Breaking News

Babban Yaro Boo 3 Complete Hausa Novel

 [12/3, 9:02 AM] .: *BABBAN YARO*



*MALLAKAR BINTA UMAR*




*71*



Daurewa kawai yayi ya karasa kusa dasu cikin yanayin tafiyar sa ta jarumin namiji, baby Aysha ya dauke daga jikinta kawai ya fuce daga dakin. Kallo granny tabi shi dashi itanan ta kira shi ne tayi musu fada shi da Asma'u gashi ya futa, cigaba da rarrashin Asma'u tayi kusan mintuna ashirin tukkuna ta futa daga dakin, parlor ta same shi ya tasa baby a gaba yana kallo. Tace"Kai da zaka rarrashe ta kuma sai ka dauko 'yar ka ka futo Asma'u tana bukatar Dan rarrashi." Da Jan ido ya kalleta yace." Granny nima Neman Wanda zai rarrashe ni nake domin bata fini jin ciwo ba." Tace"Ai kai namiji ne kana da jarumta ita kuwa macace don Allah ka rike yarinyar nan amana k'ato kar ka hofintar da ita zakaji dadin zama da ita domin jikina na bani akwai alkairi a auran Ku da ita."



    Shuru yayi kawai ta cigaba da cewa a yanzu tana cikin damuwa saboda haka duk wani bori da zata yi maka kayi hakuri kar ka biye mata domin an shiga hakkin ta ne.... Ranshi a Dan bace yace." Granny wato ni ba a shiga nawa hakkin ba kenan? Hararasa tayi zata yi magana ya katse da sauri yace." Nifa bani nace ina son ta ba domin ni yanzu babu maganar aure a tsarina, gaskiya amma dai tunda kun kulla Allah ya sanya alkairi, amma kiyi mata fada sosai duk wasu halayen ta da nasa ni a da to ta sauke su domun bazan zauna da ita dasu ba."



   Granny tace." Insha Allahu zaka ji dadin zama da ita kuma zan ja mata kunne da kyau kai dai ka zama namjin duniya a gidan ka." Shiru yayi mata ita kuma ta cigaba da yi masa fada har sanda Jahid ya shigo, ya same su. Kusa da Amjad din ya zauna yana fadin "Ya zamu yi ne gasu Khalid can sun shirya walima kamar yanda aka saba sai ka kimtsa bayan sallahr magariba zamu fita." Gyada kansa kurrum yayi Jahid din yaji babu dad'i yace." My friend nasan nayi maka katsalandan cikin rayuwar ka amma ina me baka hakuri don Allah idan hakan bai maka dad'i ba, hak'ika banaso in rasa Asma'u saboda kyawawan haleyen ta tunda Allah ya kaddara cewa ba matata bace shine nayi maka sha'awar auran ta ko don baby nasan gaba zaka ji dadin wannan abun insha Allah kayi hakuri ka sasssutawa zuciyar ka idan ka saki ranka na tabbata itama Asma'u zata saki nata Ku zauna lafiya.



    Amjad ya dafa kafadunsa cin kyakyawan lafazi yace"Jahid babu abunda zance maka wallahi sai dai fatan gamawa lafiya ka nuns min kulawa a rayuwata babu shakka zan karb'i Asma'u saboda kai zan rike ta amana dalilin ka, insha Allah." Jahid yaji dad'i sosai hannu ya bashi suka yi musabaha kana ya mike yana fadin bari inje in sanya a kara gyara guri yanzu." Amjad din yace." Zan fito Yanzu insha Allah. "



Granny ma mik'e wa tayi ta nufi kicin gurin Iyami dake had'a abunci na tarb'ar amarya nan granny ta sanya mata hannu suna yi suna hira da yadda abun ya faru har suka kammala tsaf Iyami ta fito ta gyara daining lokacin Amjad ya tashi daga gurin yana bedroom d'insa shi da baby Aysha da take was an ta kan bed din sa, wanka ya fito daure da towel ya tsane jikin sa tsaf gaban dressing mirror ya tsaya ya gyara sumar kanshi hade da shafe ta da Maya mayai masu asalin tsada jikinsa ya shafe da turare kana ya shafa mai sama-sama , wardrobe din shi ya bude ya dauko sabbin kaya cikin ledar su, yadin plitex ne blue black dark yana da taushi sosai sngjilet ya sanya fara kal kana ya Dora rigar a kai wacce ta sakko masa har kasa din ki Muhammad Abacha kenan tsaf ya gyara links ya d'aura a gogon shi Dan Asali turare ya fesa a jikinsa. Ya aje inda yake zuciyarsa na tuno masa shararran k'amshin Asma'u Wanda yake kwadayin sake jin shi, amma ya lura kamar yarinyar da rigima ta shigo gidan dole ya kiyaye kar ta raina shi, zai yi kokari gurin ganin bai shiga harkar ta ba, baby ya gani na kokarin saukowa daga bed yayi saurin d'aukar ta yana fadin"Kin fiye kiriniya Momy sai kinje kin fad'i ko." Dariya take bangala masa tana wasa da kwantaccan sajan sa dake shek'i, haka suka futo parlor shi da baby suna dariya.


