Breaking News

Tantiriya a Gidan Yari Book 1 Paga 91-95



🏫 TANTIRIYA 🏫

        A GIDAN YARI


 BOOK 1


                  91-95



Official


By

AsmaBaffa



SADAUKARWA GA

AIDA MAMAN TASNIM



Page naki ne

REINA



*MISKI 4in1 Hamil musk*🌹 munkawo original miski daga *Egypt* miskin da indai kinyi amfani dashi zakiji dadi  sosai domin  kuwa sekinyi godiya hajiya💃💃 👍 yana dauke: 1.*Musk oil*  Ana sakashi acikin gaba  sannan zaki iya ringa shafawa a pant dinki  lokaci zuwa lokaci  ba lallai  sai bayan gama al'ada inda hali za'a iya ringa sawa Koda yaushe yana maganin infection yana gyara gaban mace sosai 🙈ko yaushe gurin yakasance cikin kamshi 😇 kamshin sa yana zama sosai bayaga haka sunnah ne amfani da miski 

  2.*Musk cream* Ana shafawa ajiki gaba daya musamman  irinsu  cinyoyi,  kasan mara  yana sa jikin mace koyaushe yakasance cikin kamshi kuma yana gyara fata, yasa tayi laushi 

 3.*Musk soap* sabulun tsarki na Musk; wannan sabulun miski ne  ana tsarki dashi  yanada kyau sosai👍👍 yana kashe infection sannan yana  wanke duk wani  datti dake  gaban mace da karni musamman bayan gama period 🙈 

4. *musk powder* Ita wannan powder din ba normal powder bace tana da sinadarai masu kyau acikin ta🤭 tana magance warin jiki, warin kashi sannan duk gurin da ake sa turare zaki iya ringa shafawa ita a ko ina ana iya shafawa har fuska in kinso  zaki iya sawa ko ina dai ajiki zaki iya ringa shafawa💃😇


Gefedaya munasaida ingantattun magungunanmata nasokoto munamaraba damasu siyandaya kosari numbermu itace 09039320715 pls inbasiyazakiyiba hajiya karmubatawa juna lokaci



DAN GIRMAN ALLAH KU DAINA FITAR DA SHI,NA GROUP DINKU NE FA KU KADAI LITTAFIN,IYA GROUP DINKU,DAN ALLAH MASU BAYARWA TA PRIVATE KU SANI BA IZINI NA WLH.




      Goggo ce ta fara fada tace zaki tsaya ko sai na make ki,da kyar Naila ta bari suka duba ta,Goggo ta hau salati tace anya kuwa ba sai anyi dinki ba,duba ki gani Tani,Tani tace dole a nemo Likita fa mace ta duba mana,Goggo ce ta fito sai ga Spark ya Sha wanka cikin wata sabuwar Gezna Yana walwali kalar Silver, sai annuri yake Goggo tace ka kira Likita mace ta duba yarinyar mu,mu tabbatar ba sai anyi dinki ba,wannan wlh ni na san za ayi haka,Spark yace ba fa wani dinki ni nasan kan abin na gani ba komai,Goggo tace Dan Allah idan zaka Nemo Likita ka nemo ko wallahi na fita da ita har asibiti,Spark ba yanda ya iya da su haka ya kira Nurse din Mummy tazo gidan ta duba Naila sosai tace babu dinki ba sai anyi komai ba zata warke ta rubuta magunguna tace a siyo mata zata fi saurin warkewa,sannan Dake babbar macece ce ta kira Spark gefe tace ya bari ta warke kar ya sake nemanta Kuma ya dinga bi a hankali ta bashi shawarwari.


   Spark Yana gama ji yace tabi ta bayan kunne a gaban Nurse din, sai kace kune Allah to bazan bi dokar ba,ba abinda zai faru,za a raina min hankali,Allah yace ayi kuzo Kuna min shishigi, arna dubu nawa na kashe jiya sai Allah ne yasan adadi,Ina ta kashe su a cikin dadi ba wani takobi,Nurse tace ai Kai zaka aikata Spark banyi mamaki ba,idan ka gama da ita ai ka rasa Kuma,bazan rasa ba inshaallah,ku likitoci kullum sai mugun fata,sanda Naje nayi aure na da wa nayi shawara shike nan ban isa nayi komai ba sai a dawo ana damuna.


  Su Goggo dai sai da suka tabbatar an siyo magani sannan suka yi sallama da Naila zasu tafi gida Kuma,Naila ta bawa su Rayya powder da jambaki da sabulai na kwalliya cikin na lefe ta eba,ta bawa su Goggo ma suka ce baza su karba ba suje su kwashe mata kaya dama kawaye ake bawa kawai.

  Rakasu tayi har mota suka tafi,daga can Spark yasa cikin cousin dinsa yace ya Maida su gida na Kano su kawayen Umma ne sun waye a sasu a jirgi zuwa Kano,su Kuma na riga sunfi kusa da Jos a sasu a na Jos ya rakasu har kauyensu sannan ya dawo,Yana murna zai samu kudi yayi yanda ake so kuwa.


   Naila da kyar ta koma sama tayi wanka ta kalkale ko Ina a jikinta ta fito ta shirya a hankali ta saka atamfa half boubou wacce gaba yafi bayan tsayi da skirt,ba karamin kyau tayi ba,tayi daurin dankwalinta me kyau Wanda shima daurin koyo take faman yi kullum a waya iri iri,tana da basira shi yasa take iya nadawa kanta.

   Tana shafa turare ya shugo bedroom din,Nan take ta koma kalar tausayi dan kar ma Spark ya ganta normal,abincin da Mummy ta kawo ya shugo musu da shi yasan fitar ma matsala ce a wajenta.


