Breaking News

THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE BOOK 1

 

[1/4, 9:59 PM] Oum Hairan&Affan: *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE*
_(Amaryar mataimakin gwamna)_

*STORY AND WRITING*

*FAUZIYYA TASIU UMAR*

*OUM HAIRAN*

*BOOK ONE*



*_1-2_*

*GARGAƊI*
_Wannan labari mai taken  *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE* Mallakina ne, ban yarda wani ko wata ya juyamin shi ta kowacce siga ba sannan ban aminta a karanta shi a kowacce channel ba kuma ban aminta wani ko wata ya mayar min dashi document ba wannan ikona ne Ni kaɗai saɓawa wannan doka zai iya janyo dakatawar lbrn koda kuwa ka biya haƙƙin karatu, saboda haka a kiyaye._

________________________________________________________________________

*Mafari*

Ƴammata ne guda biyu sanye da wata farar atamfa chiganvi ɗinkin riga da sikert kayan sunyi masifar yi musu kyau matuƙa kansu naɗe da farin mayafi ƙarami shiga dai ta ƴammatan birni na wannan zamanin,dukkansu bazasu wucce shekaru sha takwas zuwa ashirin ba, daga yanayin tsaiwar tasu zaka fahimci sun gundura da tsaiwar da sukeyi a bakin titin.
Chocolate ɗin ce ta kalli farar tace “Aunty Nana wlh na gaji da tsaiwar nan kullum Indai Ya Man ne zaizo daukarmu saiya ɓata mana lkc dubi yanda duk mukayi futu² da iskar hunturun nan don Allah kizo mu samu napep kawai mu tafi gida kinsan Baffa yau baya ganawa da baƙi zaiyi mana faɗa"
Batare data kalleta ba taja tsaki tace “Hauwah kin cika gajen hƙr Gara Baffa faɗa kawai zaiyi mana shikuwa Ya Man idan yazo bai ishemu anan ba duka zaiyi mana kinga wanne yafi sauƙi kenan?" Wadda aka kira da Nana ta ƙarshe mgnr tana juyowa inda ita kuma Hauwah ta turo baki gaba irin na sangartattun yaran nan ta fara buga ƙafa tana yarfa hannu tace “ni nagaji Allah Annabi na gaji da sanyin nan da yake busani ke ko tausayin mutane bakiji wata banziya dake....."

Naushi Nana takaiwa bakin Hauwah ta janye da sauri tana mata dariya tare da gwalo.
Haushi ya cika Nana lamarin ƙanwar tata yana bata hayaƙi akanta, gaba tayi ta barta a tsaye tabita da sauri tana cewa “Haba Mrs Hussain banfa sanki da fushi ba tsaya kiji wata mgn nasan zakiyi dariya waima kinsan ya mukayi da Luvy na jiya kai NK ya rainamin hankal...."
Wayar dake hannunta ce ta ɗauki ruri tayi saurin dubawa da sauri ta rufe baki tace “uffararan bazan ɗaga ya kwashewa gyatuma albarka ba kinfi daidaito ɗaga" hannun Nana na rawa ta karɓa ta kara a kunnenta “To" kawai Hauwah taji tace ta dubeta tace “Guy ɗinnan ya kamata mu bashi gwale² Auta kinsan wai cewa yayi ya manta damu saida Yakumbo tayi masa mgn waishi yanzu yana Ahmad Musa suna ƙwallo mu hau napep mu ƙara sa gda" taɓe baki Hauwah tayi tace to tumbi kuma yau ya saba ganin bako aini duk wanda nabawa shawara yaƙi ɗauka ƙarshensa nadama" matsawa tayi tana dariyarta ta sakarci tace “ga irinta nan ai kin mugun rainani Aunty Nana kawai don kin samu inace miki Aunty ai nama kusa daina ce miki auntyn nan gaba kaɗan ma nice zan zama auntyn taki....."


“Sallari zaka kaimu" abinda taji Nana na faɗawa ɗan sahu kenan ya girgiza kai yayi gaba Hauwah ta ɗebi ƙasa ta watsa masa tace “Gantalin gantalewa da hauka nakeyi zan hau wannan napep ɗin tsautsayine ya kirani ya haka kawai ya yankeni ƙafata ta ruɓe...."
Dafe kai Nana tayi tace “Zanci ubanki Hauwah idan bakiyimin shiru ba" nitsogyn tasha ta maida kanta ƙasa ta fara latsa wayarta, Nana ta kuma tare wani ta faɗa masa inda zai kaisu har suka gama ciniki Hauwah bata ɗago ba saida Nana tace shiga mu tafi sannan ta ɗago ai kamar wadda taga wani bala'in taja baya da sauri tace kan ubancan na shiga uku Ni Autar Baffa wlh bazan shigaba rashin darajata baikai nan ba ɗan duba fa kiga yanda set ɗin suka yage kalan ya ɓatamin kayana" 
Wani takaici ne ya cika Nana tace da ɗan sahun “kaje kawai kayi hƙr, ƙwafa yayi yaja mashin ɗinsa ya tafi sukayita tsaiwa duk wanda suka tsayar sai yace bai zuwa, nandanan idon Hauwah ya raina fata.


Allah baiyi ta da juriyar tsaiwa ba ta dubi Nana tace “Aunty Nana mu hau kawai Ni nagaji" kallon bakida wayo Nana tayima Hauwah ganin hakan yasa Hauwah yin ƙasa tace “Allah ko wanne ma mu hau Ni nagaji bazan iya ba dubi yanda sanyi yake kaɗani skin ɗina sai bushewa yakeyi"
Taɓe baki Nana tayi tace “Me akayi da maza yarinya munanan har sai ansamu wanda yayi miki...." Abinka da jiƙaƙƙiya sai kuwa ta rushe da kuka ta miƙe ta miƙi titi ta rinƙa tafiya Nana na kiranta taki tsayawa dole tasa Nana binta.
Daidai lkcn da wata mota ta sulalo a guje hakan yasa Hauwah saurin yin baya da sauri motar ta giftasu Hauwah ta haɗiye takaici tare da duba gefenta titin state road ne babu datti bare ta samu dutsen rotse wannan yasa cije leɓe ta kuma saita hanya zata tafi taji Nana ta riƙeta ta baya tana cewa.

“Anya kuwa kina da hankali Hauwah kinga fah Magrib ta wucce kike ƙoƙarin kaimu inda bazamu samu abin hawa ba...." Hucin tsayawar motar da sukaji ne yasasu saurin juyawa a tare motar data kusa sheme Hauwah ce ta tsaya a kusa dasu ta kuwa gyara tsaiwarta tare da karkace baki tana jiran a fito tayi bala'i.
Buɗe motar akayi aka fito dukkansu suka aro wata nutsuwa ta musamman suka azawa kansu Nana tayi ƙasa tace “Barka da wannan lkc His Exalency kayi hƙr wlh bamusan kaine ba"

Idanunsa akan Hauwah yace “Ina kukaje da yamman nan haka?" Turo baki Hauwah tayi tace “Munje Tarauni gidan Iya Mama shine wannan muguwar taƙi ta sama mana ɗan sahu kaga ƙafana har yana ciwo" murmushi yayi yace “Hauwa'uh ta Baffa sha lele kedai komanki rikici yanzu daga sallarin nake na tambayi Baffa ina sarƙarsa me rikicin gangan yace rabonsa dake tun safe" shafa fuska Nana tayi tace “Ranka shi daɗe adaidaita huɗu na tare mana tace basuyi mataba"

Kallon Hauwah yayi yace “wai haka auta?" Ɗaga kai tayi tace “to ni ɗin sa'ar yarace da zata taremin ruɓaɓɓen vabur tace shine zai kaini gda salon idan sun ganni nan gaba su rinƙa cewa dubeta nan na ɗauketa nakaita guri kaza" dariya duka abin ya basu ADN Sooraj ya shafa sumarsa ta fulanin asali yace “Hakane Hauwah gsky bai dace ba yanzu kuzo na kaiku gdan tunda kunga dare ya fara bazaa samu wani mashin anan ba duba da wahalar mai da akeyi kwana biyun nan"
Kaɗa kai Nana tayi da sauri tace “Aa wlh mun gode zamu samu a gaba" da sauri Hauwah tace “Kaji ƴar baƙin ciki ko so take na kasa tafiyar to wlh bazan biye miki ki cuceni ba nikam da azaneni Gara a zanani da duka biyu Gara ɗaya haka kawai nakai gda daƙyar sannan a dakeni akan nakai dare ai gara ayimin dukan na hau lipt"

Tana mgnr tana shigewa motar dole itama Nana cikinta taf da ruwa ta hau Alh Adnan Sooraj Yaja suka tafi babu mai cewa ƙala har suka shiga unguwar yayi parking daidai lkcn Baffa na fitowa daga masallaci ya tsaya ya zubawa motar idanu Nana ta hau ɓarin jiki da yarfa hannu tana cewa “shikenan yau an kashemu an gama yau kawai a tafi haƙan kabarinmu......"
Rufe mata baki Hauwah tayi tace “Firgitacciya nikam saidai a kasheni" ADN Sooraj ne ya fito a motar yana dubansu yace “bama abinda zai faru insha Allahu ku shiga gda zan gaisa da Mal Baffa"
Yana mgnr ne lkcn da yake isa gaban Baffa ya rusuna suka ƙara gaisawa Baffa yace “Ranka shi daɗe ina ka samo waɗannan yaran tun safe babarsu ta aike su Tarauni gidansu sai yanzu suke dawowa" murmushi Alh ADN Sooraj yayi yace “nagansu ne suna neman abin hawa sun kasa samu kasan wahalar man nan da ake yasa abun hawa yana wahala ayi musu hƙr Mal káda a taɓa su tunda sun dawo lfy an auna arziƙi"

Murmushi Baffa yayi yace “Tunda ka shiga lamarin ai babu komin" shiru ce ta ɗan ratsa kafin Alh Adnan yace “Mal Hauwah ta gama secondary School kuwa?"
Tambayar ta bama Baffa mamaki yaja fasali yace “Aa bata gama ba tana shekarar ƙarshe wani abu ne?" Murmushi Alh Adnan yayi yana shafa sumarsa ta fulanin asali yace “Aa kawai dai naga yanayinta ne zatayi fikira da alamun tana ja a makaranta don ba'a tsokana da surutu ayi rashin ƙwaƙwalwa"
Daɗi ya cika Baffa an yabi lelensa yace “ksmar ka sani duk yaran gdannan babu me basirarta barta dai da fitinarta auta akwai tsokana Indai ta zauna a gda saita buwayi kowa" hakanan Alh Adnan yaji bayaso a daina hirar ya rinƙa jan Baffa da mgnr har saida Baffa ya fara fahimtar wani abu sannan ya zame da cewa “na manta har na tafi ban faɗa maka zanje England zanyi sati Uku idan Allah ya dawo dani zanzo akwai mgnr da nakeso mu tattauna"

Miƙa masa hannu yayi sukayi musabaha Baffa yace “babu damuwa Allah ya taimake ka ina tsumayi dawowar taka.Har jikin mota Baffa ya raka Alh Adnan ya zaro raffers na kuɗi ya mikawa Baffa yace “ga wannan abawa auta ta ƙara kayan kwalliya" sanin hallin manya basason suyi kyauta a mayar musu yasa Baffa karɓa yana cewa “aikuwa suna godewa zan huta kwana biyu Auta aljanar kwalliya kenan idan ta fara shafe²n fentin nan sai ta shafe awannin" murmushi Alh Adnan yayi yaja motar ya tafi zuciyarsa cunkushe da tunanin sabon yanayin daya fara shiga tun sati biyu Baya daya fara ganinta a gdansu wani zuwa da yayi gurin Mal Aliyu Gashua mahaifinta kenan.
Tsoro da firgici sun ɗarsu a zuciyarsa ta yaya zai fara fitar da sirrin zuciyarsa? Ta ina zai fara kamarshi geme² dashi shekara hamsin da uku yace yana son yarinya ƙarama wadda bazata wucce sha takwas ba kamar Hauwah to ta inama zai fara?

Tambaya mara amsa ita yaketa yima kansa daƙyar yakai kansa gdansa dake cikin Government areas ɗin yayi parking masu hidima suka taso suka buɗe masa ya fito wani yasa tsumma ya goge masa ƙafarsa sannan aka baza jami'ai sukayi masa Rakiya saida ya shiga sashinsa sannan suka juya suna masu sarawa a garesa.


Hularsa ya cire ya ajiye yasa tisue ya goge gumin dake karyo masa duk da yanayin sanyin da ake ciki zuba idanunsa yayi akan uwar gdan nasa dake saukowa daga sashinta taci kwalliya da gwala² sai walwali takeyi ganinsa da karantar sabuwar damuwa a fuskarsa yasata jin faɗuwar gaba ta tako ta iso kusa dashi ta ajiye tambulan ɗin ruwan tataccen Inibi a kan glass table dake gabansa ta tsiyaya ta miƙa masa tana karyar dakai tace “Mun daɗe cikin damuwa Ni dakai hakan yasa komai ƙanƙantar damuwarka bana kasa ganeta Allah shi taimakeka tun sati biyu Baya na fahimci akwai wani abu dake bijirowa zuciyarka da kaketa kokawa dashi ka kasa kuma jurewa shin ko zan iya sani, duk da nasan ba lallai inada mafitar baka ba amma bazan rasa kota shawara ce ba"

Wani wahalallen numfashi ya sauke ya zuba mata matsakaitan idanunsa lumsassun gaske wanda hutu da kwanciyar hankali Sukasa baka gane girmansa ta kowacce siffa ta jikinsa saita idanun nasa.
Mayar dasu yayi ya rufe yace “Na'ilatu kina burgeni ta wajen saurin fahimtar yanayi na wato a karon farko Soja ya faɗa koma wlh wani tashin hankali ne yake fuskantoni da yake neman bijirewa ƙwazo na  Madam help koda shawara ce Please"
Murmushi tayi ta kama yatsansa yace “shiyasa nace inason sanin meye damuwar" jirkitacciyar ajiyar zuciya ya sauke yace “Hauwah itace matsala ta yarinya ce ƙarama bata wucce sa'ar yarmu ɗaya da muka haifa ba wato Khairiyyah kinga kenan a lissafin haihuwa ma itan bazata gaza ƴa a garemu ba wlh tun ranar da azal ta haɗani da ita na ɗora idanuna akanta naji duk duniya yanzu banida burin daya wucce na mallaketa matsayin matata ta sunnah Na'ilatu ta ina zan fara abinda bantaɓa ba soyayya tunda jajayen sawu ma banyita ba bare yanzu geme² dani gashi Hauwah sakaliya ce dole sai ka shiga jikinta kafin ta fahimceka"...........

_Wannan littafi ba free bane na kuɗine 300 regular Wanda basason group wato special 1k acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama don samun damar karanta wannan littafi cikin aminci._

*OUM HAIRAN*
[1/9, 11:51 AM] Oum Hairan&Affan: *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE*
_(Amaryar mataimakin gwamna)_

*STORY AND WRITING*

*FAUZIYYA TASIU UMAR*

*OUM HAIRAN*

*BOOK ONE*

*_3-4_*

*GARGAƊI*
_Wannan labari mai taken  *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE* Mallakina ne, ban yarda wani ko wata ya juyamin shi ta kowacce siga ba sannan ban aminta a karanta shi a kowacce channel ba kuma ban aminta wani ko wata ya mayar min dashi document ba wannan ikona ne Ni kaɗai saɓawa wannan doka zai iya janyo dakatawar lbrn koda kuwa ka biya haƙƙin karatu, saboda haka a kiyaye._

_Masu son siyan littafin nan kuyimin mgn tanan_

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
________________________________________________________________________

Bayan tafiyar Alh ADN Sooraj Mal Aliyu Gashua ya juya ya shiga cikin gidansa mai gadi ya rufe get ɗin ya nufi bangaren matan gdan cike da Al'ajab na wannan ninniƙeƙiyar kyauta ta Deputy Governor  ga autar tasa, tuni zuciyarsa ta ɗaukeshi ta kaishi wani guri daban sai yaƙi bata damar nisa a tafiyar yayi saurin tsayar da ita daga karakaina cikin wasuwasin gangan ya takanta burki tare da kumburata da saƙon ba komai bane illa kyautayinsa na ɗabi'a.
A babban falon gdan Hajiya Sahura ce zaune saman kujera ta harɗe ƙafa ɗaya bisa ɗaya ƙasa kuma wasu ƴammata ne su uku zaune sun zagayeta wanda alama ta bayyane take nuna duk yanda akayi ƴaƴanta ne,
Ƙasa duka sukayi da kansu suka haɗa baki sukace Barka da shigowa Baffa" jinjina musu hannu yayi ya nemi guri ya zauna sukuma suka tashi suka nufi hanyar da zata sadasu da ɗakinsu daidai lkcn.


Hajiya Mariya ta sauko daga sama ta nemi guri ta zauna tana cewa “barka da shigowa Mal" da sakin fuska ya amsa yace “Gashi Mai girma Deputy Governor yaga ƴaƴanki a hanya sun rasa abin hawa shine ya ɗebosu ya kawosu gda harma yabada wannan abin arziƙin yace abawa Auta tasai kayan kwalliya...."
Da sauri Hajiya Sahura tace “Auta kuma meye haɗinsa da Auta?" Murmushi Baffa yayi yace “kinsanshi da kyauta haka yake kamar wanda abinsa yake tsunkuni musamman akan yara Allah ya jarabceshi da son yara sosai har tausayi yake bani ƴarsa ɗaya tal a duniya kafin su sameta sunsha wahala bayan samun natama har yanzu nema sukeyi Allah bai kuma kawowa ba yayi aure²  sosai amma bai dace ba harma ya hƙr ya zauna da matarsa ɗaya" jinjina kai sukayi cike da tausayawa Hajiya Mariya tace “Allah sarki har ya bani tausayi idan yanada rabon sake samu ubangiji ya bashi idan bashida rabo kuma Allah yasa hakan ya zame masa kaffara"


"Amin" abinda Baffa ya amsa dashi kenan Hajiya Sahura tace “Amma wannan kyauta tayi yawa Mal koda yake su kuɗin ba wahala sukeyi musu ba yawwa Mal Ni kuwa ina mgnr auren yarannan ne ta kwana ta tashi?"
Cire hular kansa yayi yace “mun gama yanke hukunci nida Babansu Jafaru nanda watanni biyar zamu auraddasu kowacce nayi mata miji Nana ma mun gama mgn da iyayen Hussain sunce lkcn yayi musu saboda haka ku fara shiri kunsan bana canza lkc"
Ya miƙe Yakumbo tace “To Mal Uwata fa?" Murmushi yayi yace “Barta nabata dama ta fitar cikin masoyanta tananan tana wasa da damarta na lura hankalinta yafi karkata akan wannan yaron Nabeel wannan mawaƙin yo in banda sakarci na Auta yaushe zani bawa mawaƙi auren ƴata kuma yarma autata ina gsky bazan iya ba" Dariya Hajiya Sahura tayi zuciyarta wasai da alamun hakanta ya kusa cimma ruwa tace “Aa Mal Auta ce fah mowar ƴaƴa ta Baffa dangware sha lele ya kamata ayi mata abinda takeso"

Sarai Baffa yasan Hajiya Sahura abinda take furtawa daban abinda ke ranta daban musamman akan autarsa wannan tasa yaja samarin ƙafafunsa ya shige turakarsa.
Kwance a saman gado Hauwah ce da littafi a gefenta kunnenta maƙale da Bluetooth tanabin wata waƙa tana murmushi.
Ɗala mata dukan da akayi ne ya dawo da ita hayyacinta ta kashe waƙar ta juyo zatayi masifa ganin Hajiya Mariya tsaye ta kafeta da idanunta yasata saurin shiga nutsuwarta tace,

“Lahh Yakumbo..."
Daƙuwa ta watsa mata tace.
“Na Yakumbawa uwarki Auta nace na Yakumbawa ubanki wato kinanan kina sakarcin sauraron waƙar sakaran yaron nan shine duk ƴan uwanki sun fashe sun tafi makaranta ke kinanan ko?"
Idanu ta hau matsewa tace
“Aa ne Yakumbo ba haka bane cikina ne yake ciwo shine yasa na kwanta idan yayi sauƙi saina fito...." Sumsum ta miƙe ta zari hijjab ɗin ta ta zura saboda kallon da taga Yakumbo nayi mata tsaf zata mazgeta ta tara mata gajiya.
Ƙur'aninta ta ɗauka ta nufi babban falon da suke karatun daren tana ƙunƙuni yau ta kwalo hira da Nabeel ɗin ta Yakumbo ta watsa mata burget, tana shiga falon Baffan su Ya Habu da Ya Abbas suka fara yi mata gwalo takaici yasata zubewa a gurin ta haɗiyi takaici ta ƙume Baffa yana musu karatun yana kallonta ashe shima Ya Man da Ya Abees ita suke kallo kawai saijin shigar bulala tayi a jikinta ta kuwa saki ƙara don shigar bazata bulalar tayi mata.

Baffa ya tashi da sauri yace “Subhanallahi Abees meye hakan meyesa kake da saurin kai hannu ne zonan Auta meye waye ya taɓa min ke?"
Da sauri ta isa gaban Baffa ta rushe da kuka tana shure²n sangarta ya kamota jikinsa yace “ya isa haka Hauwalen Baffa Abees sai naci mutuncinka in kana saurin kai hannu jikin Auta kaji dai na faɗa maka kake harararta to naji na gani ko an faɗa maka dolene ita a kanta sai tayi karatun da zaku dameta, kema Mariya ai harda ke da kika tashi kikaje kika wani tasota"
Share mata hawayen yayi yace “to ya isa ayi karatun idan an tashi naji meye ya haɗoku"

Karatun ta shiga aka fara da ita har aka tashi hankalinta yanakan wayarta da taketa ring babu halin ɗagawa can taji Ya Habu yace “Matar megadi" tsokanar da sukeyi mata kenan tun tana ƙarama aikuwa dake dama a kusa take saita rushe da kuka tana dire²n ƙafa Baffa dake shirin shiga ɗaki ya rufawa su Habu baya a guje yana cewa “Uwariyonka kaida megadin an faɗa maka jiddarh matar yara ce Kululuwa sai babban mutum babban ma sai babansa babanma saiya tara ko Autancy" Miƙa masa hannu tayi suka tafa ta kyakyale da dariya ta shige jikinsa tana cewa “Allah Baffa don bakaga irin son da Nabeel Wizkeey yakeyimin ba harfa waƙa yayimin...." Basar da zancen Baffa yayi da cewa “kije kiyi alwala kiyi sallar raka'a biyu ki nemi zaɓin ubangiji Bayan kin idar ban yarda kiyiwa kowa mgn ba  kiyi addu'a ki kwanta duk abinda kika gani cikin baccin naki ki faɗa min, mu kwana lfy uwar kowa"

***       ***      ***      ***

Haka suke gudanar da rayuwarsu a wannan ahli cikin so ƙauna da tattalin farin cikin junansu basuda wata matsala data addabi rayuwarsu da suka kasa maganinta.
Alh Aliyu Gashua babarbaren Yobe ne haifaffen garin Patiskum wanda yawon almajiranci yasa mahaifansa dawowa Kano da zama inda anan Allah yayi nasibin Arziƙin Mal Kurrah yake ya tara almajirai na ban mamaki wanda a zamanin Mal Kurah saida ya kasance duk Kano babu tsangaya me yawan almajiransa wannan tasa ya samu tallafi daga gwamnatin wannan lkc ta gina masa guri babba ta killaceshi ta bashi jari me tsoka hakan yasa almajiransa suka fita daban da sauran almajirai ko yaushe Indai kaga almajiri ɗan gayu to na makarantar Mal Kurah ne matar Mal Kurah ɗaya Hajja Yanah kuma ita ce Uwar ƴaƴansa guda Hudu  Baffa Jafaru Baffa Aliyu, Baffa Musa, Baffa Muntari wanda suke kira Babagana.

Ba Baffa Aliyu ne babba ba amma kasancewarsa mutum nutsattse yasa lkcn da girma yazowa Mal Kurah saiya ɗora Aliyu akan maƙamansa dama kuma tun Aliyu yana ƙarami Mal Kurah yake nuna masa sirrin kundi shida ƴan uwansa sai akayi Sa'a Ali duk ya fisu ganewa wannan tasa bayan rasuwar Mal Kurah sai Aliy ya ɗora daga inda ya tsaya aikuwa dake abun baiwa ce kowa da irin tasa nandanan sunan Mal Baffa ya Fantsama duniya manyan attajjirai suka rinƙa yi masa sunturi wannan tasa ya samu karɓuwa dake kuma yasa tsoron Allah cikin harkar Malamtarsa zaiyi wuya ya roƙa Allah yaƙi amsawa.
Mal Ali ya Auri Hajiya Sahura babarbariya ce tanada yaranta biyar Aunty  Zulaiha tana auren wani minista a Abuja sai Ya Mansur shikuma Engineer ne sai Ƴammatan gabanta Munirat  Salmah da Bilƙisu.
Hajiya Hauwa Itace mace ta biyu a gidan Shuwa'arab ɗin Maiduguri ce tanada yara Huɗu Aunty Khadijah itace Babba sai Ya Abees sa'anni suke da  Mansur wato Ya Man sai Ya Khamal sannan Autar Baffa wato Hauwah wacce taci sunan Mahaifiyarta da Allah yayiwa rasuwa ana gobe sunanta mace me kawaici hƙr da rashin hayaniya duk da cewar basuyi zaman daɗi da Hajiya Sahura ba amma hakan baisa na waje sun fahimta ba.

Hajiya Mariya itace mace ta uku kuma ta ƙarshe a jerin matan gidan tanada yara uku Yaya Abubakar sai Yaya Abbas sai Nana A'isha wacce suke kira da Nana.
Bilƙisu Nana da Hauwah kusan sa'annin juna ne Nana itace Babba watanta biyu aka haifi Bilƙisu Bilƙisu tanada kwana goma sha bakwai aka haifi Hauwah, tunda cikin Hauwah Hajiya Kulu bata ƙara samun lfy ba hakan yasa da aka haife ta aka rasa ruwan nono Mal Ali yaso yabawa Hajiya Sahura Hauwah ta shayar da ita amma fir taƙi wai ita batada ruwan nonon da zata shayar da yara biyu,
Allah sarki yana zuwarwa Hajiya Mariya da mgnr tun kafin ya furta ta karɓa tace ita dama tanaso don ba'a bata bane ta karɓe ta shayar ta goye abarta babu abinda yake kai Hauwah gurin mahaifiyarta saidai idan anyi mata wanka akaita ta kalleta tayi murmushi yarinya son kowa masha Allah zubin shuwan asali ita ce ta ɗauko kyawun uwarta sak babu abinda ta baro sai hasken fatar.

kwana shidda ta haihuwar Hajiya Kulu cikin dare Allah yayi ikonsa ta cika da kalmar shahada tare da barin wasiyyar ƴarta a hannun Mariya kada a rabata da Mariya.
Wannan dare hatta Hajiya Sahura saida tayi kukan wannan rashi ashe hauka takeyi batasan ta shaƙu da Hajiya Kulu ba sai yau da taganta kwance kamar tace mata tashi muyi faɗan da muka saba amma babu hali.
Bayan watsewar makoki rayuwa taci gaba da tafiya yanda aka tsarata wa wannan ahli zumuncinsu yana bawa Kowa sha'awa yana burge mutane matuƙa, inda a cikin ahlin kuma abu ɗaya ya zamewa yaran ahlin damuwa ba komai bane face rashin bawa soyayya muhimmanci da iyayen nasu suka ɗauka matsayin gata,
Ya kasance a wannan ahli babu wata ɗiya mace da aka taɓa bawa dama ta zaɓi abokin rayuwa da kanta duk wacce ta taso kafin takai ga nuna gwaninta anyi mata gwani koda kuwa tana da gwanin haka zata sanya jibgegen dutsi ta danne zuciyarta ta karɓi wannan zaɓi.
Ba kowa ne gwanin zaɓin ba face Mal Baffa to dake yafi sauran ƴan'uwansa ƙumbar susa sai ya zamana duk abinda ya zartar bi kawai sukeyi kuma cikin ikon Allah dake zaɓin nasa na Allah ne babu wacce suka taɓa aurarwa ta dawo Amma fah mutanen gari sun ɗiga musu ayar tambaya kan cewa, meye yasa Mal Baffa baya bawa talaka aure kuma basa aurowa yaransu maza ahlin talakawa?.

_Wannan littafi ba free bane na kuɗine 300 regular Wanda basason group wato special 1k acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama don samun damar karanta wannan littafi cikin aminci._

*OUM HAIRAN*
[1/10, 8:47 AM] Oum Hairan&Affan: *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE*
_(Amaryar mataimakin gwamna)_

*STORY AND WRITING*

*FAUZIYYA TASIU UMAR*

*OUM HAIRAN*

*BOOK ONE*

*_5-6_*

*GARGAƊI*
_Wannan labari mai taken  *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE* Mallakina ne, ban yarda wani ko wata ya juyamin shi ta kowacce siga ba sannan ban aminta a karanta shi a kowacce channel ba kuma ban aminta wani ko wata ya mayar min dashi document ba wannan ikona ne Ni kaɗai saɓawa wannan doka zai iya janyo dakatawar lbrn koda kuwa ka biya haƙƙin karatu, saboda haka a kiyaye._

_Masu son siyan littafin nan kuyimin mgn directly ta nan Please serious buyers kawai_

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
________________________________________________________________________

Wannan tambaya ita ce zaka samu a bakin duk wani wanda yasan wannan ahlin ciki harda masu yiwa Mal Baffa kallon wani azzalumi ga zuri'ar tasu domin sukance yana danne haƙƙin yaran baya basu damar da zamani ya basu na yin zaɓin abokin rayuwa akwai wasu nau'i na mutane ma da sukeyi masa kallon wani mai aikata babban saɓo a ban ƙasa.
Babu abinda yake damun Mal Baffa da maganganun mutane domin shidai yayi imanin akan daidai yake wannan tasa yake rayuwarsa cikin kwanciyar hankali,

To yau ɗin ma kamar ko yaushe bayan ya  sallameta ta shiga ɗakin nasu maimakon tayi alwala kamar yanda ya umarceta sai ya kasance ta zauna ta rusa waya a gaba tana kallon sabbin hotunan masoyin nata daya turo mata, yayi hotunan ne shida wata budurwa a gurin shooting wata waƙarsa a Abuja yayi kyau sosai.
Ta shagala sosai da kallon hoton taji an fizge wayar ta ɗago a fusace ganin Nana ce tsaye a gabanta yasata rufeta da bala'i tana cewa “Banason iskancin kinnan wai meye yasa kukemin abinda kukaga dama akan Nabeel ne kunsan kuwa yanda nakejinsa a zuciyata Allah banason rashin mutumci zanyi wulaƙanci....."
Rufe mata baki Bilƙisu tayi suna dariya dukkansu Bilki tace “Tujararriya saiki lallaɓa kije yana gerden yana jiranki...." Wani ihu ta saki ta faɗa kan gado tana burburwa tace “Wayyoh daɗi tafi dani karka kasheni My Nabeel kana bawa zuciyata aiki inasonka inasonka mijinaaaaa Alkhairinaaaaa!" Tafi suka shiga yi mata ta miƙe zumbur ta ɗauki mayafinta ta fice da sauri tana ƙuƙƙunshewa gudun kada iyayen nasu sugsnta Allah ya taimaketa ta samu ta fice ta yafa mayafin ta nufi gerden ɗin batasan ashe shuka take a idon makwarwa ba tun shigowarsa Baffa yagansa har zuwan su Nana da fitowarta.


Isa tayi bayansa batare da yasani ba tasa hannunta ta rufe masa idanunsa yayi murmushinsa mai tsada ya sanya hannunsa saman nata yace “Amincin Allah ya tabbata ga Sarkin sarakunan birnin zuciyata shugabar shugabannin majalissar ɗinkin duniyar zuciyata aminci da karamci ya tabbata ga tauraruwata fiye da kowacce tauraruwa My Jiddarh nayi missing wannan ni'imtacciyar soyayyar taki mara silki da ɗigon algus ko almundahana, wai yaushe ne ranar zatazo ne wlh na matsu tazo My Auta....."
Rufe masa baki tayi tana dariya ta zagayo gabansa ta tsugunna ta zuba kyawawan manyan idanunta akansa suka kafe juna da idanu zuciyar kowannensu na karɓar saƙo daga idanun ɗayan,
Kawar da ido sukayi suka saki ajiyar zuciya a tare ya zamo daga kujerar da yake zaune ya zauna sosai a saman grass ɗin dake mamaye da wajen yace “wai yaushe ne za'a bani dama na turo a gidanku Hauwah shekaruna sun fara nauyi na ƙosa nima na fara sha daga taska tsabtatacciya na ƙosa na samu lasisin cika cikakken namiji My Jiddarh Ina matuƙar buƙatar aure fah kodai Baffa bazai banike bane bankai ba?"

Da sauri ta ɗago idanunta tace “Aa My Nabeel daina yi mana wannan fatan wlh mutuwa ma nasan zanyi idan Baffa yaƙi barni na aureka kasan kuwa mugun sabon da zuciyata tayi da taka aini inaganin rabani dakai tamkar sanya takobi a datse zaren ruhina ne don inada yaƙinin kona rayu to farin cikina ya mutu....."
Ƙanƙame hannunta yayi yace “Are ur sure My Jiddarh?" Ɗaga masa kai tayi tace “wannan shine gaskiya My Nabeel yanzu bani lbrn waƙar da kake tsara mana"  murmushi yayi ya gyara zamansa ya tanƙwashe hannunsa ya zuba mata idanu ya karyar dakai gefe yace.
“Ƙarfe goma sha biyuu.....
Tabbas ɗaya tai biyu......
Sannunki biyun biyu.....
Hauwahta uwar biyu .....
Uwar ƴaƴa gimbiya!!!....."
Wani ihu ta saki me ƙarfi tace “Wow! My Nispul More grease elbow  dama na iya rera waƙa dana rera maka amma bari kaga wacce nake rubuta mana ta bikinmu nayi part one yanzu part two nakeyi ta wurin dinner kasan dama na faɗa maka nice zan rubuta mana waƙar auren mu saidai kawai ka gyara min"


Wayarta ta miƙa masa ya karɓa yana dubawa yana murmushi yace “kinyi fasaha sosai bari kiga ƴan gyare-gyaren ki" nan suka shantake yana nunnuna mata tana ganewa bai tashi duba agogo ba sai yaga tara da rabi ya miƙe da sauri yace “ya Salam My Jiddarh zanja Miki faɗa kiyi hƙr bana gajiya da ganinki ne muje ki rakani mota na baki saƙo" miƙewa tayi cikin sanyin jiki tace “banaso ka tafi My Nabeel nidai gsky ka zauna ka kwana anan" yanda tayi mgnr da son tabbatar da ita da gaske takeyi yabashi dariya yace “zamu kwana tare ne My Jiddarh har sai na gundureki wataran...." Zaro ido tayi tace “Uffararan kayi istigifari kana zuwa gida kayi aswaki wlh Nabeel ɗina bazai taɓa gundurata ba kyakkyawan saurayi fari dogo son kowa gashi me zamani wanda maza mata yara da manya suke yayi a wannan ƙarnin mata da dama sunfini kyau sun fini kuɗi sunfini wayewa Amma ka nunani kace nice zaɓinka tayaya nikuma da Allah ya zaɓeni ya bani kai zance banaso? Bama wannan ba My Nabeel...."


Kallonta ya tsaya yanayi tayi murmushi tace kawai banason ka tafine" lakace mata hanci yayi ta riƙe hannunsa tayi kissing nasa yayi murmushi ya ɗauko wata leda a motar yabata ta noƙe kafaɗa ya zubanta ido da yanayi na takaici ta tsugunna ta kama kunnenta tace “sorry My" murmushi yayi ya tsugunna ya kamo hannunta yaja ajiyar zuciya me ƙarfi ya miƙe ya nufi motarsa “Idan ban sameki ba bazan taɓa maye gurbinki da wata ba"
Abinda ya furta kenan lkcn da yake shiga motar tayi masa murmushi ta ɗaga masa hannu ya fice daga gdan ta juya ta nufi ciki, firgici ne ya shigeta lkcn da ta iske Baffa a falon ya goya hannunsa a bayansa yana zagayawa, tsayawa tayi cikin son aro dauriya tace “Sa...Sannu Baffa...."
Hannu yasa ya yafitota ta matsa a tsorace ta tsugunna ya zauna a kujera ya sauke numfashi yace “Waye yazo gurinki?" Cikin mamaki tace “Baffa Nabeel ne fah...." Zubanta ido yayi cikin wani yanayi data kasa gane meye a zuciyarsa,
Shiru na dogon lokaci sannan yace “tashi ki shiga ciki" miƙewa tayi da sauri yanayin mahaifin nata ya firgitata  tana shiga ta zube a tsakar ɗakin Nana ta miƙe zaune tace “Dallah ni kinbani tsoro kin wani shigo kamar an jefoki" ɗagowa tayi idanunta ya kawo ruwa tace “Waini yaushe ne Baffa zai daina tuhumata akan Nabeel ne?"

