya tayi sai sunyi Kabbara,sun gama Raina mata hankali,Misam tayiwa magana siiiiii....siiiiii...hey ..hey....siiiiii,dagowa yayi daga danna wayar da yake suka hada Ido, fito tayi Masa ta nuna kofa da bakinta wai ya fita,Malama da fito,ko kulata baiyi ba yaci gaba da danna wayarsa,Mohsin ya radawa Amarya su Spark duk gasu da Kamala kyawawan gaske gasu da aji sai iskanci fal ciki,Beauty tace naga alama kuma kamar basu suke yi ba,sai su Fadi Abu su fuske,su Rafeeq basa saurarar Malama waya suke dannawa amma ko ya tayi magana sai sunyi Kabbara Allahu Akbar.


    Malama tana Jan Aya da hadisi tana wa'azinta sosai da sosai,ta Fadi mene ma auren gaba daya,da sharudan Dake ciki,sannan ta dawo kan yanda ake zaman Aure,ake tattalin me gida da kula da shi,tazo tana koyawa Amarya yanda ake tarairayar miji dama duk irin malaman Nan fitsara sukeyi su fake da wa'azi,da Allah Amarya ayi dinkunan zaman Palo Banda zuwa a dinga manne jiki a gidan miji,ki dinga saukaka Masa yanda zai cire su cikin sauki,Rafeeq kasa kasa yace wannan fadakarwa ce me kyau dole na dakko malamar Nan har Abuja ta koyawa su Mima rayuwa,akan kula da yara da musu tarbiyya,Misam yace maulidi zamu ce zamu hada sai mu dakkota.


  Chikar gayu tace wannan gaskiya ne ke Beauty kinji dai a saki a Palo su Sha iska,Malama tace ashe Kuna ganewa Alhmdllh Alhmdllh,ba ruwanki da kishiya kiyi ta kanki Amarya,me gida idan ya dawo yasha aiki ya gaji ya kamata ki tayashi cire kaya,idan ya hada zufa ki tanaji handkerchief dinki me kamshi ki goge masa gumi,sannan ki tarbe shi da ruwa me Sanyi,ko wani dan zobo haka me Sanyi,Maza suna son girmamawa,karki zo ki wani tsaya Masa kerere kamar namiji,da karairaya da kissa cike da girmamawa zaki bashi zobonki me Sanyi,idan ta kama ma ki bashi a baki,Maza suna son kulawa,Rafeeq yace haka muke Malama musamman ni,Malama ta Harare shi.


  Tace shimfidar aure Amarya, Chikar gayu tace a tafawa Malama anzo Inda muke jira a bata darasi,Naila tace bari na bude kunne Malama nima Amarya ce anzo Inda muka fi wayo,yeeeee suka saki shewa mata.

  

    Kamal yace ni dai wajen Nan Ina da mutuncina bazan iya zama ba ya tashi ya fice,Misam yace mu mun zubar da namu wlh sai naji komai,Maza matasa duk sun zuba kunne,wani har cewa yake Malama mu ba a zo kan Maza ba,tace zanzo ne ku saurareni.

    Sanda ta fara bayanin kwanciyar aure Mohsin kunya ce ta lullube shi,Rafeeq yace ni dai na kamu da son Malama ta San harkar irinta nake so,Misam yace idan ka aureta zaka Sha dadi ko Mai ta iya,yace musamman idan aka fada bedroom.


    Naila kuwa cewa take an gode Malama Allah ya biya da Aljanna Munji mun dauka zamu yi,Rafeeq yace Kai nima na tashi daga wajen Nan kar a rainani Chikar gayu sai raini take kawo min,Misam yace dani za a kare sai an rufe addua da Dani,Rafeeq ma ya tashi ya fece,Maza duk masu Yar kunya arcewa suka yi,Mohsin ya gaji shima badan dole ba Ina zai zauna sai dai su Tantiriya irin wajen sune,da kyar ya daure aka gama wa'azin Nan,Misam ana shafa addua yace har an gama gaskiya anyi sauri,Malama ta gasa Masa harara.