   A baya idan ya Kalli Naila sai yaga tana Jin dadi amma yau sai yaga ta dauke Kai da sauri duk ta diriri ce ta fara soshe soshe kamar me kaikayin jiki,yace wai me nayi ne? Naila tace wa ta nuna kanta tace ni a'a ba abinda kayi,kalle ni to hannayenta ta hade waje daya ba tare da ta kalle shi ba tace to ni da na kalle ka Kuma sau nawa Kuma ko a prison ai na kalleka da yawa tayi dariyar dole Kuma duk Bata kallonsa sai kallan gefe da gefe take,hannayenta ya ruko a hankali,idon Naila ya ciko da kwalla,yace mene ne? Ko Kari kike so ne? Kai yanzu idan nace ka Kara sai ka Kara yi? 


    Wa yaki dadi da gudu ma zanzo,Naila shuru tayi tare da canja zancen tace ni dama gidanku ka kaini,gidan Mummy? gidanku na asali gidan Mima naga da yara kannen ku da yawa sai ka kaini yau ma na yini mu Saba da su sosai,Spark ya gano wayon Naila, yace ni ba gidanmu bane,ko ance miki ni gidanmu ne ban taba kwana ciki ba,to kira Chikar Gayu tazo ,tace baza ta zo ba sai yamma, Gani na isheki nima ai Chikin gayu ne idan ita Chikar gayu ce to ai nima Chikin gayu ne,zaki sa ma na kulle gidan gaba daya,shuru tayi ya dakko ta ya Maida ta gefen bed din suka zauna ya hada musu tea da kayan soye soyen a Baki yake bata har suka koshi,ya kwashe komai ya Kai kitchen masu aiki sunzo suna ta gyara gidan ko Ina, shine ya gyara bedroom din ya samu har ta fara bacci,tashinta yayi da kiss a baki,ture shi tayi da sauri tana harararsa, yace makwaftanmu sunzo gasu can sun Kai su biyar.


   Naila jiki ba kuzari ta mike tace ya zanyi yanzu tafiyar ma da kyar nake yi kana gani ga mutane kowa ya gani sai ya gane sabo da Allah wannan abin kunya Ina zan kaishi,Spark yace ni tafiyar ma birgeni take yi wlh sai naji kamar sake yi nake yi,taso na dauke ki,Zasu ce bamu da kunya,ai gwara suce bamu da kunya akan a Ganki kamar wata Yar kaciya Kuma da gefe daya fa kike tafiya,Spark daukanta yayi cak ya fice da ita Yana mata rada a kunne,tana wutsil wutsil da kafafu,har Palo ya kawota ya ajiyeta a kujera sannan yace bata min lokaci zata yi na dakko muku ita,Yan layin ne dukkansu sun San Spark sabo da shi Spark duk Inda ya shiga ana zama da shi lfy duk Yana zuwa suna gaisawa da makwaftan sa,sabanin wasu suzo unguwa babu Wanda suke kulawa sabo da suna da shi,babu kyakyawar mu'amula da mutane,ba abinda zai faru na jaje mutum yaje ko na farin ciki yaje,ko Kuma Ta'aziyya,wani maigidan ma sai makwafcinsa ya rasu bai sani ba,baya kula kowa ya fita da sassafe ya dawo da dare bai ma San me ake ciki ba a unguwa,wani iyalan sa ma bazai bari suyi harka da kowa ba,wani abin kuma idan ya same ka kafin ma Dan uwanka yazo makwafcinka yayi Maka shi,shi yasa Spark Yana zuwa duk abinda ya faru har gudun muwa yana bayarwa komai kudin mutum.


   Yaran layin indai yaga wasu ko bai sansu ba Yana basu kudin school sai yayi ta rabawa yara alawa da kudi,duk sun San Spark matan ma da basu sanshi ba sun San sunansa a baki.


   Zama yayi a gefen Naila yace wannan duk makwaftan ki ne,Kinga Hajiya Babba,ga Aunty Maryam,Aunty Maijidda,wannan Ummu Salma,Kinga Aunty Naja'atu,Naila da fara'a ta gaishe su suka amsa tace Sunana Naila,suka ce kamar yanda ya fada miki makwaftanki ne mu da fatan watarana zaki kawo mana ziyara,Spark yace zan kawo ta ai gidan ko wacce,Hajiya Babba tace ai ka kyauta wannan shine zaman tare ai hakkin makwaftaka ne,ace sai dai talakawa suyi mu banda mu ai bai dace ba sabo da Allah ya rufawa kowa asiri,Naila haka duk langonta ta mike tana daidaita tafiyarta ta shiga kitchen.


    Ruwa da lemo ta kawo musu sai kayan gara da aka yi mata dublan da Alkaki harda Chin chin ta kawo musu,tace Dan Allah kuci idan ma baku ci ba sai na zuba muku abinku a Leda,kadan suka ci suna hira,Hajiya Babba tace Amma Spark matar nan taka Yar Fulani ce ko? Spark yace sosai ma,tace ai naji maganarta gaba daya gata mashaallah kayi dace,harda cewa na gode cewar Spark.

    Sun Dan jima sannan suka tafi,Naila tace gwara na zauna a palon kar wasu suzo,kafin ta rufe baki kuwa sai ga wasu makwaftan suma sun zo,suma Spark ya gabatar dasu basu Dade ba suka tafi,sai Kuma ga Yan uwan Spark Badia da Anam,sai wasu Yan matan su biyu suka zo,sai Arham,da Shahid suka zo gidan.


  Badia tunda ta shugo take kallon gidan tana wani tabe baki,Naila tace sannunku da zuwa,iya mazan ne suka amsa da fara'a ba ruwansu amma su Badia ko amsawa basu yi ba,Badia tace Kai ku zauna mu da gidanmu  suka zauna,Naila tunda Taga haka sai ta kama kanta suka gaisa da mazan kawai ta share su Badia,au mu baza ki gaishe mu ba? haba yara Kuna kannensa ni zan gaishe ku Yayanku nake aure fa.

    Arham yace da gaskiyarki Aunty wlh karki gaishe su.