Tsaki tayi tace “to ke ina ruwanki da tuhumarsa tunda kinason abinki" Bilƙisu ce ta cafe da cewa “Ni wlh na gaji da wannan baƙar al'adar ta wannan gdan don masifa Kanada wanda kakeso sai ace bashi akeso ba yanzu gashi duk ya rabamu da masoyanmu" Salma ce tayi dariya tace “kuma dai son wahalar da zuciyoyinku ne yasaku ɓatawa kanku lkcn soyayya Ni wlh ban damu ba koma waye ya zaɓamin tunda dama banida wani da nakeso"  taɓe baki Munirat tayi ta gyara kwanciyarta tace “Auta kinso wahalar da kanki ne banji a raina Baffa zai yarda ya aura miki Nabeel ba don na daɗe da fahimtar ko zancensa bayaso ayi masa...." Dakata....dakata Yaya Munirat banson fatan tsiya kada ki ƙara faɗamin haka wlh ranki zai ɓaci" Hauwah ta faɗa tana miƙewa daga gurin ta shige bayinsu Salmah tace “duk ma abinda zakiyi kiyi gsky ce sai an faɗa miki ruwanki kiji ki ɗauka ruwanki kiji kiƙi ɗauka" tsaki Munirat tayi tace “ku rabu da ita tayi nisa fah"

Koda ta fito daga bayin bata saurari kowa ba ta haye katifarta tayi.

kwanciyarta zuciyarta tayi baƙi an taɓa makullin ruhinta, hatta fara bacci ta tuna da sallar da Baffa yace tayi ta miƙe ta ɗauro alwala tayi sannan ta zauna tayi addu'o'inta akan burinta na samun damar rayuwa da rayuwarta.
A saman sallayar bacci ya ɗauketa kamar yanda Baffa ya bata umarni da asuba da sukayi sallah suka zauna karatu basu tashi ba sai bakwai saida kowa ya watse sannan ta isa ga Baffan ta sunkuyar da kanta.
Hannunsa yasa ya dafa kanta yace,

“Yarda da amincin Allah ya tabbata ga uwar kowa meye ke tafe da autar Baffa ne?"

Ƙasa ta kumayi da kanta zuciyarta na bugawa da ƙarfi tace

“Nayi sallar kamar yanda ka umarceni Baffa" nutsuwarsa ya haɗa guri guda yace.

“To masha Allah uwar kowa meye ya biyo bayan ibadar?"

Shiru tayi ƙirjinta na lugude batasan meye yasa takejin kamar karta faɗawa Baffa gskyr abinda ya faru cikin baccin nata ba.

Murmushi yayi yace “Ki faɗa min inajinki lelen Baffa"

Cikin in...Ina tace “Baffa ni bangane komai ba kawai naga wani mutum babba ba yaro ba ya miƙomin wasu ƙwayaye farare yace nakai a ƙyanƙyashe masa....."

Ɗaga mata hannu yayi yace “kafin nan fah?" Ɗagowa tayi tace “Nabeel ne ya fara bani nakai hannu zan karɓa ƙwayayen suka tarwatse suka fashe....."

Wata nannauyar ajiyar zuciya yayi yace “Alhmdllh Uwar kowa kiyi hƙr kije zamuyi miki zaɓi da zaɓin ubangiji Allah kayi mata zaɓi da alfarmar Gatan farko gatan ƙarshe Annabi Muhammad (S.A.W)"

Jikinta a sanyaye ta miƙe ta nufi ɗakinsu ta sanya Uniform nata suka tafi makaranta ko a makarantar kasa hassala komai tayi maganar Baffa da son jin fassarar mafarkinta na bijiro mata har aka tashi ranar bata tsinana komai ba suka tafi gda bayan sun cire kayan makarantar.

Sukayi sallah sukaci abinci ta dubi Nana tace “Aunty Nana gdan Yaya Hadiza zan tafi"

Zaro ido Nana tayi tace “me zakiyi acan?" Turo baki tayi tace “Kuma don mutum zashi gdan ƴar'uwarsa sai zaiyi wani abu kawai inason ganinta ne"

Miƙewa Nana tayi tace “ok muje" tashi Hauwah tayi ta dauki wayarta da Bluetooth ɗinta Suka fice daga gdan dake Alhamis ce basu suka shigo gdan ba sai ana kiran magariba,

Yakumbo ta tanƙwashi kansu tace “Kun cika yawo ƴan ƙaniya Auta zo ɗauki wannan furar ki kaiwa Baffanki yana falon baƙi.

Sunkuyawa tayi ta ɗauka tace “Wai komai nice zankai Allah na kusa daina kaiwa baƙi ruwa da fura"

Da sallamarta ta shiga dukkansu suka ɗago suka dubeta tayi saurin yin ƙasa da idanunta gabanta na luguden taɓare ta rusuna cikin ladabinsu na ɗabi'a ta gaishesu ADN Sooraj ya sauke wani gwauron numfashi yace

“Auta ya gdan" ɗagowa tayi cikin Sa'a idanunsu ya sarƙe da juna tayi saurin ƙasa da nata tace “lahh Allah ya taimakeka dama yauma kaine ashe sannu da zuwa yau kuma waka ragowa hanya?"

Murmushin fuskarsa ya faɗaɗa yace “Yau zuwan kaina ne Hauwa'u tun 2 weeks baya zuciyata ta faɗa koma nakeyin komai a dole bisa ƙarfin hali da ƙumajin ƙuwwar son yakice abinda yake bijiro mawa ruhina a jiya mikin ya dawo sabo Hauwah na kasa jurewa tafiya ma zanyi zuwa England zanje wani taron gwamnoni mai girma gwamna ya wakiltani amma naji nakasa bazan iya tafiya batare dana furtawa Baffa damuwata ba"


Narkar dakai tayi cikin salo na ƙuruciyarta me burgewa tace “Allah sarki dama kowanne bawa da kalar jarabawar da yake faɗo masa a kowanne lkc ina maka fatan nasara Allah yasa Baffa nada maganin matsalarka"

Numfashi ya ajiye yace “Mal Baffa ya gamamin komai yanzu komai ya rage nawa dama iri nazo roƙo a gurinsa idan da rabona saina samu to dake Allah almusawwiru ne ya azurtani da samun wannan irin yanzu aikin gabana shine ƙoƙarin karɓar shi"

Dariya tayi data bayyana jerarrun haƙoranta na Jinin shuwa sirki da Barebarin asali tace “Kayy dama kaima kana noma to shukawa zakayi a gonarka?"

Jinjina mata kai yayi yace “ni Manomi ne na gaske Hauwah amma bansan meye yasa ba bansan dalili ba gonata bata yabanya tunda tayi so ɗaya tayi tsiro me kyau ya fito yayi kyau har aka girbeshi bayan girbin kuma sai komai ya lalace wannan tsuron yaketa ciwo ƙarshe yananan shi bai mutu ba shi bai rayu ba"

Jinjina kai tayi tace “Insha Allahu idan ka karɓi irin nsn na Baffa gonarka zatayi kyaun huda zata baka amfani me kyau" murmushi yayi yace “naga alama Hauwah me kikeso na taho miki dashi idan zan dawo?"

Taƙarƙarewa tayi ta kama yi masa lissafi ya zubanta ido a ransa yana jinjina girman ƙuruciyarta wato shi abinda ya fahimta ma kwata kwata bata fahimci inda ya dosa ba.

Numfashi ya sauke ya miƙe ya zaro wani ƙaramin cute box ya miƙa mata yace “nayi record na komai da kikeso Insha Allahu babu abinda zaki rasa amma banji kince kinyimin addu'ar samun damar shiga gonata da wuri don na fara yi mata ban ruwa ko Allah zaisa tayi kyawu ba?"

Dariya tayi tace “Aima nasan zatayi kyawun...." Ji tayi ya kama hannunta ya riƙe ya buɗe tafin hannun ya murza tsakiyar tayi saurin shigewa jikinsa tace “Wayyoh ka bari Allah ya taimakeka babu daɗi" murmushi yayi yace “Not wani abu kawai na duba kije na gde ki turomin Baffa"




_Wannan littafi ba free bane na kuɗine 300 regular Wanda basason group wato special 1k acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama don samun damar karanta wannan littafi cikin aminci._

*OUM HAIRAN*
[1/12, 7:43 PM] Oum Hairan&Affan: *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE*
_(Amaryar mataimakin gwamna)_

*STORY AND WRITING*

*FAUZIYYA TASIU UMAR*

*OUM HAIRAN*

*BOOK ONE*

*_7-8_*

*GARGAƊI*
_Wannan labari mai taken  *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE* Mallakina ne, ban yarda wani ko wata ya juyamin shi ta kowacce siga ba sannan ban aminta a karanta shi a kowacce channel ba kuma ban aminta wani ko wata ya mayar min dashi document ba wannan ikona ne Ni kaɗai saɓawa wannan doka zai iya janyo dakatawar lbrn koda kuwa ka biya haƙƙin karatu, saboda haka a kiyaye._

_Masu son siyan littafinnan   please serious buyers chat me for this Link👇🏼_

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
________________________________________________________________________

Ficewa tayi bakinta ɗauke da addu'ar nasara ga Deputy Governor ɗin ya lumshe idanunsa tare da komawa ya zauna saman kujera yace “The Young shell grow" daidai lkcn Baffa ya buɗe ƙofar parlourn da sallama Alh ADN Sooraj ya miƙe saida Baffa ya zauna sannan ya zauna yana shafa kansa hakanan ya tsinci kansa da jin wata matsananciyar kunyar Baffa yama kasa sanar dashi abinda yakeso ya sanar dashi dole sai miƙewa yayi yace.

“Ina gdy da karamci Mal samun mutane irinku a zamanin nan sai an tona wlh nayi alƙawarin riƙe maka Hauwa'uh bakin rai bakin fama insha Allahu zata samu kulawa fiye da wacce kake tunani insha Allahu kafin na tashi gobe zanje Gda na sanar da magabata sai su iso su nemamin aurenta, amma Baffa kana ganin ba'a shiga haƙƙinta ba?"

Murmushi Baffa yayi yace “Haba shiga haƙƙi Alh Adnan nine fa mahaifin Hauwah nafi kowa fatan naga ta samu ingantacciyar rayuwa Wato Adnan ba irin Hauwah ake bawa yaro aure ba hauka zasuyi dole Hauwah tana buƙatar me hankali wanda yasan ciwonta shine zata samu rayuwa me inganci, kaje Allah ya tsare insha Allahu kafin ka dawo zan gama da ita amma ranar abarta yanda take ko kuwa a sauko maka da ita, dama ansata hakane saboda suyi candy to idan kanason matarka sai kawai a ɗaura aure idan sunyi candy sai ayi biki idan kuma ka aminta saitaje ta zana a ɗakinta duk ɗaya ne"


Ƙasa yayi da kansa yace “duk yanda kayi Baffa Ni ina farin ciki da hakan"

Jinjina kai Baffa yayi yace.

Shikenan kaje zamuyi nazari.

Daga haka ya rakashi ya shiga mota sukayi sallama ya tafi.

Bayan tafiyarsa Baffa ya shiga gdan ya ishesu sun baje a parlourn sai ƙuruciyarsu sukeyi.
Zuba mata idanu Baffa yayi cike da ƙauna da tausayawa, ɗagowa tayi tace “Yawwa Baffa kabawa Dr ADN ɗin irin da yazo nema gurinka Allah bakaji inda ya bani tausayi ba to dama Baffa suma masu kuɗi suna noma?"

Ta ƙarashe mgnr da sigar tambaya, Baffa bai bawa shirmenta muhimmanci ba yace
“Ya zanyi Hauwah yanada ƙima da darajar da bazan iya hanashi duk wani abu da ya nema a gurina ba matuƙar ikona ne"

Dariya tayi tare da kwantar da kai tace “Yawwa Baffa jiya Nabeel yake cemin wai yaji lbrn an nemi Hussain ya kawo dukiyar aurensa ga Nana wai shi yaushe zaka nemeshi?"

Zubanta idanu yayi har saida ta shiga hankalinta yaja fasali ya nufi ɗakinsa tayi ƙasa da kanta jikinta a sanyaye ta miƙe zatabar gurin Nana tace “Wato Hauwah na fara hango tsanar Nabeel a idanun Baffa fa...."
Zaro ido tayi tace “Don Allah da gaske Aunty Nana? Ni bansan ta inda zan gane tsana ba amma nima ina tuhumar kaina meye yasa Baffa bayason nakeyi masa zancen My Nabeel ne?"

Ya Abees dake shigowa shine yace “Ai bazamu bashi bane mu fison mu bawa me cikakkiyar tarbiyya aure bawai ɗan kame² ba saboda haka ki fara haƙurƙurtar da heart ɗinki tunda kin kasa yima kanki zaɓi zamuyi miki yarinya yo ba gara mu bawa Lado megadi ba da mubawa wannan yaron aurenki...."


Wani kallo ta rinƙa bin Ya Abees dashi har ya gama zantukansa ya fice bata sami dama ta furta ko kanzil ba sai dukan tara da ƙirjinta yakeyi ta taɓe baki tace “aidai ba Baffanne ya faɗi ba kaine kuma ina kyautatawa Baffa zaton bazaimin zaɓin da ba zaɓi na ba saboda haka ɗan baƙin ciki saidai ya mutu"

Ɗakinsu ta shige dake ba sallah zatayi ba ta kwanta bayan ta ɗauro alwala tayi addu'o'inta bacci ya fara ɗaukarta taji wayarta tayi ƙara alamun shigowar saƙo kamar ƴar albashi haka Hauwah take da saƙo daya shigo bata samun nutsuwa saita duba saboda tana ganin abinda takeso yawa yawansu idan ka cire na kamfani to yakan zama sakon bawa fure ruwan ƙauna daga namiji mafi girman matsayi a ƙasan ruhinta.

Tashi tayi zaune da mamakin da batasan yaushe ya ɗarsu a ƙalbinta ba tace.
“Kayyy waye wannan?" Sake duba saƙon tayi sosai _“My Bride nakasa tunda nabarki na kasa bacci zuciya tana azalzalar ruhi da son kasancewa da abin buƙata Allah Auta yau ina cikin farin cikin daya zamemin shauƙi na son samun damar yima shuka ban ruwa a sabuwar gonata, inajin kamar nazo na taho dake saidai kashhh.... Ƙaddara ta riga fata dole nayi hƙrn dannar maitata har zuwa lkcn da za'a kawomin Hauwah gdana a ajiyemin ita a turaka ta abani damar yin komai ba tare da komai ba...."_

Mutsttsuke idanunta tayi tace “Ikon buwayi wannan wanne ɗan girin-giɗishin ne da yake iya ɗaukar alƙalaminsa yake zanamin waɗannan yaudararrun kalaman masu kama da gaske?"

Zuciyarta tayi nisa wajen tuntuntunin yanayi wani saƙon ya shigo ta buɗe tare da zubawa fuskar wayar idanu buɗe sakon tayi _“saura kwana 145 ki zama sashi mai bawa sashi kulawa"_ mamaki da rashin sanin cikakken abinda me sakon yakeson bayyana mata ne yasata ajiye wayar ta kishingiɗa.
Bata jima ba wayarta tayi ruri ta ɗauka ganin sunan Nabeel ya sata saurin karawa a kunnenta tace.
Ina mamakin yanda kake bayyana cikin kowanne tunani nawa My Nabeel meye sirrin?" Murmushi yayi ya gyara kwanciyarsa yace “Inaso muyi jawwala a bayan gdanku ina jiranki"

Zaro ido tayi tace “Dare fah yayi my Nabeel 8:30pm Baffa ya samu a magarƙama" fasali yaja yace “wasa nakeyi miki kewanki ya dameni inason samun tallafi daga gareki zuciyata na hasasomin ranar da zan ganki a gefena na matso ki matsa na janyoki jikina na kashe mana fitila naka mana bargo nayi mana addu'a mu lula duniyar da kowanne masoya suke burin shiga My Jiddarh washhh Ahhhh wayyoh Baffa Yakumbo bazasu sanya na ƙyaleki ba saina shayar dake wannan zumar da na shekara talatin da ɗaya inayi miki tanadinta"
Kunyace tasata yi masa shiru yayi murmushi yace “Matar Nabeel kina burgeni saboda kunyarki amma Jiddarh sashi yana faɗawa sashi bazai samu ba duk Waɗanda aka bawa ƴan'uwanki sunfini komai sunfini kuɗi ƴaƴan manya ne Ni kuma ɗan talakawa ne kuma Maraya Jiddarh Baffa kamar bai karbeni ba...."

Katseshi tayi tace “Don Allah ka daina ka rinƙa yi mana fatan alkhairi faifayayye banson kana kashemin gwiwa inaji a jikina Allah bazai bawa soyayyarmu kunya ba zamu mallaki juna koda kowa bayaso"
Ajiyar zuciya yayi sukaci gaba da hirarsu sunata dariyarsu sai 12:30am sukayi sallama ta miƙe ta sake ɗauro alwala ta kwanta zuciyarta cunkushe da tunanin makoma tabbas bataga abinda zai rabata da Nabeel ba.

**********

Washegari tun safe suka tashi suka tafi makaranta cikin walwala suke aiwatar da komai ita da Nana da Bilkisu.
Fitowarsu break ya bata damar buɗe wayarta cikin sa'a tana buɗewa kiransa ya shigo ta tashi daga cikin ƴan uwannata ta koma gefe ta kara a kunnenta tace.
“Lucky Man buɗe wayar kenan Mabuɗin zuciyat...." Shassheƙar kukan dataji yanayi yasata saurin miƙewa tace “Meye ya faru My Nabeel waye ya taɓamin kai me ya sameka???" Ta jero tambayoyin cikin kiɗima.
“Baffa" taji ya furta ta kuwa zabura ta dafe ƙirji tace “Me yayi maka?" Cikin dashewar murya ta wanda yaci kuka ya koshi yace “Nakasa jurewa My Jiddarh jiya banyi bacci ba ke yarinya ce bazaki gane abinda nake nusarki ba ina buƙatar aure sosai, da safe naje na sake samun Abbanmu nace yaje ya samu Baffa ya ƙara roƙamin alfarmar aurenki.
Baijamin ba ya ɗauki abokinsa Tukur suka tafi gdanku kinsan me Baffa yace musu?"


Ya faɗa muryarsa na ƙara karyewa tace “faɗamin don Allah Nabeel ka tashi hankalina" ajiyar zuciya yayi yace “cewa yayi suyi hƙr yayi miki miji...." Katseshi tayi da cewa “Ya isa Nabeel ba haka bane basuje ba Baffa bazaimin haka ba Baffa yanason duk abinda nakeso...."
“Sunje Hauwa'u Ni dama tunda naga yanda Baffa yake dojewa maganar aurenmu jikina ya fara sanyi Amma fah ban sare ba Jiddarh ke kaɗai nakeso zanci gaba da nema gurin Allah ya bani ke wlh babu wata mace da zan iya bawa dama a zuciyata ke kaɗai nakeso iya wuya sai mun zama abu ɗaya"


Kashe wayar yayi ta zauna a gurin ta haɗa tagumi zuciyarta na ƙuna hawaye ne yake zuba a idanunta batare data sani ba saida taji an dafata tayi firgigit ta ɗago Nana ta zauna ta sanya gefen hijjab ɗin ta ta goge mata hawayen tace “Yanzu Hussain yake faɗa min abinda yake faruwa Nabeel ya gaji da jiran kiran Baffa ya tura masa magabatansa Baffa yace  yayi miki miji waye mijin Hauwah?" Sai lkcn ta aro juriya tasawa kanta ta miƙe tace “Ba haka bane ku daina maimatawa Baffa yanason duk abinda nakeso bazaimin haka ba nasan ya faɗane don ya gwadani"
Miƙewa Nana tayi tace “to Allah yasa hakan" Class ɗin su suka koma badon ɗaukar karatu ba sai don jiran lkc ana tashi Drivern gdan yazo ya ɗauke su.

Suna zuwa gdan ta jefar da jakarta ta nufi sashin Baffa ta isheshi zaune shida wasu baƙi ta juya zata fita yace “Ta Baffa zo mana ya akayi ne?" Matsawa tayi ta zauna tare da ɗora kanta a jikinsa tace “Wlh Baffa bada wasa nake maka ba kuma nasan bazaka taɓa zaɓamin abinda zai zama cutawa gareni ba Baffa banasonsa koma waye ka zaɓamin Nabeel nakeso....."
Rufe mata baki yayi yace “naji dama nasan abinda zakice kenan jeki zan nemeki" miƙewa tayi ta nufi ɗakinsu tana shiga ta faɗa katifarta ta rushe da kuka cikin kukan taji alamun shigar saƙo ta miƙe ta ɗauki wayar ta buɗe “Yau Rana ce me girma da zata shiga cikin kundin tarihin rayuwata Hauwah Baffa ya karɓi kuɗin aurena da sadakina lkc kawai nake jira....."

Cilli tayi da wayar ta miƙe da sauri ta kurma ihu tare da ƙanƙame Nana tace “Da gaske ne ko wasa Nana?" Janyewa Nana tayi ta ɗauki wayar ta duba tare da jinjina kai tace “Da gaske ne yau Baffa Jafaru ya karɓi kuɗin aurenki...."
Shaƙar Nana tayi tace “Karki kuma faɗamin ba haka bane Nana Nabeel nakeso nashine Baffa ya karɓa?" Hannun Hauwah ta ɓanɓare daga jikinta ta nufi ƙofa tace “bansan waye ba amma ba Nabeel bane koma waye zaki sanshi ai nidai ina ganin ki kwantar da hankalinki kamar yanda kowa yakeyi tunda ba kanki aka fara ba"


Hawaye nabin kuncinta tanabin Nana da wani banzan kallo tace “Aikuwa muddin ba Nabeel bane zaa fara bijirewa daga kaina"
Turo ƙofar ɗakin da taji anyi ne bayan shigarta bayi yasata saurin kammala abinda takeyi ta fito ganin Baffa yasata jan numfashi ta zauna a ƙasansa ya dafa kanta yace “Uwar kowa kenan, kinajin zaki iya bijirewa Baffanki saboda so? Son da bazai zame miki bango kuma alkhairi cikin rayuwarki ba? Kada ki soma bawa zuciyarki wannan damar Ni nafi kowa sonki a duniyar nan wacce zata fini sonki bata ban ƙasa bare nabi bayanta Hauwa'u banyi miki zaɓi don cusgunawa ko cutawa gareki ba nayi miki ne don haka Allah ya tsara ta bakin Manzonsa duk da cewar Manzon Allah yace.
“Idan mutum na gari yazo neman aure gurinku ku bashi" amma ki sani idan cancanta biyu ta haɗu ta abu mafi dacewa shine ɗaukar mafi cancanta hakance ta faru gareki badon Nabeel bai cancanci aurenki bane na hanashi a'a saidon kasancewar abokin takararsa yafisa cancanta kiyi hƙr da zaɓin da nayi miki idan kikayi biyayya zakiga ribar abin ba kowa na zaɓa miki ba face Mataimakin gwamna Dr ADN Sooraj".........


_Wannan littafi ba free bane na kuɗine 300 regular Wanda basason group wato special 1k acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama don samun damar karanta wannan littafi cikin aminci._

*OUM HAIRAN*
[1/13, 5:53 PM] Oum Hairan&Affan: *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE*
_(Amaryar mataimakin gwamna)_

*STORY AND WRITING*

*FAUZIYYA TASIU UMAR*

*OUM HAIRAN*

*BOOK ONE*
*GARGAƊI*
_Wannan labari mai taken  *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE* Mallakina ne, ban yarda wani ko wata ya juyamin shi ta kowacce siga ba sannan ban aminta a karanta shi a kowacce channel ba kuma ban aminta wani ko wata ya mayar min dashi document ba wannan ikona ne Ni kaɗai saɓawa wannan doka zai iya janyo dakatawar lbrn koda kuwa ka biya haƙƙin karatu, saboda haka a kiyaye._

_Masu son siyan littafinnan   please serious buyers chat me for this Link👇🏼_


https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
________________________________________________________________________

Da mugun sauri ta ɗago idanunta da tuni ruwa ya cikashi ta kafe Baffa da manyan raunannun idanunta, Miƙewa yayi zai fice tayi saurin riƙe hannunsa tace
“Kayi hƙr Baffa bawai ina jayayya da hukuncinka bane a'a, wlh idan baka bani damar kasancewa da Nabeel ba banji a raina zan iya yima wani biyayya ba Baffa ka taimakeni shi nakeso shima Ni yakeso Baffa....."
Rufe mata baki yayi yace “Zaki iya Auta kiji a ranki dama ƙaddararki ta Adnan ce bata Nabeel ba Hauwa'u babu abinda zan canza wannan shine ƙarshen mgn....." Zame hannunsa yayi ya fice daga ɗakin ya barta da rawar jiki da luguden zuciya ta rushe da kuka tace “Nashiga uku Baffa wlh mutuwa zanyi idan baka bani Nabeel ba....."


Rufe mata baki akayi ta ɗago idanunta daketa shatatar ruwan hawaye ta saukesu a fuskar Aunty Hadiza da itama idanun nata suka kawo ruwa suka rungume juna tace “Zaki iya bazaki mutu ba Auta kema bulaliyar Baffa tazo kanki bantaɓa zata ba wlh da ban barki ba Alh Adnan yaje gurin Alh Sani ya sanar dashi cewa ƙanwata zai aura Allah ɗaya ban kawo ke ba shiyasa banyi yunƙurin dakatar dashi tun acan ba HAUWAH kiyi biyayya kamar yanda mukayi nasan zakiyi alfahari gaba dukka da haka muka fara gashi komai ya wucce......"
Saurin kallon Aunty Hadiza tayi tace “Kina tunanin na bari kenan Aunty bafa Nabeel bane wlh bazan iyaba Nabeel nakeso dashi kaɗai zan iya rayuwa...."
Ɗaga mata hannu Hadiza tayi tace “Idan kika kuma cewa a'a wlh sai ranki ya ɓaci kada ki kuskura kiyi jayayya da Baffa zakiyi nadama lkcn da bata da amfani" shiru tayi saboda itadai bataji a ranta zatayi biyayyar ba saidai duk abinda akaga dama ayi mata zuciya na kaita tana hasaso mata girman rashin adalcin da ake shirin yi mata ADN Sooraj shine zaɓin da Baffa yayi mata?" Zama tayi tare da rushewa da kuka daidai lkcn da wayar Nabeel ke shigowa tana kallon wayar tana ring ta kasa ɗagawa batason ya fahimci halin da ake ciki kuma tasani ɗagawarta daga muryarta zai fahimci da damuwa shiyasa ta zaɓi ƙin ɗagawar.

Haske tagani saman wayarta saƙone na masoyin nata ta buɗe cikin yanayi na dahuwar zuciya tana dubawa taga _“Ƙin ɗaga wayata bashi yake nufin samun mafita garemu ba saima haskamin amincewarki da hukuncin da Baffa ya yankewa soyayyarmu"_
Bata ida gama karanta saƙon ba wayarsa ta shigo ta ɗaga cikin shassheƙar kuka me karya zuciya tace “Ashe kasan komai dake faruwa My Nabeel Baffa ya zaɓamin wani bakai ba a sunan miji don Allah ya zanyi wacce mafita zamu nemawa kanmu nikam bazan taɓa lamunta ba....."

Iska ya furzar me zafi yaja fasali ya tashi zaune yace “Na daɗe ina faɗa miki inajin tsoron zuwan wannan ranar kina cemin bazatazo ba to yau gashi dai tazo Hauwah Baffa ya rabani dake ya zanyi inajin a raina idan ban sameki ba to banida rabon aure har abada....."
Kanajin zamu rabu kenan  Nabeel? Da gaske zaka iya rabuwa dani? Hmmm ni bantaɓa bawa raunin zuciyata damar jimin zan rabu dakai ba har yanzu ina ƙarfafawa kaina gwiwar samunka don Allah kada ka sare ka zama jarumi ni na yarda zanyi komai don cikar burinmu"

Kashe wayar tayi ta ajiye ta kama Safa da marwa a ɗakin zuciyarta na kai kawo a tsakanin ƙirjinta Nana ta shigo ta zauna tanabin ƙanwar Tata da kallo itanma ita take kallo idanunta na matso hawaye suka sauke numfashi a tare Nana tace.
“Nasan zuciyarki na saƙa miki abubuwa da yawa Auta saidai inaso ko ta jaki kar kije ki bata kunya inba hakaba ke zata baki kunya Hauwah ki daure a karon farko na rayuwarki kiyima Baffa biyayya kiyi abinda yakeso hakan zai ƙara dawwamar dake cikin kwanciyar hankali da soyayyarsa Hauwah wlh sone yasa Baffa ya zaɓa miki Alh Adnan Sooraj matsayin miji yeah nasan kinaji a ranki Baffa ya zaɓa miki tsoho to ki taushi zuciyarki gata yayi miki....."


Ɗaga mata hannu tayi tace.
“Dakata Malama banason gatan yabar abinsa wlh ba zanyi biyayya na cutu ba shikenan saboda farin cikinsa sai na rushe nawa farin cikin shekara nawa ina gina rayuwata da Nabeel kawai rana tsaka zai wargaza mana shiri Nana bazan iya wannan biyayyar ba cutuwa zanyi"
Kwanciya Nana tayi tana cewa “Dama kin kwantar da hankalinki da kinfi samun nutsuwar zuciya Baffa tunda ya riga ya zartar saiya aiwatar"
Bata samu damar bawa Nana amsa ba saboda kiran da Yakumbo ta ƙwala mata ta miƙe ta fita tana jiri, daƙyar takai ɗakin Yakumbo ta rusuna cikin ladabi Yakumbo ta shafa kanta ta ɗauko wani rubutu a roba ta bata tace “gashinan Baffanki yace kisha maza" kallon Yakumbo tayi tace “kinada taimakon da zakiyimin Yakumbo kice da Baffa ya janye aurena da mutumin daya haɗani dashi wlh baimin ba banasonshi Nabeel nakeso....."
Daƙuwa Yakumbo ta watsa mata tace “naci ubanki keda Nabeel ɗin waike meye yaron nan yayi miki da akansa bakijin kunyar ɓatawa da kowa? To ahir ɗinki ki kiyayeni zanci ƙaniyarki idan na kumajin wannan kalamin a bakinki haka dole zaki hƙr kamar yanda ƴan'uwanki suka hƙr tashi ki bani guri...."
Sumsum ta miƙe ta nufi ɗakinsu tana zuwa tayi jifa da gorar rubutun ta kuwa buɗe ya tsiyaye a carpert ɗin ta zube a gurin ta rushe da kuka me tayar da hankalin na kusa tana kukan tana kiran ”Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un" haka ta yini bata iya hassala komai ba kowa na parlour anata harkoki ita tana duƙunƙune a ɗaki dare ne yasa aka ankara da shirun nata yayi yawa Yakumbo ta tashi daga parlour ta nufi ɗakinsu ta shiga tana faɗan zaman nata a ɗaka ita kaɗai tayi mata banza ganin hakan ya ƙara hassala Yakumbo ta nufeta da zafinta abin mamaki saita tarar da ita sai rawar ɗari takeyi.


Ta durƙushe da sauri takai hannunta jikinta zafin da taji yasata saurin janyewa tace “Ya subhanallahi Ni Mariya meye kuma yake damunki Hauwah?"
Riƙo hannunta tayi jikinta yana rawa ta buɗe bakinta da rawar murya tace “ƙir...ji...na zaz...za...fi Yak...umbo ki tausayamin zan mutu wayyoh Allah Yakumbo Nabeel ma bashida lfy yana asibiti ki barni naje na ganshi....."
Inuwar da Yakumbo ta gani akanta ne yasata ɗagowa ga mamakinta sai taga Baffa rungume da hannu a ƙirjinsa ya zubawa Hauwah idanu fuskarsa wasai babu alamun wata damuwa, baice komai ba ya juya ya fice daga ɗakin Yakumbo ta sauke numfashi tace “kinga alamu sun nuna ran Baffanki ya fara sosuwa Hauwah ki daure kiyi masa biyayya wlh Alh Adnan mijine na nunawa Sa'a Hauwah in kika ɗauke ƙuruciya babu abinda Nabeel zai nunawa Adnan mutum me hƙr da ɗaukar rayuwa da sauƙi gashi da kawaici sannan mariƙin gdansa Hauwah kinsan waye Adnan abokin miji Yayarku ne Hadiza bashida hayaniya ta sanadin Alh Sani muka sanshi amma yanzu yanda ake zumunci dashi ya zama tamkar ɗan'uwa Hauwah Tunda Alh Adnan ya furta yanason aurenki babu yanda za'ayi Baffanki yaƙi basa kada ki manta fah ya ɗauki mahaifinki kamar nasa bashida abokin shawara sama dashi bashida uban da yafisa sannan uwa uba duk wata matsalarsa nan yake juyeta Hauwah Alh Adnan abin a tausaya masa ne inada tabbacin babban burin rayuwarsa bata wucce sake samun haihuwa ba"

Shiru Yakumbo tayi kana ta sake kama hannun Hauwah tace “Auta zakiji daɗi ina tabbatar miki sai kinyi Zarrah cikin abokai ƴan'uwa da ƙawaye muddin kika karɓi wannan zaɓin zakiyi farin ciki kinji"
Tunda Yakumbo take mgnr idanunta a lumshe yake wani haushi da takaici yana ƙara mamaye gurin da yayi saura najin ƙumajin nasara a ƙasar ruhinta ta janye hannunta tare da juyawa Yakumbo baya, ganin hakan yasa Yakumbo miƙewa ta ɗauko magani ta bata tace kisha kizo kici abinci kinsha rubutun da Baffa ya baki kuwa?" Kaɗa kai kawai tayi ta miƙe har yanzu idanunta tsiyayar hawaye yake ta zura hijjab ɗinta ta fito parlour ta zauna babu wanda bai ɗago ya dubeta ba Ya Habu da Ya Abees suka ƙunshe dariya so suke su tsokaneta suna tuna kashedin Baffa garesu wannan tasa suka gimtse.

Tashi tayi ta fita daga parlourn ta nufi get domin ficewa daga gdan duk da cewar tasan dare yayi amma ranta yana faɗa mata idan bataje taga Jikin Nabeel ba da matsala wannan tasata ficewa batare da megadi dake ɗakinsa yana sallar Isha ya ganta ba zuciyarta ce taji tayi mata rawa ta juya ta koma tana shiga ta ishe Baffa a bakin ƙofar shida Lado megadi taja ta tsaya Baffa ya nufota a fusace tayi saurin yin ƙasa cikin girmamawa.
Hannu yasa ya ɗagota yace “Ina zaki kika fita da daren nan uwar kowa?" Zuciyarta ce ta karye ta shigar da kanta jikinsa tace “Baffa... Nabeel ne bashida lfy shine zuciyata take faɗamin naje na gano jikinsa yana asibiti...."
Da sauri Baffa yace “Subhanallahi meye yake damunsa ai da kin faɗamin sai nasa Abees ya kaiki zo muje kuje da ƴan'uwanki ku dubosa"

Cike da farin ciki da mamaki tayi dariya tare da rusunawa tace “Na gde Baffa Allah ya ƙara girma" murmushi yayi ya kama hannunta suka shiga yana ƙwalawa Abees kira ya fito da sauri daga ɗakin Yakumbo ya nuna Hauwah yace “Ta fita zataje ta dubo yaronnan Nabeel ka dauki mota ka ɗaukesu ita da Bilkisu da Aishatu ka kaisu su duboshi ga wannan ku siya masa kayan dubiya amma kada ku daɗe"
Jinjina kai Abees yayi baya ƙaunar Nabeel Amma ya lura shi Baffa kamar ma shima yafison Auta da Nabeel ɗin, Bilkisu da Nana Baffa ya kira yace maza suzo suje dubiya babu musu suka tafi cike kowacce da mamakin salon na Baffa ita kuwa Uwar gayyar zuciyarta wasai tanajin kamar zatayi nasara akan Baffan.


Tsakanin unguwarsu da unguwarsu Nabeel da nisa wannan tasa duk suka ƙosa suna zuwa asibitin ta buɗe motar ta fice ta nufi cikin asibitin cikin saa tayi kiciɓis da abokinsa Nura yana ganinta yace “Aa Exalency  Barka da shigowa" haɗe rai tayi tace “Ina My Nabeel?" Ɗakin dake facing ɗin su ya nuna mata ta shiga da sallamarta taja ta tsaya ganin Yarinyar da tafi tsana a rayuwarta a gefensa ta kuwa yi kicin² mugun ya motsa ji takeyi kamar ta juya amma babu hali yariga ya ganta harma ya fara ɗago mata hannu taja ƴammatan ƙafafunta ta isa ga gadon ta sanya hannunta  cikin nasa nandanan idanunta ya ciko da ruwa  shima ɗauke ƙwalla yayi yace “Waye ya kawoki a daren nan My Jiddarh?"
Numfashinta ta saita tana danne abinda takeji yana taso mata tace “ya jikinka My?" Murmushi yayi me haɗe da hawaye yace “Sai abinda hali yayi inajin zuciyata kamar zata faso ƙirjina ta fito Hauwah meyesa Baffa bazai tausaya mana ya bar zuciyoyi biyu su rayu a tare ba kada ya rabasu bazasu jure ba...."

Shigowar su Nana ne yasashi sakin hannunta ya zubawa Nana ido tayi ƙasa da kanta cikin rashin kuzari tace “Wlh ba laifinmu bane Nabeel Baffa baya jinkiri wajen yanke hukunci idan ya yanke kuma saiya zartar ra'ayinsa me tsaurine Ni nayi mamaki ma daya bamu damar zuwa dubenka, kuci gaba da hƙr kuma kuyi ɗammarar ɗaukar kowanne irin ƙunci akwai yiwuwar idan kuka dage zakuci nasara...."
Wata Uwar harara da Abees dake shigowa ya jefeta da ita yasata saurin gimtsewa taja ajiyar zuciya dubi Ma'idah tace “Aa ƴar takara dama kece anan? Akwai yiwuwar zakici zaɓe Baffa ya shirya rusa muradan masoya" murmushi Ma'idah tayi tace “Banso faruwar hakan ba Nana naso Ya Nabeel ya auri masoyiyarsa Hauwah duk da cewar inayi masa son jini bana zuciya ba inayi masa so na rai bana zuciya ba amma soyayyata gareshi bata hanani yi masa fatan samun abinda yakeso ba, Nana Ya Nabeel yana mawa Hauwah son da bazai taɓa haɗa matsayinta dani ba naso su kasance tare idan Allah ya hukunta zan sameshi to nasan da farin cikin Jiddarh nima zanyi farin ciki amma idan ya rasata to ko na aureshi bazanji daɗin rayuwa dashi ba saboda banice a ransa ba......"
Tsaki Abees yayi yace “idan kun gama ƙarairayin ina jiranku a waje in kuma kun ɓata lkc zan tafi Wizkeey Allah ya sauwaƙe yasa maka dangana wannan dai ta riga ta faru".........