Granny ya samu zaune cikin kujera zaune ta k'urawa TV ido yana futowa tace"Yawwa dama kai nake jira ka futo ka shiga gurin Asma'u nayi-nayi ta fito taci abunci taki kaje ka rarrashe ta." Zama yayi cikin kujera ba tare da ya bawa maganar ta muhimanci ba yace." Ba sai ki k'yaleta ba cikin ta ne idan taji yunwa zata futo taci." A"a baza ayi haka ba ka shiga dai ga lallab'ata. " Cikin mamaki yake kallon Granny yayi 'yar dariya hade da Sosa kansa yace." Granny ni baza ki rarrashe ni inci abunci ba sai wata daban ni kike sawa ma in rarrashe ta alhalin nima Neman Wanda zai rarrashe ni nake ni babu inda zanje idan ta gadama ta futo taci kanta tayiwa." Bata fuska granny tayi tace"Bana son gaddama yarinyar nan amana ce a gurin mu bana son abunda zai kuntata mata da wanne zata ji." Shiru yayi ganin ranta ya b'aci sai ya zab'a baby a kafad'a suka shiga dakin da Asma'u take. 


    Ina kwance har yanzu ina sak'awa da kwance wa naji an turo kofar dakin an shigo tun kafin in d'ago kaina naji k'amshin turaran sa rintse idon nayi da sauri Sam! Bana son mu hada ido dashi. Idonshi a kanta har ya k'araso gurin, baby ta dinga zillo wai ya sauke ta, yana aje ta ta fara kokarin hawa bed din da kansa ya d'ora ta jikin Asma'u dake kwance rif da ciki. Hucin numfashin sa naji a dai-dai wuyana, tsigar jikina ta mike k'amshin sa duk ya baibaye ni. Gabana fad'uwa kawai yake. Shima nashi b'angaran hakan yake domin wata irin sha'awar ta ce ta bijiro masa mai zafin gaske. Yanayin kwanciyar da tayi ya ya sanya shi cikin halin k'aka ni kayi...... Gyaran murya yayi had'e da had'e fuskar sa sosai ya ambaci sunan ta sama-sama." Asma'u.'!! Yarrrrrr!! Naji a jikina domin bai tab'a kirana da irin wannan muryar ba.... Shiru nayi. Tsaki yaja hade da fad'in"Nasan kina jina kika min shiru Ok ina so ki shiga hankalin ki ki nutsu sosai ki San da wa kike zaune naji na karb'a an lak'aba min saboda gujewa sharrin ki jama'a suke gudun had'a zuria dake ni don an raina ni sai a wani d'aura min aure dake.... OK naji na karba amma ki kiyaye wallahi domin bana son shirme da gatsali nayi rashin matata mai biyayya kiyi koyi da halin 'yar uwarki Mimi sai mu zauna lafiya dake ina fatan kin gane ko."!!!!? 


*Ikon Allah mutumin da aka turo yayi rarrashi shine yake gasa wannan maganganun masu zafi Wanda zasu iya sanya zuciyarta ta buga a take babu shakka Kalmar da malam bahsushe yake fad'i gaskiya ne Namiji tabarmar k'aya ne waiii*


   Tun kafin ya karasa maganganun sa nake wani irin kuka yayin da nake jin wani irin zafi da zugi a cikin zuciya ta, ji nayi bazan iya kyaleshi ba, domin a ganina idan na barshi ya saba min da wannan cin mutumcin to babu shakka nice zan sha wahala da sauri na mike zaune ina goge hawayen fuskata da gefan lifayar dake jikina. Ido muka hada dashi yaji gaban shi ya fad'i ganin yanda idanunta sukayi wani irin ja!! Dama gasu masu girma..! Kauda kansa yayi da sauri! Yana wani ya mutse fuskarsa..... Murya ta bata futa sosai nace"Ni ake gudun had'a zuri'a dani."? Daga kafad'a yayi yana kallona. Na cigaba da cewa "Saboda ana gudun mugun halina, shi Jahid din ne yace maka haka." !? A d'age ya kalleta yace." Idan shine ya fad'a min ke Baki isa ki na fad'a miki E ko A'a ba."  Cikin takaici da ciwon zuciya nace"Ni nasan Jahid don an fi k'arfin shi ya sanya ya hak'ura dani, amma babu shakka soyayyar da yake min babu algus a cikin ya nafi tunanin wannan maganar daga bakin ka ta fito saboda mugun sharrin ka da b'ata sunan ka, ita kanta mahaifiyar Jahid din da ta hana faruwar auranmu bata yi min wannan mummunan  kazafin fa sai kai.! Tom nagode K'warai amma nima ina fada maka cewar "Wallahi irin zaman da kayi da Mimi kai baka isa kayi irin shi dani ba, sharrin ka zai koma kanka! Kuma baka isa ka kashe ni da bakin Cikin ka ba, ko Mimi ma itace ta sa kanta har ta mutu ta sanadiyar ka ni baka isa kayi sanadin mutuwa ta ba, sai Allah." 