   Spark ne ya sakko daga step ya daure fuska ba wasa ganin su Badia, System dinsa ya dakko ya sa a charge sannan ya dawo ya zauna ya jawo Naila ya dorata Saman cinyar sa,Arham yace Yaya Spark ya kalle shi babban yatsa ya dagawa Spark wai yayi dai dai,dariya Spark yayi yace  yaro kayi biyayya ka samu aikin yi,Arham yace ai tun jiya nabi ma,Dan Allah ka bani kudi na siyi wani agogo da wando,Spark yace ai baka da matsala indai kabi Amarya ba wando ba har da rigar ma sai a siya Maka,Shahid yace gaskiya Yaya wlh ka iya zabe,Spark ya mika Masa hannu yace mu gaisa,Naila dariya tayi tayi derere Saman cinya tace Arham Dan shiga kitchen ka debo muku drinks nidai bazan tashi ba,ya shiga kuwa ya debo musu harda kayan gara din ya zubo musu,a hankali Naila ta zame ta koma Saman kujera,Badia taki ci tace sai kace mayya,Spark yace to da mece ke? Ai mayyar ce ke duk gidanmu ai kece kike kama da mayun,ai kece full definition na mayya,Anam tayi dariya,yace Ido kamar na kwado zaki zo ki min iskanci,ko baki San gidan wa kika zo bane.


   Naila ce ta katse maganar tace ya ka bar System din a can? so nake tayi charge,tace okay tun safe muke baki ai,ni fa Chika bata zo ba har rana tayi,Spark fuskarsa ya dora a Saman kafadarta yace zata zo ne.

   Spark kannensa ya kalla mata Wanda basu da aure yace kai kuyi Maza ku saka kuka kuce Papa ya muku aure akwai baiwa a cikinsa,Arham suna dariya suka ce Lallai Yaya ka fara canjawa baka taba fa shiga harkar mu amma gashi yau sanadin aure muna ta Hira harda dariya,yace ka taba ganin me Iyali shashasha? yanzu ko kanka na shafa sai kayi albarka yaro,har su Badia dariya ya basu,Da kuwa ni kaina bani da albarkar bare na shafawa wani yanzu kuwa yaro kayi kokari na sa ma albarka binka zata yi, sun Dade suna cin dariya Spark yayi aure ba zaman lafiya,suna komawa gida suka hau bawa Mima labari,wlh Yaya bashi da kunya har muka taho tana cinyarsa,Mima tace ku kuka Kai kanku ai ,Kuma ko me tace Mima wlh baya musu Inda kisan rakumi haka take jan sa cewar Badia,tace itama ashe irinsa ce tayi shuru har da gyara zama sai faman rada suke yi,Mima tace wannan anyi tambadaddiyar Amarya,ai zanje ne da kaina.


  Kwanciya Naila tayi a kujerar tayi matashi da cinyar Spark Yana ta mita yace ko dan Nono ban taba ba yau an hanani sakewa sai an jawo min ciki ya fito banyi komai ba ban more ba Amarya ta samu ciki yau lafiya gobe Amai...kafin ya rufe baki Misam ya shugo, ya tashi Naila yace ke tashi kar gaban rigarki yayi kasa Mayen mata yazo kar ya ganar min nawa na sunna,Misam yaji haushi ya juya zai tafi Spark yace Allah ya raka taki gona dama ni haka nake so duk kunbi Kun takura min,Misam dawowa yayi yace to na fasa tafiyar ya zauna,Rafeeq ne ya shugo shima yace girki ne ya kawoni Muji hannun Amarya,Spark yace sabo da matarka ce ba,ko ni banci ba bare kai,a dinga godiyar Allah Spark, jiya ka koshi fa da dare, Amarya ba ta ciyar dakai ba,Naila duk rashin kunyar ta sai da taji kunya,su kuwa ko a jikinsu,Spark yace girkin akwai dadi ba'a koshi ai,Misam zaiyi magana Spark yace karka ce mana komai ato, baya so ya tonawa Misam asiri yace Yana neman mata,dariya Misam yayi yace zan baku mamaki wlh,Rafeeq yace Ashe Spark sabon Uba zaka yi kwana Nan? Uban wa?Spark ya furta yace sai dai uban wasu ba nawa ba, Mummy zata yi aure Ashe cewar Rafeeq,Spark yace shine Kuma Ubana,Rafeeq yace naga Sai zumudi Mummy take,Misam yace ai tuni na gane Maman Spark Harija ce,ai wajenta yayi gado,Ubanka ne Hariji marikin ka dai shine me mataye,Naila tana ji a ranta tace yau na shiga uku sai buzu na,Hannun Hariji na fada shi yasa abin yayi yawa sai hawaye ita kadai ta boye fuskarta a Jikin Spark suna ta hira ita Kuma tana ta kuka,Spark yaji dumin hawaye a jikinsa da sauri ya dago fuskarta yace me aka yi miki Kuma? Naila tace ba komai,Rafeeq ne ya Kalli Misam suka hada Ido yace ka tsorata Amarya ba ruwana,Misam yace ni me nace daga nace Hariji ne sai kuka,idan kasan zaluntar yarinyar nan kake yi ka fada mana,Naila tana goge hawaye tace ni Allah ya Gani zaluntata yake yi,bana son soyayyar nan Dan Allah ku kaini gida.


   Rafeeq dariya ya kama yi a boye,yace Allah na gode Maka,Spark Allah ya biya yau naga tsoron Naila,dama tunda nake ban taba ganin Amarya irinta ba babu ta Ido,yau Naila ce take gudun Spark tab abin babba ne.


    Misam yace to ke Amarya haka ake yi daga wasa Kuma,Naila tace ai nasan ba wasa kuke ba tunda ai ni nasan mene baza ku gane ba,Misam yace baki dauki wa'azin Yar gidan yari ba kenan,Spark yace ki daina biyewa yaran nan fa zasu kaiki su baro,Chika ce tazo gidan a motar Misam ta jiya,ta Sha gayu cikin Arabian gown,ta shugo da sallama,Rafeeq ya kalleta kawai ya dauke Kai,Misam ma haka,Spark yace dama kuka take kinki zuwa,Chika tayi mamaki tace Naila da kuka? a'a sai dai na karya Naila da bata kuka.