_Wannan littafi ba free bane na kuɗine Nrml group 300 VIP 600 Wanda basason group wato special 1k acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama don samun damar karanta wannan littafi cikin aminci._

*OUM HAIRAN*
[1/14, 10:03 AM] Oum Hairan&Affan: *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE*
_(Amaryar mataimakin gwamna)_

*STORY AND WRITING*

*FAUZIYYA TASIU UMAR*

*OUM HAIRAN*

*BOOK ONE*

*_FREE 11-12_*

_Wannan littafi ba free bane na kuɗine nrml group ₦300  VIP ₦600 Wanda basason group wato special ₦1000 acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama don samun damar karanta wannan littafi cikin aminci Or directly for this Link👇🏼_

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
*GARGAƊI*
_Wannan labari mai taken  *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE* Mallakina ne, ban yarda wani ko wata ya juyamin shi ta kowacce siga ba sannan ban aminta a karanta shi a kowacce channel ba kuma ban aminta wani ko wata ya mayar min dashi document ba wannan ikona ne Ni kaɗai saɓawa wannan doka zai iya janyo dakatawar lbrn koda kuwa ka biya haƙƙin karatu, saboda haka a kiyaye._

_Masu son siyan littafinnan   please serious buyers chat me for this Link👇🏼_

________________________________________________________________________

Ba Nabeel ba ba Hauwah ba hatta Ma'idah saida tabi Ya Abees da kallo shikam ya fice ko a jikinsa, kamo hannunta yayi tare da matsewa cikin nasa yaja numfashi yace “ba iya shi kaɗai bane a gdanku dagake sai Nana kuke maraba dani Jiddarh kiyi hƙr Insha Allahu burinmu bazaici ƙasa ba kije gda zanzo gobe ganinki kawai yasa na samu sauƙi"
Badon ranta nason tafiyar ba saidon ta zame mata dole ta juya ta nufi ƙofa tana share hawayen idanunta Nana ta biyota suka tarar har yatada motarsa zai tafi suka dubi juna Nana tace “Kada wannan abun ya kashenki jiki akwai alamun nasara a tafiyar taku"

Murmushi tayi lkcn da suke shiga motar ta kifa kanta a kujerar tace “inajin kamar da gaske bazan sameshi ba amma wani sashi na raina yana ƙaryatani Nana wlh duk ranar dana tabbatar da bazan sameshi ba zuciyata bugawa zatayi Ma'idah tayi wata mgn da ruhina ya ƙaryatata nice nakewa Nabeel wannan soyayyar da take  lissafawa"
Dafata tayi tace “Shiyasa nace karki sare kiyita addu'a" bata kuma cewa komai ba sukaje gda a harabar gdan suka tarar da Baffa idanunta akansa shima nasa akanta ya matso ya kama hannunta ɗaya ya nufi sashinsa da ita batayi masa musu ko gardama ba ta shiga ya zaunar da ita saman sallaya ya ɗauko wani magani a sabon ƙoƙo ya bata.
Dake shine dakansa batayi masa musu ba ta karɓa tasha yayi murmushi yace “Nasa bikinku wata biyar Amma magabatan Adnan sun roƙi alfarmar a sauko musu dashi duba da wasu abubuwa dake faruwa wannan tasa na saukeshi na dawo dashi wata biyu za'a riga bikinki kafin na ƴan'uwanki....."


Ɗagowar da zaiyi yaga ashe tuni ta zube masa a gurin ya nufota da sauri yana faɗin “Ya Salam Hauwa'u ya haka?" Daidai lkcn da Innah ta shigo ta iso da sauri tace “Subhanallahi Mal ya haka meye ya sameta?" Sharce gumi yayi ya ɗauki ruwa yayi mata addu'o'i ya fesa mata taja  wata ajiyar zuciya me ƙarfi ta kuma bajewa a gurin,
Zama yayi ya ɗago yace “Kiramin Mariya" miƙewa tayi ta fice basu jima ba suka dawo su biyu ya dubi Yakumbo yace “Dama Hauwah nada Mutanen ɓoye?" Ƙasa tayi da kanta tace “Gsky bata taɓa nuna wata alama ba saidai nasan baya tana yawan firgita da dare"
Jinjina kai yayi yace “Bakuda kula kuna sakaci tun watannin baya na fahimci Auta tana abu saɓanin na mutane so amma ban bawa abin muhimmanci ba kije ki ɗauko min wannan takardar dana baki jiya ki rubuce mata"


Tashi tayi ta fita bata jima ba ta dawo ta miƙa masa ya janyo Allo da tawada ya rubuta wasu ayoyi ya bawa Inna ta wanke ya karɓa ya watsa mata take ta saki wata ƙara ta miƙe zata zuba a guje ya riƙe ta nan ta kuma zubewa ya matsa gabanta ya kama kunnenta ya saita bakinsa yanayi mata karatun ruƙiyyah take ta rinƙa sakin ƙara tana tureshi wasa wasa saida suka raba dare suna abu ɗaya duka gdan babu wanda hankalinsa bai tashi ba daƙyar aka samu ta sauka bacci ya ɗauke ta Baffa da kansa ya ɗauke ta yakaita ɗakinsa ya kwantar da ita a gadonsa yasa Yakumbo ta zauna da ita.
Sai asuba ta farka tana buɗe idonta kalaman Baffa suka dawo mata ƙirjinta ya buga da ƙarfi ta tashi zaune Yakumbo dake shigowa tayi saurin ƙarasowa gabanta ta tashi tana ƙoƙarin fita Yakumbo ta riƙeta ta kwantar da kanta a kafaɗar Yakumbo tace “zuciyata jikina ciwo Yakumbo kibarni naje gurin Baffa yaji tausayina karya haɗani da Alh Adnan Yakumbo banasonsa bazan taɓa iya yi masa biyayya ba idan kuma banyi masa biyayya ba bazan haɗu da ubangijina salin-alin ba Yakumbo banson abinda zaija mu shata layi da rahamar ubangijina....."

Tabbatar da cikin hayyacinta take yabawa Yakumbo damar fice mata daga ɗakin saboda batada kalma ɗaya da zata iya nuna mata abinda yake daidai akayi mata,
Baffa dake saman sallaya yana Wazifa ya dubi Yakumbo yayi mata alamar ta tsaya ta nemi guri ta zauna ya ida kai aya sannan ya dubeta yace “Mariya Autar tawa ta farka ne?" Jinjina kai tayi tace “Ta farka Baffa saidai Ni jikina ya fara sanyi da lamarin yarinyar nan tun jiya mgnrta ɗaya a rabata da Adnan kada a aura mata shi anya mal bakuwa zaka Duba lamarin nan ba?"

Murmushi Baffa yayi yace “Mariya kunsani idan muka yanke hukunci Bama canzawa kada ki damu da yanayin ƙuruciyar Auta idan yaro yana shirmensa ƙyaleshi akeyi Indai ba gani akayi abun zaiyi yawa ba Muhammadu Nabeel ne bazan iya ɗaukar aure na bashi da hayyacina ba kada ki manta zuwan iyayensa na farko gdanan Alh Umaru cemin yayi ƴarsa yakeson bashi tun tana ƙarama take sonsa amma shi ya nace sai Hauwah harma ya ƙaramin da cewa mahaifiyar Nabeel batason tarayyarsa da Auta kuma bashida samanta babbar damuwar nidai yanda mutane suka sanni abin turr ne ace na ɗauki ƴata nabawa mawaƙi bayan waƙar ma har Film fa yakeyi , To tun a wannan lkcn zuciyata ta tafi tunanin wanda zan bawa Auta ya riƙe min amanarta da farko nayi tunanin haɗata da Yayanta Khamaluddeen to kafinma takai da hakan shikuma Alh Adnan yazomin da buƙatarsa buƙatar da bazan taɓa iya tanƙwabar da itaba bazan taɓa iya ƙin karɓarta ba wannan lamari Mariya aje kawai ayi addu'a amma tabbas idan auta ta fiye takurawa zan ɗaura wannan aure a jira lkcn tariya" kaɗa kai tayi cikin sarewa tace.
“To shikenan Mal Allah ya dafa yasa hakan ya zame musu alkhairi baki ɗaya"


“Amin"
Ya amsa da ita daidai lokacin da Hauwah ta fito daga ɗakin ta zauna a gabansa idanunta sun kaɗa sunyi jajir saboda kukan data kwanta dashi.
Gaisuwa ta isar gurin baffan sannan tayi shiru tana wasa da yatsunta dafa kanta yayi yace “dama kinyi shiru kin hƙr da furucinki Hauwa'u nariga na gama mgn bazata canzu ba kije kiyi addu'a ki jira lkc kawai sannan abu na gaba daga yau na haramtawa duk wani namiji bayan ƴan'uwanki zuwa gareki na haramta miki ɗaga wayar kowanne namiji matuƙar ba Adnan bane, ki tashi kije Allah yayi miki albarka"

Kasa miƙewa tayi saboda waɗannan gunduma gunduman dokokin sunyi mata tsaurin da bataji a ranta ko ɗaya zata iya bi ba.
Tsawar da taji ya buga mata yace “Ko bakiji bane!" Yasa zuciyarta girgiza karon farko a tarihin rayuwarta da Baffa yayi mata tsawa, ta miƙe da sauri ta nufi sashinsu ta nemi guri ƙarshen ɗakin ta rakuye  tama rasa abinda ya kyautu tayi banda suya babu abinda zuciyarta keyi.
Daidai gaɓar kuma wayarta ta dauki kuwwar neman ɗaukinta tana dubawa taga habiby Da'iman tayi saurin kai hannu zata ɗauka sai kalaman Baffa suka rinƙa yi mata yawo a ƙwanyarta.
Tana ganin wayar har ta katse wata ta kuma shigowa itama ta yanke bata samu ƙwarin gwiwar ɗagawa ba saida saƙo ya shigo sannan ta ɗauka ta buɗe.

_"Ki ɗaga wayata My Jiddarh Ina cike da ƙishirwa kewa da yunwarki muryarki tana ragemin raɗaɗi da damuwa, ita dama soyayyar gsky tana zuwa ne cike da ƙalubale ƙunci da ƙaƙanikayi idan ka sare saika rasa masoyin gsky wanda zai dawwamar da rayuwarsa wajen sanya taka rayuwar farin ciki Jiddarh kada ki karaya mune da nasara mu manta da komai muci gaba da rayuwa kamar ba komai kinji"_
Wani kuzari da ƙarfin gwiwa taji ya shigeta ta ɗauki wayar ta kirashi bugu ɗaya ya katse ya kirata tace “Hello My Nabeel kana lfy ya jikinka?"
Numfashinsa ya saita dake fita ƙasa da bugun zuciyarsa yace “Ina sa ran zan samu sauƙi idan rana tazo da zanganki kwance a ƙirjina nasa hannuna na rungumeki ina shafa bayanki serious Hauwah wannan ranar itane ranar da zan warke najini kamar kowa Adam Fasaha ya ƙarfafan gwiwa yace kada na sare faɗuwar gaba asarar namiji yace shi so biyar baban budurwarsa yana sawa ana dsgargaza masa glass na mota sau uku yanasa ana kamashi ana ɗaurewa da azaba me tsauri ƙarshe yarinyar da kanta tazo take roƙonsa kada ya karaya akwai yiwuwar samun nasara aikam sunyi nasara bayan sunci wuya nacinsu yakaisu gaci, My Jiddarh muma muyi juriya kinji iya wuya kada mu rabu da juna kada mu fasa ƙarfafawa juna"

Karyar da murya tayi cikin salo mesa kasala tace “My Nabeel kana hango mana nasara kuwa anya Baffa fa ya sauko da lkcn wai wancan tsohon najadun yace da wuri yakeso wlh ji nakeyi kamar inje inda yake na shaƙeshi saiya mutu"
Shiru Nabeel yayi yanajin sautin bugun zuciyarsa na ƙaruwa yace “Zan sake turowa yau Hauwah bazan gaji ba" kashe wayar yayi itama ta aje tata batakai da tashi ba kira ya shigo ta janyota ga mamakinta batayi saving number ba Amma sai taga ansa His Exalency Dr Adnan Sooraj.......
Gabanta yabada wani dam ƙirjinta ya rinƙa harbawa da ƙarfin gaske har saida wayar ta yanke wata ta shigo sannan ta ɗaga hannunta da bakinta nayi mata rawa.

“Assalamu alaikum"
Abinda ta iya furtawa a karkatse kenan.
Wata ajiyar zuciya taji ya sake me ƙarfi yaja numfashi ya tashi daga kwanciyar da yake cikin wata murya me kama da tajin bacci ko maye yace.

“Kina lfy My Bride?"
Shiru tayi masa saboda jin sukar fitar furucin daya kirata dashi “wai amaryarsa" Hmmm taja numfashi tare da gyara kwanciya,
Rashin bashi amsar yasa gabansa faɗuwa tare da tantamar anya Hauwah ce ta ɗaga wayar? Tambayar ta sulalo daga ransa zuwa kan laɓɓansa yace “Hauwa'uh ko ba ita bace?" Shirun dai aka kuma yi masa, daganan ya fara fuskantar tabbas akwai matsala yaja fasali cikin kasalar yanayi yace “My Hauwah meye damuwar ne?" Kamar me jiran tambayar tace “Kace bakaso ka fasa don  Allah Exalency inada wanda nakeso na shirya rayuwa dashi dukkan wani farin cikina dominsa nayi tanadi bazan iya taɓukawa rayuwar waninsa komai ba....."

Sosai kalmomin sun sagar masa da gwiwa tare da tsinka lakar jikinsa a rayuwarsa bai yarda saboda farin cikinsa ya tauye farin ciki wani ba yanasonta ƙaunar da bayason cutar da ita ko kaɗan.
A gajiye yace “Wannan dalilin yasa na kiraki Hauwah karon farko da Allah ya jarabceni da soyayya kenan da girma na da komai nakejin idan babu ke zan iya rasa numfashi Hauwah nayi aure² yakai biyar bantaɓa cin karo da macen da sonta yake yawo tare da raina a jikina ba saike inasonki Hauwah so irin na ɗa da mahaifi zan rayu dake a duk yanda kika tsara mana amma ki sani bazanyi miki dolen ki rayu dani ba duk da cewar nine nace da Baffa inason samun tagomashin irin mutum daga tsattsonsa zanji kunya matuƙa na koma nace masa nafasa Bama zan iya ba ya wucce haka a gurina, da wannan nake miki albishir na kasancewarki matata ta sunnah a safiyar yau ina tayamu murnar zama abu ɗaya karon farko a rayuwarki da kika mallaki mahaɗin dazai rinƙa ɗaukewa ruhinki kewa Hauwah bansan meye dalilin ba nidai Baffa ya kirani ya sanar dani na turo waliyyi na a yau ɗin nan da sadaki na turo kuma an ɗaura"............

*OUM HAIRAN*
[1/15, 6:51 PM] Oum Hairan&Affan: *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE*
_(Amaryar mataimakin gwamna)_

*STORY AND WRITING*

*FAUZIYYA TASIU UMAR*

*OUM HAIRAN*

*BOOK ONE*

*_FREE 13-14_*

_Wannan littafi ba free bane na kuɗine nrml group ₦300  VIP ₦600 Wanda basason group wato special ₦1000 acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama don samun damar karanta wannan littafi cikin aminci Or directly for this Link👇🏼_
https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1

*GARGAƊI*
_Wannan labari mai taken  *THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE* Mallakina ne, ban yarda wani ko wata ya juyamin shi ta kowacce siga ba sannan ban aminta a karanta shi a kowacce channel ba kuma ban aminta wani ko wata ya mayar min dashi document ba wannan ikona ne Ni kaɗai saɓawa wannan doka zai iya janyo dakatawar lbrn koda kuwa ka biya haƙƙin karatu, saboda haka a kiyaye._

_Free page ya ƙare daga yau don Allah na roƙeku kada ku fitarmin da littafi idan bazaki iyaba dole saikin fitar to kibarshi basai kin siya ba kema da kika gani kiyiwa Allah  karki karanta min baki biyani haƙƙin karatu ba, wlh tallahi billahil'azeem bazan yafe miki ba domin wahala nasha na rubuta abuna._

________________________________________________________________________

Suɓucewar wayar daga hannunta yayi daidai da sulalewarta ƙasa suma ta gaske wanda faɗuwar Tata yayi daidai da lkcn da Bilkisu ke shigowa ta kuwa saki ƙara tace “Innanillahi mutan gda ku kawo agaji Auta ta sake zubewa...."
Ya Mansur daya sawo kai ɗakin ya sunkuya gabanta ya ɗaga hannunta yajishi a sake yayi murmushi me ciwo ya miƙe yana cewa “Dama Hausawa sunce ɗan gata ɗan banza yanzun gashinan abinda gatan yaja mata an ɗauki soyayyar duniya an ɗora mata wai ita Auta ga sakayyar nan karon farko a rayuwarta ta kasa sadaukar da farin cikinta ga wanda ya ƙare rayuwa wajen nemawa tata rayuwar farin ciki"
Abees ne ya ɗagota tare da ɗaukar waya ya kira layin Baffa ya faɗa masa abinda ke faruwa Baffa dake cikin mutane ya miƙe yace “Waye ya faɗa mata?" Cikin ladabi Abees yace “duka muna falo mukajiyo zubewarta" jinjina kai yayi yace.


“Kayi mata abinda ya dace" gdy Abees yayi yasa Bilkisu ta bashi ruwa a cup yayi addu'a ya shafa mata take taja ajiyar zuciya ta angajeshi ya faɗi gefe Ta saki wani azababben ihu daya sanya kowa na gurin toshe kunnensa ta miƙe batare da kowa ya lura ba ta fice da mugun gudu Mansur da Habu Suka riƙeta ta zubar dasu tayi waje daidai lkcn da Baffa da Baffa Jafaru suka kawo kai Baffa Jafaru yayi saurin riƙeta take ta sulale a gurin.
Ɗaukar ta sukayi suka koma ciki da ita suka kwantar da ita a parlourn suka fara yi mata addu'o'i  Baffa na karanta mata suratul Baƙara a kunnenta tanata juyi tana buge² wannan rana sunga tashin hankali iyakar ƙarewarsu sun kasa samun kanta ƙarshe sai ido suka zuba mata suna kallon sarautar Allah.
Abu kamar wasa maganin sukeyi amma lamarin kamar ana tunzurawa motsi wannan saidai a motsata bata iya ko buɗe idanunta, Baffa ya shiga damuwa da wannan lamari.

**********

Can kuwa ɓangaren Nabeel Tunda iyayensa suka koma suka sanar dashi sunje sun tarar ana ɗaura auren Hauwah da mataimakin gwamna harma suka ƙara masa da cewa sufa bazasu sake shiga maganar ba domin ta kare tunda aka riga aka ɗaura aure kuma koma ba hakaba faɗa da aljani ba riba dole abarwa masu gari iko.
Wannan kalami Sukasa zuciyarsa harbawa aikuwa baiyi yinin lfy ba yana tashi ya fita baikai ga shiga motarsa ba ya yanke jiki ya faɗi Adam Fasaha da Nura ƙaninsa sukayo kansa suka kamashi suka sanyashi a mota suka koma dashi asibiti suna isa aka shiga dashi ɗakin da za'a duba shi don bashi agajin gaggawa likitan ya fito ya dubi fasaha yace “Wai meye yake damun guy ɗin nan ne zuciyarsa fah ta kamu da ciwo meye yasa a ransa daya janyo masa wannan ciwon me wahalar sha'ani?"


Hawaye Fasaha ya ɗauke a idanunsa yace “Soyayya itace take neman ɗaukar rayuwar aminina wannan duniya ta cika da azzalumai meye yasa Mal Baffa yasan bazai bashi auren Hauwah ba yabarshi yayi zurfi a soyayyarta meye yasa ƙaddarar tazo a haka Nabeel meye dalili?"
Yana maganar yana kuka kamar ƙaramin yaro jinjina kai likitan yayi yace “To gaskiya akwai damuwa idan ba cirewa kansa ita yayi ba zai kashe kansa a banza mace ba tabbas ke gareta ba tana samun wanda yafisa iya soyayya mantawa zatayi dashi"


Jinjina kai Fasaha yayi yace “Bana tunanin haka har yanzu da aka ɗaura auren Hauwah da Mataimakin gwamna banji zuciyata ta karaya ba inajin kamar zata dawo garemu"
Shidai likita gaba yayi abinsa ya kama harkokinsa a asibitin Hajiya Naja Mahaifiyar Nabeel tazo ta samesu tayi faɗa kamar zata haɗiyi baki ƙarshe taci alwashin ko zai mutu sai an ɗaura masa aure da Ma'idah har tana furucin muddun tana raye bazata taɓa aminta ya auri ƴar mutumin nan ne son zuciyar masifa ba.


Kwanaki sukayita tafiya Nabeel Kullum ciwonsa gaba yake ƙarawa babu wata siffa ta sauƙi kamar dai Hauwah da itama saida ta kwana biyar bata cikin hayyaci saida Mal Baffa ya kira wani malaminsa a Maiduguri ya sanar dashi abinda ke faruwa yayo tattaki yazo kanta sannan ta miƙe amma babu ƙarfin jiki ga raɗaɗin zuciya da ƙunarta tunda ta tashi taƙi yima kowa mgn sai kuka da takeyi abinda ya ƙara tashin hankalinta tanata kiran wayar Nabeel Bata tafiya.

Sosai firgici ya shigeta cikin ranta tana roƙon Allah yasa ba wani abunne ya sameshi ba, bata tsinke da lamarin ba saida ta yini sur tana kiran wayar bata shiga da la'asar tana kwance idanunta na tsiyayar da hawaye ranta na faɗa mata ta shirya barin gdannasu ta tafi wani gurin a ɗaura mata aure da Nabeel ɗinta, wata zuciyar tana hanarta da aikata hakan.
Tananan kwance Salma ta shigo ta dubeta da takaici domin a ɗakin Hajiya Sahura wato Inna Bilkisu ce kawai batayi baƙin cikin wannan dami a kala da Hauwah ta samu ba mataimakin gwamna kuma ɗan takarar gwamna na zaɓe me zuwa wannan abu ya tashi hankalinsu hatta Baffa fushi sukeyi dashi don sunce baƙin ciki yakeyi musu yana nuna musu fifiko suda suke da yawa gasu duk mata ya kasa ɗaukar wacce zai bawa mataimakin gwamna a cikinsu sai wata Hauwah bera da batasan ciwon kanta ba.


Taɓe baki tayi tace “Ai saiki samu damar tashi maigida na kiranki a falon baƙi....."
Kafin Salma ta rufe bakinta gaban Hauwah yayi kwance² ya yanke ya faɗi tace “Parlourn baƙi kuma Yaya Salma su waye sukazo?" Harara ta zabga mata tace “to aikeni na gano miki banza dake"

A kasalce kuma a wahalce ta tashi rigar bacci ce kawai a jikinta ko bra babu gata ubangiji yayi mata baiwar sama da ƙasa komanta girgiza yakeyi.
Batare da tunanin komai ba ta ɗauki ƙaton hijjab ɗin ta har ƙasa ta zura tasa takalmi ta fito idonnan jawur saboda kuka daɗin daɗawa har lkcn hawaye kebin kuncinta ta ratsa falon zata fita taji anja tsaki ta bayanta ta gane Muryar shiyasa bata wahalar da kanta wajen waiwayawa ba tayi gaba tabar parlourn ta buɗe ƙofar baya ta nufi na baƙin tun daga harabar gdan tasan koma su waye to manyan baƙine don taga alama ta motocin dake Parke a harabar gdan.
Tana tafe jiki a mace harta isa ƙofar ta tura ta shiga da maƙalalliyar sallamarta da bata samu damar gama fita ba saboda idanunta da yayi mata tozali da mutum mafi munin halitta a idanunta gabanta ya bada wani dammm!

Ranta ya fara yi mata hudubar  ta juya amma batada damar hakan domin Baffa ya kasa ya tsare ya kafeta da ido, dole badon ranta yanaso ba saidon bata isa motsi ba ta nufi cikin parlourn da sassarfa ta nemi guri ta zauna Baffa yaja numfashi tare da miƙa mata hannu yace.
“Auta matso gareni mana ya jikin naki?" Yayi tambayar yana ɗora hannunsa akanta lkcn da take matsowa kukanta na neman rinjayar juriyarta.
Murmushi yayi ya kama hannunta ya ɗago yace “Cancata ce tasa nabaka auren Autata Adnan ga Hauwa'u nan amanarka ce tun Hauwah batasan kanta ba kasanta kasan kuma ya take a gurina bata kuka face nima na koka koda idona bai koka ba zuciyata zata koka bata dariya face nima na dara, Adnan Allah shaidane bantaɓa yima Auta dole ba sai akanka don nasani kafi cancanta cancantar mallakarta kasani yarinya ce ƙarama me tashen ƙuruciya da wauta wadda ta samo asali daga gatan da na nuna mata cikin ƴan uwanta. Na sanar dakai komai game da ita kace zaka iya to alhmdllh gaka gata matarka ce halalinka ce Adnan Ina fatan Hauwah ta samu alfarma da alfarmarka ta samu tausayi da tausayinka ta samu kulawa da kulawarka gatanan Adnan gatanan Adnan ga Hauwa'u nan kayi hƙr da ita insha Allahu zakayi alfahari da aurenta bayan wuya sai daɗi"


Koda gama wannan furuci saiya kamo hannun Adnan ya ɗora hannun Hauwah yayi musu murmushi yace “ku rayu cikin aminci inayi muku fatan alkhairi"
Daga haka ya juya ya fice yabar Alh Adnan da rikicin Hauwah da tunda Baffa ya fara mgn take kuka me cin zuciya gabaɗaya yanayinta ya kashe masa jiki ji yakeyi kamar shima yasa kukan baisan damuwarta ba balle yayi mata maganinta.


Sun jima a zaune batare da kowannensu ya iya furuci ba babu abinda ke tashi a parlourn daga sautin iskar fan data AC sai sautin kukanta da bugun zuciyar Alh Adnan da bakinsa ya sarƙe ruhinsa yake zugi da zugin zuciyar Hauwah.
Daƙyar ya aro juriya ya sanyawa kansa ya sauko daga kujerar ya tsugunna gabanta ƙamshin turarensa da hucin numfashinsa na shiga jikinta shima nata ƙamshin na narkar da lakar jikinsa tare da saukar masa da kasala me cike da shauƙi tausayi da ƙauna, a ɗarare yakai hannunsa masu taushi da wani ɗumi me ɗauke kuzarin jiki ya ɗago face nata ta lumshesu tare da sanya hannunta zata cire masa nasa ya sake riƙeta sosai ya sunkuyar da kansa ya ɗora lips ɗinsa saman lips ɗinta, tayi wani saurin ja baya saboda wani azababben shorck da taji tun daga tsakiyar kanta har babban yatsan ƙafarta.


Yaji fiye da abinda taji amma hakan baisa ya saketa ba saima janyota da yayi da sauri ya haɗe tazarar dake tsakaninsu ya saki wata ajiyar zuciya da take bayyana irin girman yanayin daya tsinci kansa game cikakken hankali a gurin Hauwah kuwa babu abinda ta fahimta illa tsagwaron iskanci da wulaƙanci, tayi duk ne yuwuwa ta janye ta kasa saima ɗumin jikinsa dake sauke mata wata kasala me ƙarfi.
Yanayin yayi mata wahala lkcn data tsinkayi harshensa saman kuncinta yana tsane mata ruwan hawayen dake zuba ta ijiyarta da harshensa ta lumshe idonta shima ya lumshe nasa ya sake sanya hannunsa ya matseta tare da yin ƙasa da hannun nasa daidai mararta yayi mata riƙon tsauri ya cire bakinsa daga fuskarta cikin wata murya me rawa yace “My Bri...de....." Bai iya ƙarasa abinda yakeson yace ba saboda tsigar jikinsa da yaji tana tashi ya maƙaleta sosai yanajin yanda take jan zuciya tare da ɗigar hawayenta a saman hannunsa.


Cikin rauni yace “Nasan komai babu abinda Baffa ya ɓoyemin dangane da damuwarki kada ki zargeni Hauwa'uh Baffa ya faɗamin ne a daidai gaɓar da banida wani yunƙuri da zan iyayi bai sanar dani kinada wanda kikeso ba sai bayan ya ɗaura aurena dake, kiyi hƙr haka Allah ya tsara babu me iya canzawa hukuncinsa ne ikonsa ne......"
Cikin kuka ta ɗago ta zuba masa manyan idanunta masu rikita mazan gaske ta buɗe baki tace “Hukuncinsa ko hukuncinku? Allah ba azzalumin sarki bane baya taɓa jarabtar rai da abinda zai wahalar da ita Adnan kune azzalumai masu son zuciya da kuka take haƙƙina dana My Nabeel kukayi amfani da ƙarfinku da isarku kuka hukunta hukuncin daba na ubangiji ba, Adnan kayi amfani da damar ka kana ganin ka rabani da Nabeel ka aureni Ni Hauwah na rantse da Ubangijin daya jarabci ruhina da ƙaunar Nabeel bazan taɓa yi maka biyayya ba bazaka taɓajin daɗin rayuwa dani ba Ni Hauwa'uh saina buwayeka na addabeka Ni kaɗai saina hanaka kwanciyar hankali dole da kanka saika gaji da lamari na abubuwa da yawa zasuyita faruwa mabanbanta a siffa masu kamanceceniya a ma'ana kaje ka rubuta ka ajiye daga rana irin ta yau bazan ƙara yiwa Baffa musu ba bazan ƙara nuna masa ƙuncin zuciyata game da aurenka ba amma wlh kasani bansonka ba kuma zan taɓa sonka ba daganan har ƙarshen rayuwa, kace komai kaji ka gani zaka iya to ka ƙara shiri duk abinda nazo maka dashi ka karɓe shi kawai".........


*OUM HAIRAN*
[1/17, 8:39 AM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB15-16_*

_Wannan littafin na kuɗine Nrml 300 VIP 600 Wanda basason group wato special 1k acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama don samun damar karanta wannan littafi cikin aminci._

Ko ku tuntuɓeni direct ta wannan Link ɗin👇🏼

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
________________________________________________________________________

_*THDGB15-16*_


Da wani yanayi na tsananin sanyin jiki Alh Adnan yakebin laɓɓan Hauwah da kallo bai dakatar da ita daga furta abinda ke ranta ba sai bayan ta gama sannan ya lashi lips ɗinsa jikinsa a mace ya sauke ajiyar zuciya ya janye hannunsa daga fuskarta ya miƙe yana saɓa babbar rigarsa yace “am ready My Hauwah kizo da duk abinda kika tanada nima na shiryawa hakan Allah ya bamu saa ya baki ikon aiwatar da duk abinda kika furta mugani Ni dake waye zai saurin karaya"
Bai jira abin cewarta ba ya fita a falon ya karasa sukayi sallama da Baffa kamar babu komai, duk da cewa Baffa yaso gano matsala amma ADN Sooraj yaƙi bashi dama, ya ƙarasa jikin motarsa ya buɗe ya dauko wani akwati babba ya kira me gyaran flowers ya bashi yace ya shigarwa da Hauwah gda tare da zaro wata rufaffiyar takarda ya bashi yace duk yakai mata, kafin Mudi ya tafi saida Alh Adnan yayi masa kyauta me tsoka sannan ya shiga motarsa yaja ya fice zuciyarsa jagule da tunanin kalaman Hauwah da suka girmi shekarunta.


Wata iska ya furzar tare da dukan sitiyari yace “Oh My God! Allah kana yawan jarabtata akan mata bansan meye dalili ba, ka jarabceni da Ummah tayi zamaninta ta tafi ka jarabceni da Maryam tazo har shege ta haifamin ta tafi, ka kuma jarabtata da Juwaira tabar gdana babu hayyaci ta fita mota ta bugeta ta mutu ka kuma jarabtata da Amina itama ta mutu Allah ka jarabceni da Fiddausi na jarabtu da tsoronta da tsanarta wadda tasa na yanke shawarar sallamarta, Allah  ga Hauwah nan furucinta ya girmi shekarunta kada ka bani ikon cutar da ita ka bani ikon riƙe amanar wannan bawa naka"


Babu wani kuzari ya nufi gdansa yayi parking ya fito dakarunsa suka nufosa ya dakatar da kowa ya nufi hanyar da zata sadashi da sashinsa, cire babbar rigarsa yayi ya ajiye ya faɗa kan gado zuciyarsa nayi masa raɗaɗi lamarin Hauwah ya firgitashi kalaminta sun tsoratashi, ba'a taɓa halittar macen data faɗa masa kalaman da yake neman hargitsa kwanyarsa ba sai Hauwah.
Shafa kansa da yaji anayi shine yasashi buɗe idanunsa ya saukeshi akan Salma tayi masa murmushi tace “Meye dalilin damuwar taka?" Ajiyar zuciya yayi ya tashi zaune yace “Ki bani ruwa me sanyi" miƙewa tayi ta ɗauko masa ruwan ya kurɓa ya haɗiya kamar ya haɗiyi magani ya zuba idanunsa saman fuskar Salma yace “Ina Na'ilatu?" Yatsina fuska tayi tace “Tana inda ka ajiye ta mana"

Lumshe idanunsa yayi yace “Ok" shiru ce ta ratsa daga bisani ta ɗago ta dubeshi tace “His Exalency baka kawo mana Amaryar mun ganta ba koda yake abinne kamar a ƙure amma dai koma mene ya kamata a kawo mana ita" murmushi yayi na yaƙe yace “Salamatu kenan saurin me kikeyi abu da zatazo ku zauna tare" ƙasa tayi da kanta tace “ai dayake naga kayi nisa a ƙaunar bbyn nan kamar tafi sauran mata"
Shiru yayi mata saboda gudun kada yayi suɓul da baka bayason kowa ya fahimci matsalarsa da Hauwah yafison ya shawo kan abun dakansa, Da wannan ya miƙe ya shiga bathroom Hajiya Salamatu tayi saurin ɗaukar wayarsa ta lalubi number da dake tsammanin itace ta Amaryar tasa domin taga yasa My third Wyf ta ɗauki hoton number ta mayar da wayar ta ajiye ta.
Ruwa ya watsa saman tattausar fatarsa ya ɗauki towel ya goge jikinsa ya shafa mai ya fito har zuwa lkcn Hajiya Salmah tana zaune ta miƙe ta buɗe wardrobe ta ɗauko masa doguwar riga me gajeren wando ya karɓa ya saka tana tayashi ya juya ya fice daga ɗakin domin tafiya masallaci sallar Magrib,

Hakanne yabawa Hajiya Salma damar tashi ta nufi ɗakinta ta ɗauki sabuwar wayar da tasa aka siyo mata ta sanya mata sim ta buɗe  sannan ta copy number ta shiga gurin rubuta saƙonni ta rubuta saƙonta ta tura ta kashe wayar gabaɗaya.


Ta ɗaga katifar gadon ta sanya wayar ta sake gyara fuskarta ta fito daidai lkcn da Khairiyya take janyo ɗuwawu tana saukowa daga saman benen Hajiya Salma ta watsa mata harara tare da jan tsaki Hajiya Na'ilatu ta fito itama ta dubi Khairiyya ta watsar tace “Ƴar wahala kin janyo gindi kin fito zaki addabeni" harararta Hajiya Salma tayi tace “aikin banza ƙiba a kunne ke kyace wata tsiya take mata...."
Turo ƙofar parlourn da akayi ne yasasu nufar Khairiyya dukkansu suna cewa “Sannu Khairiyya fitowa kikayi aida kin bari anzo an ɗaukoki me kike buƙata a kawo miki?" Wani daɗine ya cika zuciyar ADN Sooraj ya ƙarasa ga Khairiyya ya ɗauketa cak ya zaunar da ita a kujera ya shafa fuskarta da take zubarda hawaye yace “Bana ƙaunar ganin kukanki Fatimah ke gashi ba baki gareki ba bare ki faɗamin damuwarki" lumshe idonta tayi ta buɗe su akan mahaifin nata ta daga hannunta takai bakinta alamun tana buƙatar abinci" Hajiya Salma ya duba tayi murmushi tace “Uwar masu gda kin fiye rikici yau kinƙi cin abinci komai nasa aka dafa sai kice bakiso to kodai na sabuwar mamanki kikeso?"