   Ranshi yayi mugun b'aci jin kausasan lafuzan ta, dama hausawa sun ce baki in yasan abunda fad'a to bai San abunda za a mayar masa ba... Take yanayin fuskar sa ya sauya sai wani huci yake yi yana kallonta tana kallonsa... Gyada kansa yayi yace." Kinci albarkin baby Aysha dake jikin ki Yanzu amma da baby shakka sai na miki abunda Baki tab'a tsammani ba." Da sauri nace" Bans so inci albarkacin kowa kayi min abunda kayi NIYYA don Allah."!!! Bai saurare ta ba ya bude kofar da sauri ya fuce kamar kububuwa. Granny na zaune taga futowar sa yayi waje kamar zai tashi sama da sauri ta shiga dakin Asma'u sai ta tadda ita ta rungume baby tana gursheken kuka har da majina. Hankali a tashe ta karasa dakin tana fad'in " innalillahi ASME me yayi miki kike Wannan kukan nagan shi shima ya futa da b'acin rai ki daina kuka ki fada min damuwar ki."!  Cikin kuka nace"Granny zaman mu da abban baby bazai yi wu ba."" Hankali a tashe! Tace"kan wane dalili kika fad'i haka." Kasa fada mata komai nayi sai kuka domin ji nake kamar in mutu ya ilahi wai same zanji ne."!!? Kuka ta fashe dashi itama sosai take fad'in "Kiyiwa girman Allah da Annabi kiyi hakuri babu shakka nasan abunda ya faru tsakanin ki dashi ba me dadu bane da nasan zai shigo yayi b'arna da ban turo shi ba, kiyi hakuri ki dubi wannan yar lab'ub'uwar yarinyar dake jikin ki ki zauna da ubanta ba don halinsa ba, nasan yana da fushi amma ba shi da rik'o don Allah dukan abunda kika San zai hasala masa zuciya ki guji yin sa kin ji ko." Duk cikin kuka take wannan maganar.

 Sosai tsohuwar ta bani tausayi goge fuskata nayi ns rike hannunta dake karkarwa nace"Granny ki daina kuka don Allah insha Allahu zanyi abunda kika ce din zanyi kokarin ganin na kawo zaman lafiya s zamantakwar mu dashi insha Allah nasan ni tawa kaddarar kenan kuma zan karb'e ta hannu biyu." Tace"Yawwa ko kefa Allah yayi miki albarka." Ameen nace. Ina jin wani irin kaunar tsohuwar Cikin zuciyata. Tace"Muje kici abunci don duk ga alamu nan sun nuna ba kici abunci ba." Nace"zan fito yanzu insha Allah ." Mik'ewa tayi tana kokarin d'aukar baby dake wasa kan bed yarinyar ta sa kuka Granny ta fuce tana fad'in "Ja'ira kawai yau ni din kike gudu saboda kin ga uwarki." Murmushi nayi kawai na mike ina warware liffayar jikina toile na shiga na wanke fuskata kana na dauro alwala na futo k'arfe hudu da rabi na yamma, dadduma na shimfid'a na tada sallah cikin nutsuwa bayan na kammala addu'a ne na mike a nutse na tsaye gaban wani dressing mirror dake cike da kayan shafa, fuskata na kalla naga duk ta kode dama ban yi wata kwalliyar kirki ba aunt Hauwa babu yanda batayi dani ba naki  raina babu dad'i na futa  daga dakin. Da babu a hannu granny da Iyami da wasu mata uku s zaune a parlor suna magana sama-sama da suka ga na futo sai suka yi shiru, Kai tsaye gurusu na nufa a nutse na gashe da matan kana na mike na isa gurin cin abunci ina mamaki kallon banzan da d'aya daga cikin su take min....... Magana suka cigaba da yi Wanda bana fahimtar me suke fada na dai lura kamar ransu a b'ace yake dukanin su,  kad'an na zuba abuncin ina ci kamar magani baby nake bawa àbinci kad'an kad'an ganin tana so taci babu laifi taci kad'an hankalina na mayar kan su granny jin abunda matar nan dake hararata take cewa"Yo!! Da kike wannan maganar idan Hafsatu ya aura kina nufin ita bazata kula masa da baby ba, ai kusancin sa da Hafsatu yafi Wanda ita take da Uwar yarinyar, ni dai wannan al'amari bai min dad'i ba kuma an munafurce ni."!! Iyami da bata so a tab'a mata granny tace" Haba ke kuwa da girman ki da komai kike magana irin ya yara k'anana shi ga aure nufi ne na Allah kuma babu laifin Uwar dakina anan, tunda ba itace tace Dole sai anyi auran ba Allah dai ya kaddara za'ayi.....! Cikin hayagaga Inna Suwaiba mahaifiyar Hafsa tace"Kinga  bana son munafurci da iya samu guri Yaro dai danmu ne mu muke da magana a kansa ba ke kar ki kara sanya mana baki anan, ai INA zaune a gurin nan har Amjadu ya shigo gidan a matsayin na uwarsa yan umarce shi da iya yi min Abu kuma sai yayi, Granny tace"To idan ya shigo sai ki umarce shi kina da iko dashi duk hukuncin da kika yanke a kansa dai-dai ne dank'i... Matan da suka rako inna Suwaiba suka ce K'warai kuwa maganar ki hakkun kamar yanda kike da iko dashi muma haka nake dashi..........