  Naila hawayenta ta goge da sauri tana dariyar dole kamar ba komai,tace naga idonki a kumbure Amarya lafiya? Naila tace Abba na tuna,Chika tace tabara ce wannan kawai ta ganin miji in ba iskanci ba kawai ki kama yiwa mutane kuka,Kaine kake kulata ma,Spark a ransa yace wayyo cika barkono da gishiri na barbada mata,Chika ce ta Kalli Misam ta dauke kai,hannun Naila ta fisgo ke taso dalla,Spark kamar shi aka fisgo yace wayyoooo......yasan kwanan zancen,Naila kamar gurguwa haka take dingishi tana tafiya da gefe daya,Rafeeq yace agwagwa tana wanki,Spark yace zan ci uwarka wlh, dama sa Ido ya kawo mu cewar Misam,duk nasan ai Yan sa Ido ne suke zuwa Spark ya fada Yana harararsu Yana danna waya.


     Chika har bedroom din Naila tace ke ban fa gane ba lafiya na ganki tafiya kamar Yar kaciya ke Naila menene haka? Naila ta Maze tace ke dalla Beauty bata yi karya ba dadi sosai fa,just that na bashi maganin yayi aikin da yawa yaki gajiya amma duk da haka wahalar kadan ce sai dadin yafi yawa,Chika ta sauke ajiyar zuciya tace yanzu naji zance,to ya love din? gashi kin Gani Ina ta shagwaba Ina kukan samun sarari da sangarta ai shi nake yi,kin San Kuma danginsa sai ka nuna musu kai ma A ce sannan ake zama lafiya da su shi yasa ai kika ga Ina ta Masa kuka.

   Amma jiya Madarar Nido ai na kwankwadeta,kamar kar a daina,Chika tace Shegiya kawata anji sweet dole kiyi shagwaba,Naila tace ei mana karki auri gajere yarinya ba kowanne gajeren ba amma Mafiya yawa tasu kubewar Miya ce,Chika tace ke nifa tun yanzu ma nake karewa ta saurayin da nake so kallo,Naila tace Misam din? Chika tace ae mana amma har yanzu ban ganta ba maye boye kayarsa yake yi a boxers bare ma a kallar Masa.


     Naila tace kawata kiyi sauri akwai dadi kar mu barki a baya,tausayinki nake ji,to nice jaraba ma nayi kwantai duk anki so na,wannan Misam din sai wani iyayi yake min na ma daina kulashi,muje ki tayani girki abinci wai suka zo ci,da nace bazan yi ba,Chika tace kiyi mana karki dogara da surukanki wannan marasa mutuncin ba kawowa zasu yi ba sai sunga dama,gwara ki zage ki rike mijinki,Naila a ranta tace rike Miji manya bari kiyi kiji tukun.

    Fitowa sukayi zasu shiga Kitchen Misam yabi Chika da kallo,har ya hango irin dadin da Chikar zata yi ma,Rafeeq yace tunda za ayi bikin Mummy ni zan dakko malamar gidan yari zan bawa Chika kudi ta dakko mana ita mu da bama bin mata ma rage zafi da zancen harkoki ko banza naji Badala.


    Spark yace idan za  kuyi aure kuyi aure ku daina walagigi Kuna tangal tangal da rayuwar ku,ni Kunga kullum Ina da komai a gidana duk Inda naje zan dawo na samu,Rafeeq yace yaushe ma na fara balaga ni tab naje na tsufa da wuri,Spark yace to kar a dinga yawan zuwa gidana ana kallar min mata kuje kuyi ta iskancinku a gari.


   Naila tace me za a dafa musu ne? Chika tace a musu me sauki jollof din taliya,Naila tace Baby baya son taliya fa gaskiya,Naila tace ita dai tuwo zata yi,Chika ta dinga dariya tace Amarya guda da tuwo ai sai ayi dariya,ta Dora taliyar haka ba a son Naila ba,taji nama da hadin kayan lambu, kida  Rafeeq ya kunna,Chika tana kitchen tana tikar rawa, har suka gama komai suka shirya a dining sannan Rafeeq Wanda dama shi daga School yake ya riga kowa zama a dining,Misam ya zauna harda gyara riga Yana cewa girkin Amarya zanci,Spark yace Amarya me dadin tuwo da Miya yau me taliya ce kenan,Naila ta tuna Indomie dinta da salat.


     Chika bata da kunya tana ganin Spark ya tashi tana zaune tana rawa,Misam ya kalleta yayi murmushi,Rafeeq yace ashe su Chika dai ko Ina da ku rawar ma an iya,Chika tace Kai a gidan yarin ma mune shegun ciki,Rafeeq yace naga alama kece akan kin fito daga gidan yari kika dinga rawa,Chika tace ai kowa ranar sai da na raba musu alakoro suka kalla,Misam yace na hanya ma ai sun gani,tace ai gwara ni bani da permanent uhm uhm...a cikin hot....Rafeeq yaci gaba da cin abincinsa,suna zaune suna ci suna Hira harda Chikar gayu ita da Rafeeq suke hira,Misam abincinsa yake ci baya kula su,wata yarinya ya latso a waya ya nuna Rafeeq yace Kalli,Rafeeq ya leka ya kalla harda kashe Ido daya duk sabo da kallon mace,yace tayi ka sa pics Dina ko zata kyasa na yaudare ta,Dariya Chika tayi wai ya yaudareta wato ma ba aurenta zaka yi? Rafeeq yace a'a wanne aure Kuma ai ni da kike Gani Yaudara ce burina,ba Kuma abinda zan taba mata kawai na yaudari mace na wuce amma matan ma sai su dinga tafiya wajen Yan iska,da wajena suke zuwa ai da sun huta, ba gara ba zago zan yaudare su kawai suyi gaba lafiya lafiya,Chika ta samu hanya tace wasu kuwa sai bin mata ana lalata musu rayuwa.