Kwantar dakai Khairiyya tayi tana nuna kanta tana murmushi Alh Adnan ya kama hannunta shima yayi mata murmushi, abinda yasa Hajiya Na'ilatu da Hajiya Salmah kallon juna suka taɓe baki Hajiya Salma tayi ƙarfin halin cewa “Hakane yarinya ta kusa zuwa ai bari na ɗauko miki kununki" sashin da kitchen na falon yake ta shiga ta haɗo mata kunun ta fito tana juyawa Alh Adnan da kansa ya karɓa ya rinƙa bawa Khairiyya tanasha tana kallonsa idanunta na tsiyayar da hawaye maganganu ne,


A bakinta saidai babu halin furtasu Khairiyya kenan baiwar Allah Ƴa ɗaya tilo gurin ADN Sooraj wadda ya sameta bayan dogon zaman jiran tsammani Mahaifiyarta Ruƙayyatu Allah yayi mata rasu itama kamar Hauwah tun ranar haihuwarta Ruƙayyatu tayi zamaninta ne matsayin mata ta uku ga Alh Adnan, Hajiya Na'ilatu itace Babba sai ya auri Ummulkhairi batayi dogon zango ba ta fita a gdan, bayan rabuwarsa da itane ya auro Ruƙayyatu itace mace ta biyu da tafi kowa daɗewa bayan Na'ilatu domin ta ɗauki shekara goma sha biyar tare dashi hƙrnta da taƙawarta sune suka zaunar da ita a gdan bawai tsantsar jin daɗin zaman ba.
Bayan dogon lokaci zaman jiran dako da nema bacan banan sai ubangiji ya nufi Hajiya Ruƙayyatu da samun rabo, huuuu kuzo kuga tashin hankali gurin Hajiya Na'ilatu tabi ta damu kanta ta rinƙa rama kullum kalmarta ɗaya ce, dama Adnan zai iya haihuwa yaƙi yi mata ciki itama ta haifi nata? Wannan tambaya ta tashi hankalinsa lkcn data furta masa ta rinƙa kuka tana roƙonsa itama yayi mata ciki.

Bashi da abin cewa daya wucce ya bata hƙr badon kalmomin hƙrn nasa suna aiki a gunta ba saidon batada abinda ya wucce shi yasa ta saduda saduda ta zahiri baɗini kuma cike da tunane²n neman mafita domin taci laya ba'a isa a haifi wani ɗa ya rayu a gdan  ya kwashe kaso na dukiyar Alh Adnan tana zaune tana kallo ba.
Hajiya Ruƙayyatu na rainon cikinta kullum ita kenan a rashin lfy babu yau babu gobe komai bata iya taɓukawa kanta saidai ayi mata, tunma Alh Adnan baikai wadatar yanzu ba haka ya zuba mata ƴan aiki suke kula da ita cinta Shanta komanta.
A bangaren Hajiya Na'ilatu kuwa itama bakin ƙoƙari takeyi don ganin ta nunawa Alh Adnan babu komi, shikuwa Namiji dake ba komai na kaidin mace yake ganewa ba saiya amincewa zuciyarsa cewa babu komi ɗin hakanan akaci gaba da gurgurawa daɗi rashin daɗi har zuwa lkcn da ciwon naƙuda ya kama Ruƙayyatu lkcn Alh Adnan baya Kano yana Lagos burin Hajiya Na'ilatu ya cika gata ga Ruƙayyatu ga gogan bayanan aikuwa tasa me aiki ta kunna mata garwashi ta rinƙa yima Hajiya Ruƙayyatu Hayaƙi tana zuba mata sannu tana cewa ai Hajiya babba wato surukarsu tace muddin aka hayaƙa wannan magani to salamun salamun za'a haihu.

Meye zai faru anayin wannan hayaƙi sai ciwo ya tattara nasa ya nasa ya tafi saiga Hajiya Ruƙayyatu ta miƙe damfamfam tanata harkokinta kamar ma an ƙara mata ƙarfi to basai haihuwa ta koma ta zaune ba ciki kullum sai ƙara hanƙara yakeyi yana rinjayar Ruƙayyatu tun anasa ran haihuwa cikin watan har wata ya ƙare aka shiga wani shima ya ƙare wani ya kama shima ya tafi ciki ya shekara kenan a jika.
Nanne hankalin Alh Adnan da iyayen Ruƙayyatu ya tashi suka bazama neman mafita asibitoci gurin likitocin gargajiya amma abu kamar turi idan akace da ruƙayyatu kinajin ciwon mara sai tace ita lfy ma aka ƙara mata,
Ƙarshe sukaje gurin wani me magani a Niger cikin garin Niamey ɗan surkullen ya dubesu ya girgiza kai ya kuma dubansu ya girgiza kai Alh Sani ya dubeshi yace “Allah gafarta aikin mal kayi mana bayani mana damu dakai dukka musulmi ne zamu karɓi ƙaddara yanda ta sauka babu wani bawa da ya isa canzata saidai ya zama sila ta faruwar ta amma dama rubutaccen al'amari ne daga buwayi ɗayantaccen Sarkin da baayi masa dole"

Jinjina kai Mal Gogi Buzu yayi yace “Hakane Muhammadu Sani Haƙiƙa lkcn haihuwa ya wucce tuntuni Bama wuccewar tasa ce matsala ba domin akwai hikimomi da za'a iya aiwatarwa don samun saukarta lfy da yardar mai duka, inda matsalar take shine"
Shiru yayi yana jinjina girman al'amarin ya kuma ɗagowa yace “An sanya miyagun shaiɗanu sun toshe mahaifar ne sannan anyi musu kyauta da ɗayan biyun jinin abinda za'a haifa ko me haihuwar dole koda za'a haihu to za'a rasa ɗaya....."
Wata zabura Alh Adnan yayi yace “Wa....Wazaa rasa matata ko ƴata Mal a'a duka inasonsu abarsu basai an rasasu ba gara tayita zama da cikin tunda ba ciwo takeyi b.........

*OUM HAIRAN*
[1/18, 7:28 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB17-18_*

_Wannan littafin na kuɗine Nrml 300 VIP 600 Wanda basason group wato special 1k acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama. Na rantse da Allah ɗaya Sarkin da bashi barin zalumci bazan yafewa wacce ta fitarmin da littafi ta janyomin zagi ba, da kuma wacce ta karantamin bata biyani haƙƙina ba._

Ko ku tuntuɓeni direct ta wannan Link ɗin👇🏼

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
________________________________________________________________________

Sunkuyar dakai Mal Gogi yayi yana jan casbahar hanunsa ya ɗago idanunsa cike da hawayen tausayin wannan bawa na Allah yace “Bakin alƙalami ya riga ya bushe Adnan dole ɗayan biyun zata faru sanin wanda zai rasa rayuwarsa a cikinsu sai Allah amma da jaririn ne zai rasa ma da da sauƙi kuje kawai kuyita addu'a Allah ya sanya komai yazo cikin sauƙi"
A matuƙar saluɓe suka miƙe suka fito tunda suka taho Alh Adnan bai iya furuci ba tsakanin Niger da Nigeria da tazara gashi sun riga sun taho da mota ga kuma dare ya shigar musu dole tasa suka nemi hotel suka sauka suka kwanta amma Alh Adnan bai iya runtsawa ba gabansa sai faɗuwa yakeyi aikuwa sun fita sallar asuba suna dawowa ya tarar da miscall rututu ya ɗauki wayar da fargaba yaga mabanbantan lambobi ne sukayi kiran bai bawa Kowacce number muhimmanci ba kamar ta Hajiya Na'ilatu yana kuwa kira ta ɗaga cikin kuka me sagar da jijiyoyi tace “Shikenan ta faru ta ƙare Ruƙayyatu ta haihu amma ta tafi ta barmu da ɗanyer jaririya Alh kadawo yarinyar nan tana buƙatar kulawa....."


Bai gama sauraron kalamin nata ba ya saki wayar tare da durƙushewa yana tasbihi ga ubangijin da yake zartar da hukunci batare daya shawarci kowa ba, dsƙyar Alh Sani ya rarresheshi suka nufi airport suka diro Kano suna isa ana fitowa da gawar Alh Adnan ya riƙe makarar yana kukan da saida kowa ya tausaya masa, ga ƙoshi ga kwanan yunwa kenan an daɗe ana nema Allah ya kawo kuma ya ɗauke cikon jin daɗin.

Daƙyar aka ɓamɓareshi daga jikin makarar aka fice da ita zuwa gdanta na gaskiya aka suturtata  ranar Alh Adnan ko gaisuwa baya iya amsawa saboda tashin hankali daga ƙarshe saida ya kwanta jinya ta kwanaki kafin abin ya gama nusarshi ya saduda amma duk sanda ya tuna Ruƙayyatu yakan yi kuka har ya rasa me rarrashi matar arziƙi wacce har yanzu bai maida kamarta ba.

Bayan an watse ne daga zaman makoki lkcn akwai wata ƙanwar Hajiya Ruƙayya tana goyon jariri ita aka bawa Ruƙayya ƙarama wato Khairiyya ta shayar da ita saida ta isa yaye Hajiya Na'ilatu ta matsa akan ya karɓota su raineta sa rinƙa ganinta sunajin daɗi.

Tabbas da ace Alh Adnan yasa ƙudurin Na'ilatu da bazai karɓo Khairiyya daga hannun ƙanwar uwarta ba, to amma ina ƙaddara ta riga fata.

Haka yaje ya ɗauko Khairiyya ƙanwar uwarta Kubrah na kuka itama yarinyar nayi don har guduwa tayi dake tana yawonta ko ina, da hikima Alh Adnan da Hajiya Na'ilatu suka ɗaukota suka taho da ita Hajiya Na'ilatu kamar ta mayar da ita cikinta saboda nuna ƙauna yanata jin daɗin yanda takeson ƴar tasa.


Koda sukaje gda goye Khairiyya tayi tana rarrashinta itace ɗauko wannan ɗauko wancan tana bawa yarinyar nan danan abin yaro saita ware taketa harkokinta a ranar dai abin gwanin gwasama a haka kuma ta gama shirinta tsaf na lalata rayuwar yarinyar amma sai Allah bai nufa ba, tabbas Khairiyya tasha wahala sosai sanadin wahalar da aka rinƙa gana mata da ciwukan da aka rinƙa ɗora mata ne yasa bakinta da ƙafafunta daina aiki gadai ƙafa sambal ko irin shanyewar nan batayi ba amma bata isa ta takata ba anyi maganin anyi har an gaji, duk wata ƙasa da yasan inya kaita zataji sauƙi yakaita amma babu wani sauƙi saina ubangiji.

Harma dai ya hƙr ya zubawa sarautar Wahidun ƙahharu idanu, Alh Adnan Allah ya jarabci ruhinsa da ƙaunar haihuwa kuma an tabbatar masa shiɗin ƙwayayen halittarsa basuda ƙarfi ba kowacce mace yake da damar bawa ciki ya shiga mahaifarta ba wannan ne yasashi aure² a burinsa na ganin ya samo wacce ƙwan nasu zaiyi daidai ko ya samu a samawa Khairiyya ƙani amma ina haƙa ya gaza cimma ruwa sai lalube a duhu hardai karshe ya hƙr ya zauna da Na'ilatu ita ɗaya inda a shekarun baya bayan nan da basu wucce shida ba ya auro Salamatu wadda tazo ta ɗauki hannu harma tafi Na'ilatu iyawa ita iyakar masifar mutum bazai gane inda ta dosa ba baka gane abinda takeso da wanda take ƙi makira ce ta yankan shakku hakan yasa suka ɗinke da Na'ilatu suke shuka tsiyarsu son ransu.
  

Ko lkcn daya nuna yanason auren Hauwah Hajiya Na'ilatu ce ta taushi Hajiya Salma akan kada su kuskura su nuna masa sun damu da auren nasa yayi ya kawota badai yarinya bace itama zasubi da ita saita zama yar partynsu  sai sun juyata sun bata umarnin abinda zatakeyi a gdan kuma haihuwa ce Indai suna zagawa a gdan babu macen data isa ta haihu muddin basu haihu ba.
A haka ake zaune a gdan Alh Adnan kowa da abinda ya binne a ransa inda shi kuma ya ɗauki yardar duniya yabawa na'ilatu yayi imanin bazata cutar dashi ba baisan itace ashanar ƙona gdansa ba.

***********

A Hauwah kuwa bayan tafiyar Alh Adnan ta koma gda kenan Mado ya shigo da akwatin da Alh Adnan ya bashi ya ajiye a tsakiyar Parlourn ya dubi Hajiya Mariya yace “Hajiya Exalency ne ya bada wannan a kawowa amarya" kallon Hauwah tayi data taɓe baki tare da turo ɗankwali gaba tace “Dama ya bar abinsa ya kaiwa guzamen matansa....." Hannu Yakumbo takai zata buge mata baki tayi ƙasa da kanta duk da haka saidata samu tagomashin ranƙwashi tace “Zanci ƙaniyarki akan waɗannan miyagun kalaman da kikeson sabarwa bakinki akan mijinki"


Miƙewa tayi ta shige ɗakinsu ta ɗauki wayarta tana bin saƙonnin Nabeel tana dubawa taji an shigo ta ɗago suka haɗa ido da Yaya Salma ta galla mata harara tace “Wata sakarya dake waike ƴar so an zaɓeki an baki irin mijin dana daɗe ina mafarkin samu"
Murmushi tayi tace “to ayi musanye mana Yaya Salma kibani naki na baki wannan tsohon gwangwanin don inaganin ƙila arziƙin ƙuruciya yasa nayiwa Jamal biyayya tunda baikai Wannan najadun shekaru ba kuma shi matarsa ɗaya"
Salma ganin Hauwah tamai da ita sauna yasata harararta ta juya ta fice a ɗakin bayan ta ɗauki abinda zata ɗauka Bilkisu ta shigo da gudu tana cewa “Kuttt Auta Allah ya kashe ya baki ke kinga kafuran kayan da guy ɗin nan ya kawo miki harda agogon gold kayy wannan kyautar girma ta tsumani Hauwah kin samu irin wanda ake yayi yasan darajar soyayya....."

Ruwan dake hannunta ta jefeta dashi tace “Zanci kutmar uban Babanki idan baki ficemin anan ba shegiya ƴar son zuciyar masifa kije ki ɗauka babu uwar da zanyi dasu inma kun barsu wlh saina bayar don bana ƙauna me kayan bare na ƙaunaci kayansa"..........
Wata shewa Bilkisu tayi tace “Ahayye nanaye arangwaɗi maɗiso kajimin wata yar asarar wai batason me kayan toke dan ubanki an faɗa miki megida yana zaɓin banza ne kina ganin mutum zabgege kyakkyawa son kowa ƙin wanda bai samu ba sannan ga mahaɗin rayuwa ya samu hatimin nasara yaci ya tada kai ke yanda kike da siffar manyan matan nan kina zuwa kika lumtsuma cikin hutunnan ga kuma ban ruwa anayi miki ai Inkin fito bazamuke ganeki ba saikinyi mana bayanin kanki...."



*OUM HAIRAN*
[1/19, 8:01 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB19-20_*

_Nrml 200 VIP 500 Wanda basason group wato special 1k acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama. Na rantse da Allah ɗaya Sarkin da bashi barin zalumci bazan yafewa wacce ta fitarmin da littafi ta janyomin zagi ba, da kuma wacce ta karantamin bata biyani haƙƙina ba._

Ko ku tuntuɓeni direct ta wannan Link ɗin👇🏼

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
________________________________________________________________________

Bata ƙara sauraron Bilkisu ba kasancewar ta fahimci so take ta fusata mata zuciya da maganar wannan banzan mutumin a cewarta,
Haka rayuwar taci gaba da tafiyar hawainiya babu wani daɗi da Jiddarh ke tsinta a lamarin rayuwarta ta yanzu kullum zuciyarta da ƙunci har aka cinye wata ɗaya da ɗaura aurensu.
A lkcn ne kuma Nabeel ya fara samun kansa, duk yanda Baffa yaso ya darajta aurenta taƙi bashi dama kullum suna manne da Nabeel a waya idan kuma sun tafi makaranta ta raɓe yazo suyita hirarsu ta soyayya mantawa ma sukeyi da wani abu aure idan ba faɗo musu abin yayi.

Takai yanzun sai yazo bayan gdansu ta ɗauki wanka ta ɗau kwalliya taje suyita hirarsu suna dariya, duk wannan abin da akeyi Baffa bai sani ba domin daga ita sai ƴan uwanta mata suka shirya abinsu Nana itane me gane mata hanya.
To yauma kamar ko yaushe suna cikin mota suna hira Allah ya jefo Baffa ya dawo daga Bauchi har ya wucce Abees yace masa “Baffa wacce a motar can kamar Auta? Ko Exalency ɗin ne yazo?"

Faɗuwa gaban Baffa yayi ya zaro wayarsa ya kira wayar Alh Adnan suka gaisa yace masa “Kwana biyu bakazo gurin Amaryar taka ba kodai tayi laifi ne?" Cikin kunya Alh Adnan yace “aa Baffa wlh wani uzuri ya kaini Lagos sai jibi zan dawo insha Allahu" jinjina kai Baffa yayi cikin ƙunar zuciya sukayi sallama daidai lkcn da Abees yayi parking ya fita a motar yana ce masa kaje koma dawa take tare ka tahomin da ita.

Murmushi Abees yayi ya juya ya fita ya nufi inda suke ya tsaya a jikin motar tana ɗagowa taganshi gabanta ya faɗi amma saita dake ta fito ana haka saiga Ya Mubarak ya nufo gurin yana zuwa ya tarwatse glass ɗin motar abinda ya sabbaba mata fitowa kafin takai ga motsi Abees ya ɗauke ta da mari Nabeel na fitowa Mubarak ya kifansa tafi yace.
“Dan farka da baisan arziƙin aure ba wato amma auratta ɗin bazaka barta tayi biyayyar iyaye ba bare ta aure to kuwa zakayi bayani a station" yana rufe bakinsa motar ƴan sanda na tsayawa suka kuwa rufe Nabeel da duka Hauwah ta fashe da kuka tana cewa Innanillahi na shiga uku kada ku kashemin shi don Allah ku daina dukansa bashi......"


Jinin daya wanke mata fuska ne yasa jiri ɗibanta tayi baya zata faɗi Mubarak ya finciketa Suka nufi gdan, duk da kukan da takeyi da kuma jinin dake zuba a bakinta bai hanata nemawa masoyin nata sassauci ba amma police ɗinnan basu tausaya masa sun fasa tafiya dashi ba motarsu ta tafi ita kuma sukayi gda ta ida suna shiga suka watsar da ita gaban Baffa dake zaune a parlournsa ya rafsa uban tagumi.
Ganin sun watsar da ita ne yasashi ɗagowa idanunsa ya kaɗa yayi jajir ya cije lips ɗinsa tare da furzar da iska yace “Kin bani kunya Hauwa'u haƙiƙa kin bani kunya bantaɓa tunanin wannan aikin jahilan daga zuri'ata ba kaico Hauwa'u kaico da wannan mummunan aiki naki banyi zato ba Hauwah meye yasa kike ƙoƙarin bawa zuciya dama shaiɗan ya rinjayeki aikata alfasha ya salam! Ya salam Auta naji tsananin kunya da nasamu wannan aikin tur a gareki tabbas yau kin mutu kin lalace yau sai buzunki Hauwah Abees kuje ku haƙamin kabarinta nidai da wannan mummunar hanya da kike shirin daukarwa kanki....."

Takaici ne da baƙin ciki yasa Baffa yin shiru yanajan zuciya yanajin tafashin kukan Autar tasa a kasan ruhinsa miƙewa yayi zaibar gurin ta riƙe ƙafarsa cikin kuka tace “Na rantse da Ubangijin talikai banason Alh Adnan Baffa kaji tausayina ka samawa ruhina sururi ka rabani dashi Baffa inada zaɓi...."
Ɗauke yayi da marin daya sanyata zabura ta miƙe karon farko a rayuwarta daya taɓa kai hannunsa fuskarta, zuciyarta ta ƙara ƙuntata dafin tsanar Alh Adnan ya dawo ɗanye ta buɗe baki tace “akanka Adnan Sooraj akanka Ne Baffa yayimin dole, akanka ne yayimin tsawa kuma akanka ne ya daga hannu ya mareni tabbas kaiɗin babbar masifa ce cikin rayuwata na rantse da girman Allah kaima saika koka kamar yanda bakin cikinka yasani kuka.

Tunda ta fara mgnr Baffa ya shige ɗakinsa ya ɗauki wayarsa bugu ɗaya yayima Alh Adnan ya ɗaga yace “Yaushe zaka dawo?" Da mamaki yace “dadai sai nan da kwanaki uku zan dawo amma idan kana da buƙatar ganina yanzu ma saina wakilta Speaker tunda muna tare Ni na taho" shiru Baffa yayi irin tasu ta malamai can ya sauke numfashi yace “a yau ajiyarka bazata kwana a gdannan ba wato ina nufin matarka Hauwa'u idan kanada gurin ajiyeta a gdanka xansa akai maka ita idan babu kuma zan sakota a jirgi kazo airport ka tareta wannan kawai shine abinda na yanke.
Wata marainiyar ajiyar zuciya Alh Adnan Sooraj ya sauke yace “Amma Baffa meye ya faru haka....." Daga hannu Baffa yayi yace “kada ka tambayeni dalili kawai ka shirya taɓarta yau dai tare zaku kwana sannan na haramta mata riƙe waya nanda wani dogon lkc kuma na haramta mata zuwa makarantar har sai tayi hankali"

Jinjina kai yayi yace “Shikean Baffa ta shirya yanzun zansa azo a taho da ita nan ɗin daganan ma gaba zanyi akwai yuwuwar zan wucce Saudiyya zanyi Umrah idan tanada passport a haɗa a taho dashi"
To zamu duba Bara nayi musu passport sunje Umrah Indai Bata wulaƙantar dashi ba".............


*OUM HAIRAN*
[1/20, 10:04 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB21-22_*

*_ANNOUNCED FROM OUM HAIRAN_*

_Sakamakon bina pc da kukeyi kuna roƙona nayi muku tagi to na duba kokenku nayi muku Nrml group dake 300 ya koma 200 VIP dake 600 ya koma 500 Special dake 1k ya koma 800 ga hanyar da zakubi ku biya nan👇🏼_

_Acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta number nan dake sama. Na rantse da Allah ɗaya Sarkin da bashi barin zalumci bazan yafewa wacce ta fitarmin da littafi ta janyomin zagi ba, da kuma wacce ta karantamin bata biyani haƙƙina ba._

Ko ku tuntuɓeni direct ta wannan Link ɗin👇🏼

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
________________________________________________________________________

Suna gama wayar Baffa ya sake kiran matan gdan yace suzo yanason ganinsu babu wacce ta ɓata lkc don sunsan ba ɗabi'arsa ce kiran gaggawa ba.
A tsaye suka isheshi yana kaiwa da komowa suka haɗa baki sukace “Mal Lafiya?" Guri ya nuna musu suka zauna shima ya zauna yayi gyaran murya yace “A a haɗawa Hauwa'u komai nata yau zatabar gdannan...."
Dukkansu suka ɗago yaja numfashi yace “Eh haka nace bazan ɗauki iskanci da aikin jahilci ba  yanzu ace a gdannan don bananan komai saiya lalace kuna gani kuka barta take kula wancan taɓararren yaron? To ƙarshen tukatuki tuk dai da wanda yakewa Hauwah tsawa akan kurakuranta da wanda yake zubanta ido idan ya koma gefe yayi dariya yaudai zamanta ya ƙare a gdannan zata tafi taje tayi zaman ibada kamar kowacce mace zataje tayi zaman hƙr kamar yanda kowacce mace takeyi aje asata ta shirya a kawomin ita nan"

Juyawa yayi ya shige ɗakinsa ya zauna tare da ɗaukar ruwan faro ya juye masa wani zamzam a ciki ya kafa kansa yayi addu'o'i hucin numfashinsa yana shiga cikin kofin sannan ya ajiye ya dauki wata takarda yayi rubutu ya sanya a ciki ya kuma ɗiga wani ruwa a ciki ya mayar ya ajiye,
Daidai lkcn da Yakumbo ta shigo hannunta riƙe dana Hauwah ta zaunar da ita itama ta zauna, Baffa ya zubawa Hauwah idanu duk da ta fusata zuciyarsa da abinda ta aikata har zuwa wannan lkcn yanajin ɗigon tausayinta musamman da yasan irin gdan da zata shiga zaman tsakiyar kishiyoyi gata yarinya bayan ƙuruciya ga wauta gashi abokan zaman nata Duk sun haifeta.

Fasali yaja ya ɗauko wannan ruwan addu'ar yace tasha ta ɗago ta dubeshi ya kawar da kansa ganin yanda take kuka dole cikin mutuwar jiki ta karɓi ruwan tasha ta ajiye kofin ya jinjina yace “Kije kiyi biyayya kiyi hƙr ki zama mace ta ƙwarai me farin ciki da farin cikin mijinta me ƙunci da ƙuncin mijinta Auta yau zaki tafi gdan mijinki saboda na lura ba mafita bace barinki anan nidai nasan bantaɓa auradda ɗan daya bani kunya ba duk da kin fara nunamin rashin isata da kuma rashin amfanin gatan dana nuna miki hakan bazai hanani yi miki fatan alkhairi ba amma Hauwah cikin rayuwata ɗa daga na ƴan uwana har nawa babu wanda ya taɓa ɓatamin rai kamarki banyi fushi ba kije kiyima Alh Adnan biyayya wannan shine ruwan wankin zuciyata idan kika saɓa daga hakan to tabbas zamu saɓa saɓawa me girma....."


Wayarsa dake ring ya ɗauka ya kara a kunnensa ya amsa dacewa “to gamunan"
Hauwa ya duba da tunda ya fara mgnr tayi mutuwar tsaye zuciyarta na bugawa da ƙarfi, ta ɗago zatayi mgn Baffa yace “bana buƙatar cewar komai daga bakinki biyayya kawai nakeso kije kiyi tashi mu muje"
Saida Yakumbo ta daka mata tsawa sannan ta miƙe tana me rushewa da kuka tace “Na shiga uku na lalace Baffa wlh na tuba bazan ƙara ba kabarni naci gaba da rayuwa a gdannan banaso Ni wlh banason zuwa gidansa....."


Murmushi kawai Baffa yayi ya juya ya shige ɗakinsa ya kira Ya Man yace yazo ya fita da ita ga motar da ADN ya turo tana kukanta da gunji tare da rungume Yakumbo aka ɓamɓareta aka fitar da ita daga ita sai Hajiya Sahura sai Nana suka shiga motar sai airport daga cikin airport babu ɓata lkc jirginsu ya ɗaga sai birnin Ikko ikon Allah.
Alh Adnan dakansa yazo tararsu airport har zuwa lkcn kuka Hauwah takeyi bata daina ba Nana keta aikin rarrashinta Hajiya Inna kuwa tana ganin Adnan zuciyarta ta cika da ƙunci hassada ta motsa tama kasa cewa Hauwah ko kanzil sai aikin harara, takowa yayi da fara'arsa Excourt ɗinsa na take masa baya ya rusuna da ladabi yace “Sannunku da zuwa Hajiya kunyo tafiyar gaggawa babu shiri" wani yaƙe tayi da yafi kuka ciwo tace.
“Yo ina wani shiri a wannan gantalalliyar yarinyar ai dole Mal ya liƙa maka matarka tunda tana neman janyowa mutane abin kunya yanzu Allah ya taimake ka ace kamar Auta har tasan satar hanya ta tafi gurin saurayi"


Da sauri Alh Adnan ya dubi Hauwa da taketa gursheƙen kuka tace “Yanzun ma ba fasawa zanyi ba wlh duk abinda yake mallakina zan mallakawa Nabeel saboda shine zuciyata shi nakeso ba wanna....."
Rufe mata baki Nana tayi Alh Adnan da kalamin mutum biyun Sukasa kwanyarsa juyawa yayi ƙarfin halin yin murmushi yace “Babu komai Hajiya ƙuruciya ce Autar Baffa nawa take bandama garin jiki yaja mata auren insha Allahu kwananan zata haɗa hankalinta guri ɗaya nidai burina ku tayani addu'ar sauke haƙƙin amana"
Ba haka Hajiya Inna taso ba taso ace yayi fusatar da zatasa yaji ya tsani Hauwah maimakon haka ma sai taga ya nufi Hauwa'un da take sanye da ƙaton hijjab ta janyoshi ya rufe mata fuskarta ya sanya hannunsa yana ƙoƙarin riƙo hannunta ta janye ya basar tare da cewa “your Are Welcome My Bride" ji tayi wani mashi me tsini na tsanarsa ya caki zuciyarta ta haɗiye wani yawu na baƙin ciki daidai lkcn da suka isa ga motar Excourt ɗinsa suka buɗe musu suka shiga Nana da Hajiya Inna mota ɗaya suka hau inda shi da Hauwah suka hau ɗaya badon Hauwah ta sani ba saboda ita tunaninta ita da Nana da Inna mota ɗaya suke ciki,saida tafiya ta fara nisa ta ɗago fuskarta data dame da kuka karaf idonsu ya sarƙe da juna tayi saurin kawar da nata saboda wani shorck na masifa da taji da kuma wani saƙo da ta karɓa ta cikin idanunsa.


Bata tsammata ba taji ya riƙo hannunta da nasa ya matse sosai ya saki wata ajiyar zuciya ya lumshe idanunsa ya kwantar da kansa a kafaɗar kujerar motar yanajin yanda taketa ƙoƙarin janye hannunta shikuma ɗumin hannun na saukar masa da kasala me nauyi data hanashi hassala komai..........

_Sorry My Fans naje unguwa na gaji daƙyar ina gyangyaɗi nayi muku wannan kuyi marnege da wannan_

*OUM HAIRAN*
[1/21, 1:57 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB23-24_*

*_ANNOUNCED FROM OUM HAIRAN_*



_Sakamakon bina pc da kukeyi kuna roƙona nayi muku tagi to na duba kokenku nayi muku Nrml group dake 300 ya koma 200 VIP dake 600 ya koma 500 Special dake 1k ya koma 800 ga hanyar da zakubi ku biya nan👇🏼_

_Acct details 3184512451 First Bank or 0255526235 GTBank idan kati zaki turo ki tura ta 09013718241 kuma ƴan Niger zaku iya turo katin airtel ta wannan number +227 95 04 58 22_
_Na rantse da Allah ɗaya Sarkin da bashi barin zalumci bazan yafewa wacce ta fitarmin da littafi ta janyomin zagi ba, da kuma wacce ta karantamin bata biyani haƙƙina ba._

Ko ku tuntuɓeni direct ta wannan Link ɗin👇🏼

https://wa.me/message/LFSVQWEXOXAHF1
________________________________________________________________________

Ta kasa cire hannun nata daga nasa shikuma yaƙi sakinta maimakon haka ma sai ƙara matseta da yayi yanajin wani sanyi me shiga jiki da narkar da zuciya na shigarshi yaja numfashi ya ɗago ya buɗe idanunsa akanta.
Har yanzu kukanta take rerawa cikin yanayi na rashin madafa ya ɗan muskuta yakai hannu zai dafa kanta kamar wanda ya tuna wani abu haka ya fasa kawai ya juya yaci gaba da kallon hanya har sukaje unguwar Victoria Island basuyi tafiya mai tsayi ba suka isa jikin wani katafaren guri da aka ƙawata shi da manyan gine-gine masu ɗaukar hankali yanayin iskar gurin kawai ta isa ta bayyana maka ina kake wato unguwa ce ta manyan ƴan kasuwa da kuma manyan ƙusoshin gwamnati sai turawa da Chinese da Indiawa sune kaɗai zakaga suna kara kaina a unguwar.


Duk da cewar bata cikin nutsuwa hakan bai hanata kallon ƙasan grass ɗin dake harabar gdanba wadda tsakiyarsa wani miƙaƙƙen lailayayyen kwalta ce me kwantar da hankali.
Kwaltar sukabi suka isa gaban wani gini motar nasu na tsayawa Excourt suka iso suka buɗe ya fito yana saɓa Gariyarsa ya zagaya ɓangaren Hauwah ya buɗe mata da kansa ya kamota suka fito yana riƙe da hannunta suka nufi hanyar da zata sada mutum da asalin cikin gdan Hajiya Inna da Nana sai raba idanu sukeyi, ƙauyancinsu bai ƙara tabbata ba saida suka shiga parlourn a nan ne sukayi mutuwa irin ta tsaye saboda girma da tsaruwar parlourn ko a ƙasashen Larabawa albarka ga wani ƙamshi me kashe jiki da parlourn yake badawa.

Wata ajiyar zuciyar takaici Hajiya Inna ta saki a ranta tana ayyana dama Bilkisu ko Munirat ko Salma wani Allah yayiwa wannan ni'imar,
Baƙin cikinta ya daɗa ƙaruwa data tuna yanzu fah inma arziƙin ne ba ita zataci ba Hajiya Mariya ce, nandanan zuciyarta tayi ƙunci.
Muryar Alh Adnan ce ta katse mata sukuwa a dokin hassadar da cewa “Hajiya ga ɗakunan nan ku shiga ku zaɓi wanda yayi muku nan sashin baƙi ne ku shiga ku fito saiku rakata nata sashin"
Harara ta watsa masa ta cikin hijjab ɗin bai masan tanayi ba jinsa yake kamar wani ɗan shekara ashirin da biyar saboda nishaɗi, a haka har suka shiga sashin baƙin dakuna ukune a cikin parlourn Hajiya Inna ta buɗe na farko suka shiga taja numfashi tace “Masha Allahu Auta guri yayi kyau saidai fatan zaman lfy" shafa kansa yayi yajata jikinsa yace.
“Nan ɗin yayi muku Hajiya?" Jinjina kai tayi tace “Yama wucce yi ai"

Jinjina kai yayi yace “Ok kuyi wanka kuyi sallah bari nasa a kawo muku abinci" yana faɗin haka ya juya Hauwah na maƙale a jikinsa yana ƙoƙarin fita ta kuwa ja ta cake taƙi motsawa batare da tunanin komai ko kunyar Hajiya Inna ba ya ɗauke ta cak ya nufi sashin da yake na masu gdan da ita.
Wani abun tausayi duk mugun tanadin tada shirya masa saita samu kanta da kasa yunƙurin ƙwacewa har saida yashigar dasu Parlourn ya wucce parlourn ya buɗe wani ɗaki ya shigar dasu ya direta saman wani tattausan carpert yaja baya yanayi mata murmushi tare da kai hannunsa ya janye mata hijjab ɗin tayi baya ta jingina da bango ta buɗe idanunta akansa natan suka shiga cikin nasa tayi saurin ƙasa saboda wani kwarjini da taga yanayi mata walainiya a idanunta batare data shirya ba ta lumshe idanunta ta tsakanin idanun nata hawaye na tsiyaya zuciyarta na ɗaukar zafin da takasa samun ruwan yayyafa mata.

Gariyarsa ya cire ya rataye jikin racket ya tako  gabanta ta janye yayi murmushi yace “ki daina ja baya babu abinda zanyi miki kawai dai inason naga kin saki zuciyarki kin daina kukannan"
Batace masa komai ba ta mayar da idanunta ta lumshe tare da juya masa baya ta kifa kanta a bango taci gaba da jan ajiyar zuciya, a sanyaye ya iso bayanta ya jingina da jikinta tare da sanya hannu ya riƙe ƙugunta irin riƙon nan na tsauri ya ɗora kansa a kafaɗarta yaja wata wahalalliyar ajiyar zuciya ya kira sunanta cikin wata murya me rawa da ta sanya zuciyarta bugawa da ƙarfi.


Sake shigewa yayi jikinta yace “Bansan meye aibina ba Hauwa'u da kikemin kallon wani mutum daya kawo damuwa cikin rayuwarki wlh Hauwa'u alkhairi ne ya kawoni cikin rayuwarki ban shigeta da niyyar cutawa gareki ba Ki bani dama ki gani Hauwa'u zan baki kwanciyar hankalin da yaron da kikaƙi kallona dominsa bazai taɓa baki ba ki tsaya ki bani dama ki gani kinji!"
Ya ƙarshe mgnr da sigar rarrashi amma maimakon ma yaga tayi sanyi sai yaji ta sanya hannunta ta ɓamɓare nasa ta nufi ƙofa don fita yayi saurin janyota ya rungumeta ta gaba ya haɗa ƙirjinsa da nata abinda ya sanyashi saurin dire gwiwarsa a ƙasa kenan saboda wani spark da jijiyoyinsa suka bayar.
Jikinsa ya mutu murus hakan ya bata damar janyewa ta miƙe ta buɗe ƙofar ta fice batare da ya iya ce mata ƙala ba saima zamewa da yayi ya kwanta ya zubawa selling idanu cikin kasala da mutuwar jiki da kuma buƙatuwa da mahaɗin rayuwa"

Ya jima kwance kafin wayarsa ta ɗauki ruri yajs numfashinsa ya dire ya janyo wayar ganin me kiran yasashi ɗagawa da kasala yace “uwargida da damuwa ne?" Daga yanayin muryarsa ta fahimci akwai abinda ke damunsa tace.
“Eh hakane akwai damuwa His Exalency Amma kai meye taka damuwar kafin sanin tamu?" Gyara kwanciya yayi yace “karki damu nasan za'a samu mafita insha Allahu"
Sanin tunda ya coge to bazai furta bane yasata yin ƙwafa tace “Ai shikenan dama Khairiyya ce take buƙatar pampars da part da kuma dogayen riguna sannan muma munason muyi shop kayan kwalliyarmu sunyi ƙasa" batare da bawa abin wata mafaka ba yace ok kuje kuyi mana" cikin kwantar da murya tace “To Alh idan munje kuɗin fah?" Murmushi yayi yace “Hajiya kenan zan tura muku kuɗin kowacce ta account ɗin ta sai kuje kuyi Khairiyya kuma zan turo nata itama ta account ɗinki ina fatan hakan yayi?" Guɗa tayi tace “wannan shine daidai Mai girma gwamnan gobe"
Aje wayar yayi yana murmushi ya tashi ya watsa ruwa ya ɗauro alwala yasa doguwar riga ya fita domin zuwa Masallaci.