   Suna fitowa aka Maida Amarya gidan Ubanta dangi aka mata nasiha sosai Daddy ma sai da yayi nasiha sosai,yace wlh idan naji watarana ko da wasa kin Masa gori na bashi gida da jari ko wani Abu ko kika yiwa kishiya gori wallahi Beauty sai Kinga fushina,na fada miki banza son gori a rayuwa,kayiwa mutum Abu tsakani da Allah mace tazo tana yiwa miji gori shi yasa Maza basa son zama a gidan mace ko gidan Baban mace,badan ke na bashi wani Abu ba,karki sake naji gori ko kiyuwa kishiya gori,Beauty tace to ko kuka itama sabo da sun Saba da gidan yari akan aure Kuma wanne kuka zasu yi,yayi mata fada Sosai sannan ya sata a mota da kansa,ga Yan uwa da kawaye,Naila har da ita a Yan Kai amarya suna gefe suna yiwa Amarya rada,Beauty tace karku damu fa ni kishiya Bata gabana,bana tsoron kishiya, gidan ta tarar sai na bata littafina dictionary na duk wani iskanci sai ta haddace shi tsaf.


   Hanan Kuma daga ita sai Yan uwanta a Palo suna zaune suna jiran Amarya,Hanan tace a yau ana watsawa zan mata dukan tsiya wallahi,yau sai na daki banza,Kuma ba uwar da zai iya yi min,ai nasan lagonsa ko me nayi Ina bude Masa Nono sai Kiga yayi mukus,sabo da haka yau ma haka zanyi baza kuji komai ba,shi da nono ai Inda kisan asiri.

   Dariya suka yi da shewa,suna habaici habaice tun kafin Amarya tazo.


   Naila suna mota tace babu fa wata Amana da zamu bawa Hanan,kawai a wuce da ita part dinta,Chika tace Amanar Beauty ita ta isa ma mu Bata Amana har wani a fara Kai mata Amarya ita din banza,Beauty tace muna zuwa ku wuce Dani part dina,kar muje ma ta fada mana magana bazan iya kyaleta ba.

   Suna zuwa manya dangi suka yi suka yi a fara Kai Amarya wajen uwargida a bata Amana,Beauty tace ku nuna min hanyar bangarena akan a bata amanata gwara na Kai kaina dakin miji wlh bazan yarda a bata Amana ta ba.


    Su Naila suka ce muje ke suka tafi da Amarya bangarenta Wanda ya gaji da haduwa,suna kaita,sai ga Hanan da sauri tace ko ba a kawota wajena ba zata fito ne a banza na ganta,Dan ba a kawota ba sai me ko ance muku Ina son a bani amanarta,ko an bani Amana sai na ci,Shewa kawayen Amarya suka saki da guda,Naila tace 2+2 ga sabo ga tsoho wlh sai dai Yaya ya dauki sabo.


   Amarya yau akwai harka a sakarwa Yaya jiki so nake da safe naga bakinsa kamar gonar auduka a shayar dashi zumar da  ai taba Sha ba,wata Maryam itama daga gidan yari ta fito tace gobe Dan Allah Beauty idan munzo mu iske gadon nan a balle,karki ji komai ko an balla Daddy a ranar zai iya siyi miki sabo.

   Chikar gayu tace an taho da ruwan zafin ne kizo ki Kara gasa wajen Nan,yau akwai Kwalbewa,Zaiji sabon ihu.


   Hanan ba shiri ta bar dakin ta koma bangarenta tana huci,suna ta shewa sun cika dakin Amarya, Dattijai sai barin dakin suka yi,ba a dade ba aka kwashe Yan kawo Amarya kaf daga Naila sai Chikar gayu aka bari a gidan suna zuba iya shege.

     Spark Naila ya kira yace sun wuce Abuja,tace ko sallama ai shike nan ka kyauta,to ba yanga kike min ba,ai jibi za a kawoki ne yan mata Ina Nan Ina jira,Hallare ce bana tsoronta ni,dariya yayi yace hmmmm Allah ya kaimu.


   Bangaren Mummy kuwa ta samu Chikar gayu tayi tafiya sai soyayya suke zubawa da Basiru har an fara maganar aure,Mummy tace ni Alhaji zaka iya dinga zuwa gidana ma idan munyi auren nayi zamana a gidana,Basiru yace a'a a gidana zaki zauna bangarenki daban na Suhailat daban,Mummy sai murna take yi tace daga Nan sai mu wuce kasar waje,yace ba Inda bazan kaiki ba,Mummy farin ciki ya mamayeta.




Masu Sharhi Ina godiya





AsmaBaffa

No comments