   

    A dinga bibiyar mata kamar yaran akuya,tana magana tana kallon Misam,yasan da shi take,tace sai lalata kannen wasu,'ya'yan wasu,yayyen wasu,matan wasu aikin kenan,me za ayi da Maza irin wannan basu san darajar mata ba Sam,ko aurensu kayi basu iya dainawa sai dai ka mutu da bacin rai,Misam ya gama daukan zafi,Spark ne ya fito zai tafi masallaci Sallar Azahar,Rafeeq ya fara dariya ashe an musulunta,Spark yace Chika rabu da su kije kiyi sallah abinda zai amfane ki,Chika ta mike ta wuce bedroom a kass,Misam jira yayi bai fita masallacin ba,Rafeeq yabi Spark sun tafi.


     Suna tafiya Misam ya shiga dakin da Chika ta shiga tana shirin shiga toilet taji an fisgota,ta fado jikinsa da sauri ya ture ta sannan ya sake fisgota ta fado jikinsa ta baya,hannu yasa ya toshe mata baki zata Masa ihu.

 

     Da hannu daya ya rike hannayenta ta kasa kwacewa, seletape ya hango a Saman mirror ya dakko ya yanko wani ya manne mata baki,hannayenta rike a hannunsa,Chika sai hawaye Shar Shar, tana ji tana gani ya fara cire mata kayan jiki,sai da ya cire mata rigarta duk yanda taso tayi kokawa ta kasa yafi karfinta ta ko Ina.

   Toilet din ya bude ya jefa ta ciki yasa key,Sannan ya kalleta sosai yace kinci darajar Spark wlh da yau sai na gama da budurcin da kike takama da shi,ba abinda zan miki so nake na nuna miki ba abinda bazan iya yi Dake ba idan nayi niyya ta karfi ma zan iya,amma yau wanka zan miki tas,ya jawo kujera ya zauna Yana rike da hannayenta.


    Chika sai hawaye Daya na bin daya,ta durkushe a kasa alamar roko,shi Kam surarta ta tafi da Imaninsa,ya tsura mata Ido hankalinsa ne ya fara barin jikinsa ya jawota jikinsa ya rungumeta,tana ciki cikin kwacewa ya cire Seletape din ya fara kissing dinta a nutse kamar wata matarsa,Chika tana ta kici kici abinka da so dama kadan take jira sai ta tsaya kamar gunki tana ta hawayenta,Yana ta faman tsotse mata Baki dama gashi gwani a sanin mata,Yana dan fara tabe mata kirji ta karo kukanta bayan dadi take ji tsabar gulma tana kuka ta fake da burburwa tana girgiza kirji wai duk cikin kuka ne,sai da ya tattabeta sannan badan yaso ba ya hakura,ta fice da gudu ta dawo bedroom tare da kwashe rigarta a hannu ta bude sip ta shige ciki ta rufe kanta a ciki ta Maida rigarta,sai lokacin ta tuna bakinta ya toshe mata ta cire tana hakki,tace kaiii tab amma lallai wannan guy din Dan iska ne,ba ruwana da shi daga yau har abada.


   Misam kuwa Sallar ma baza ta yuwu ba yanzu dai Kam sabo da ya kunna kansa da kansa,ficewa yayi ya samu Spark sun shugo,yace wai yau baka je masallaci ba Kai da baka wasa da jam'i,yace nayi tawa a daki yau,Spark yace okay idan Kun tafi ku rufe min kofar Palo na ni baccin rana zanyi,Naila tayi sallah ta rasa Ina Chika ta shiga har tayi wanke wanke ta gyara wajen ma neat,tana karasa goge kitchen Misam yace Aunty mun gode mun tafi,Naila tace nice ai da godiya suka fice,suna fita Rafeeq yace me kayiwa Yarinyar Mutane Misam.


     Me zan mata kuwa da ya wuce na lallatseta na fito wlh taci darajar Spark amma indai taci gaba da zagina da mazinaci wlh sai na yi da ita,Rafeeq yace haba mana Dan Allah karka yi ta daina ma daga yau,amma taji dadi? Misam yayi dariya yace taji dadi zaka ce ko naji,kawai sai na fada Maka sirrinta baka da hankali,ko Karuwa ce bazan fada ba bare Chika mutuniyar mu,kawai dai tana Dan birgeni shi yasa ma na damu naje na kalleta in and out sai Kuma ta tsokane ni,ni yanzu wlh ma akan wata ta bani kanta gwara Chika ta bani kirjinta yafi min.


   Rafeeq ya dinga dariya yace karfa ko ka tabowa kanka Kuma anzo madakata,Misam yace to wa ya sani ne ni kaina ba gane kaina nake ba karbi key kayi driving dina,har suka shiga mota Yana cewa amma yarinyar nan anyi baiwa,na daina ganin laifinta da take raye raye ashe gadara take da baiwar,anya kuwa..anya..wai ka aureta to mana cewar Rafeeq ,wannan yau tayi fushi baza ta so ni ba,tasan ma fa me nake yi wace zata so namiji a haka,Rafeeq yace baka San so ba Misam,indai ta kwanta Maka ka aureta.

   Yace ni dai jikinta ya min ba wai so ba,hmmm Allah yasa wani yazo yayi wuuf da ita ai ka huta.


   Spark kuwa Naila ta fake da gyare gyare har dare yaje yayi Sallar Isha ya sameta a Palo ta idar da Sallah,wato sallah ma a Palo zata yi sabo da tsoro,sai addua take yi taki karewa Allah kar ka bawa Spark sa'a a kaina,Allah kasa yaji ya gaji,Allah ka saka Masa bacci me nauyi ya dauke shi,Spark bai san me take roka ba ya daga hannaye sama wai Yana amsawa da Ameen,Allah gashi Nan kasa muna zuwa ciki bacci me nauyi ya kamashi,kar ya farka sai asuba.