A ɗakin dasu Hajiya Inna suka sauka Hauwah ce kwance saman gado tanata rera kukanta da suka gaji da rarrashinta Nana tausayi ƙanwar Tata ke bata rabuwa da masoyin daka tsara rayuwarka danshi akwai ciwo ba duka raine yake iya jura ba barema ita da bata taɓa loosing a rayuwarta ba ta taso cikin gatan duk abinda ta nema bata akeyi arziƙin maraicinta sai gashi yau rana a tsaka lamura sun sauya Baffa ya zaɓi rabata da abunda ta rayu da ƙaunarsa tun ƙuruciya ya haɗata da wanda bata shirya rayuwa dashi ba tabbas kowa ma haka akeyi masa a gdan amma nata ya bambanta dana kowa domin da yawa bamasu da samarin idan ma akwai basuyi shaƙuwar da tayi da nata ba.
Itakuwa Hajiya Sahura damarta take dubawa Hauwa'u batason auren nan saboda haka zatayi amfani da damar wajen sake tura mata ƙiyayyar Auren a ranta ta yanda zata gunduri Alh Adnan ya gaji da tsiyarta ya sakota in yaso sai a haɗashi da Munirat ta ƙuduri niyyar bazata bari a haɗa auren Munirat da Kaseem ba domin baikai mata suruki ba.......


Taɓa ƙofar da akayi ne ya dawo da ita daga duniyar lissafin data lula ta kama ƙoƙarin takurawa kanta tayi fara'a tace “Saikuma Auta ta gudo Alh ai da zan dawo da ita sai naga fitarka yo banda wauta da sakarci ina ita ina sashin baƙi ki baro maigida ki taho cikin baƙin gda"
Da fara'a yace “Ah babu komai Hajiya aini nace ta dawo kinsan baƙunta sai a hankali zata saki jikinta   ina fatan dai kunci abinci?" Alhmdllh Alh munci abinci mun ƙoshi" jinjina kai yayi yace “Aishatu idan kin gama ki tambayeta abinda takeso nayima driver mgn zai kaiki ki siyo mata kuma saiku siyo abinda kukeso"

Gdy sukayi sanda yake ficewa Hauwah taja wani dogon tsaki abinda ya sabbaba masa tsayawa cik tare da juyowa suka haɗa idanu da Hajiya ya shafa sumarsa ya fice daga ɗakin"

Zuciyarsa na bugawa da ƙarfi yana furta “tsaki! Tsaki Hauwa'u!! Tsaki!!!"  Har yakai ɗakinsa ya zauna a bakin gado abinda yake maimaitawa kenan zuciyarsa na zafi a rayuwarsa bai jure tsaki ba musamman a gurin mace ya rabu da mace saboda tayi masa tsaki amma ita babu abinda ya isa yayi mata.


Hajiya Inna ce ta dubi Nana tace “Ke ki tashi kije ki samo mana rabonmu" miƙewa Nana tayi tace “Allah ya taimaki Exalency me kikeso a taho miki dashi?" Bata samu arziƙin kallon tsiya ba bare na arziƙi tayi murmushi tace “Hƙr zakiyi Hauwah komai yayi farko akwai ƙarshensa akwai ranar da zakiso Alh Adnan yanada abinda zaasoshi duk abinda akeso ya samu......"
Katseta Hajiya Inna tayi tace “Yafa samu zahiri sai rashin haihuwa ni wannan abu shine yake kashemin jiki da auren nan naki Hauwa'u"............


*OUM HAIRAN*
*_THDGOVB25_*

*_LAST FREE PAGE 25_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

Wani abu Hauwah taji ya caki zuciyarta ta ɗago da sauri tace “Rashin haihuwa Kuma Innah bashida yara dama?"
Taɓe baki Inna tayi tace “ina fah yake da yara ai ko ɓari ba'a taɓa yi masa a gdansa ba saidai ba kowane ya sani ba saboda ya lulluɓe abin da wata musakar yarinya daya ɗauko a gdan marayu tananan kowa kallonta yakeyi a zuwan tashi ce nan kuwa basusan rufe kura yayi da fatar akuya ba"
Taɓe baki tayi ta koma ta kwanta tace “ni meye ma damuwata da haihuwarsa" ba haka Hajiya Inna taso ba taso taga Hauwah ta tashi hankalinta sai taga saɓanin haka.
Murmushi tayi a ranta tace “daɗaɗɗen tsumi na me wayo ne yarinya a hankali zan aiwatar da nufina"

Hajiya Inna tayi amfani da wannan damar ta rinƙa yima Hauwah muguwar huɗuba abinka da me jiran kaɗan ta kuwa ɗauka har Hajiya Inna nace mata “Wlh duk yanda zakiyi kiyi kada ki bari ya Kwanta dake indai haka ta faru to koda na taimaka miki kin rabu dashi bazaki haihu ba domin kuwa shi duk matar daya kwanta da ita ko tabar hannunsa bata haihuwa"


Sake tashi tayi zaune tace “Ni nasan ma babu abinda zaiyi min Inna don Allah kada ki bari na daɗe da wannan mutumin Allah idan na gansa zuciyata bugawa takeyi ji nakeyi zanma iya kasheshi" dafa kanta tayi tace “in kinga aikin nan yayi wahala to kece kikaso yayi sai abu na gaba....."
Kama kunnenta tayi ta raɗa mata ta rufe idanunta sukayi dariya tare daidai lkcn da Nana ta shigo da kaya niƙi² a hannunta ta ajiye tana binsu da kallon tuhuma Inna tayi kicin² da fuska tace “Ganta sarai meye kika siyo mana" zama Nana tayi tace “Wato Inna yau nayi kallo iya kallo na bawa idanuna abinci Ni Hauwah da Baffa zai bari da zamana zanyi harsai lkcn namu bikin na koma"
Komawa tayi ta kwanta tace idan kin gama surutun ki kashe mana glub nikam banida lkcn ɓatawa wajen nazarin gajeren lokaci"
Da sauri Nana tace “Anan kuma Hauwah ki tashi ki tafi ɗakinki mijinki yanacan yana jiranki yama ce idan na shigo nayi miki mgn" ta ɗago zatayi mgn Hajiya Inna tace.

“Ba musu tashi kije kawai dai ki kula saboda tsaron kai da kaya" badon ranta yaso ba taso ma ta coge Inna tace “cikin sharaɗi na ns faɗa miki babu gardama in har zakiyimin gardama to zan fasa taimaka miki kuwa"
Don tanason taimakon ta tashi ta sanya hijjab ɗinta ta nufi sashin gdan ta sanya hannunta gabanta na bugawa da ƙarfi ta buɗe ƙofar falon ta shiga taja ta tsaya da wani irin luguden zuciya saboda ganinsa tsaye saƙale da waya a kunnensa yana amsawa.


Kafeta yayi da rikitattun idanunsa masu sagar da jijiyar jiki ya jingina jikin bangon dake kusa dashi yana ƙara kafeta da Lulu eyes ɗinsa tayi saurin ƙasa da kanta saboda faɗuwar gaban nata gaba take ƙarawa ga wani feshin raɗaɗin wutar tsanarsa da takeji a ƙasan ruhinta.
Da wannan ta lallaɓa ta nufi ɗakin daya shigar da ita ɗazun har zuwa lkcn da yaji ta rufo ɗakin bai daina bin hanyar da tabi da kallo ba yana haɗiyar yawu me ɗaci saboda wani abu dake azalzalarsa game gareta.

Zama yayi ya aro juriya tasawa kansa yaci gaba da wayarsa koda ya gama kwanciya yayi a gurin yana saƙawa da warwarewa abubuwa masu yawa suna susar zuciyarsa yanata ƙoƙarin dannesu bai tashi daga gurin ba sai 10:30pm ya  nufi ɗakinsa saboda baison shiga rayuwar wanda bai shirya shiga tasa ba ya sake watsa ruwa ya dauki wata riga airmles bayan ya shafe jikinsa da mai me ƙamshi ya ɗauro alwala ya tada sallar nafila bayan ya kaita ya ɗauki tsawon lokaci yana karanta Littafin addu'o'i sannan yayi addu'o'insa ya miƙe ya nufi gadon ya kaɗeshi sau uku kamar yanda ma'aiki (S.A.W)  ya umarcemu ya kashe hasken ya kwanta yana me karanto ayatul kursiyyu ya tofa gabas da yamma Kudu da Arewa sannan ya ƙarashe neman tsarinsa yaja duvet ya rufe jikinsa yana me lumshe idanunsa tare da rungume pillow a ƙirjinsa yaja numfashi ransa yana kwaɗaituwa da son kasancewa da iyalinsa.


Saidai yasan ko giyar wake yasha bazai tunkari Hauwah a yau ba yasan tana kan tsinin da bazata saurareshi ba bare kuma gashi tana masa kallon wani annoba kuma masifa cikin rayuwarta.
Miƙa yayi tare da sake ƙanƙame pillow ya sake rintse idanunsa yanason yin bacci baccin ya gagareshi sai miƙa kawai da yakeyi wannan dare bacci ɓarawo ya samu damar saceshi ne biyu da rabi na dare........


Hauwah kam tunda ta shiga ɗakin ta buɗe kayanta ta ɗauki wata sabuwar rigar bacci mara nauyi tasa taje ta ɗauro alwala ta dawo ta kwanta zuciyarta fal tunanin abin begenta da tunanin hanyar da zatabi tajisa murmushi tayi lkcn da dabara ta faɗo mata ta gyara kwanciyarta ta ɗan samu sauƙin abinda takeji na kewa domin tasan mafita zatayi mata sauƙi tunda ga Hajiya Inna nan.
Juyi tayita yi a gadon ta saba su raba dare suna waya da masoyinta yau gata kwance gdan wani wai matsayin miji matsayin da Nabeel kawai ta shirya bawa shi a duniyarta, babbar damuwarta a wannan dare rashin sanin halin da yake ciki shin ƴan sandan sun sakeshi ko yana hannunsu?


Shuuu bacci ɓarawo ya saceta na ƴan awanni sama² taji ana taɓa ƙofa ta buɗe idanunta tana salati tace “Oh Nana bacci bai isheni ba wlh...." Maƙalewa mgnr tayi a maƙogaronta ganin wanda ke tsaye jikin ƙofar hannunsac harɗe a ƙirjinsa ya tako ya shigo tare da jingina da jikin ƙofar ya kafeta da ido na ɗan wani lkc abinda yasata bin jikinta da kallo yaja Numfashi tare da shafa kansa yar yaloluwar rigar baccin jikinta me bayyana sura tayi bala'in bata kunya, tayi saurin juyawa domin ɗaukar hijjab ɗinta ya lumshe idanunsa zuciyarsa nabada wani sauti fat² ba tare daya shirya juyawa ba ya juya da sauri yana haɗa kalma daƙyar yace “kiyi alwala kiyi sallah"

Jin ya fita yasata sauke ajiyar zuciya don matuƙa taji masifar kunya daya isheta a wannan yanayin bata taɓa tunanin zuwansa ba don tasan baffansu baya shiga gurinsu da asuba saidai yasa su Yakumbo su tashesu  to yau ɗinma ta manta cewa ba'a gda take ba tunaninta Nana ce ko Yakumbo saboda dukkan mafarkinta na yau dasu tayishi.
Juyawa tayi ta koma ta mayar da ƙofar ta rufe ta shiga bathroom tayi alwala tazo ta shimfiɗa sallaya tayi sallarta ta zauna azkhar bayan ta ida ta miƙe ta koma gado ta naɗe abinta bacci ya kuma ɗauketa.
Cikin baccin taji ana shafa fuskarta takai hannu ta riƙe hannun tace “kin takuramin Aunty Nana ki barni na gaji nace miki na gaji....."


Sunkuyawa yayi daidai kanta ya ranƙwafo ya tallafo kanta ya ɗora bakinsa saman nata wani ɗumi me sagar da gaɓa da tsinka lakar jiki ya ratsata wanda ya haddasa mata wata mummunar faɗuwar gaba ta buɗe manyan idanunta da mayen bacci yasasu ƙanƙancewa karaf suka faɗa cikin na ADN Sooraj daya kafeta da nasa masu fitinannen fusgar yanayi a tare suka lumshe idanuwansu shi salon saƙon ƙiyayyar da yake karanta cikin ƙwayar idanunta da kuma wani yanayi na tsananin neman agaji da yake jinsa a ciki sune suka haddasa masa lumshe idanunsa inda itakuma tsabar firgici tsoro da tashin hankali sune suka sanyata rintse nata.
Ta samu damar daga hannunta tanason tattara ƙarfinta ta tureshi, gane nufinta da yayine yasashi sanya tafin hannunsa cikin nata ya sake shigewa jikinta tare da haurawa gadon har yanzun harshensa yana cikin bakinta yana tsotsar harshenta yanajin wani yanayi me fitar da mazan gaske cikin hayyaci yana ratsashi.


Musamman lkcn daya ɗora ƙirjinsa saman nata manyan boobs ɗin ta masu zubin kyau da ɗaukar hankali suka gogi sumar ƙirjinsa yakai hannunsa cikin wani irin sauri saboda ƙoƙarin janyewar da takeyi ya kama ginshikin Boobs ɗin nata ya saita nipples ɗinta da nasa ya haɗesu batare da ya cirenta rigar jikinta ba, shi dama dake babu rigar a jikinsa hakan ya basu damar sauke ajiyar zuciya a tare yaci gaba da goga nipples ɗinsa jikin nata yanajin wani irin shauƙi na dole na fuzgarsa batare daya shirya ba ya cire bakinsa daga nata ya saki ginshikin nononta ya kama nipples din da salon ƙwarewa ya murza tare da sanya tafin hannunsa ya lailaya shi ta kuwa saki ajiyar zuciya gami da kuka a tare lkcn daya janye rigar ya ɗora harshensa saman nipples ɗinta yana lasa tayi saurin sanya hannuta ta rungumeshi tare da maƙalƙaleshi ta buɗe baki cikin kukanta na sangarta da shagwaɓa tace “Nashiga uku Exalency zaka kasheni wayyoh zaka ciremin nono shikenan na mutu wayyoh Inna wayyoh Nana na mutu na lalace daman ashe ɗan iskane Baffa ya haɗani dashi shikenan zai ciremin nono wayyoh wayyoh Allah....."

Please wannan shine ƙarshen free page in kinga wani kin karanta na haramun ne Wlh billahil'azeem bazan yafe haƙƙina ba yake ƴar uwata me albarka kiyi hƙr ki rintse idnunki daga haramu kiji daɗi daga halal babu tsada book ɗin nan kuma zaki ƙaru fiye da ƙaruwa zaki samu nishaɗi THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE littafine ɗaya tamkar da dubu wanda alƙalamina ya daɗe bai rubuta kamarsa ba THE DEPUTY GOVERNOR'S BRIDE nrml group 200 VIP 500 SP 800 Amma iya wannan watan idan muka shiga February zai koma farashinsa na asali normal group 300 VIP 600 Sp 1k.
Ku hanzarta ku ɗebi garabasa kafin ta ƙare Oum Hairan ke muku fatan alkhairi.

[1/24, 7:50 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB26-27_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

Da azama ADN yasa hannunsa ya rufewa Hauwah baki saboda fahimtar tsaf zata tara masa mutane a ɗakin wanda shi kuma yasani bazai iya bari ba duk da cewar bai shiryawa kusantarta a yanzu ba ya ƙuduri niyyar bazai shiga jikinta ba harsai ranar daya tabbatar data saki jikinta gareshi ta shirya karɓar kowanne yanayi daga gareshi.
Numfashin da yaji tana fusgowa da ƙarfi shine ya sanyashi janye hannunsa daga bakinta ya kwanta sosai a jikinta yana shafata tare da tura yatsunsa cikin sumarta yace “So...Sorry My Bride...." Ruƙunƙumeta yayi yana sakin wata ajiyar zuciya me ƙarfi tare da gwaggwama numfashi.
Da ƙyar ta samu ya saketa ya koma gefe ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya.
Hakan ya bata damar dirowa daga gadon ta zari hijjab ɗinta ta nufi ƙofa a guje jikinta yana rawa, duk da yanayin mutuwar jikin da yake ciki hakan bai hanashi tashi da sauri ya tarota ba.

Hijjab ɗin ya samu nasarar cafka tayi baya ya sanya ƙirjinsa ya kareta taja ajiyar zuciya tare da fara ƙoƙarin fita daga jikinsa ya sakaleta da hannunsa ya sunkuyo da kansa ya ɗora saman nata yace “Idan kin fita a ɗakinki ina zaki?"
Idanunta ta ɗago da suka ciko da ƙwalla razani sun cikashi jikinta sai rawa yakeyi so take tayi masa rashin kunya amma bakinta ya sarƙe ta kasa furta masa kalma ɗaya mara daɗi dole tasata ɗaga hannunta domin share hawayenta taji ɗumi a kuncin nata ta lumshe idanun zuciyarta na bugawa da ƙarfi ta shige jikinsa kawai saita rushe da kuka.
Wannan yanayi ya firgitashi ya sanya hannunsa ya rungumeta tare da ɗora tafin hannunsa saman Bombom ɗinta ta lumshe idanunta tsigar jikinta na tashi ta tsinkayo muryarsa yana cewa.
“Banason kuka Hauwa'u kiyi hƙr komai nisan dare gari zai waye kiyi hƙr ubangiji yasan manufa shiyasa ya hukunta wannan auren Hauwah bazakiyi nadama da kasancewarki tare dani ba...."
Janyewa tayi a jikinsa tace “Nasani nidai Ka taimakeni Excellency ka barni na rayu da rayuwata inasonsa fiye da son da nakewa kaina wlh bantaɓa ƙaunar kaina samansa ba zuciyata ta rayu ne da soyyyarsa idan nace zan haɗashi dakai zan cutu domin babu mukullin ikon hakan a gurina"


Shiru ce ta shiga tsakani bayan idar da furucin nata ya kafeta da idanunsa yanajin kamar yayi mata abinda ta durƙusa gabansa take roƙonsa saidai yasan ko babu Baffa tsakani bazai iya sakin Hauwa'u ba yanajinta kamar rayuwarsa bayajin akwai wani dalili da zaisa ya tsinke alaƙa tsakaninsa da ita.
Jin yanda kukan nata ke ratsashi yana neman kashe masa jiki da karya masa zuciya yasashi juyawa ya fice daga ɗakin yaja mata ƙofar ganin ya fice ne yasata tashi ta koma kan gadon tayita kukanta me tsuma zuciya gashi babu me rarrashi ta jima a gurin sannan taji ana taɓa ƙofarta ta tashi da sauri ta goge idanunta ta nufi ƙofar ta buɗe tare da matsawa suka shigo Hajiya Inna tabi ɗakin da kallo taja ajiyar zuciya me ciwo ta juyo ta zubawa Hauwah idanu ganin yanda idanunta suka kumbura sukayi ja yasata jin faɗuwar gaba ta isa gareta tace.

“Wani abu ya faru ne Auta?" Da rashin fahimta tace “Ni...Ni kuma Inna kamar me kenan?" Kallon Nana Inna tayi kallon daya sanya Nana ficewa daga ɗakin Hajiya Inna ta ƙara ware injin idanunta akan Hauwah tace “gwari² ina nufin wannan tsohon najadun kin bari ya raɓeki ne?" Sunkuyar dakai tayi ƙasa ɗabi'arta ce bata ƙarya shiyasa a gdansu ake ce mata wautacciya, hakan ya tabbatarwa da Inna abinda take gudun ya faru ya faru tace.
“Ya Salam Hauwah kin bashi ko kin bari ya shigeki ko shikenan kin rusa man shiri yanzu shikenan kin cuceni...." Tana mgnr tana matsar Hauwa tasan idan ta bari Inna ta cafketa bazataji da daɗi ba hakan yasata cikin kuka da kiɗima tace “Wlh tallahi na rantse da Allah bai ciremin pant ɗina ba rigata kawai ya ɗaga yasha nono na....."


Zuba mata mari tayi ta saki ƙara daidai lokacin da Hajiya Inna tayo kanta tace “Nononki Hauwah kika bari daga zuwanki har ya fara sha miki nono kuma kika bari eh lallai dole ba banzaba ki nacewa Nabeel ashe duk wani salo na iskanci kinsanshi kin iyashi yo meye yayi saura Hauwah daga shan nono ai sai cin tsuliya daga haka kuma saime to wlh ki san da saninki bazan taɓa taimaka miki ba muddin kika bari wani abu ya shiga tsakaninki da wannan mutumin saidai ki mutu da baƙin cikin......"
Buɗe ƙofar da yayi ne yasa Inna sauya akalar maganarta da cewa kiyi biyayya ki rayu cikin aminci banason sakarcin banza"


Juyowa tayi tace “Saidai fah hƙr lamarin yarinyar nan Allah ya taimakeka kayita hƙr a hankali zatayi hankali" zubawa Hauwah idanu yayi daga shigowarsa yasan canza akalar maganar akayi ba abinda take faɗa ta faɗa masa ba amma dake shima cikakken ɗan duniya ne sai ya shafa kansa yace.
“Wannan ba wani abun damuwa bane Hajiya Hauwah ai yarinya ce dama nasani kinga kuwa duk wanda ya shirya zama da yaro dole ya tanadi kayan wasa, ina gdy da kulawa Allah ya bar ƙauna ina fatan kun gama shiryawa saina kaiku airport ɗin da kaina"

Hararar Hauwah tayi tace “Mun gama me zamu jira ranka ya daɗe ai mu ƴan aikene kuma mun isar da saƙo" murmushi yayi har yanzu idanunsa nakan Hauwa'u ya taka ya matsa gabanta yakai hannu ya ɗago kanta da tunda ya shigo yake a ƙasa yaga hawaye nabin kuncinta yayi saurin cewa.
“Ya Salam meye kuma ya taɓa min amaryata har take zubar da wannan hawayen me daraja?" Zame fuskarta tayi a hannunsa tana kallon Hajiya Inna ta kanne mata idanu hakan yasa Hauwah jan ajiyar zuciya tace “Ba....bana....so su tafi su barni Ni kaɗai tsoro nakeji"


Murmushi yayi ya dafa kanta yace “shikenan shirya muje mu rakasu sai mu dawo" sake kallon Hajiya Inna tayi ta jinjina mata kai hakan yasata miƙewa ta nufi wardrobe ta buɗe ta ɗauki kayanta ta nufi bathroom tasa ta fito Inna ta fice saura shi ɗaya yana ganinta ya saki numfashi yace “Barakallah My Bride kinyimin kyaun gani"
Batace masa komai ba ya kama hannunta suka fito a babban parlourn suka ishe Su Hajiya Inna masu hidimar gidan suka ɗauki akwatunan da yasa aka hado musu tsaraba niƙi² suka fita zuwa rumfar aje motocin duk yanda Hauwah da Inna sukaso su shiga mota ɗaya ya hana dole sai daban² suka tafi kowa da abinda yake saƙawa a ransa har sukaje airport yaƙi basu damar sake keɓancewa Nana taji daɗin hakan don tun zowarsu ta fahimci Inna koyawa Hauwah saƙa a mugun zare takeyi, Inna taso ƙeɓewa da Hauwa amma babu dama dole badon ranta yaso ba ta shiga jirgi tana ƙwafa suka lula zuwa birnin dabo.

Tashinsu yayi daidai da lafewar Hauwah a jikin ADN Sooraj ta saki wani marayan kuka na tausayin kai tana narkewa a jikinsa hakan yasashi sanya hannu ya tallafo kanta ya zuba idanunsa a kan kyakkyawar fuskarta ya ɗora bakinsa a goshinta yanajin saukar sautin kukan nata a ƙahon zuciyarsa ya lumshe idanunsa tare da janye jikinsa daga nata yaja hannunta suka nufi mota ya buɗe mata ta shiga tanabinsa da wani kallo dake nuna tsantsar tuhuma.
Saida ya zauna sannan yace “muma jibi zamu bar ƙasar...." Da sauri ta ɗago tana shirin mgn yace “Umarah zamuje muyi bazamu dawo ba sai bayan sallah tunda lkc ya ƙure a can zamuyi azumi"

Kawar da kanta tayi ƙirjinta kamar ya fashe zuciyarta ta fito ga kukan zuci gana fili bata zataba taji hannunsa a weast ɗinta ta rintse idonta tasa hannunta ta ture masa hannunsa cikin hasala tace “banason Iskanci karka ƙara taɓani...." Saboda dukan da kalmar iskancin tayi masa baisan sanda ya take burki ba suka tsaya wani ƙiyy! Kakeji “Iskanci?" Ya faɗa yana waiwayowa ta dubesa da sauri tace “Na shiga uku kayi hƙr don Allah bansan sanda kalmar ta ƙwacemin ba"
Iska ya fitar daga bakinsa yace “Ok karki ƙara banson wannan kalmar Hauwah ke ba jahila bace kada ƙiyayya ta rufe miki ido ki rinƙa ƙoƙarin mayar da halal Haram Ni mijinki ne komai ƙi inada haƙƙi akanki kamar yanda kike dashi a kaina bazan karɓeshi ta ƙarfi ba a hankali nakeson karɓarshi ina fatan zaki bani haɗin kai Hauwah ni ba ragon namiji bane idan kin bani dama zan nuna miki Ni jarumi ne tabbas da yawan ƴammata ana cutar dasu idan aka haɗasu da dattijai masu nauyin shekaruna Amma fah ke kisani Indai ta fanni kwanciyar aure ne to ɗan shekara talatin ma bazai faɗamin jin iko ba Hauwah ki bini a hankali na biki a hankali bana fatan kiyimin abinda zanyi miki dole cikin rayuwarki"
Taɓe baki tayi tare dayin ƴar ƙaramar ƙwafa ta zubawa titi idanu ranta na faɗa mata ta zazzageshi mana ko yayi zuciya ya saketa in yaso ko da ƙafa taje Kano ai garin masoyi baya nisa bare daga Lagos zuwa Kano.........
[1/25, 9:32 AM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB28-29_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

Ganin yanda take yatsina masa fuska yasashi jan motarsa sukayi gaba suka nufi wata hanya me ƙarancin mutane suna tafe ne Ƙira'ar Shaikh Mishary na tashi a motar ta kifa kanta a jikin kujerar ta rinƙa bin suratul Nahl cikin sanyin muryarta ta ɗabi'a, hakan ya bata damar tattara ADN tabawa banza ajiyarsa to shima jin ba aikin banza takeyi ba yasa bai wani sa damuwa a ransa ba yaci gaba da Driving ɗinsa har Suka isa inda yayi nufin kawosu yayi parking ya  kwantar da kansa shima jikin kujerar motar yace
“Me zakici?"
Dakatawa tayi da karatun ta dubeshi babu alamun ɗaukar raini hakan yasata kamewa yanayi mata kwarjini ta kuma tsinkayo muryarsa yana cewa “Me kikeso kici a kawo miki?" Da kasalar yanayi ta buɗe bakinta da ta lura Indai zatayi mgn dashi sai taji yayi mata nauyi kwarjininsa ne ko kuma girmansa ne oho.

"Babu komi" abinda ta furta kenan da yanayi me nuna gajiyawa hakan ya bashi damar ɗago kansa ya zuba idanunsa akanta ya buɗe baki zaiyi mgn sai kuma ya fasa ya zari waya yayi yan latse²nsa ya ajiye.
Cikin abinda bai wucce few minutes ba sai ga wani matashi ya fito ta cikin ginin da suke fuskanta ya ƙara so jikin motar ADN ya buɗe masa but ya zuba kayan daya taho dasu suka ɗagawa juna hannu ya koma shikuma yaja motar suka tafi kai tsaye gda suka koma yanayin parking baikai ga gama tsayawa ba ta buɗe motar ta fita ta nufi hanyar da zata kaita cikin gdan yabita da kallo yana murmushin da shi kaɗai yasan ma'anarsa ya buɗe motar ya fito Hadimansa suka nufoshi ya bawa Jibril remote na motar yana tafiya yana cewa ka shigo ma da Hajiya kayan sashinta duk wanda yazo ace bananan"


Da girmamawa Jibril yace “angama Excellency" yana shiga parlourn yaji ta rufo ƙofar batare da wata damuwa ba ya shiga nasa ɗakin ya ɗauki wasu takardu ya baje a tsakar ɗakin ya zauna yana dubawa yana murmushi.
Ita kuwa tana shiga kwanciya tayi tana aje numfashi tare dasa hannunta biyu ta dafe kanta zuciyarta na kai kawo cunkushe da tunanin halin da Nabeel yake ciki tana matuƙar buƙatar jin muryarsa batada damar hakan, tunawa da batada damar jin Muryar masoyin nata duk wata ƙofar ƴanci Baffa ya kulle mata ya karɓe wayarta yasa wasu hawaye masu ɗumi suka tsiyayo mata tace “Zan nemi mafita"


Ji tayi alamun an shigo parlourn ta miƙe ta buɗe ƙofar ta fita ganin Jibril yasata ɗan sakin fuskarta ya rusuna yace “barka ƙaramar Hajiya Excellency ne yace a shigo maki da wannan duk girmanki ne" murmushi tayi tasa hannu ta karɓa tace “ina gdy Jibril ina Yallaɓan kallon hanyar sashinsa yayi yace “ai yana sashinsa kinada mgn ne?" Girgiza kai tayi tace “So nake na aikeka kuma kada ka kuskura Excellency ya sani idan ka bari ya sani" jinjina kai yayi yace.
“Wlh ki ɗaukeni ɗan amanarki Hajiya mu haƙa mu binne babu maiji sai Allah" daɗin kalaminsa taji ta zaro kuɗi yan dubu dubu raffers ta miƙa masa tace “kaje ka siyomin waya ka siyomin layi ayi register sa da sunanka" dariya yayi yace “angama Hajiya me dsngwale dangwale?" Kada masa kai tayi tace “eh ita ka siyomin ka riƙe canjin" tsalle yayi yace “wlh Hajiya daga yau na zama ɗan ki kin zama babata amma Hajiya akwai abinda nakeson sanar dake kiyi takatsantsan dashi koda yake bari na dawo dole mu baki tsaro"


Murmushi tayi tace “shikenan kaje tayi mgnr batare data bawa shirmensa muhimmanci ba dan ta lura Jibril irin mutanen nan ne ƴan bankwa akwaishi da abin dariya"
Juyawa tayi ta zata shige ciki daidai lkcn da Alh Adnan yake isowa bakin ƙofar saida gabanta ya faɗi ta raɓeshi zata wucce yace “ina kika aikeshi yana mgnr yana zuba idanunsa akan Jibril da yayi ƙasa da kansa" Jibril cikin sanyin munafurci yace “Allah ya taimakeka yalo da agwaluma tace naje kan gada na siyo mata su takeson ci"


Dariya abin ya bawa ADN Sooraj ya kamota ya haɗata da jikinsa yace “My Bride kodai mun samu ƙaruwa ne....?" Da sauri ta dubeshi idanunta suka faɗa cikin nasa ya ɗaga mata gira tare dayo ƙasa da kansa ya ɗago nata ya ɗora harshensa a lips ɗin ta ya lumshe idanunsa yana lasar lips ɗin nata yana ƙara shigar da ita jikinsa tare da zagaye ƙugunta da hannunsa ya ɗorasu saman tudun mazaunanta ya matsa a hankali yaja wata ajiyar zuciya me ƙarfi tare da janye bakinsa daga bakin nata yace “kar....karɓa zanyi Hauwah wlh zanyi farin ciki idan da zaacemin kinada ciki Hauwah babu abinda nake buƙata a duniyar nan daya wucce haihuwa don Allah ki tayani da addu'a idan nayi ban ruwa a wannan gonar irin ya nutse ya bani tsiro me kyau ya fito mu raineshi ko iya shi kaɗai ne zanyi alfahari da hakan Hauwah inason wanda zai tuna dani yayi kuka yayimin addu'a lkcn da bana raye Hauwah ki bani dama ina buƙatar sha daga gareki wlh ina cikin yanayi....."


Ya faɗa yana ɗora hannunsa a saman mararta ya zubawa lumsassun idanunta da suke ɗigar da hawaye idanu yana tura hannunsa cikin zaninta tayi saurin janyewa a firgice ta buɗe idanunta a kansa jikinta na karkarwa ta buɗe baki zatayi mgn yayi saurin girgiza mata kai ya kuma janyota ya rungumeta sosai shima nasa jikin yana rawa yace “babu dole Hauwah zanci gaba da shan magani har zuwa lkcn da zaki aminta dani babu wani abu bayan daɗi rayuwar auratayya tanada daɗi zan kashe miki ƙishirwa kema zaki kashemin zanci dake na shayar dake sannan na baki vitamin water daga jikina kema nasan zaki bani ko?"


Girgiza kai tayi da sauri tace “Aa Ni a'a tsoro nakeji Ni bazan iya ba...."
Rufe mata baki yayi yace “shikenan could down na hƙr my Bride muje ki tayani aiki" ajiyar zuciya tayi tabisa da kallo ya kada mata kai yace “Yeah inason ki tayani aiki...." Bai rufe bakinsa ba ya sunkuceta ya nufi sashinsa da ita tanason ta gardame ta kasa kawai saita kwantar dakai a jikinsa tasa kuka ya zubawa fuskarta ido yana murmushi har suka shiga bata buɗe idanunta ba saida tajita a wata duniyar laushi me tada tsigar jiki da fitar da hayyaci.
Hakan yasata saurin buɗe idanunta daidai lkcn da duhu ya mamaye ɗakin wai ashe remote ne da labulayen yana dannawa duk suka rufe ko ina yayi duɗum, bata iya ganin ko tafin hannunta.
Wani firgici ya shigeta cikin Muryar tashin hankali tace “Wayyoh Excellency na shiga ukuna lalace ka kunna banason duhu wasu abubuwa nake gani wayyoh sun taho ADN zasu kasheni da wuƙaƙe a hannunsu Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un lahaula wala ƙuwwata illah billah....." Da sauri yakai hannunsa ya kunna hasken cikin razani daidai lkcn da ta miƙe ta kuwa yanke jiki ta faɗi ya nufeta da sauri yana faɗin “Ya Subhanallahi Hauwah! Hauwa'u meye ya sameki?" Ya rinƙa jijjigata taƙi tashi hakan ba ƙaramin tayar masa da hankali yayi ba take ya shiga ruɗun da bai taɓa shiga ba shi yanzu meye hakan yake nufi me  ya janyo hakan?" Waye zai kira ya faɗa masa?"


Wayarsa ya ɗauka ya kara a kunnensa Baffa ya ɗaga tare da cewa “Sun motsa kenan ka kayi salatin Annabi guda ɗari ba ɗaya a hucin numfashinka akeso yake shiga ciki idan ka ida saika guntsi ruwan a bakinka ka fesa mata kafin hakan ka tabbatar ka rufe ko ina idan ka fesa matan zata zabura ta miƙe ka mayar da ita ka kwantar sauka karanta mata Fil da ayatul kursiyyu sannan ka karanta mata suratul Junnu sai suratul Baƙara insha Allahu zata dawo hayyaci, abu na gaba kafin ka kashe muku haske ka rinƙa bismillah saboda matar taka ba lafiyayya bace Indai aka kashe haske kuma guri da duhu yanzun zata firgita"
Jinjina kai yayi yayi gdy cike da mamakin yanda akayi Baffa yasan abinda ya faru ya fara yin abinda ya sashi aikuwa yana yarfa mata ruwan yaga ta wani miƙe a sukwane tare da sakin ƙara yayi maza ya mayar da ita ta kwanta yaci gaba dayi mata karatun a kunnenta tanata shure²nta da buge² dake shiɗin ƙaƙƙarfa ne bata iya tureshi ba saidai sunji jiki  ga A.C ga komai amma gumi suke ketawa ya daɗe yanayi mata karatun sannan yaga tayi miƙa tare da salatin Annabi, ta buɗe idanunta akansa ta lumshe ta janyo jikinta ta dawo saman jikinsa dake a kwance yake yayi rigingine.


Hannu yasa ya maƙaleta yana sauke ajiyar zuciya ya ɗora bakinsa a saitin kunnenta yace “Sannu My Jiddarh" lumshe idanunta tayi ta ɗora hannunta a saman sumarsa kwantacciya luf² ta Fulani me santsi da sheƙi tace “My Nabeel in....inason...."
Rufe mata baki yayi da bakinsa ya lumshe idanunsa zuciyarsa na bugawa da ƙarfi jikinsa ya ɗauki rawa kishin ƴan maza ya motsa baisan sanda ya birkitata ta koma ƙasansa ya sake kama bakinta yaci gaba da tsotsa yana jan numfashi iyakar sonta data ceci kanta ta kasa saida ya gama tsotse mata bakin tas sannan ya janye ya zubawa fuskarta idanu tare dasa hannu yana shafawa ya buɗe bakinsa yace “karki ƙara zan saɓa miki alƙawari"..........
[1/25, 7:59 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB30-31_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

__________________________________________________________

Lumshe idanunta tayi ta mirgine a jikinsa ta koma gefe ta kwanta tare da juya masa baya ya ɗora hannunsa a ƙugunta ya zagayo dashi cikinta ta sauke ajiyar zuciya shima ya sauke tare da matsawa ya haɗe ta da ƙirjinsa yanajin wani sanyi da nutsuwa suna shigarsa ya lumshe idanunsa ya jingina kansa da bayanta yana sauke wani wahalallen numfashi tare da kiran sunanta can ƙasa wanda ko itan da ya kirayi sunanta can ƙasa taji saukar Muryar tasa yana saukar mata da kasala ta hanyar sauke mata numfashinsa a bayanta wanda hakan yasa duk wata gaɓa ta jikinta ɗaukar charge me canza yanayi jikinta ya ɗauki rawa ta sakeyin kasaƙe tanajin yanda yake yawo da hannunsa a ƙasan mararta yana wasa da cibiyarta cikin salonsa me mantar da zuciya komai.
Wani masifa dake ziyartarta hakanan takejin wani matsanancin yanayi game dashi zuciyarta na narkewa gaɓoɓinta na macewa batare data shiryawa Hakan ba taji hannunsa cikin bra ɗinta ta motsa saboda rashin tsammani hakan ya bashi damar sake tura ɗaya hannunsa ƙarƙashin ta ya matseta sosai jikinsa da bakinsa na rawa yace


“Pl... Please help me My Bride am feeling you...." Yanda yayi mgnr a karkatse yasata jin wata muguwar faɗuwar gaba tare da tsoro amma ta kasa ko motsawa a jikinsa sai ɓarin jikin daya ziyarceta so take tayi masa musu ta kasa gashi kalaman Hajiya Inna sunayi mata tariya a kunne kamar yanzu take furtawa.
Wannan yasata saurin janyewa yayi amfani da damar ya birkitota ta faɗa samansa ya lumshe idanunsa saboda yanda yaji ta danne masa Penis sai yaji kamar ta ƙara masa ruwan masifar dake addabarsa ya maƙaleta da sauri cikin narkakkiyar muryarsa me bayyana asalin halin da yake ciki yace.
“Kiji tsoron Allah kada ki bar mijinki ya cutu Hauwa'u kinada maganin matsalata wlh kika barni a wannan yanayin sai nayi jinya Please Hauwah ko bazaki bani duba ki taimakeni naji sauki da sauƙin ki Hauwah sanin da nayi miki ke me tausayi ce kinada imanin da bazaki barni na cutu ba zanbiki ta yanda kema zakiji daɗi....."


Daɗi? Ta maimata a ranta “to wanne daɗine yasa taji da yawan mata suna cewa wahala daren farko wahala farkon fara sanin budurwa da namiji?"
Zuciyarta ce ta fara hasaso mata shima fah Nabeel Kullum cewa yake zai jiyar da ita daɗin da bata taɓa ji ba a daren farkonsu tuni kanta yayi mata nauyi ta fara ƙaryata maganganun da takeji na cewa kusancin farko akwai wahala ta barshi a daɗin ta kwaɗaitawa kanta itama yau dai gata ta samu freedom daga ita sai Alh Adnan kuma ta fahimci da gaske yakeyi daɗin zai jiyar da ita.
Ƙara ƙarfafawa kanta gwiwa tayi da cewa “to banda ma an rainawa yara hankali babu daɗin kowa yakeson auren itakam tunda ta samu wannan batin saita ɗana domin ance duk wanda yaga bati ya ƙyale ya tabbata jahili.


Batakai da gama tunanin ba taji yana zare mata rigar jikinta ta rintse idanunta da mugun faɗuwar gaba bata ankara da aikin ADN Sooraj ba saida taji ya ɗagata cak ya azata a gadon yayi bismilla ya kashe glub ɗin lkcn duhun Magrib ya shiga ɗakin yayi duhu so saboda ya firgita ɗazu baibar ɗakin a duhu ba saida ya kunna ƙaramin haske sannan ya zare rigar jikinsa daidai lokacin data buɗe idanunta ta saukesu saman faffaɗan ƙirjinsa me cike da gargasa ta lumshe lkcn daya iso ya sunkuyo ya ɗora bakinsa a goshinta yayi kissing nata ya kwanta a gefenta  yace “kin bani dama?" Rufe idonta tayi yabi eyes lasher's nata da kallo yayi kissing idanun nata ya sanya hannu ya ɓalle bra ɗinta ya zareta sannan ya kama big Boobs ɗin ta masu taushin auduga yaja wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya yace “oh Allah na My bride....."


Zafin da tajine yasata ɗora hannunta kan nasa cikin firgici tace “wayyoh Allah ɗazuma da safe haka kasa nonona yayita zafi don Allah nidai ban hanaka ba saboda inason tantance ɗanɗanon amma kayi a hankali....."
Ruf ya rufe mata baki da nasa ya fara shan bakinta da wani salo na fitar hayyaci saida yasha me isarsa har tana wani tallafo kansa shikuwa ya sakar mata jiki tana shafa bayansa yanajin wani daɗi me haukatar da mutum yana fuzgarsa a haka ya gangara ya sanya bakinsa saman nipples ɗin ta ya buɗe idanunsa tar da suka ƙanƙance kuma suka kaɗa saboda jaraba akanta ganin sun haɗa idanu yasata rufe nata hakan ya bashi damar fara shan nonon nata aikuwa baisan sanda ya saki ba saboda ƙarar data saki tana kiran “Ahhhh wayyoh zafi zafi zafi kan nonona zai cire...." Rufe mata baki yayi yana girgiza mata kai yace could down please a hankali zafin zai tafi"

Tashi tayi zaune tana share hawaye tace “inbe daina bafa?" Dariya mgnr taso bashi a ransa yana jinjina wautar Hauwa amma dake a matse yake bai biye mata ba yace “bama zaiƙi dainawa ba idan kika bari nasha na few minutes zaki dainaji kwata²
Aikuwa dake sauna ce saita miƙa masa tace “Allah idan naji zafi ihu zantayi maka" shidai dake a matse yake haka ya rinƙa lallaɓa mata kan nono yanasha yana mulmula ɗayan yanajin wani yam-yam a jikinsa Penis ɗinsa sai ƙara kumbura takeyi.
Ganin tayi luf tana shafa sumarsa ya bashi damar zamar da ita ya kwantar ta yaci gaba da wasa da kan nonon nata a bakinsa yana mamakin yanda ta bashi haɗin kai da wuri haka irin alwashin da yaji tana ci baiyi tunanin samunta da sauƙi hakaba.


Zame mata sikert na jikinta yayi ya janye pant ɗin yasa hannunsa yana wasa da tudun gurin yanaci gaba da shammatarta ta hanyar shafe kowacce gaɓa ta jikinta aikuwa Hauwa akwai saurin ɗaukar charge ta biyu matuƙa har wani narke masa takeyi kafin taji hannunsa cikin gabanta yasa yatsansa yana wasa da ɗan tsakanta yana turawa ciki a hankali ta yanda bazataji zafi ba.
Da dabara sosai ya kashe mata jiki duk wani yanayi da zaisa ta fahimci azabar dake tsakanin zuwa da zowar ya ƙi kaita gurin zumar kawai yake lasa mata har yakai ga kai harshensa ƙasanta ya fara tanɗewa yana karkaɗawa yana lasar ruwan da taketa fitarwa yanajin yanayinsa na hauhawa musamman dayaga irin ruwan da taketa tsiyayarwa abin ya tsumashi tabbas Allah yayi mata baiwa da wata ce a yanayin nan na ƙila waƙala ƙafewa zatayi ƙaf sai anci wuya amma ita da alamun da sauki zaiyi ban ruwansa a gonarsa.


Hajiya Excellency Hauwah bata fara fuskartar gangancin datake shirin aikatawa ba saida taji Alh Adnan yayi mata rumfa ya sanya ƙafarsa ya buɗa tata yana karanto addu'ar saduwa da iyalin sannan hayyaci ya fara zuwa mata ta tattara ƙarfinta tana ƙoƙarin tureshi saidai kash ta makara har ya sanya hannu ya buɗa fatar ɗan tsakanta ya fara goga mata Penis ɗinsa numfashinta yayi sama yana barazanar ɗaukewa ta haɗa kalma daƙyar tace “sh...shhhh Ran...ka shi....daɗe ɗaɗi zai tafi da rayuwa....." Ai wani ihu ta sake saboda azabar da taji ta mamaye gurbin daɗin daya fara lasa mata ta saki kuka ta angajeshi da ƙarfin da batasan inda ta sameshi ba,
Kafin ya miƙe ta dire a gadon tana wani tsalle tana ihu cewa “take shikenan bayan iskanci har kisa yakeyi yasa wuƙarsa ya yankemin gindina na mutu na lalace Baffa wlh bazan zauna dashi ba jini wayyoh jinina zai ƙare jama'a ku kawomin agaji"


Nufarta yayi da sauri ta kuwa zube a gurin ta rushe da kuka tana cewa “Na haɗaka da girman mahaifiyarka ka ƙyaleni wallahi tallahi na fasa jin daɗin dama tsautsayine na yarda babu wani daɗi sai wuya shiyasa ashe mugaye sunsan kashe mutum akeyi a dawo masa da rayuwarsa shiyasa kowa sai yace kayi hƙr nikam nabi hƙr da gudu ba wando na fasa auren yau bayan Yakumbo nika kwan...........


*OUM HAIRAN*
[1/26, 8:02 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB32-33_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

____________________________________

Chafkarta yayi ya rufe mata baki tare da bubbuga bayanta cikin yanayi na sigar rarrashi yana tattaro yawun bakinsa daƙyar ya haɗe ta da jikinsa ya tura Penis ɗinsa tsakanin cinyoyinta ya matse yace  wata wahalalliyar murya me nuna kwaɗaita da abin buƙata ”kik... Kiyi hƙr na fasa" da sauri ta ɗago rinannun idanunta tace “da gaske Ni tsoro zafi gurin kamar na ƙone" jinjina mata kai yayi yana mayar da hankalinsa ga samawa kansa mafitar da yake ƙoƙarin yi ya jata yace “ki kwanta kiyi relax bazanyi miki komai ba zan samawa kaina mafita ne"


Tureshi ta shigayi ta kasa dole ta ƙyaleshi tanaji yana sarrafata yanda yakeso hardai ya samawa kansa nutsuwar kamar yanda yaso sannan yayi luf a jikinta yana shafa sumarta sun jima a haka kafin yayi juriyar janyewa Hausawa sunce da babu gara babu daɗi Alh Adnan a hakan ya ɗan rage zafi ya shiga bathroom ya watsa ruwa tare da ɗauro alwala ya fito ya matsa gareta duk tayi laushi yayi murmushi yace “Banfa yi miki komai ba ki tashi ki gyara jikinki kiyi sallar Magrib Ishar ma gata can yinta akeyi.
Turo masa baki tayi tare da juya masa baya yaja numfashi yakai hannu ya ɗagata cak ya nufi bayi da ita tana shusshureshi tana tureshi tana cewa zanyi ka barni.
Saida ya shigar da ita bathroom ɗin ya direta ya juya ya fita tabi bayansa da harara tanajin kamar ta jefeshi da hoge haka dai daƙyar tayi wankan badon ranta naso ba.


Cikin Sa'a data fito bayanan hakan ya bata damar ficewa daga sashin nasa a parlourn taci karo da leda taja baya tare da tunanin waye ya ajiye mata? Numfashi ta sauke data tuna da Jibril ɗan aikenta ta ɗauki ledar ta shiga ɗakinta yalo ne da agwaluma a ciki da yawa ta ƙara dubawa bataga wayar ba takaici ya cikata ta miƙe ta tayar da sallarta tana cikin sallar taji ana taɓa ƙofa ta katse bayan takai Magrib ta fita tana tambayar waye?
Jibril yace “Ni...nine Hajiya ki buɗe da sauri Alh na gab da shigow...." Bata gama jinsa ba ta buɗe ya miƙa mata wayar yace “komai anyi yanda kikace har kati na loda miki na dubu biyar?"
Jinjina masa tayi ya juya da sauri itama ta juya taje ta ɗaga katifarta tasa wayar ta ƙarasa sallarta ta kulle ɗakin da key bayan ta nemi abinda zataci ta zauna tanaci tana saita abubuwan wayar taji an taɓa ƙofar tayi saurin tura wayar ƙarƙashin gado ta miƙe tana kallon ɗakin can ta tsinkayo muryarsa yana cewa.


“Ok tunda kin kwanta saida safe" ajiyar zuciya tayi ta matsa ta leƙa ta kafar ƙofar taga ya juya ya tafi ta taɓe baki tare da komawa ta zauna


Taci gaba da saita wayarta bayan ta gama ta sanya kayan bacci ta haye gado ta ɗauko wayar ta latsa number Nabeel gabanta na faɗuwa ta kirashi har tayi ring ta katse ba'a ɗaga ba, cikin zullumi tace “Innanillahi Allah yasa ba wani abune yake faruwa ba...." Sake kiran wayar tayi saida ta kusa tsinkewa aka ɗaga murya can ƙasa yayi sallama.
Ƙirjinta ya ƙara bugawa da ƙarfi tanajin zuciyarta kamar zata faso ta fito jin ya kuma cewa “Hello" cikin raunin murya yasata jan zuciya tace “My Nabeel nice Jiddanka ce...." Birkitowa yayi daga katifar da yake kai yace “Hah.... Hauwah Jiddarh ina kike wacce number ce wannan ina wayarki Hauwah ina mijinki?"
Daga yanda yake jera tambayoyin tasan bashi a hayyaci ta sake narkar dakai hawaye ya zubo mata tace “My Nabeel a wanne hali kake yanzu?"

Wata ajiyar zuciya ya sauke me ƙarfi yace “ni kaina bansan halin da nake ciki ba Hauwah an rabani dake inajin tamkar an rabani da rayuwata ne Jiddarh shikenan yanzu na rasaki ko?"
Numfashi ta fusgo ta sauke tace “Don Allah ka daina wannan mgnr nifa nasan dole sai mutumin nan ya rabu dani domin zaren ba kalar yadin bane babbar damuwar itane na shiryawa mutumin nan cin mutuncin da bazai iya jurewa ba amma na kasa aiwatarwa tun jiya nake ƙoƙarin naga na fara keta alfarmarsa saidai na kasa Nabeel wlh banason mutumin nan..."
“Na sani Hauwah yanzu meye tanadinki gareni?" Da rashin fahimta tace “ban gane ba kamar wanne irin tanadi kenan?" Murmushi yayi me ciwo yace “ko dame kika dawo zan karɓeki a haka saidai zanso alfarmar ki adanamin kanki wlh zanji baƙin ciki idan wani ya rigani saninki Hauwah, rigani aurenki baya nunamin rigani samunki abinda zai nunamin hakan shine rigani saninki"

Cikin sanyin jiki tace “wai kana nufin kusanci kenan? Karna bari ya kusanceni shine cikon farin cikin ka?" Da sauri yace “Hakane Hauwah don Allah kimin wannan alfarmar kinji" shiru tayi har saida yaji gabansa ya faɗi yace “kodai aikin gama ya gama ne?" Saurin kaɗakai tayi tace “Allah ne mafi sanin daidai Nabeel nayi maka alƙawari indai kaga bai cika ba to badaga Ni bane"
Kwantar dakai yayi yace “nasan zaki iya ina wawan naki" dariya tayi tace “yana part ɗinsa saboda inason jin muryarka nasai sabuwar waya da sabon layi naka kai kaɗai waccan Baffa ya ƙwace harda wani yi masa kashedin kada ya bani waya yanzu"
Da sauri yace “kayyy kuma baki tsoron su ganomu?"
Taɓe baki tayi tace saime don sun gano ai nafiso ma su gano ɗin" murmushi yayi yace “auta rigima har naji ƙarfin jikina da naji muryarki" nan suka shantake da hira shikam mantawa ma yakeyi da aurenta ita kuma shauƙin soyayya ne yake ɗibanta ta manta komai gashi ta samu ƴanci hira har ɗayan dare suna yima junansu alƙawuran ƙauna daƙyar sukayi sallama ta aje wayar tana miƙa taja duvet ta rufe jikinta bacci me daɗi ya ɗauketa cike da mafarkan data sabayi masu firgitata yauma mafarki tayi da macijin da take yawan mafarki dashi kullum ƙara kusantota yakeyi to yauma sai taga ya ƙara kusantarta sosai har yana neman kamota ita kuma tanaja baya daƙyar ta samu ta ƙurewa gudunsa daidai nan ta farka tana neman tsarin wannan mafarki daya zame mata sababbe.


Daƙyar ta miƙe cikin mutuwar jiki ta nufi bathroom ta sake ɗauro alwala tayi sallah raka'a biyu ta zauna saman sallayar har lkcn asuba yayi tayi sannan tayi azkhar ta kwanta bacci ya sake ɗauke ta zuuuu ɗin da taji wayarta nayi ne yasata tashi da sauri ta ɗauka saƙon Barka da sfy ne daga makullin ruhinta tayi murmushi tace “tnks My Nabeel" ta miƙe tayi brush tayi wanka ta canza kaya ta zauna ta kirashi ya ɗaga yace “ina fatan zuciyata tana cikin aminci?" Murmushi tayi tace “da sauƙi tawa fah?" Jan numfashinsa yayi yace “tawa ma bata samu aminci ba bare taki ai muda aminci sai ranar da tsohon nan ya  sakomin....."

Wani ihu ta saki ta miƙe saboda jin fusgar wayar da akayi idanunta ya sauka kan Alh Adnan da idanunsa sukayi jawur Allah yayishi da masifaffen kishi baya ƙaunar ko barorin gdan yaga matansa suna shigewa wannan yasa idan ba Aiken dole ba basa shiga sashin matan gdan to yau ga wata sabuwar musifar a gdansa Hauwah take waya da wani.
Takawa yayi tanaja da baya yana binta har suka ƙure ɗakin yasa hannu ya shaƙota yanason magantuwa ya kasa kawai saiya saketa ya juya ya fice da wayar.
Tafasa sosai ransa yakeyi ya fahimci taurin kan Hauwah na gaske ne notinan kanta sunyi sako² saiya ɗaure mata su sannan zasu daidaita fita zaiyi amma yanda yaji ransa na zafi ko yaje taron bazai iya hassala komai ba hakan tasashi rafsa tagumi a parlour yana fama da tuƙuƙin zuciya.


Baisan iya lkcn daya shafe a gurin ba yana zaune yana tunano mafitarsa ya kasa samu dole ya tashi ya nufi ɗakin nata ya buɗe tana kwance itama inda ya watsarta a gadon tana kukanta na shagwaɓa ya zauna da sauri gabansa na faɗuwa yanabin bombom ɗinta da suka baje da kallo.
Hannu yakai ya ɗora samansu ya shafa tare da birkitota ya zuba idanunsa a fuskarta har wani lumshewa shagwaɓaɓɓun idanunsa sukeyi saboda ɓacin rai da ƙuncin zuciya yace “Kina wasa da dokar ubangiji Hauwah meye yasa wlh duk da cewa naji ciwon kamaki kina waya da wani amma nafijin takaicin shiga gonar Allah da kika shirya yi Jiddarh meye ribarki idan kin yarda son abokin Halitta yasaki kinyi baram² da mahaliccinki wacce riba kika samu?"

Tashi tayi zaune tace “Ya subhanallah Astagfurullah wallahi na manta Ni matar aure ce Ranka shi daɗe inason Nabeel ka taimaka ka sakeni naje na aureshi..."
Kafeta yayi da ido yana jinjina girman wautarta ya jinjina kai tabbas yaro yaro ne akwai aiki a gabansa kafin Hauwah ta nutsu tasan daidai sai yaci wuya kamata ma yayi ya daina damuwa da lamarinta ya rinƙa barinta a shashasha shine zuciyarsa zata samu salama
Janyota yayi jikinsa yace “Ki daina shima neman saki saɓawa Allah ne" turo baki tayi tace “kayy to wai meye ba saɓawa Allah ba a cikin aure ni komai nayi sai kacemin saɓon ubangijine to faɗamin da bakinka meye zankeyi maka da zaisa ka tsaneni ka gaji da zama dani ka sakeni naje na auri My Nabeel nasan zai jirani"
Haɗe rai yayi kamar zai faɗi gaske yace “Ki daina yimin mgnrsa sannan duk abinda nasaki kiyimin ni wannan ne kawai zaisa na tsaneki na iya rabuwa dake a rayuwata banson naga mace tanamin biyayya haushinta nakeji kinga idan kikayi biyayya cikin sauƙi zaki yar da ƙwallon msngwaro ki huta da ƙudaje"
Wata dariya tayi tace “Dan ɗan wannan ma aini tun yau ma zan fara yanzu me kakeso nayi maka?"..............
[1/27, 7:10 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB34-35_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

____________________________________

Tashi tayi tsaye ta riƙe ƙugu tace “wai biyayya komai kasani nayi maka shine zaisa ka tsaneni saboda ka ɗaukeni a gantale to nabi biyayya da gudu ba wando naci uwarta naci babanta a tuɓe bazanyi ba kada ka tsaneni ɗin....."
Wani ihu ta saki lkcn da taji ya haɗe ta da jikinsa ya sanya hannunsa ya matse nononta ta rintse idanunta tace “wlh Idan kana taɓa min nono saina faɗa wa Baffa kaiɗin ba mutumin ƙwarai bane taɓa wa mutune nono kakeyi kuma harsha kakeyi tiƙaƙa dakai ko kunya bakaji....."
Bakinsa yasa ya rufe mata natan yace “nakedai shawa matata ba nake shawa mutane ba to ke in ba shirmenki ba idan mutane nake shawa ai da kafin ki sani Baffa saiya rigaki sani" tureshi tayi ta nufi ƙofa zata fice ya riƙota ta fusge tace Allah idan ka ƙara taɓani saina......"
“Saikin zaneni?" Murguɗa masa baki tayi ta fizge ta fice da gudu yayi murmushi yace “Yaro man kaza ki gama shirmenki akwai ranar fanshewa"


Fita yayi bai taddata parlourn ba ya hangeta a dinning tana haɗa abin karyawa, isa yayi ya sunkuya ya sumbaci kuncinta ya miƙe yace “ki fara shirinki gobe karfe biyu da rabi zamu tashi" bai samu arziƙin ko uhmm daga gareta ba ya fice ta taɓe fuska tare da jan tsaki tace “Hotiho kawai" yaji tsarkin nata sani yayi tankawar ma ba wani amfani zaiyi masa ba shiyasa ya fice ya ƙyaleta.
Abin duniya ya taru yayi mata zafi gda ita kaɗai saidai ta shiga nan ta fita ta shiga can haka ta yini gashi ko wayar da zata latsa babu itama wacce ta siyo ɗin ya karɓe haka ta yini tana kai kawo tsakanin ƙarya da gaskiya.
Data gaji dole ta koma ta kwanta baccin dole ya ɗauke ta shine bata tashi ba sai 3:30 tayi sallolinta ta zauna a parlourn tana kallo badon tana ganewa ba sai don inta zauna shirun tayi mata yawa da ɗan abin ɗauke kewar abin zaifi armashi.


Tananan zaune har biyar sannan taji dirin tsayawar motoci ta miƙe da sauri ta shige ɗakinta ta zauna a saman sallayar dake shimfiɗe.
Koda ya shigo yaga bai ganta ba ɗakinsa ya shiga ya cire kayansa ya watsa ruwa sannan ya fito sanye da jallabiyya ya tarar da ita tana karatun Alkur'ani ya zauna ya zubanta idanu yana mamakin lamarinta gatadai a haka zubin nutsattsu amma shirme yayima kanta yawa murmushi yayi ya miƙe ya matsa gabanta lkcn da ta ida karatun ya karɓi alƙur'anin ya ajiye  ya dawo ya zauna a kusa da ita yace “Barka da gida My bride kin yini lfy?"
Maimakon amsa sai yaga ta kawar dakai tana ƙoƙarin tashi a gurin ya riƙota ya mayar da ita ta zauna ya furzar da iska sannan yasa hannu ya ɗago kanta ta lumshe idanunta.
Zubawa idanun nata ido yayi yaja zuciya yace “gaki a haka kamar cikakkiyar mace amma kin kasa fahimtar komai" buɗe idanunta tayi akansa suka shiga cikin nasa ba mace ba hatta mazan ba kowa yake iya zuba idanunsa cikin na ADN su daɗe batare dayaji wani yanayi ba.
Hakance ta faru da Hauwah babu shiri ta sauke idanunta daga nasa taja fasali ta sanya hannu zata janye nasa ya riƙe ta sosai yace “kina wahalar dani tunda na fara sanyaki a idanuna har yau ban huta ba"


Da ƙarfi ta banƙara hannunsa ta cire fuskarta tace “Ina ruwa na kar Allah yasa ka huta ɗin kaine kaga zaka iya yanzun da bakasa rayuwarka cikin tawa ba aida ba wannan zancen akeyi ba, murmushi yayi yace “yanzun kuma da ake wannan zancen ya kenan?"
Harararsa tayi ta miƙe tace “Sai kayi hƙr da duk yanayin da zaka gani hakan shine ya kamaceka" lumshe ido yayi yace “ok nima bazai zama laifi ba idan nayi miki abinda ya kamaceki kenan?" Banza tabawa ajiyarsa ta kama ƴan waƙoƙinta yana kallonta ta cire kayanta tsaf ya rage daga ita sai under sikert tajashi ƙirjinta nonowan nan kamar su cakar masa ido ga iyayen ɗuwaiwaka ta zare band ɗin jikin gashinta ta bajeshi har tsakiyar bayanta ta juya ta shige bayi yayi kasaƙe yana kallonta kamar robot tsabar shiga yanayi har wani jiri yaji yana ɗibansa a zaune

Zuciya Na faɗa masa yabita bayin duk wacce za'ayi ayi shikuma yana tausarta yana haƙurƙurtar da ita ya miƙe ya hau gadon ya kwanta yanajin jijiyoyin jikinsa sunayi masa wani yammmm daƙyar yake haɗiye yawu saboda wata mahaukaciyar guguwar sha'awar Hauwah data dirar masa iyakar ganin da yakeyi mata yasan yanasonta matuƙa amma bai taɓa jin mawuyacin hali akanta irin wannan ba daƙyar yake sauke numfashi burinsa kawai yajishi a jikinta amma baisan ta ina zai ɓullo mata tabarshi cikin kwanciyar hankali ba bayason takura mata amma ya fuskanci alamu suna nuna sai yayi da gaske.


Yananan kwance ta fito daga wankanta ɗaure da towel tana tsane gashinta da wani tana yan tsalle²nta tana cewa wayyoh wayyoh Sanyi wayyoh Allah sanyi....."
Ganinsa kwance ya zuba mata idanu yasata haɗe rai tace “ni banson sa ido ka wani yimin sanƙanƙan a gado kamar gawa ka kafe...." Bata ida mgnr ba sai buɗe ido tayi taganta kwance a samansa yasa hannunsa ya fincike towel ɗin sai gata tik haihuwar gyatumarta aikuwa wani tsoro ya shigeta tace.
“Na shiga uku shegen bakina wlh na tuna nabi Allah da Annabin Allah nikam banaso wannan abun naka me kama da aska har yankani yayi Allah idan kace zaka kuma gogamin mutuwa zan....."


Bakinsa na rawa yace “Shiru Auta bazaki mutu ba a hankali zanbiki" zaro ido tayi tace “aa wlh jiyama fah daka fara tsotse²nka sai ka ɓatamin wankana nikam ka barni nayi kwalliya....."
Tsinkewa zaren mgnr yayi lkcn da taji hannunsa ƙasan nononta ya sauke wata ajiyar zuciya me ƙarfi yana ƙara riƙar nonon ya matsesu sosai yanda yasan bazataji zafi ba yace.
“Zan zansha kaɗan...." Bai jira amsarta ba ya sanya bakinsa ya cafka ta fashe da kukan shagwaɓa don a zahiri ba zafin takeji ba kawai tunanin haɗuwarsu ta jiya ne yasata kukan babu shiri,
Shikam Alh Adnan yayi nisa bazai iya tantance yanayin da yake ciki ba babban burinsa ya jisa a ruwa yana nutso yaukam baijin zai iya kawar mata da ido haƙurinsa ya ƙure rabonsa da jin mace a ƙasansa ya kusa sati biyu baima sami zama ba bare ya samu lkcn matan nasa.

Yanda yake tsotson nonon kaɗai ya isa ya tabbatar maka da cewa shiɗin cikakken ɗan son rayuwa ne itakam Hauwah ga daɗi ga tsoro a hankali yanayin daɗin ya rinƙa cire mata firgicin ta saki jiki sosai zuciyarta na faɗa mata don wuya ai bazaaƙi daɗi ba abinda ya kamata kawai idan taga yana ƙoƙarin shigarta ta gudu inyaso su rinƙa tafiya a haka saboda ta fahimci babu kalar wasan da yakai shan nono daɗi daɗinsa azimun ne a cikin ƙwaƙwalwa akejinsa.
Da wannan tunanin taga ya ɗagata ya kwantar da ita a gefe zare rigarsa ya ɗagota ya saita bakinta saman nipples ɗinsa yace “Suck me" ɗagowa tayi idanunta a lumshe tace “Ban iya...." Bakinsa ya ɗora saman nata yana zagaya harshensa yana ɗan lasar kan nonon nata tare da dannawa a hankali ya jima yanayi mata itane harda wani kwantar dakai tana cewa.
“Excellency bar... bari  wayyoh daɗi ahhhh" tanayi tana riƙe masa kai ya cire bakinsa ya dubeta da idanunsa da suke wani lumshewa yace “ki gwada haka akeyi"..............

*Manerge*
[1/28, 7:41 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB36-37_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

____________________________________

Kwantar da kanta tayi luf jikin pillow tana matsa pillow ɗin da hannunta, yaja ajiyar zuciya ganin batada niyyar yi masa yace “ok kada kicemin komai tunda bazakiyimin yanda zan samu relief ba Hauwah banson shigarki a wannan lokacin akwai matsala shiyasa nake ƙyaleki amma idan kika gaza dani to zan nemawa kaina mafita bazan jurewa azabar dake cin ruhina ba"
Buɗe idanunta tayi akansa yaja baya da sauri saboda tashin hankalin daya ɗarsu cikin nishaɗinsa yana ja baya gabansa na faɗuwa yana faɗin “Allahu Muhammadur Rasulullah   (S.A.W) ba komai ne ya firgitashi ba face ganin ƙwayar idanunta ta canza kala ta koma blue wani shuɗin haske ya fito ta cikinsa ya haske ɗakin gabadayansa.
Cikin matsanancin tashin hankali yake karanto addu'o'i masu zafi da ƙarfi yana tofawa a ɗakin kansa na juyawa da ƙarfin gaske kafin daga bisani yaga hasken ya ɗauke duhu ya mamaye ɗakin yaja ajiyar zuciya me ƙarfi ya kai hannu ya kunna fitilar ɗakin ya zubanta idanu yaga tayi miƙa tare da salati ta buɗe idanunta akansa ta yunƙura kamar zata miƙe sai kuma yaga ta koma ta kwanta taja bargo.

Fasali ya sauke ya matsa jikin gadon ya zauna a ɗan ɗarare yakai hannunsa kanta ya shafa dogon baƙin gashinta ya kira sunanta ta motsa ya sake kiranta ta buɗe idanunta a kansa tayi masa murmushi tace “zaka iya nima zan iya"
Daga haka bacci ya ɗauke ta me nauyi inda ya tashi yana mayar da yawunsa na kwaɗayi yaje yayi tsarki ya ɗauro alwala ya nufi masallaci lkcn ana shirin shiga sallar Magrib yayi ya zauna cike da tunani barkatai na sabbin lamura da yanayi da ya gani a Hauwah yau,
To me hakan ke nufi? Meye ma'anar kalaminta zai iya itama zata iya? Bashi da amsa wannan tasa ya tashi ya nufi gdan ya  shiga da sallamarsa  ya kullo parlourn ya nufi ɗakin nata ya isheta saman sallaya da littafin bulugul maram tana dubawa ya zauna ya zuba mata idanu ta ɗago idanunta cike taf da hawaye ta saukesu akansa ta buɗe bakin cikin bazata tace.


Wace Na'ilatu wace  Ruƙayya wace Khairiyya wace  sannan wacece Ummu Salma?" Da sauri ya ɗago idanunsa ya saukesu akanta
yanajin wata faɗuwar gaba na shigarsa ya buɗe baki yace “Ahli nane ya akayi? Wani abu ya samesu ne ina kika sansu?" Babu sigar wasa ko shirme taja numfashi tayi ƙasa da kanta tace “Na'ilatu ƴar Mal Hudu dillali itace matarka ta farko da bayan ita sai Ummu Kulsum sannan sai Ruƙayya wadda ta haifa maka Ruƙayya ƙarama wacce kuke kira da Khairiyya, ta rasu a wani yanayi da har yau aka kasa gano sila Uhmm! hmmm!! Bayin kanka bane Khairiyya ta gamu da lalurar shanyewar ƙafafu a zahiri batada matsalar shanyewa domin ba shanyewar tayi ba dabaibayi akayiwa ƙafarta sannan aka kulle bakinta wanda har yanzu an kasa samun makarinsa.
Ummu Salma yanzu ita da na'ilatu duke zamani a gdanka wannan shine gskyr abinda ke akwai ko?"


Da matsanancin mamaki  ya jinjina mata kai ya buɗe baki zaiyi mgn ta ɗagansa hannu tace “karkace komai kowannensu zan ɗora shi a ma'auni abinda caca ta gani shi takeci"
Daga haka ta miƙe ta shige bathroom ta fito ta sanya kayan baccinta tayi addu'a ta kwanta bisa dole shima yayi abinda tayi suka kwanta itakam baccine ya ɗauketa cike da kwanciyar hankali, shikuwa juyi kawai wakeyi abubuwa sunyi masa yawa ya ƙosa ya samu nutsuwar da yake buƙata daga Hauwah saidai ya lura kamar akwai matsaloli cikin tarayyarsa da ita hakan tasa ya dangana ya janyota jikinsa tare da ja musu bargo sukayi bacci farkawa tayi a firgice tana kiran “Ubaid! Ubaid!! Khairiyya!!!" Firgigit shima ya tashi cikin kiɗima ya janyota jikinsa yana girgizata yana kiran sunanta itakuma sai ƙoƙarin ƙwacewa takeyi ya ɗago kanta da sauri ya cafki harshenta da bakinsa hakan yasata sakin jikinta a nasa tare da sauke ajiyar zuciya ta sanya hannunta ta saƙalo wuyansa ta janye bakinta cikin murya me sanyi tace “Ina Ubaid?" Zuba idanunsa yayi a cikin nata yace “wayeshi?"

Janyewa tayi daga jikinsa tana me zubawa bangon ɗakin idanu ta buɗe baki da sanyin jiki tace “Bakasan Ubaid bin Nasr ba?" Jinjina mata kai yayi ta jinjina kai ta sauke idanunta da cikin ƙwayar yayi brown sosai maimakon baƙi tace “Karkaji tsoro bazasu cutar dakai ba sun kasance masu bawa sashi makusancin sashi kulawa suna sanar dani abinda ya faru shekara ɗari baya kafin wanzuwata Indai ya kasance abin ya shafeni Alh a yanzu haka wasu gungun matsafa sun sanya an sace ƴarka ƙwaya ɗaya tal a duniya wato Khairiyya antafi da ita kudancin China za'a tsaface ruhinta sannan a dawo da ita matsayin fitinar da zata fitini rayuwarka....."

Miƙewa yayi a firgice yace “Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un wannan ba gaskiya bane Hauwah banason zancen banza uban waye zai ratsa gdana duk irin tsaron dana bashi ya saci ƴata ɗaya tilo da masu tsaron lfyrta ma basa bacci wannan shirm...."
Tsawa ta daka masa data sanyashi haɗiye mgnrsa saboda yanda yaji kalmar “Kayyyy!" Ɗin tana amsa amo a ɗakin, sau ɗaya ta faɗa amma ta maimaitu takai sau goma sannan shiru ta gauraye ko ina ta miƙe a gadon ta nuna bangon ɗakin da hannunta  wani haske blue me ƙarfi ya daki bangon ya rabe biyu tace “kalla" a mugun kiɗime yakai dubansa gurin da sauri ya taka ganin Khairiyya zaune cikin wani ɗaki an ɗaure mata idanunta sai gunji takeyi babu damar mgn" yana isa gurin ta sake nuna bangon da hannunta take ya haɗe ta buɗe bakinta tace “Bantaɓa faɗar mgn batare dana tabbatar da itaba Allah ne mafi sanin daidai Adnan Amma tabbas akwai wani da yake neman rayuwarka data Khairiyya wanda har yanzu alƙaluman bincike basu bayyanamin shi ba ya ɓuya cikin duhun tsafinsa ya samu kariya daga kariyarsu ta tsafi yana shuka a baƙar gona bawai gagararta sani yayi ba har yanzu taswira lalubena ce batakai kansa ba"


Dafashi tayi tace “karka damu Amincin Allah ya tabbata ga bawan da bai zalumta ba ake zalumtarsa kayi hƙr ka jure zaka dace tabbas shaiɗanun cikinmu da shaiɗanun cikin bani adama sun haɗa kai suna cuta da wanzar da zalumci a doron ƙasa mu muna cikin jinsin Junnu bana shayaɗin ba, Khairiyya zata dawo cikin aminci karka damu munsa aje a taho da ita zata isheku a Saudiyya kajeeee....."
Sulalewa tayi ta koma saman gadon baccinta taci gaba dayi batare da damuwar komai ba.


Shikam yanda yaga rana haka yaga dare bai iya sake rintsawa ba zuciyarsa ta i cika da tsoro wacce iri ce Hauwah meye yake faruwa da rayuwarta shi gabaki ɗaya ma tsoronta ya ɗarsu a zuciyarsa iya kwana biyun nan tanata fito masa da wasu siffofi saɓanin wanda hankali zai yarda dashi.
Da asuba yayi mazantakar tashinta tayi miƙa tayi salati sannan ta tashi zaune tana ƙarewa ɗakin kallo tace dashi “kayy dama tare muka kwana?" Da rashin fahimta yake dubanta yace “eh bakisan tare muka kwana ba?" Ɗagansa kai tayi tace “nidai nasan mun kwanta anan kuma sai naji ka tasheni kace zaka tafi ɗakin ka to yaushe ka dawo" shirmenta ya girmi tunaninsa wannan tasa ya fice ya nufi masallaci kafin ya dawo har tayi wanka ta kama gyaran gdan sanda ya shigo ta gama komai tana fesawa parlourn turare yace.
“Waye yasaki aikin nan?" Kallonsa tayi ta  rusuna tace “Ina kwana?" Murmushi yayi ya shafa kansa yace “Eh to wani bangaren lfy" murmushi tayi tace “Bayan fitarka Masallaci Ubayd ya bani saƙo yace na faɗa maka komai yana tafiya daidai" tana gama faɗin haka ta shige kitchen ta fito da tea a hannunta ta zauna tana haɗawa taganshi har yanzu tsaye inda tabarsa.