   Tana shafawa shima ya shafa harda cewa Ameen,tana cire Hijab ya dauke ta,ya karkashe kayan wuta ya kulle ko Ina yace ko waye bazan bude ba dare yayi.


    Sama suka haura,itace ta fara shigewa wanka harda danna key,sai da ta gama har brush ta fito yace ki koma na saka miki maganinki na Yan kaciya,kin yarda tayi zata yi kuka,kamar ya hakura yaje yayi wankansa shima Yana fitowa har ta gama shirinta ta saka dogon wandon jean blue da riga me wuya da hannu kamar ana Sanyi,dariya yayi Taga ya dakko almakashi yace mu fa komai mun tanada ko ki cire da kanki ko suma ayi asararsu,Naila ba shiri ta daura towel ta cire,ya dakko wata Yar iskar riga me Dan gajeren hannu da kadan ta rufe duwawu,Kuma baza a sa pant ba,Naila tace wlh sai nasa,yace karki bata min wanka ki bar min abina,ke bai fi ma kyau ba ki dinga Shan iska,Naila abin ya zarce tunaninta a haka ta saka pant dinta,Yana Juyowa yaga ta saka harda hade rai ba wasa ba mutunci yace ba Kya ji ko bari nazo,cirewa tayi ba shiri Yana kallonta tayi jifa da wandon wai tayi zuciya ta koma Jikin Kofa ta rakube tana kuka,yace saka wandonki,ta dauka da sauri ta saka,yayi fushi wai shima ya daina kulata,tana kallonsa ya shirya ta zaci zai saka kayan shiko ko wando yace idan matar taki ai sai miji shi yayi shi,Naila tace a'a saka saka zan cire,yace a'a ba wannan zance,ni kin San dai dai nake dake,Ina son mace me taurin Kai ai.


   Hannu ya Kai zai rukota ta matsa da sauri duk ta firgita,yace ba abinda zan miki fa ni wlh,wai kin maidani abin tsoro,Naila da hannu tana nuna Hallare tana ja da baya tace wannan ce shegiyar Aradu ban yarda,tayi mugun bashi dariya yace alright ya saka kayan baccinsa wasu maroon sannan yace to kwanta,rigar jikinta ta kalla,a rigar daidai nipple dinta botin ne a wajen ko wanne side,tace kallo rigar Nan ka nuna min ma'anarta wlh tunda naga ka nace sai na saka da wata a kasa,Wannen botin fa? Yace na wasan Ango ne,Ni da iya nan zaka tsaya da sauki amma Sam baka da Amana Spark.


    Ban San sau nawa kike so na rantse ba please mana wai kamar ba Tantiriya ba,shammatarta yayi ya dakkota yace kina min kuka sai nayi,gwara ma ki rufawa kanki asiri mu kwanta.

   Saman bed ya kwantar da ita shima ya shige ya kwanta ya dakko wayarsa Yana dannawa Yana dariya shi Daya,Naila ta kalle shi tace ya ma rainani Ina gefensa waya ta fini,idan wata ce fa suke chat, wayar taga ya manna a kunnensa cikin girmamawa taji yace Abba Ina yini,Abba ya amsa ko Naila bai tambaya ba wai Kara yake kar ace ya damu da yarsa,Spark Yana ta jira yaji ko Abba zai tambayi Naila amma shuru har sun gama waya sai shine ya gaji yace ga Naila,Naila wayar ta karba da sauri.


      Ai kuwa tana wayar taji Spark yana wasa da botin rigar dake saitin nipples dinta,sai ya hade har Boobs din,ba abin tayi magana ko wani sound ba Abba yana wayar zai iya ji, Umma ya mikawa yace ga Gyatumar ki,Umma tace nice Gyatumar ma zan rama wlh,Naila tana jinsu tayi dariya suka gaisa Umma tace kalau kike kuwa? Naila tace to Gani nan dai, a tambayi lafiya a wajen Amarya Umma,kema fa kin San harkar nan karara Ina naga wata lafiya ni,da za a bani gado a asibiti ma ai da Hakan yafi kawai nasan jinya nake yafiye min.


     Umma tace ai zama da masoyi akwai dadi,Naila tace Kai Umma daina zancen nan duk karya nake ashe ban San komai ba,daga yau har abada bani ba maganin Maza ba uwar da na sani ashe haukata nake kawai,Ina ta cewa nasan Hallare ashe ko ta fitsarin yara ban sani ba,Kaka yaci gaba da sana'arsa kawai na dinga tura Masa customers.

   Umma tace a'a Naila ayi haka ke da kika San kan komai Kuma,Naila tace kuruciya ce na gane gaskiya,Umma tayi dariya kamar ba gobe ta kashe wayar tana cewa amma Allah yayiwa yaron Spark albarka.


    Abba yace ke dai wlh kina abin kunya baki da tausayi, yarinya kamar ba jininki ba,ke sanda aka kawo ki watanki nawa kina guje guje a riga,sai dare yayi a nemeki a rasa kin gudu sabo da tsoro,wanne kuka ne bakiyi ba,duk garin Nan sai da kowa yasan Hashimu ya angwance,kika cika gari da ihu,mutane da safe aka dinga gulma jama'a ihun wa nake ji? akace Kubra ce wlh da Dan dolonta Hashimu ai Hashimu jiya Kuma an Sha dadi,Kubra tace to yanzu nayi mana ihun,Hashimu yace zaneki zanyi wlh ko da wasa kika ce zaki sake wannan iskancin naki,me yayi saura Kuma,Kubra tace zaka zo ne,yace nazo din ai dole ki hakura dani bana kuri,kin isa kiyi komai Kubra ta, a nan ke kike da power.