Ta miƙe ta isa ta kama hannunsa tace “Inason Nabeel Amma Yarimah Ubaid yacemin dole na barsa inba hakaba zasu kasheshi bashi da kariya kamarka kuma bashida juriya kamarka sannan ya sanar dani dole na zauna dakai domin kasancewa garkuwa agareka na hƙr zan rayu dakai bisa sharaɗin duk abinda nace maka bazaka musamin ba domin bazan taɓa cutar dakai ba Allah ne mafi sanin daidai Mijina amma naji a raina kai alkhairi ne tunda Ubayd ya karɓe ka kuma har yabani umarnin rayuwa dakai cikin aminci"
Numfashi ta sauke tace “yanzu Bama wannan ba ka kira gda kaji meye yake faruwa ne?" Dafe kansa yayi yace “kaina ya kulle Hauwah ban iya neman kowacce irin mafita ba meye ma ya kamata nayi ne?" Jansa tayi ya zauna ta zauna a cinyarsa ta shafa sajensa tare da jan hancinsa tace “kada ka kira Salma ka kira Na'ilatu itane zata faɗa maka daidai"
Har zaiyi mgn sai kuma ya fasa ya ɗauki wayar ya kirata ta ɗaga suka gaisa kamar babu komai yace “ina Ruƙayya ne kwana biyu banjita ba" hakanan taji kamar an matsata tace “Wlh bamusan meye ya faru ba mudai mun tashi munga babu ita yau da safen nan kuma duk mun cikita masu tsaron gdan sunce babu wanda ya shigo"

Cikin faɗuwar gaba yace “da gaske ne bata gdan...." Bai jira me zatace ba ya katse wayar suka kalli juna da Hauwah tayi murmushi tace “zata dawo" miƙewa tayi tace “yau ɗin nan"
Ɗakinta ta shiga ta kwanta ta barshi cikin damuwa yanason bata dama shine yasa yaƙi yin wani abu amma yana cikin zullumi, agogo ya duba 12:30pm suda zasu tashi biyu gashi ko karyawa baiyi ba haka ya  miƙe yashiga ɗakinsa ya canza kaya ya zuba wanda zai buƙata ya fice ya shiga ɗakinta ya tarar da ita ta zuba kayanta a trolley ya Kira wayarsa Jibril ya shigo ya ɗauki kayan suka fita Musa driver yajasu zuwa airport.
[1/29, 9:28 AM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB38-39_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

____________________________________

Basu wani ci lkc ba suka tashi VIP yayi musu ta kuwa samu yanda takeso ta kwanta a jikinsa tana shafa kuncinsa shikuma yana shafa bayanta zuwa mazaunanta da haka bacci ya ɗauke ta saida sukaje airport na Sarki fahat taji harshensa na yawo a kunnenta tayi miƙa tare da buɗe idanunta ta saukeshi akansa ya kanne mata ɗaya yayi ƙasa da murya yace “munzo" tashi tayi tace “kayyy zuwan da mukayi bara sai naji tafiyar tafi tsayi"
Murmushi yayi yace “Eh ai wancan tafiyar babu mahaɗi kikayita shiyasa kikaga nisanta" bata gane nufinsa ba kuma bata tambaya ba ya kamo hannunta suka fito daga jirgin motar hotel ɗin da yayi musu booking tazo ta taresu Suka tafi zuwa masauki koda suka isa ta kalli hotel ɗin sosai har saida suka hau lifter suka isa ɗakinsu sannan taja numfashi tace “Yanayin gurin sai yayimin kama da fadar sarki Nasr"
Da sauri ya dubeta yace “waye sarki Nasr?" Itama idanu ta zubansa ta matso tace masa “Bakasan Sarki Nasr ba?"


Jinjina mata kai yayi yace “Hakane bansanshi ba" takawa tayi ta zauna saman kujera tace “Sarki Nasr shine mahaifin Yarimah Ubaid na ƙasar Rum sun kasance jinsi daga cikin jinsin junnu da sukayiwa Annabi Sulaimanu hidima zamaninsa sannan sun kasance tun wancan zamanin suɗin musulmi ne kafaffiyar daular musulunci ta kafune bisa taimakonsu rundunarsu a wannan duniya sun kasance cikin jin aljanun da ubangiji yayi maganarsu cikin Suratul Jinnu yake cewa(“Ƙuul'uhiya ilaihi annahussama nafaru minal jinnu fa ƙalu, faƙalu Inna sami'ina ƙur'anal ajaba, yahadi ilar rushdi fa'amannabi.) Zuwa ƙarshe, sun kasance masu gaggawa wajen aikata daidai a rayuwarsu sannan sun barranta kansu da shaiɗanun cikinsu"


Zubanta idanu yayi yace “Ya akayi kika sani" murmushi tayi ta miƙe tace “Basa mutuwa ranka shi daɗe kuma duk wanda suka so cikin Insiy shima yakan zama ƙaramin abu baya sheƙeshi sukan baza hadimansu masu yaƙi da zalumci a doron ƙasa sannan......"
Shiru tayi tace “an kawo Ruƙayyah....." Da sauri yakai dubansa ga ƙofa tayi murmushi tace “baya sauka ta ƙofa amma yana sallama kafin ya shiga duk inda yake buƙatar shiga" tana rufe bakinta sukaji wata iska me sanyin daɗi ta mamaye gurin kafin Alh Adnan ya gama tunanin abinda ke shirin faruwa yaji anyi sallama cikin wata murya mai zaƙi ance “assalam Alaikum ya Ikwan" juyawa yayi da sauri inda Hauwah tayi saurin riƙe shi tare da girgiza masa kai yayi saurin haɗa nutsuwarsa ta amsa da “Wa'alaikassalam ya akhee Ubaid" wani ƙamshi sukaji ya mamaye gurin sannan haske ya cika dakin Adnan yayi saurin rufe idanunsa cike da firgici yaji “muryar da tayi sallamar tace “Barka Mai girma shugaba"


Daƙyar jikinsa na rawa ya buɗe idanunsa yaja baya da sauri ganin Khairiyya da gaske a gabansa a zaune yakai dubansa ga mutumin da yake tsaye sanye da kayan manyan sarakai na alfarma ya zubansa idanu fuskarsa ɗauke da murmushin rahma ya miƙa masa hannu, Alh Adnan ya dubi Hauwah ta ɗaga masa kai ya miƙawa Ubaid hannu sukayi Musabaha wani shorck ya ratsa jikin  Alh Adnan Ubaid ya janye hannunsa yanayi masa murmushi ya juya ga Hauwah ya rusuna cikin girmamawa yace “Amincin Allah ya tabbata ga uwar ɗakina na cika umarninki wannan yanayin yayimin tsauri zan koma zuwa yankin da muke rayuwar ƴanci rayuwa cikin bani adama akwai wahala saidai ka zama mutum kamarsu ko ka zama dabba"
Jinjina masa hannu tayi ta dafa kansa tace “Hakane kaje ka rayu cikin aminci idan buƙatar nemanka ta kama zan nemeka" daga haka ya sunkuyar da kansa take ya zama farin haske ya ɓace bat yabarsu da ƙamshinsa.
Hauwah ta matsa ga Khairiyya ta shafa fuskarta take ta zabura ta miƙe daga dogon baccin da Ubaid yasata ta kama dube² Alh Adnan da razani ya shigeshi ya kafe Hauwah da ido yaja baya ganin Khairiyya ta tashi zaune da kanta yace “Ruƙ...ayyah" dubanta takai gareshi takai dubanta ga Hauwah tanason mgn amma babu dama Hauwah ta share hawayen tausayin yarinyar ta matsa gabanta tace “Shekarunki goma sha shidda da shekara uku na girmeki taurarin rayuwarki 750 Ruƙayyah Ni matar mahaifinki ce kuma waraka gareki, kinason yin magana?"


Da sauri Khairiyya ta ɗaga mata kai ta nuna bakinta da hannunta tace “zakiyi mgn da izinin Allah amma ki adana abinda ke ƙasan ruhinki harsai ranar dana buƙaci ji da sani" wani blue ɗin haske ya fita cikin yatsanta manuni ya shiga bakin Khairiyya take wani baƙin hayaƙi ya rinƙa tashi daga bakinta ya rinƙa yin sama yana ɓacewa take Khairiyya taji kamar an ture mata wani gingimemen dutsi a bakinta ta buɗe baki tace “Da... Daddy...."
Tuni Alh Adnan ya zube saman gwiwowinsa yayi sujjada ga Ilahi ya miƙa ya isa ga Khairiyya yace “Ruƙayyah taga?" Rungumeta yayi itama tasa hannu ta matseshi saita fashe da kuka tace “Ashe ka nemota ka aura Dad Malama tace itan itace kullum take koyamin karatu a cikin bacci ko ido biyu so tari kasha zuwa ka ganni da littafi ina rubutu na Arabic kona boko kana tambayata inane na iya banida damar sanar dakai wannan itace mu'allima ta"


Kallon Hauwah yayi da alamun tuhuma shifa wannan lamari ya girmi tunaninsa ya buɗe baki zaiyi mgn tace “Bani bace mijina mu biyu ne akwai abokiyar tagwaitaka ta Amma ba'a jinsi Insiy ba komanmu munayinsa tare a cikin bacci kamar yanda ta sanar dakai nima itace Mu'allima ta zata bayyana lkc ne baiyi ba mijina Ruƙayya zata miƙe ta taka ƙafarta amma iyakar ƙasar nan idan mun koma gida zata zauna taci gaba da rayuwa inda takeyi a baya a zahiri amma a ɓoye zata rinƙa rayuwa kamar kowa idan ka amince yanzun zata miƙe"
Da sauri yace “na...na amince" murmushi tayi ta rufe idanunta ta buɗe bakinta tare da miƙa hannunta take saiga wani magani ya faɗo hannunta ta buɗe idanunta tamayar dashi hannun hagunta sannan ta ƙara miƙawa saiga kasko cike da garwashin wuta jajir.
Da mugun sauri Alh Adnan ya matsa cikin tashin hankali yana gani ta tsugunna ta buɗe wata kwalba ta tsiyayi wani ruwa ta shafa mata daga gwiwarta zuwa tafin ƙafarta ta janyo wannan kaskon ta buɗe wannan ƙullin maganin ta zuba shi a cikin garwashin ta rinƙa zagaya Khairiyya dashi tana cewa “Ƙum bi izinillah"
Hayaƙin na ratsa Khairiyya tanajin ƙafarta nayi mata wani irin zugi ta saki ƙara take ta fice daga  hayyacinta Hauwah ta danneta da hannunta ɗaya take ta kasa motsi har saida ta gama turarata sannan kaskon ya ɓace ɓat, ɗagowa tayi ta dubi Alh Adnan tayi masa murmushi ta cire hijjab ɗinta tace “ina buƙatar watsa ruwa ka ɗorata a sama" ya zama kamar robot zuciyarsa ta kasa tuna komai sai zillo takeyi masa shikam baiga mata ba lamarin Hauwah akwai Questions mark da yawa to dama abinda Baffa yake nufi kenan da yace masa bazai iyaba lamarinta azimun ne shi kuma ya dage kan zai iya?


Bashi da amsa bashi da me bashi haka ya ɗauketa ya ɗora a gadon sannan ya fita ya kama musu wani ɗakin ya tafi nema musu abinda zasuci sanda ya dawo Hauwah harta canza kayanta tayi sallah ta kishingiɗa a saman sallayar ya dubeta yaja fasali ya aje kayan ya matsa yace Barka da hutawa My Bride" tashi tayi zaune tace “ka barni Ni kaɗai ina kaje...." Shafa fuskarta yayi yace “baga ƴarki can ba tana bacci" murmushi tayi tace “tama tashi ta shiga  wanka" da sauri yace “da kanta?" Jinjina masa kai tayi yayi ajiyar zuciya tare da godewa Allah ya buɗe ledar yace “tashi kici abinci yau me zan samu My Bride?" Kallonsa tayi ta turo baki tace “yanzu sai kace zakasha nono....." Saurin rufe mata baki yayi ganin Khairiyya na fitowa daga bathroom ɗin ta tsaya tare da yin dariya tace “barka da hutawa Dad" cikin muryarta irin ta mahaifiyarta.


Tashi yayi ya riƙo hannunta hawaye ya zubo masa yace “bansan da wuri wannan ranar zatazo ba My Daughter ashe tana kusa saura abu ɗaya...."
Rufe masa baki tayi tana dariya tace “ka samamin ƙani nasan kullum shine burinka Dad shima very soon zai faru ko Mu'allima?" Murmushi Hauwah tayi yace “Allah ne mafi sanin daidai Ruƙayya idan ya samu zamu bashi kariya da kariyar ubangiji amma...."
Zubanta idanu sukayi tayi murmushi tace “Zai yiwu fah zakiyi ƙani son saidai bazai kasance kamarki ba zai kasance mutum ne amma....." Sai kuma tayi shiru tace “mu bari kawai zan sake bincike"

Bubbuɗe ledar ta rinƙayi tana dubawa saida ta gama dubawa sannan tace da Khairiyya ki shiga ɗaki cikin kayana bazaki rasa wanda zaiyi miki ba" jinjina kai tayi ta shiga ta ɗauki wata doguwar riga sannan ta fito Hauwah tayi mata dariya tace “ko powdar baki shafa bafa" murmushi tayi tace “ban iya shafawa ba Mu'allima" murmushi itanma tayi ta miƙe tace muje na gwada miki da murnarta ta tashi suka shiga ciki suka shashance da kwalliya sunma manta da ADN shikam zuciyarsa ta tafi hasashen abubuwan dake faruwa amma ya kasa hassala komai ƙarshe dai ya yanke shawarar kiran Baffa ya sanar dashi abubuwan da suketa faruwa tun zuwan Hauwah gdan.
Koda suka fito shiriricewa sukayi a cin abinci da game sunata dariyarsu shikam kallonsu yakeyi gsky ne dama yaro abokin yaro ne dubi dukkansu yanda suke cikin nishaɗi da walwala kamar basu taɓa shiga cikin damuwa ba musamman Khairiyya da kullum take cikin kunci damuwa da kukan zucci dana fili.
[1/29, 9:15 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB40-41_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

____________________________________

Da dare ma bayan sunyi sallar isha saida Khairiyya tayi bacci sannan Hauwah ta dubi ADN tace “kaje ɗaya ɗakin ni zansa mata katangar kariya tukunna" girgiza mata kai yayi ta matsa jikinsa tace “Allah babu abinda zai faru bayan alkhairi Allah ne mafi sanin daidai Excellency amma Ni nasan babu abinda zai samemu nida Khairiyya" yanda ya kafeta da idanunsa da suke a lumshe ne ya sanyata matsawa a jikinsa tana sunkuyawa wani ƙoƙo na silver ya ratso ƙasa ya fito ta ɗebi wani gari a hannunta ta miƙe tare da rufe idanunta ta hura wannan garin tare da wani haske suka zagaye gadon da Khairiyya take kai gurin yayi wani haske sannan hasken ya ɗauke Hauwah ta buɗe idanunta ta zuba su akan Khairiyya tace “ki tashi cikin aminci yake kyakkyawar ƴata tana faɗin haka da kai dubanta da wannan ƙoƙon garin take ya ɓace ɓat ta juya ga Alh Adnan da robot ma ya fisa kataɓus ta kama hannunsa ta kai hannu ta shafa gemunsa tace.
Kada ka tsawwalawa zuciyarka da tunanin abinda ke faruwa komai zai bayyanar maka batare da ka wahalar da kanka ba idan ka matsawa kanka wahala kawai zakasha babu abinda zaka gane tunda lkcn ganewar baiyi ba, muje mu kwanta inason nayi bacci sosai"
Ajiyar zuciya yayi yace “bazaki haramin ba?" Lumshe idanunta tayi ta ɗora hannunta a kansa tace “iya yau dai mu huta mana akwai gajiya musamman akai ba komai kanka yake iya jurewa ɗauka ba"


Bashi da bakin mgn hakan yabita suna shiga ta shiga wanka ta buɗe kayanta ta ɗauki wata sabuwar rigar bacci ta sanya duk abinda takeyi yana kallonta harta gama ta tako ta iso gabansa tayi miƙa tare da zuba idanunta cikin nasa da suka wani lumshe kaɗan ya buɗesu ya saukesu kan ƙirjinta tayi masa murmushi tace “Nifa inajin tsoro....." To shima a yau lamarin Hauwah ya girmi tunaninsa ko bashi kanta tayi bazaici ba harsai ya tantance abinda yake masa yawo a zuciyarsa gashi a mugun buƙace yake mararsa har ƙuƙƙulewa takeyi saboda  sperm daya tarar masa gashi ya kira wayar Baffa bata tafiya alamun da suke nuna ya shiga ɗakin aiki.
Kwantowa tayi jikinsa ta tura hannunta a bayansa ta rungumeshi ta kwantar da kanta luf a ƙirjinsa shima hannunsa ya sanya a bayanta ya matseta sukayi addu'a da haka bacci ya ɗaukesu lfyr Allah da asuba kiran sallar masallacin harami ne ya tashesu da yake suna kusa da ya tashi yayi alwala ya fice ya nufi masallaci itakuma ta fita ta tashi Khairiyya sukayi sallarsu tare sannan suka kwanta a ɗakin Khairiyya sunyi bacci sosai har saida ya dawo yaga bata a ɗakinsu ya shiga na Khairiyya ya tarar dasu kowacce tana baccinta ya matsa ya tashi Hauwah tayi miƙa ta miƙe tana muttsuke idanunta ta saukeshi akansa yayi mata murmushi yace “Morning tauraruwata" murmushi tayi tace “same to you" tana mgnr tana miƙewa suka koma falon tana cewa da Khairiyya kada ki sake kwanciya kiyi wanka ki shirya ki fito mu karya"


Basu gama fitaba ya ɗagata cak ya nufi ɗakinsu da ita ya ratsa parlourn ya sauketa a gadon yace “nima ina buƙatar karin safe" dariya tayi masa tace “kaje mana kayi Ni azumi ma nakeyi"
Zaro ido yayi yace “Wa a ina waye ya faɗa miki ana azumi babu sanin maigida to kuwa yau babu azumin nan nima ina buƙatar kulawa" bata fahimci nufinsa ba amma ta gane kurenta tabbas ba'a azumi babu sahalewar miji, da wannan taji yayi mata rumfa ya ɗora bakinsa a kuncinta yayi mata wani kiss me kashe jiki ya haɗe bakinsu ta lumshe idonta yanayin na dawo mata sabo kamar yanda ya faru a daren jiya cikin mafarkinta sai taji kamar yanzunne abin yake faruwa.

Ta kuwa sakar masa jiki ya rinƙa sarrafata yanda yakeso nononta a hannunsa yana matsasu tare da lailayesu yanashansu da ƙwarewa tare da shafa cikinta zuwa mararta zuwa saman pant ɗinta.
Ta rasa dalilin da yasa daya fara yi mata waɗannan salon takejin duk duniya batada abin buƙata kamarsa hakan yasa taji duk wuya yaudai ya kamata ta sallama masa kanta saidai tanajin tsoron Khairiyya ta fahimci wani abu. hakanan dai tasawa kanta juriya ta biye masa tare da sake masa jiki yayita juyata yanda yakeso ya rabata da komai na jikinta shima ya zare nasa ya sake saka nononta a bakinsa yana tsotsa tana wani irin jan zuciya me ƙara fitar da hayyaci ya kuwa shiga jikinsa ya ja bakinsa zuwa ƙasanta ya buɗe pupsy ɗin ta ya ɗora harshensa a kai yana lasarsa da salo na ƙwarewa wanda ya sake gigita duniyarta ta danna kansa tanajin saƙon a cikin ruhinta.
Inda ya shagalta da tsotseta ƙarfin feel ɗinsa na ƙaruwa duk daƙiƙa yanajin kamar ya shigeta kawai saidai yanason ɗauke mata hankali sosai daga wajen don yasani dole ne tasha wahala Indai ya shigeta da gaske domin shiɗin ba namijin wasa bane.


Lkcn da suka kai ƙololuwar buƙatuwa da junansu ne ya samu damar ɗagata ya zubanta idanu kyawun surarta ko a tuɓe baya ɓuya domin itan asalin me kyau ce ta gaske.
Wani shauƙi ya rinƙa fitar da wani nishi me ƙarfi.
Yana ambaton sunanta a karkatse yana shigewa jikinta da hikimominsa ya samu ya buɗata yana wasa da yatsansa a gabanta yana dangwalo ruwan gabanta yana lashewa saida ya tabbatar da tagama shiga gonarsa sannan ya fara karanto addu'ar saduwa da iyalin ya sakar mata nauyinsa ta yanda bazata iya ƙwacewa ba ya fara tura mata Sandar majalisar sa a gabanta ta kuwa saki wata ƙarar azaba me ƙarfi ta ƙanƙameshi jikinta na ɓari tace “Innanillah wayyoh Allah wayyoh Baffa ya Allahu zaka kasheni Alh kayiwa Allah da girman shekarunka ka ƙyaleni wlh zan mutu..."


Rufe mata baki yayi da nasa ya kwanta sosai a jikinta yaci gaba da shigarta cikin yanayi na rarrashi wanda ya janyo mata shiɗewa daga wannan bata sake sanin meye yake faruwa ba sai bayan dogon lkc da tajita a cikin ruwan zafi tayi wata miƙa tare da ƙanƙameshi ya kwantar da kansa a jikinta yana shafa bayanta ta sauke numfashi tare da buɗe idanunta daya kaɗa yayi jajir ta saukeshi akansa yayi mata murmushi ta rintse idanunta hawaye ya zubo mata tace “shi...shikenan ka karɓemin abinda na ƙare rayuwata wajen tanadawa mutum mafi soyuwa a guna ka rabani dashi....?"
Girgiza mata kai yayi yace “Kar ki lalata laɗanki da zunubi My Bride kin farantawa mijinki kin kashe masa ƙishirwar dake damunsa sannan kuma kinzo zaki canzawa kanki lissafi Hauwah shi ubangiji yafimu sanin daidai shine ya zartar da hukunci kada kiyi izgili gareshi kamun Allah azimun ne bana miki fatan kamunsa"
Kawar dakai tayi tana kwantar da kanta jikin bowl ɗin zuciyarta na ayyana mata abubuwa mabanbanta amma batada ikon bijirewa shawarar Me taimako Ubaid da Ahlinsa sunfi ƙarfin komai gareta zata ci gaba da ɓoye abinda ke binne har zuwa lkcn da duhu zai yaye haske ya ɓullo.


Yaso yi mata wankan da kansa bashida damar hakan domin ta kasa ta tsare ta hanashi yi mata komai daƙyar ta rinƙa gyara kanta ta samu ta gama ta koma ɗakin tana ɗaga ƙafarta daƙyar ta kwanta a gadon tana hawaye.
Ya dawo ɗauke da kayan abinci ya tasheta zaune ya rinƙa ciyar da ita yana bata hƙr hardai ya samu tayi shiru ta lafe a jikinsa ya rinƙa shafa bayanta yana hura mata iska da haka bacci ya ɗauke ta.
Ɗaukarta yayi ya mayar da ita gadon ya zuba mata idanu sannan yayi murmushi kalaman Baffa suna dawo masa da asubar yau da sukayi waya inda yake sanar dashi abubuwan da suke faruwa Baffa yaja numfashi ya sauke yace.
“Adnan shiyasa lkcn da kazo neman auren Hauwah na sanar dakai itan ba matar yaro bace a manya ma ba kowa ne zai iya riƙeta ba an daɗe ana haskamin abubuwa masu wuyar ganewa game da ita na kasa tantance inda suka dosa sai a baya bayan nan na fahimci wata runduna ce ta Aljanu suka riƙeta Gimbiyarsu zakaji tana yawan ambata maka Sarki Nasr da ɗansa.


Ubaid to itan ta kasance wani ɓangare na jikin Sarki Nasr sannan wani sashinta ya kasance sashina bawai ina nufin Hauwah ba mutum bace, a'a mutumce kamar kai amma bambam dakai ka zauna da ita domin zamanku tare shine maslaha ga rayuwarka.
Ubaid wa ne a gurinta a lissafinsu itan su biyu ne akwai Hauwah ƙanwar Ubaid an haifesu rana ɗaya da Auta saiya kasance komansu ɗaya ne kamarsu ɗaya ce basuda wani abu dazaisa ka gane ba mutum ɗaya bane, Adnan lkcn goyan Hauwah nasha ganin abun mamaki idan Yakumbonsu ta kwantar da ita a ɗaki sai naje na tarar ta zamemin biyu dana fara gani na tsorata daga baya dana fahimci Ni kaɗai nake gani sai nayi shiru na rinƙayi mata magani ashe ba rabuwa sukayi ba sundai barta a zahiri amma suna tare da ruhinta, domin Sarauniya Asiya ta tabbatar da biyu ta haifa aka ɗauke mata ɗaya akabar mata ɗaya to a bincikensu  ne suka gano wannan Hauwan tawa da Hauwa Kulu ta haifamin, shiyasa suketa ƙoƙarin karɓarta Ni kuma na tabbatar da wannan tawa ce nine nayi dalilin zuwanta duniya.
Zata zame maka garkuwa kuma kariya kayi mu'amalar aure da ita kamar yanda Yarima Ubaid ya baka dama kada kaji tsoro musulmi ne muddin bakai ka shiga gonarsu ba bazasu taɓa cutar dakai ba, ko kwanaki da kaga anata fama ba mahaɗin nata bane baƙine kafurai aka turosu su cutar da ita shiyasa gashi lkcn Ahlinta a cewarsu sunyi tafiya zuwa ziyarar kabarin Annabi  Sulaimanu"........
[1/30, 9:30 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB42-43_*

*_BONUS PAGE_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 200 VIP 500 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

____________________________________

Jinjinawa girman lamarin yayi tare da tunanin wannan wanne irin cukurkuɗaɗɗan al'amari ne me kama da almara? Tashi yayi ya fita ya shiga ɗakin Khairiyya ya isheta ta kwashe kayan data hatgitsa sai gwada ninkesu takeyi ta kasa yayi murmushi ya karɓa ya ninke yace mata “ki hutar da kanki a hankali zaki iya komai" dubansa tayi tace “Daddy Aunty fah" saida gabansa ya faɗi kafin ya samu abin faɗa mata yace “ta kwanta kuma sai zazzaɓi ya rufeta tanacan tasha magani ta koma bacci" murmushi tayi tace “Allah sarki My aunty Allah ya bata lfy" “Amin” ya amsa da ita sannan ya tashi yace “kinci abinci kuwa" girgiza masa kai tayi tace “aa ina jiran Aunty ne" saurin kallonta yayi yace “karki jirata kici abincinki zamu fita" amsawa tayi da “to" ya fice itakuma ta zauna karyawa zuciyarta cike da tausayin Auntynta.
Koda ya koma ɗakin har zuwa lkcn a kwance take tana baccinta baiyi ƙoƙarin tashinta ba ya shirya ya fita ya kira Khairiyya suka fice suka nufi cikin masallaci anan sukayi sallar juma'a suka yi duk abinda ya kamata suyi sannan suka juyo suka shiga gari yayima Amaryar tasa siyayya me yawan gaske musamman dogayen riguna da hijjabai da takalma fitinannun gaske suka isa masauki lkcn sa sukaje ta tashi harta lallaɓa tayi wanka daƙyar amma har zuwa lkcn jikinta ƙasanta mugun ciwo sukeyi.

Buɗe  ƙofar sukayi suka shigo da sallamarsu yayi saurin aje kayan hannunsa ya nufeta yace “Ya Allah Sannu My Bride ya jikin?" Zama tayi tana ɗora injin idanunta akansa Khairiyya tace.
“Aunty ashe bakida lfy ya jikin?" Amsawa tayi da cewa da sauƙi ƴata ya naki jikin I hope babu inda yake miki ciwo?" Jinjina mata kai tayi ta tsugunna ta kama hannunta tace “sai damuwar rashin lfyrki bansan bakida lfy ba sai ɗazun kafin mu tafi masallaci Daddy yake sanar dani”
Kallonta yayi ya kanne mata idanu tayi ƙasa da kanta wata muguwar kunyarsa takeji ya  zauna a gefenta ya kalli Khairiyya yace “kije ki huta daughter" miƙewa tayi tace “Ok Dad bye" ɗaga mata hannu yayi tana fita ya janyo Hauwah jikinsa yace “Subhanallah My Bride jikinki har yanzu da zafin zazzaɓi ga magunguna na samo miki kisha ki kwanta ki huta"

Saida ya ciyar da ita sannan ya bata magungunan tasha ya ɗauketa cak ya ɗorata gadon yace “ki huta sosai yanzun inane yakeyi miki ciwo?" Rintse idanunta tayi hawaye suka tsiraro mata tace “nan” tana nuna masa gabanta ta kuma cewa “ni...Ni inajin kamar ka ciremin wani abu a gurin ciwo zafi idan nasa hannu zan wanko har ihu nakeyi...."
Bata rufe bakinta ba saboda yanda taji ya zare  pant ɗinta yasa hannunsa ya buɗa fatar gurin yaga yanda yayi ja tsabar gurzar da yayi mata ta ba ƙaramin ƙoƙarinta ya gani ba data tsaya iyakar mitar a wauta irin tata bai taɓa tunanin anan haukanta zai tsaya ba.
Da wannan tunanin ya kwanta yasa hannunsa ya buɗa cinyoyinta sosai ya kamo ɗan tsakanta da lips ɗinsa tayi wani motsi me ƙarfi tanason ƙwacewa babu dama, ganin hakan yasashi sakinta ya rinƙa hura mata iskar bakinsa me ɗumi a gurin, nan ta sake baje masa ya rinƙa hurawa yana sanya hannunsa yana ɗan wasa da gefen cikin dabarar da bazata gane ba ta kuwa shagala sai ajiyar zuciya take saukewa taji bakinsa a ciki yana lasar gurin wani abin mamaki duk da jan da gurin yayi bai hanashi jiƙewa da ruwan ni'imarta ba ya sauke numfashi yanaci gaba da tsotsar gurin kamar ya samu lollipop.
Danna harshensa daya fara ne yasata janyewa da sauri tace “aa Excellency ka barni zan mutu wayyoh ka famamin ciwon zafi...." Miƙewa yayi ya zauna ya janyota jikinsa ya kifata yana shafa bayanta yace “so...sorry bansan haka ba ki daina kukan zaki dainajin zafin"


Da wannan kalamin ya rinƙa shafa bayanta yana rarrashinta hardai ya samu ta daina kukan bacci ma ya ɗauketa daidai lkcn wayarsa tayi ring ya ɗauka ganin sunan Hajiya Salmah yasashi karawa ta gaisheshi ya amsa tace “Alh ya kamata fah ka dawo kayi wani abu akan ɓatan yarinya nan yarinyar ta bace ɓat"
Ɗaga mata hannu yayi yace “ok naji saime kuma tunda kun kasa kada ku wani damu kanku faɗi buƙatar ki"
A kunyace tace “Dama inason zanje Dubai ne zan siyo abubuwan da banidasu sannan zan ƙarasa Qatar gurin Yaya Maryam mu ɗanyi zumunci" yasan dama bai wucce hakan ba yace “ok nawa kike buƙata?" Kwantar da murya tayi tace “da yake inason sai bayan sallah zan dawo kuma itama Hajiya Na'ilatu naji tana zataje China so idan kabamu 1.5 million ma kamar zai isa wanda bai isheshi ba saiya kara a aljihunsa"
“Ok” kawai yace ya ajiye wayar ya ɗauki ɗayar yayi yan dangwale²nsa ya kira wata number bugu ɗaya aka ɗaga da cewa “Allah ya taimakeka" batare da bawa abin muhimmanci ba yace “na turo maka sabon acct kasa 2 million a cikinsa na Hajiya Na'ilatu dana Salamatu ma kasa musu hakan" yana bada umarnin ya kashe wayar ya zame ya kwanta duk da cewar Magrib ta kawo jiki amma shima yanajin gajiya a gaɓoɓinsa shiyasa ya buƙaci kwanciyar

Janyota jikinsa yayi itan bacci takeyi shikam kallonta kawai yakeyi har  yaji an kira sallah ya miƙe ya fita ya nufi masallaci daga masallacin bai dawo ba ya shiga gari, sai dare sosai sannan ya dawo ya tarar su a ɗakin Khairiyya sunata hirarsu Hauwah tana yima Khairiyya kitso ya zauna ya shafa kan na Khairiyya yace “kinji sauƙi kenan tunda har kika iya kitso" murmushi tayi masa tayi masa sannu da dawowa ta miƙe tace “ki duba ki gani in yayi kibarshi in baiyi ba kuma ki tsefe sai a sake wani"
Shafa kan tayi tace “Wlh yamayi kyau ashe kin iya kitso shikenan Hajiya babba da Hajiya Salmah sun huta da zuwa kitso....." Da sauri ta dubeta tace “Hajiya babba Hajiya Salma?" Kawar dakai tayi da cewa “ok ki kwanta kiyi baccinki gobe mayi mgn" suna faɗin haka suka fice ya haɗeta da jikinsa yace “kinƙi ki zauna ki huta" shafa sajensa tayi tace “ya zanyi bazan iya zaman ba"

Kamata yayi ya kwantar da ita yace “nafiso naga kin kwanta kin huta banason wannan kaiwa da komowar" luf tayi masa ya shiga yayi wanka ya shafa mai ya kwanta a gefenta.
Yanajin shauƙin son ya nemi haƙƙinsa amma tausayinta ya hanashi da haka shima bacci ya ɗaukeshi.
Kwanansu takwas a Saudiyya aka ɗauki azumin watan Ramadan Alh Adnan kulawa ta musamman yake bawa Hauwah da Khairiyya inda hankalinsa ya tattara yanzun wajen rokon Allah ya sake azurtashi da ganin ƙwansa a duniya a wannan azumi kullum sai yayima Allah kirari da kuka na zucci dana fili akan wannan buƙata tasa inda itakuma Hauwah tausayinsa yasa  duk tayi laushi abubuwa da yawa ta gano na damuwa binne a rayuwarsa takanyi murmushi ita kaɗai tabbas ƙaddarar Alh Adnan da Khairiyya me ƙarfin gaske ce badon haka ba da tuni babu labarin su, yanzu wacce tasa a ma'auni itace Hajiya Na'ilatu tabbas akwai tsagwaron munafurci ha'inci da zamba cikin aminci a lamarinta Alh Adnan ya ɗauki yarda da amanar komai daya shafeshi ita kuma kullum neman hanyar ganin bayansa take haƙiƙa da gyara cikin lamarin rayuwar dole ta ɗaura ɗammarar yaƙar duk wani tuggu da ake shiryowa dama wanda yake binne a ƙarƙashin ƙasa wannan kenan.

_Manerge wlh yau kaina ya ɗau zafi da yawa bazan iya dogon typing ba mu haɗe tomorrow insha Allahu_.
[2/1, 11:45 AM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB44-45_*

*_BONUS AND ANNOUNCED_*

_Wannan Littafin daga yau 1/2/2022 ya koma asalin farashinsa daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 300 VIP 600 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

____________________________________

Saida akayi Eid fitr da kwanaki sannan suka fara shirin barin ƙasar Hauwah cike take da farin ciki gefe guda cike da tausayin Alh Adnan wata kusan biyu kenan tun ranar daya fara saninta har rana irin ta yanzu bai sake shigarta ba koda ma yayi ƙoƙarin hakan idan yaga tana kuka ta nuna masa damuwarta hƙr yakeyi ya rabu da ita, wannan abu ba ƙaramin kashe mata jiki yakeyi ba tabbas shiɗin daban ne a cikin mazan wannan zamanin da zuciyarsu kansu kawai ta sani takeso baya burin cusgunawa rayuwar wani ko kaɗan yafi yarda shi ya cutu zuciyar waninsa tayi haske.
Da wannan ta samu suka gama kwanakinsu suka ɗauko hanyar Nigeria zuciyar Alh Adnan data Khairiyya cike da zullumi tabbas akwai bayanai a bakin Khairiyya amma ta rasa meye yasa koda tayi yunƙurin furtawa bata iyawa haka dole take haɗiye duk wani batu dake ranta ta barshi tasan dai duk daɗewa wataran zata fasu amma tabbas rayuwar gdan mahaifinta abar dubawa ce tasgaro da kuskunda sunyi yawa a cikinta gashi ta fahimci kamar baya gane komai dake faruwa, abinda ta lura dashi ma duk cikin matansa babu wacce yaba amanna irin Na'ilatu.


Idan ta tuna wannan abu har hawaye take zubarwa a ɓoye Dad ɗinta yana ganin yayima rayuwa shiri baisan ya rufe ƙofa da ɓarayi ba don sunfi gaban ɓarawo ɗaya
Da wannan saƙe² a zuciyar kowa suka isa 9ja a Lagos suka fara sauka da nufin suyi kwanaki bakwai su huta, a nan ne kuma abubuwa suka fara canza yanayi wata rana da dare sun gama kallonsu Khairiyya ta tafi ɗakinta ta kwanta Alh Adnan ya matso kusada Hauwah ya sanya hannunsa ya shigar da ita jikinsa tare da rungumeta a jikinsa ya ɗora hannunsa a mararta, tasa hannu ta riƙe shi tare da kai dubanta ga hanyar ɗakin Khairiyya ta kalleshi ya kwantar mata da kai yace “kiyi wani abu My Bride inason agajinki wlh na ƙure hƙrna ya ƙare"
Lumshe idanunta tayi tanajin wani irin faɗuwar gaba ta kawar dakai ta yunƙura zata miƙe yayi saurin riƙota juyowar da zatayi yaga idanunta sunyi blue farin idanun ya koma gold take ya saketa da sauri ta nuna shi da yatsanta sai kuma tayi saurin kawarwa take wani baƙin hayaƙi daya keto ta saman gdan ya haɗu da wani blue na haske dake fita ta cikin idanunta da hannunta ya tarwatse nandanan hayaƙin ya riƙiɗe ya koma ja kamar jini ya ɓace ɓat.


Durƙushewa Hauwah tayi taci gaba da kallon hayaƙin tare da janye hannun data nuna gurin ta zauna a gurin tana jan zuciya tana kallon Alh Adnan inda shima ya zuba mata idanu da yanayi na mutuwar zaune ta matsa gabansa sosai har zuwa lkcn idanunta shuɗine tace “Yau wani dattijo fari gajere me baƙin gemu zaizo karɓar sadaka kada tausayi yasa ka bashi ba almajiri bane shaiɗani ne aka aikoshi zai karɓa yaje yakai a haɗa laƙanin da za'a nakastaka dashi, in kunne yaji jiki ya tsira"
Tana faɗin haka ta miƙe ta shige ɗakin da aka fara saukarta ta zauna a gefen gadon  kamar amsa mata Film tana kallo haka abubuwa suketa gudana a kwakwalwar ta ta sake miƙewa tana zagaye ɗakin tana cewa “Adnan Sooraj Ruƙayya Adnan Sooraj Rahman Adnan Sooraj....."
Wata dariya ta kece da ita me ƙarfin gaske da tasanya Alh Adnan miƙewa da azama ya nufo ɗakin sukayi karo da Khairiyya lkcn Hauwah ta miƙe tana zagaya ɗakin tanaci gaba da dariyarta.


Ganin Khairiyya yasata nufarta ta ɗago fuskar Khairiyya ta zuba idanunta cikin nata take wani haske fari ya fita a idanunta ya shiga idanun Khairiyya, take tayi baya zata faɗi da hannu ɗaya ta ɗagata ta ɗorata a gadon ta tsagaita da dariyar tace “Wani abu zai faru yau Hauwah zata samu cikin Rahman a daren goma sha takwas karka kuskura Hauwah tasan dashi zamu kareshi zamu tsareshi cikin kariyar ubangiji.
Yanda Muryar ke amsawa a parlourn saida jinin Alh Adnan ya kusa daskarewa fargabarsa ta nunku cikin kiɗima ya miƙe ya nufeta ganin tayi ƙasa da kanta ya riƙota yace “Hauwa'u ke Hauwah...." Ɗagowa yaga tayi tayi masa murmushi sai kuma yaga inuwar wata mace ta fita daga jikinta tayi gabas take jikinta ya saki ta zube bacci me nauyi ya dauketa, a yaci gaba da kiran sunanta a ɗarare gabansa yana luguden dakan taɓare daƙyar ya ɗagata ya shigar da ita ɗakinsu ranar dai bai samu abinda yakeso ba haka suka kwana cikin razani dagashi har Khairiyya da dariya da maganganun Hauwah suka sanyata shiga yanayi.

Washegari ta riga kowa tashi a gdan ta shiga bayi tayi wanka ta ƙyafe cikin wani lashi tayi kyau sosai ta shiga haɗa kayansu a akwati tana murmushi ya Kano suka kwana, farkawar da zaiyi yaganta ta gama haɗa komai nata a cikin akwatin ji tayi an dafata ta juyo ganinsa yasata ƙasa da kanta tace “Barka da tashi" murmushi yayi mata yace “kina haɗe kaya ina zaki?" Lumshe idanunta tayi tace “Idan inada sashi a gdanka ina buƙatar kabada umarnin a gyaramin yau zamu tafi Kano...."
Kallonta yayi da sauri tayi masa murmushi ta miƙe tace “karka tambayeni don Allah akwai dalili" daga haka ta miƙe ta fice a ɗakin ta nufi sashin Khairiyya ta buɗe ƙofar ta shiga ta tsaya jikin ƙofar tana kallon Khairiyya datake shiryawa cikin wani yadi tayi mata murmushi tace.
“Kina sane da alƙawarinmu ko?" Zan mayar dake yanda kike bazan rufe miki baki ba bazan zaunar dake dindindin ba amma kisani a idanun mutane babuke a mgn, a idanun mutane babuke a tafiya wannan shine hanyar da zamubi mu gane komai"

Tsugunnawa Khairiyya tayi tace “Don Allah Aunt...." Ɗaganta hannu tayi ta miƙe tace “Mafita nake nema miki" ficewa tayi ta dawo parlourn ta isheshi tsaye sai kaiwa da komowa yakeyi ta isa ta rungumeshi ta baya tace “Mijin Hau...."
Ɗagata yayi ya direta a kujerar ya tsugunna gabanta ya ɗora bakinsa a kuncinta ya sauke mata kiss me zafi ta lumshe idanunta ya haɗe bakinsu yana tsotsa da ƙwarewa suka sauke ajiyar zuciya tare.
Ta janye tana masa dariya ya kwantar da kansa yace “likitan rayuwar mijinta ki yima Allah ki bani dama...." Girgiza masa kai tayi tace “babu kyau kayimin magiya cikin abinda yake haƙƙinka nabaka damar kayi komai...." A gadon ta ida ƙarasa mgnr ya zubanta idanu yana mata murmushi me kashe jiki ta miƙe ta shige jikinsa ya haɗesu sosai yace “inyi komai?" Ɗagansa kai tayi yaja fasali ya sanya hannunsa ya zuge mata zip na rigarta ya sauketa a ƙasa ya zamar da ita ƙasa ta sauka Hauwah tayi murmushi ta ɗaga hannunta tayi miƙa hakan ya bashi damar sanya hannu ya fito da nononta ya riƙesu duka biyu a hannunsa yayi ƙasa da kansa ya ɗora bakinsa saman nipples nata ya lasa ta saki wata ajiyar zuciya me ƙarfi tace “Wash...." Batakai ga rufe bakinta ba taji ya saukar mata da wata muguwar kasala me cike da feeling me ƙarfi ta hanyar sanya nononta gabaɗaya a bakinsa yana musu wata munafukar tsotsa me kashe jiki"


Idanunta a rufe ta rinƙa janyewa har takai ƙarshe ta faɗa gadon ya bita da sauri kamar wani mayunwacin zaki ya sake cafkar nonon yanasha da ƙwarewa,
Daɗin yanayin yana ratsa duk wata gaɓa me rai a jikin Hauwah tanajin abun bashida mahaɗi. da sauri ta danna kansa a ƙirjinta lokacin da taji yana ƙoƙarin tashi da Muryar da batasan ya akayi ta ɗarsu ba tace masa “pl... Please karka...daina daɗ...."

Fasa cire bakinsa yayi akan nononta yaci gaba da shansu ya murza ɗayan da yatsunsa ɗaya hannunsa kuma ya tura shi cikin pant ɗinta yana wasa da gabanta.
Dukkansu jikinsu rawa yakeyi ta gaske an daɗe ba'a haɗu ba Alh Adnan ji yake kamar dick ɗinsa zata fashe saboda tsananin feel dake cinsa bazai iya jan wasannin da tsayi ba wannan tasashi kwance zanin jikinta ya zare mata komai ya zubawa gabanta idanu yanayin yankan gurin yana ɗaukar hankalinsa komanta me kyau ne, ji yayi yanason shan gabanta ya sanya bakinsa kuwa ya fara lasa da iyawarsa ya kuwa cireta a hayyaci baki ɗaya ya rinƙa tura harshensa yanashan ruwanta yana lumshe ido tare da sakin nishi me ƙarfi da kashe jiki.

Hauwah ta lula duniyar daɗi ta manta da wani abu wahala burinta kawai taji takai inda akeso akai kawai tajishi a samanta cikin rawar murya ya karanto addu'ar kusantar iyali ya fara shigarta yasan dole zataji zafi in taji kuma zata iya yi masa ihu shiyasa yaƙi bata dama ta hanyar haɗe bakinsu guri guda yanaji tana wani nishi me wuyar tana ƙoƙarin tureshi ta kasa sai kawai ta saka kuka lkcn daya samu damar shigarta gabaɗaya.
Dan dakatawa yayi yana kallon yanda idanunta ke zubar hawaye cikin dishewar murya yace mata.

“Af...wan Hauwah Da daɗi ohhhh" yana mgnr yaci gaba da cinta tana kuka na wahala don da gasken gaske takejin azabar yanayin shikuma yana nishi yana caccakarta yana kiran sunanta.
Matuƙa taji a jikinta kafin ya samu nutsuwa ya ɗagata yana sauke numfashi tare da sharce gumi ya kwanta a kusa da ita yaja musu bargo yace “I miss ur My Bride..." Zuciyar da tajace yasashi saurin kallonta ta, itanma buɗe idanunta tayi akansa ta ɗaga hannunta daƙyar ta ɗora a ƙirjinsa ya juyo yana facing nata hakan ya bata damar shigewa jikinsa tace “Zamu tafi?" Girgiza mata kai yayi badon taso hukuncin ba haka ta rabu dashi tanaji a ranta tunda taji tanason zuwan to saitaje,  akwai abinda takejin yana faruwa a can saboda haka zuwan shine maslaharsu.
Bacci ne me daɗi na samun abinda rai ke muradi ya ɗauke Alh Adnan bai farka ba sai biyu saura yayi miƙa tare da salati yakai dubansa inda Hauwah ke kwance babu ita ya miƙe da sauri yace “ohh God My Bride da kin bari nayi miki wankan...." Mamaki ne ya cikashi ganin bayin a bushe ya janyo da sauri ya zari gajeren wandonsa da doguwar riga ya saka ya fito yana ƙwala mata kira babu kowa a parlourn dole ya nufi ɗakin Khairiyya yana kiranta ta amsa tare da tashi daga kan sallayar ta nufo parlourn yace.

“Wai ina Hauwa'u ne?" Dubansa takeyi da rashin fahimta tace “ni tunda mukayi break na shiga ɗaki tabini mukayi mgn ai bata dawomin ba"
“What" ya furta da ƙarfi tare da nufar sashinsa yana ƙwala mata kira, baya yaja da sauri jin saƙo ya faɗo wayarsa ya zaro wayar a aljihunsa ya buɗe tare da muttsuke idanunsa yace “Tunda naji inason zuwa Kano nasan ba lau ba yanzu haka ina cikin ɓangarena na gdanka batare da kowa yasan ina ciki ba koda yake gdanma babu kowa idan zai yuwu a yau ka taho Kano zuwan naka yanada muhimmanci".......
Zamewa yayi ya zauna yace “Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un 11:30am mu kwanta dake Hauwah 1:30pm kicemin kina Kano a gdana keɗin wacce iri ce ne?" Jinjina kai Khairiyya tayi tace “Ko akan iska take tafiya banjin yaci ace taje Kano daga Lagos Dad ka kira su Hassan su shiga su duba su tabbatar idan batanan asan abinyi"
[2/1, 9:30 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB46-47_*

_Wannan Littafin ya koma farashinsa na asali ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 2
300 VIP 600 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

*_★Wannan shafin free ne ga kowa zaku iya share nasa dama duk wanda kukaha nasa Bonus a jikinsa★_*
____________________________________

Kallon kallo sukayi shida KHAIRIYYA lkcn da Hassan yake tabbatar masa ya shiga sashin nata ya tarar da ita a falo harma ta bashi dubu goma ya haɗo mata take away.
Bai samu damar kashe wayar ba saima subcewa da tayi yace “ya hayyu ya ƙayyumu bi rahmatika astagisu subhanallah subhanallah subhanallah" zama Khairiyya tayi kusa dashi ta dafashi tace “dole mu bita Dad rashin tafiyarmu yau zai iya haifar da matsala ita kaɗai ce a gdan ance su Hajiya babba basu dawo ba Hajiya Salma ma kuma bata dawo ba...." Bai gamajin abinda takeson ganar dashi ba ya mike ya nufi ɗakinsa har yana tuntuɓe.

Ko wanka bai iya yi ba ya saɓi jakarsa ya fito yace da Khairiyya “Ruƙayya muje" Jibril ne ya kaisu airport jirgin exprass suka hau zuwa Kano babu ɓata lkc suka isa bazai iya jiran motar gda yazo ta ɗauke shi ba hakan yasa suka ɗauki shatar mota zuwa gida har cikin gdan suka shiga yayi parking Khairiyya ta yunƙura zata miƙe taji kamar an ɗaureta ta saki ƙara basai bakin ma ya kuma dabarbarcewa ba, tanason mgn maganar ta gagara.
Sai sabarta Alh Adnan yayi suka fice daga motar ya shiga gdan bai take burki ba saida ya shiga sashin Hauwah ya tarar da ita tanata kaiwa da komowa dafata yayi ta juyo yaja numfashi ya rungumeta yace “Hauwah kin wahalar da zuciyata sosai" murmushi tayi ta shige jikinsa tace “kasan me?"


Wani aikine dani na gaggawa da bazan iya jiran dawowarmu ba yallaɓai idan bazai zama damuwa ba inason kayimin jagora zuwa wani sashi na gdannan, idan kuma hakan bazai samu ba to kabani damar shigo da dakaruna gdanka suyimin aikin" da sauri yace “aa inane muje na rakaki banson dakarun nan naki a gdannan"
Murmushi tayi ta kaɗa masa yatsa tace “ko baka basu dama ba Indai ina guri to ina tare dasu" bai bata amsaba tajashi sukaje har ƙofar sashin Hajiya Na'ilatu.
Nuna masa sashin tayi tace nan nakeso ka bani damar shiga" dubanta yayi tace “yeah haka nake buƙata" Juyawa tayi ta kira Khairiyya kira ɗaya sai gata ta fito da ƙafafunta Alh Adnan yaso ya musa shiga sashin na Hajiya Na'ilatu Khairiyya tace “Ka bata dama Dad inajin kamar abune me muhimmanci yasa takeson shiga sashin"

Saida ya jinjina abun ganin yanata janjamawa yasa Hauwah juyawa tace “na fasa kawai muje..." Tana faɗin haka ta juya ta haye samanta ta kwanta saman gadon ta ɗora kanta a hannunta tana maimata “Tsafi zuciya? Kurtun jini??" Firgigit tayi ta tashi zaune ta nuna bango da hannunta tare da nuna ƙofar ɗakin da ɗayan hannunta key ɗin ƙofar ya shiga ta sake duban bangon tace “Ya shugaba na ina neman sahalewar wani aiki gareka a bani aron Ɗan'uwana Ubaid da ƴar'uwata Zuwa yimin wani aiki sannan inason a bincikomin inda Na'ilatu take cikin 2 minutes but kada ya wucce haka"
Jinjina mata hannu yayi yayi mata murmushi yace “babu abinda zai gagara yake ɗiyata yanzu ɗan uwanki zai bayyana gareki Ƴar'uwarki ce bata tare damu ki kirata ta zoben dake hannunki zataji tunaninki cikin tunaninta nabaku damar shiga zuciyar juna"


Lumshe idanunta tayi tayi ƙasa da kanta ta shafe hoton da hannunta ta koma ta kwanta bata gama kwanciyar ba taga Haske ya keto rufin ɗakin ya shigo ta miƙe ya rusuna itama ta rusuna ya dafa kanta yace “Amincin Allah ya tabbata ga ƴar'uwata shugabata Gimbiyarmu meye dalilin kiran" murmushi tayi ta tashi zaune ta riƙe hannunsa suka bayyana ɗakin Na'ilatu tace “meye ke faruwa a ɗakinnan naji zuciyata bata gasƙata lamarinsa ba inason sanin komai kafin komai"
Bin ɗakin yayi da kallo tare da rintse idanunsa ya buɗe yace “ya kasance akwai wasu manyan sihirce² guda biyu masu jiɓi da mijinku Ƙanwata abubuwa zasu faru a lulluɓe cikin kwanakin nan tabbas mijinku kansa na cikin tukunya bazai gane komai ba sai kin ganar dashi, zaki gane komai a cikin komai....."


Hannunsa yakai ya jikin gadon take gadon yayi sama ya tsaya bisa iska ya durƙusa ya ɗora hannunsa saman wani tiles, tiles din ya fita ya mika hannunsa wani itace ya faɗo ya haƙa rami saiga wani kurtu lulluɓe da wata fata  ya sake sanya hannunsa ya zaro wani hoto ɗaure a cikin leda da wasu layu anyi cancel na hoton da jan jini.
Miƙewa yayi ya tura tiles din ya haɗe kamar ba'a taɓa buɗe shi ba ya sauke gadon ya juyo ya dubeta ya buɗe wannan kurtu, zaro idanu tayi.

Tace “Ruɓaɓɓen jini...." Murmushi yayi yace “jinin Ruƙayya ne da aka sadaukar shekaru sha shidda baya lkcn haihuwar Khairiyya wannan jinin a cikinsa aka sanya lalurar dake damun Khairiyya zakiyi mata taimako taji sauƙi ta taka amma Indai ba'a lalata wannan tsafin ba to bazata taɓa samun dawwamar lfy ba" hoton cikin wannan kwalba ya fito dashi ya ware yace wannan itace ruƙayya ta riga ta rigaya bayan ita kece mace ta biyu da kika samu gurbin gaske a zuciyar Adnan kuma yanzu haka kece target ɗin Na'ilatu na huɗu kece mace ta huɗu da takeson ganin bayanki idan kinason ganin sauran matan data kashe zan nuna miki su" jinjina kai tayi tace “Zai yuwu rayayye ya kashe rayayye?" Dafata yayi suka fice daga ɗakin sai gasu a bayan gdan ya dafa wani guri saiga kurtuna guda biyu a hannunsa kowanne da kwalbar sihiri da hoto a cikinsa ya zaro hotunan yace “wannan itace Maryam an haukatata ta fita mota ta markaɗeta a zahiri amma a baɗini sadaukar da jininta akayi, wannan kuma Amina kenan itama shayar da jininta a zuwan ɓarayi sunyi mata yankan rago.


Wata irin lugude ƙirjinta yakeyi tsoro ya bayyana akan fuskarta tace “Ya zanyi Ubaid?" Dafata yayi suka koma ɗakinta ya rusuna gareta yace “Allah ne mafi sanin daidai Ƙanwata amma munada tabbacin babu abinda zai sameki a wannan gda Mai Martaba ya ƙara tsaro akanki domin cimma burinsa sannan yau cikin bacci zamu bawa Khairiyya damar samun tsaro itama duk da cewar tsarinta zai zama tsarone daga ranar da wani abu ya faru ki zama cikin nasara ƙanwata zan tafi da wannan abubuwan haɗuwa ta gaba zamu tono wani abun shima zai baki mamaki"
Ɓat ya ɓace ta daina ganinsa taja ƙafarta ta zauna a gefen gadon tana jujjuya girman lamarin tabbas duk yanda take tunanin jumurɗar gidannan ta wucce haka ashe akwai ƙalubale gabanta.
Hannunta ta kai dubanta wani zoben azurfa ya bayyana a yatsanta ta murzashi a hannunta ta lumshe idanunta tace “Allah ne mafi sanin daidai Ƴar'uwata inaji a jikina kina cikin aminci" murmushi tayi tare da bayyana jikin zoben abun ban mamaki komai na jikinta irin na Hauwah ne kamarsu komansu hatta kayan jikinsu ta lumshe idanu kamar Hauwah tace “Wani ɓangaren lfy Uktee Ya mijinki?" Murmushi tayi mata tace “bani da ƙarfin gwiwa sanya hannunku cikin lamura na keda Akhee Ubaid shine sirrin nasarata ta, yanzu ya gamamin nasa aikin a cikin Hadiman dake ƙarƙashin ki inason kibawa wasu cikinsu umarnin bin kishiyata Na'ilatu China su hargitsa mata lissafi su fusato zuciyarta ta dawo ƙasar nan inason fara aiwatar da nufina akanta, Uktee ta daɗe tana zalumci, sannan inason bayani akan Salmah meye shirinta meye gudummawarta a lalacewar gidannan?"
[2/7, 5:55 PM] Oum Hairan&Affan: *_THDGOVB48-49_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 300 VIP 600 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

____________________________________

Zuba mata idanu Hauwah Aljana tayi tana Girgiza kai can tayi murmushi tace “zamu iya Uktee amma akwai wahala mu Bama tsafi ita tsafi take tabbas saimun kai kusanci ga Ubangijin Annabi Sulaimanu sannan zamu cimma nasara, karki damu da duk abinda za'a faɗa a kanki tuhuma zata rinƙa dawowa kanki kasancewar kin bayyana musu kanki komai ya faru zai zamana kece farkon tuhuma kada ki damu ki sanya a ranki sirrin nasara ce, yanzu dai buɗe hannunki Hadimai sun isa gareta a cikin tafin hannunki zakiganta ki ɗauki ƙaramin mashin iko ki caki zuciyarta take hankalinta zaiyo gda a hau zuwa safiya saita dawo in kuwa bata dawo ba bazata kasance cikin salama ba"
Jinjina kai tayi ta buɗe hannunta na dama ta zubansa idanu take ƙwayar idanunta suka koma ƙananu sukayi kore wani jan haske ya fito ya sauka a hannunta take saiga Na'ilatu ta bayyana a cikin tafin hannun nata ta fito daga wanka ɗaure da towel ta ɗauki wata kwalba da wani jan abu a ciki kamar jini ta buɗe ta ɗauko wata fata ta ware garin magani ya bayyana baƙi ta ɗiba ta tsiyayo wannan jan abun ta haɗesu ta gwamutsa ta lakata ta sunkuya zatayi matsi dashi Hauwah tayi saurin nunata da yatsanta tace “da sunan Allah Mashin daraja" take haske ya daki wannan kwalba ta subce a hannun Na'ilatu ta faɗi ta tarwatse garin maganin ya kama hayaƙi.


Abinda ya sanya na'ilatu saurin miƙewa tace “Wayyo...." Kallon juna sukayi tsakanin Hauwah bil adam da Hauwah Ruhaniya Hauwah Ruhaniya ta jinjinawa Hauwah kai tare da nuna mata ƙirjin Hajiya Na'ilatu ta ɗaga hannunta ta lumshe idanunta tana karanta wasu addu'o'i take wani haske fari ya keto ta sama ya dunƙule ya zama wani kyakkyawan mashi ya sauka a hannun Hauwah.
Miƙewa tayi ta nuna Hajiya Na'ilatu take mashin yayi tsalle ya fice a guje suna kallonsa yana katantawa yana keta gudun haske cikin 30 seconds sai gashi a tafin hannun Hauwah ya caki ƙirjin Hajiya Na'ilatu,
Ya ɓace ɓat sai gashi ya bayyana a ɗakin hannun Hauwah, ta dunƙule hannunta ta buɗe majigin rayuwar Na'ilatu ya ɓace sai kuma Salma ta bayyana.

Zabura tayi ta miƙe tana matso da hannun tace “Ya Allah Uktee zo kiga" Girgiza kai Hauwah Ruhaniya tayi tace “bana kallon ƙazanta wannan itace tata gudummawar da take badawa itan ta kasance manemiyar maza ce kuma tanayi ne don ta samo ciki ta kawoshi matsayin na Adnan ƴarta ɗaya Sameemah tayi duk me yuwuwa taga ta samu ciki abin ya faskara ƙarshe likitanta ya tabbatar mata mahaifarta ba cikine bazata ɗauka ba ƙwan Alh Adnan ne bazai taɓa zama a mahaifar kowacce mace ba ya riga ya lalace koda maniyyinsa zai fita a tsinke yake zuwa bashida wani tasirin samar da abinda ake buƙata, wannan ne yasa ta ƙudurce zatayo ciki a waje ta kawo gdan kuma zatayo ɗin koda ta kawo kada ki kuskura kiyi abinda zata fahimci kinsan wani abu dakanmu zamu tone komai"

Jinjina kai tayi ta koma ta zauna sukayi sallama daidai lkcn da Taji ana taɓa ƙofarta ta miƙe ta buɗe idanunta ya shiga cikin nasa ya tako ya shigo cikin ɗakin ya zubanta idanu ta baya yace “Fushi kikayi da ƙin amincewata da shigarki sashin Na'ilatu ko?"
Juyowa tayi ta zuba dara²n idanunta kansa tayi masa wani murmushi me kashe jiki ta tako gabansa tana rangaji ta tana cewa “Allah sarki abin tausayi bil'adam baisan komai akan rayuwarsa ba sai abinda ya bayyana gareshi, Excellency koda na nemi sahalewarka a shiga sashin matarka bawai yana nufin bazan iya shiga ɗin bane saika sahale kawai yardar taka na nema bisa tsari da al'ada so ban samu wannan damar ba hakan yasa nayi abinda ya dace, Ni yanzu Bama ta wannan nakeyi ba kawai inason kusanci da mijina ne shiyasa na buɗe maka am kafin nan Hajiya Na'ilatu zata dawo jibi ka shirya tarbarta da soyayya da kulawa Ni kuma na tanadar mata kyawawan mamaki na burgewa zan bata mamakin daya girmi mamaki...."

Bata bashi damar cewa wani abuba ta shige jikinsa ta sanya hannunta ta riƙe kugunsa tana wani narkewa a jikinsa ya haɗiye yawu tare da ɗago kanta ta sanya bakinta a dokin wuyansa ta lasa ya sauke ajiyar zuciya me ƙarfi yanajin yanda take yawo da harshenta a wuyansa zuwa kunnensa zuwa saman kuncinsa.
Zubewa sukayi a saman resting chair ɗin dake bayansu ta mirginashi ƙasa ta haye samansa tana wata kwarkwasa dake ƙara tsinka masa jinin jiki, yanaji ta zare masa
Rigar jikinsa ta ɗora harshenta saman nipples ɗinsa ta lasa ya lumshe idanunsa ta kuma sanya lips ɗinta tana wasa da nipples ɗin nasa me cikakkiyar tsoka me ɗaukar hankali, yanda take sarrafa nipples ɗinsa take fitar dashi hayyaci yayi bala'in bashi mamaki tunda suke tare bata taɓa sakewa ta nuna masa iyawarta ba sai yau ashe dai da gaske ne duk mace gwana ce saidai idan bata samu dama ba.

Bai ƙara rikicewa da lamarinta ba saida yaji hannunta cikin wandonsa ta tattare komansa ta haɗe a tafin hannunta tana mulmula twins ɗinsa zuwa jijiyar data haɗasu da Penis ɗinsa aikuwa tuni ya rikice ya fice a hayyacinsa yana ƙoƙarin ɗagawa ya mayar dasu gadon ita kuma ta haɗe bakinta da Joystick nasa ya saki wata siririyar ƙara daidai lkcn da Hajiya Salmah ta hauro saman taji shishinsa yana cewa “Ohhhh Hauwah zaki kasheni da daɗinnan ki cini da kanki ahhhh huuuu"
Cikin faɗuwar gaba ta sake matsar ƙofar ta kuma kara kunnenta can ƙasa taji Muryar mace na cewa “na cire kashamin breast ɗina sannan...." Shiru taji can taji sun saki ƙara a tare nan tayi yunƙurin buɗe ƙofar gabanta na sake dokawa tunaninta sam yaƙi hasaso mata komai sai ji da takeyi a ranta Alh karuwai ya fara bi ya samu gda babu kowa ya baje kolin sa bai taɓa tunanin dawowarta yau ba shiyasa harda shigo da karuwa yana cinta a gdansu.

Kasa zaune tayi bare tsaye zuciyarta na tafasa wannan abu da ƙunci da baƙanta rai tunaninta yaushe ne Alh Adnan ya fara niman matan banza?
Bata da amsa bata dame bata hakance ta sanyata neman guri ta zauna zuciyarta na kunci, wai wanzami baison jarfa inji hausawa, sukuwa sun jima suna more juna saida suka samu nutsuwa suka kwanta rungume da juna yana shafa kanta zuwa tsakiyar bayanta yana kissing nata lkc zuwa lkc yana sanya mata albarka saida suka huta sosai sannan sukayi wanka suka fito yana riƙe da ƙugunta ta kwanta luf a jikinsa suka buɗe ƙofar suka nufi parlourn.


Turus sukaja suka tsaya Alh Adnan ya haɗiye mamakinsa yace “Aa ikon Allah Salamatu yaushe kuma kika dawo ya kika canza shawara?"
Wani kallo tayi masa irin na ka fusatani ɗinnan tace “yaushe dama zakayi murnar dawowata tunda ka shafe idanunka da attaruhu ka shirya cin mutuncinmu Alh Meye ribarka da girmanka da komai me zaka samu a gurin wannan tatsitsiyar yarinyar ƙaramar karuwa da har ka ɗaukota ka kawo mana ita gdanmu....."
Dakatar da ita yayi saurin yi yace “banason maganar banza Salamatu Ni ba yaro bane abinda banyishi da ƙuruciya ba ba zanyisa yanzu ba Hauwah ba karuwa bace matata ce ta sunnah kamar ke kamar Na'ilatu karki kuma ce mata karuwa nine na rareta kinganta nan bata wucce sa'ar yarki Sajida ba"
*_THDGOVB 50_*

*_END PART ONE_*

_This book is paid ki daure ki biyani haƙƙina kafin ki karanta min Nrml 300 VIP 600 SP 1k, game buƙata zaku tura kuɗinku tanan  acct details  3184512451 First Bank or 0255526235 GTbank ko hoton kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 kuma ƴan Niger masu son wannan littafi zaku tuntuɓi wannan number don biyan kuɗinku +227 95 04 58 22, Na rantse da Allah Sarkin da ya hanemu zalumci bazan yafe mawa duk wanda ya karantamin littafi batare daya biyani haƙƙina ba._

____________________________________

Wani murmushi Hauwah tayi me ɗauke da ma'anoni ta taka cikin takunta na isa ta matsa kusa da Hajiya Salmah ta dafata tace “Cld down Matar mijina sha ruwan sanyi ba abinda kike tunani bani nima matace kamar ku ina fatan kin dawo lfy i hope hanya bata wahalar dake ba"
Wani malolon kishi baƙin ciki da tsananin tsana ne ya tokare Hajiya Salma game da Hauwah ta rinƙa kallonta kallon wulaƙanci wai kishiyarta wannan ƴar jaririyar itane kishiyar ta? Daƙyar ta haɗiye abinda takeji tayi yaƙe me ciwo tace “Ai dake bamu sanki ba ko a hoto shiyasa abin yazomin a bazata kiyi hƙr kinsan halin kishinmu na mata musamman dake mazan na zamani basuda tabbas" yanda Hauwah ta kafeta da idanu yasata jin wata faɗuwar gaba ta juya da sauri ta nufi ɗakinta.
Dubansa Hauwah tayi tayi masa murmushin da yake kashe masa jiki tace “Fatan nasara mijina Allah ya isar maka ya shige maka gaba"
Jinjina mata hannu yayi ta juya ta shige sashinta ta kullo zuciyarta wasai gefe kuma tana jiran dawowar Hajiya Na'ilatu taga ita kuma irin nata takun.

Tananan kwance har wajen uku sannan ta tashi ta fita ta nufi ɗakin Khairiyya ta isheta zaune tana kallon wani series na India ta zauna a gefenta ta ɗago suka kalli juna ta motsa bakinta zatayi mgn Hauwah tayi saurin dakatar da ita da cewa “Nasan me zakice lkc baiyi ba Ruƙayya, Hajiya Salmah ta dawo banason cewarki daga yau ki mayar da kanki kurma a gabansu kada ki ƙara furuci sannan kada ki ƙara miƙewa madamar kinsan zasu iya shigowa da'irarki Sarki Nasr yace zai sanya tsaro a sashinki domin samamin sauƙin aikin dake gabana amma tsaronki bazai zama tsaro ba dole saida abu ɗaya to abin ne na kasa gane menene"


Tashi tayi ta matsa gaban madubi ta zubansa idanu tana kallon Khairiyya ta ciki tace “koma menene lkc zaiyi sa ina jiran bayyanarsa Amma fah bayan tiya akwai wata caca Dad ɗinki yanada wani boyayyar nasaba da  wasu jinsi na aljanu masu masu basa kariya wanda shigowata rayuwarsa yasa sunyi nesa dashi domin sun sanar da Sarki Yusufa cewa bazasu iya rayuwa inuwa ɗaya da Zuriyar Sarki Nasr ba" juyowa tayi tace “tabbas sunyi gaskiya ba kowanne jinsi ne wannan ahli yake kusantarsu su iya rayuwa a sashin ba saidai akwai wani gardamamme ɗaya da yake neman wasa da rayuwarsa yayi furucin da iska ta ɗebo ta kawomin cewar muddin yana rayuwa a doron duniya burin Zuriyar Sarki Nasr bazai cika ba na samar da cakuɗaɗɗen jinsi a doron ƙasa ba damuwarsa Ni ɗin ba domin nima bansan ya akayi na samu a haka ba amma wata jumurɗa dake rubuce cikin ɓoyayyen kundin sirrin mahaifina zata bayyana min komai yanzu babbar damuwata banida damar ɗauko wannan kundi Ni kaɗai dole saida taimakon amintaccen bani adama wanda shaiɗani bai taɓa huda jikinsa ba kuma wanda zuciyarsa ta rayu da son kasancewa dani babbar matsalar itace, a duniyata mutum ɗaya ne na taɓa rayuwar fansar da farin ciki dashi kuma shiɗin ya kasance muradin rai wanda mahaifinki ya zama sila ta rabuwata dashi Khairiyya shi ɗaya ne nakeda tabbacin bashida kafar shaiɗan a jikinsa kuma zan sanyasa yayi in har ya samu damar ɗauko Kundin to tayaya zamu karɓesa?"


Shiru ta ɗan ratsa na tsayin lkc kafin ta ɗago zatayi mgn tace “Dad ɗina ya taɓa ganinsa?" Girgiza kai tayi Khairiyya tayi murmushi tace “dama ta farko zamu kawoshi gdannan a matsayin malamin da zaike yimin lesson ko kuma mu kawoshi matsayin ma'aikaci ko kuku tunda kukunmu ya tafi garinsu, dama ta biyu kuma wacce zatafi daɗewa munajan zarenmu har zuwa ranar da muradi zai cika itace, zamu kawoshi a matsayin mai maganin da aka haƙiƙance shine kawai zai iya warkar da ciwona baki ɗaya idan har wannan motion ɗin ya karɓu to kece zaki fara aikin Ni kuma zan tayaki sannan zamu takurawa Dad da muradinmu nason Malamin ya kasance a gidannan kinga hakan zai samar da kusancin da komai zai samu damar yiwuwa cikin sauƙi to amma ke kina ganin zai amince?"


Jinjina kai tayi tace “zai iya amincewa amma ba lallai bane gwaji shine zai tabbatar da hakan mu gwada mu ga ya hatimin nasarar mu zai kasance...."
Katse tattaunawar sukayi lkcn da zobenta ya fara fitar da wani haske ta durƙushe gwiwowinta a ƙasa ta shafa zoben wani haske ya fita a jiki ya naɗe bangon ɗakin take wani daji ya bayyana suka zubawa gurin idanu can sukaji murya me taushi tace “assalamu alaiki ya Bint Kin kasance me takar nasara da dafawata cikin rayuwarki amma ki sani kamar yanda kika zayyanawa wannan hadima da muka ƙara samu aikinku yana da wahala nasararsa abace ta ƙila wa ƙala ko a dace ko a faɗi abu mafi dacewa shine sanin nisan tafiyar da zakuyi don ɗauko wannan kundi da tasirin sarrafashi yake hannun mahaifinki tafiya ce ta shekara goma sha biyar daga duniyarku ta bil adam zuwa wannan daji dana haska miki cikin sahalewa da yassarewar ƙarfin iko da buwayar mu zamu mayar da ita ta wata biyu, ba zuwanne me wahala ba samun mukullin buɗe wannan ɗaki shine zai zama me wahala dole sai yaudara da cin amana sun shigo cikin aikin kafin biyan buƙata hakane zaki yaudari mijinki da cewar bakida lfy  rashin lfyr da dole saiya kaiki gda kuma sai kinyi yin gaske ta yanda Mal Aliyu zai ƙara baki damar shiga ɗakinsa to anan ne zaki samu damar ɗauko wannan Makullin idan kin ɗauko to muma munada damar shiga cikin lamarin zamu baki damar isa wannan guri domin ɗauko wannan kundi shima kuma kundin bazaki iya daukarsa ba dole sai kinyi amfani da Nabeel babbar damuwar bayan kin yaudari mijinki kin ha'inci mahaifinki sannan sai kin zama silar salwantar rayuwar masoyinki domin samawa rayuwar mijinki salama da kwanciyar hankali"

Miƙewa tayi da sauri tanaja da baya idanunta na kawo ruwa tace “bawai zanyi jayayya bane Ya shugabana amma wannan aikin abarshi bazan iyaba bazan iya aitaka zunubi biyu na ukunsu mafi muni ba, Inason Nabeel na barshi ne da bakina ban barshi da zuciyata ba, inasonsa bazan iya zama silar rabashi da rayuwarsa ba"
Murmushi yayi ya nunata da yatsa yace “dolene Hauwa'u tunda na buɗe miki hanyar dole kibita farko ku fara sanin yanda zakuyi ku janyo Nabeel a jikinku sannan inayi miki albishir da shigar ciki a yau ɗin nan kula dashi yana wajibi akanmu domin mune mukeda ikon kula dashi ke da mijinki bazaku iyaba rikicin akan wannan jaririn ne"...........


_Tabbas rikicin yanzu zai fara waye ba waye ba? Zaku fahimci komai a part 2 na wannan labarin wannan shine ƙarshen part 1_

*OUM HAIRAN*

No comments