    Mohsin Yana shiga bedroom din Hanan ya sameta tana rusa kuka ta fara azzalumi,macuci,kana zaluntata sabo da kayi aure ka samu Sabon hannu,yace yanzu kin min adalci kenan? Me nayi miki na zalunci? Kwananki ya zagayo ne? Yau kwana nawa da kawo Amarya? Kwana biyu kin tafi yaji,kin dawo anyhow kike shiga part dinta ya dace kenan? A matsayinki na babba abinda kike yi ya dace?ba irin karar da bana miki amma bakya gani,me yasa kishi zai sa ki Maida  kanki shashasha,yarinyar nan bata nufinki da komai,Hanan ta sake barkewa da kuka ai gashi Nan komai ita kake yabo,ni na tsufa ka daina so na,nonon nawa ma ko kallonsa baka yi,Kuma Allah sai ya saka min,Allah bazai kyaleka ba,ya Kalli Hanan yace wai tunaninki wannan shine zai sa naji tsoronki? Ki canja tunani idan zaki gyara ki gyara idan baza ki gyara ba ni bazan zauna kullum kina Bata min rai ba,kullum kina hanya kece wajen Abba kece gidanku,Ina gargadinki wlh kar ki sake zuwa part din Beauty,naji kina cewa da zaki iya kisa da ita zaki kashe ko? Zama da irinki bashi da amfani tunda kika fara zancen kisan Kai,Hanan da masifa tace to sai me ka sake ni mana,an fada maka tsoro nake ji,Mohsin juyawa yayi ya fice,Yana fita ta saka hijab ta fice sai Rumfar Abba ta tafi Kai Kara.


   Tun daga nesa Abba ya hango ta an sauke ta a Napep,Abba Sadaf Sadaf ya zaga ta bayan rumfarsa ya buya,Hanan tazo ba Abba,cikin gidan ta shiga tayi sallama,Umma ta dade bata ga Hanan ba sai yau,Hanan ta fashe da kuka tace nidai da wannan zaman bakin cikin gwara a fada Masa ya sake ni,Umma tace akan me za a sake ki,haba Hanan me yasa kike Maida kanki wata banza,yau kwana biyu kacal da kawo amarya gidan,kin Hana kanki sakewa kin Hana wasu sukuni,iskancin Nan naki ya ishe ni Hanan karki kaini bango wlh zan iya sawa ya kore ki,wannan wanne irin bala'i da masifa ne haka,ke dai bakya so a zauna lafiya,Allah ya kaddara Masa auren mata biyu kice bai Isa ba,ke din banza, wannan haukar da shirme ba Inda zai kaki gwara ma ki shafawa kanki ruwa kije ki gyara kanki ki zauna lafiya,idan Kuma kinki da kaina zan sa ya sake ki,ana daga miki kafa bakya gani,Baki da Kara baki da kunya,kin Raina kowa,Shike Nan yaro sai ya zauna a wajenki kar ya kula waccen sai ke, ubanki yazo yiwa bauta? Mohsin kowa yasan hakurinsa ba a fada da shi,ba Wanda bazai ba da shedar sa ba.


     Abba ne ya shugo yace Kubra kin so kanki Ba kiyi gaskiya ba,ba haka ake fada da sasanci ba,kin ware naki kike so,a kira Mohsin yazo Muji ta bakin kowa idan bazai iya ba kawai ya saki Hanan a huta kowa ya huta,Hanan tana Jin haka ta mike tsaye tana kuka tana cewa ni dama ba a kauna ta,bari naje gidan zan kwaci yanci na wlh,Abba yace kaji Yar jakar Uba wanne yanci kike nema Kuma Wanda ya wuce wannan da kike ciki,bayan uwarki kike so ki koma ki dinga bacci ko kuwa.


   Dama ni tuntuni nasan Mohsin hakuri yake Dake shegen jiki duk Kashi,wannan ke dai ba Yar Albarka bace,ko bacci ya kwanta nasan kullum sai dai ki dinga bibbige shi da kasusuwa,Ina amfanin Hakan,Hanan tana wani fiffika tace ai shi yasan me ya aura yasan me yake ji a jikina,da kirjina ma saita Masa tunani nake,Abba haushi ya kamashi yace au sirrin sa zaki fada mana iyaye guda,nonon naki akan Kashi mene kyansa to,Amal ta gama da shi,yarinya daya kika haifa ta tarwatsa shi,Kubra kuwa harda mijinki duk sun Sha amma ba duk budurwa ba,Abba yayiwa Hanan tas,Hanan dai ficewa tayi ta koma gidanta tace zan canja salo ba komai za a ga tuggu wlh.


    Abba ya fice ba a rumfar ya zauna ba wajen Yan majalisa ya zauna yana cewa kwana nan za aji ta fashe min,kwana nan za a fara gulma ta a gari, suna jinsa suka ce me zaka siya ne ko wani kudi ka samu? Hashimu yace bazan fada ba amma dai dama,Mohsin na biyawa aikin hajji,ban so na fada muku ba,Daya a ciki yace Kai kuwa Ina ka samu kudin? Abba yace ai tun farkon fara sana'a ta ba ci ba Sha,dama burina na Kai Mohsin aikin Hajji tunda bani da shanu,shi yasa bana cin komai na dinga tara kudin,amma ka bar iyalanka da wahala? Hashimu yace to iyalanka ne ko Kaine kake daukan nauyi na?

   Abba tsaki ya ja tare da mikewa ya koma wajen aikinsa.


     Naila dai ana gama waya da Umma sai aka kira Mohsin,suna cin abinci yace Beauty ga kawarki ya sa a handsfree,Naila tace my love,Spark yace Yaya dai ga your love a wajenki,Mohsin yace banji kanwata tana dariya ba yau ba nishadi,Naila tace hmm kawai,yace yau ba magana kenan,Naila tace akwai mana kawai dai ba damar fada ce babu yanzu,Mohsin yace ya amarci ana ta Sha, Naila tace ba dadi Yaya,yace ke na gaba zaki warke zaki Saba ne kinji bana son surutunki,ku dama Yan riga haka kuke baku shuru da baki,dan Allah karki sake fadawa wani kinji idan ba haka ba bazan zo gidanki ba,Naila tace a dake ni Kuma a hanani kuka,da ban Sha wahalar ba ai bazan fada ba,okay bakya son auren yanzu? Naila tace ae,yace to taho gida tunda baki da hankali sai ki dawo gidan ki zauna,wayar ta kashe tace kaji Yaya daga magana sai fushi,ai gwara haka ni kaina na kusa zuciya nayi fushi,Naila dariya tayi tace Kai din?, Ae mana ya furta tace to daina taba min Boobs sun gaji suma,Spark yace cikin biyu za ayi daya yanzu,ko dai ki tashi ki min abinda nake so naji dadi ko na sake yin irin na jiya,Naila tace a'a please zan Maka ni ba sai kayi ba.

   

    Naila sabo da ta samu salama ta zage duk abinda ya sata sai data yi Masa,Yana Jin dadi Yana koya mata abubuwa da yawa,yace to ga kawarki Hallare Kinga ita kadai ta dauki zafi ki samu ki shanye ta,Naila a ranta tace nidai na shiga uku,Yana faman Jin dadinsa Naila tana Masa abinda yake so sai da ya rasa Inda zai sa kansa sabo da maganin Dake aiki a jikinsa yaji bazai iya hakura ba,kwantar da ita yayi Yana Shan abinda yake so,wayo yayi mata yace bari Kiga yanda ake yin salo,har taji tsoro yace gwadawa zanyi ki gani ba abinda zanyi ai nace sai kin warke,Naila tace to, ya danne mata hannaye da nasa yasa kafafu duk ya gama da ita ko motsi bata Isa tayi ba, a hankali ya taba gabanta yaji ta zama wet,Hamdala yayi a ransa yace ashe kinji dadi,Naila tace kayi sauri ka gwada na gaji wlh,Spark a hankali yake mata wayo ya fara kokarin shiga Naila ta tsala ihu,tana rokonsa Dan Allah karka yi Dan Allah mutuwa zanyi,amma Spark baya jinta Sam haka ya shigeta a nutse,dadi har kwanyarsa ya manta ma jinya take yi babu daga kafa a harkar Spark Yana ta Sambatu kamar zararre haka yake Sambatu Yana kwasar dadi,Naila kukan ma ya kafe sai zallan azaba da take Sha,wayyo Abba kawai take iya fada,shi kuwa gogan ko a jikinsa baya duniyar ya Lula can wata duniyar Sambatu kawai yake da ihun dadi Yana furta dadi...dadi....yau ma ya shakata sosai sannan ya juyewa Naila madarar Nido tare da kankameta a jikinsa,Yana bata hakuri,yace ban San zanyi ba Aljanune suka shige ni,Naila wani takaici ya kamata,tana kuka kasa kasa tace Kai dai kawai bakin mugu.


      A hankali ya fita a jikinta yace I'm sorry,ai Spark ka zama masifa sai Sadaka cewar Naila tana hawaye,tace yanzu idan ba rashin Imani ba kana gani ban warke ba ka sake yiii.....sai kuka 

   I'm sorry kinji Aljanune suka shige ni,ya zanyi da Kai Spark tunda baka da tausayi ya zanyi,ya sake dawowa ya manne a jikinta kamar maye hannayensa ya Maida kirjinta,Naila ta rabu da shi ta gaji gaba daya,a haka baccin wahala ya kwashe ta,shi Kuma na farin ciki yake yi sosai.


     Yau makara suka yi Bai je masallaci ba sai 8am suka farka,Yana farkawa ya tashi da sha'awa matsananciya,shi kanshi ya rasa wanne magani ta bashi bai ki yayi ta yin sex ba.


     Mikewa yayi yaje yayi wanka da brush sannan ya dauro Alwala ya fito ya tada Sallah,Yana tashin Naila ta sakko da dabara da kyar take tafiya haka ta dage ta gasa kanta sosai,ta dakko ruwan Yan kaciyarya ta saka ta Nemo maganin su Goggo tayi amfani da shi shima,sannan ta fito ta Tada sallah, bayan ta idar  tayi addua ta koma ta kwanta Yana zaune Yana azkhar sai da ya gama sannan ya haura Saman bed din ya koma jikinta suka koma bacci.


    Mummy kuwa Shirin biki suke yi tare da kawayenta,Basiru Kusa ba kalar motar da baya Hawa,Yana ta zuba mata karya,har motar Misam da Chika ta dakko suka canjawa number yaje da ita zance.

   Mummy kawaye sunyi anko ana ta raba Iv kamar matashiya,Rafeeq ne yaje har gida ya samu Mummy taci gayu zata fita,ya kalleta suka gaisa yace Mummy duk cikin Yan uwanki kece bakya tsufa,kullum kyau kike yi dole ki samu miji da wuri,Mummy taji dadi tace ko Spark baya kaunata irin Rafeeq.


    Yace Mummy duk kawayen ki Yan mata ki gayyato su da zawarawa masu saukin shekaru,zamu je mu rufa miki baya,har walima zamu hada ranar da zaki tare ni da Misam,zamu dakko wata shaharriyar Malama zata yi chaji ranar ta koyawa mata kula da miji,Mummy tace Kai kuwa Allah ya muku Albarka na gode Rafeeq.


    Yace Mummy Allah ya Bada zaman lafiya kiyi Maza kiyi wa Spark kanwa ko kani,Mummy tace kani dai ai gwara na fara da mazan sunfi,Rafeeq Yana ta zugata ya mike zai tafi tace tura min accnt number Dinka,ta bashi dubu dari nan take,Rafeeq yace Allah ya biya Mummy sai munje gidan Basiru Kusa ni zan Kai Amarya,Mummy tace wannan yara da abin dariya kuke ka gaida gida dai,ya fice wajen kawaye wai shawarar Dinner suke,shi kuwa Rafeeq  ya tafi wajen Naila neman Chika za a gayyato Malama.


DAN ALLAH KAR A FITAR DA LITTAFIN NAN.


A dinga sharhi,idan ba ayi ba posting.


Masu Sharhi Ina matukar godiya.








AsmaBaffa

No comments