*3/12/2018*

[12/3, 9:57 PM] .: *BABBAN YARO*



*MALLAKAR_ BINTA UMAR*




*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*






*72*






Wani irin mamaki ne ya lullub'e ni jin abunda yake futowa daga bakin matar wai tana da iko da Amjadu zata sanya shi ya k'ara aure Ikon Allah idan Amjadu zai hada mata uku ni na zama ta hudu a halin yanzu bai dame ni ba, saboda Sam ba shine a gabana ba, abincin nake ci babu dad'i ina tunanin lamarin mutane. 

Tare suka shigo da Jahid   da Khalid Jahid yana rike da wata k'atuwar leda mai tambarin Muddansir&Broths kai tsaye inda nake ya k'araso ya dauki baby yana mata wasa. B'acin rai da bakin ci bai sa na kalli inda yake tsaye ba.... Amjadu da Khalid kuwa gaisawa suke da su Inna Suwaiba dake zaune suna jiran shigowar sa... A hankali Jahid yace." Amarya kin sha kamshi nasan nayi miki laifi a ganin ki, amma na tabbata nan gaba zaki zo kina alfahari dani a rayuwar ki, Asma'u Allah ya tabbatar da alkairi a rayuwar ki." Wata irin k'walla me zafi ce ta cika min kwarmin idona Hak'ika Nayi rashin mosoyi na hak'ika Momy Jahid ta cuce ni a rayuwa ta Tabbas duk macan da tasamu Mujahid a matsayin miji ta more wa rayuwar ta... Ledar dake hannunsa ya aje a cinya ta yace." Ni yanzu a matsayin yaya nake a guri. Ki Asma'u ba don ni ba don Allah ki tashi ki kimtsa jikin ki zamu futa walima Wanda muka shirya muku ke da angon ki.." Yana gama fadin maganar shi ya bar gurin dauke da baby a kafadar sa. Mik'ewa nayi jiki babu kwari na dauki ledar na nufi bedroom din da na fito yanzu. Daf da zan shiga naji Inna Suwaiba na fad'in"Ni dai na fada maka magana ta ta k'arshe har in dai ka dauke ni a matsayin uwa to kabi umarnina kamar yanda nace din. Saboda bamu da muhimacin a rayuwar ka ranar auran ka sai dai muji a gari bare ma yafi mu daraja a gurin ka, iyi ga yarinya 'yar Asali zakaje ka daukowa kan ka kara da kiyashi! Ai duk mun San komai mu baza a rufe mu ba... Itama mahaifiyar Abokin naka ta guji hada zuria da mugun iri ne shiyasa ta ruguza auran, kai kuma saboda baka da wayo ka karba to baza mu lamunta ba.."!!! Maganganun Inna Suwaiba sunyi tsauri  da yawa shi kanshi Amjad din yaji rashin dad'i ga Asma'u a tsaye taji komai ga abokan shi Innarsa take wannan surutun tabbas Jahid zai ji babu dad'i cikin zuciyar sa. Aikuwa Hakane ta faruwa granny ji take kamar ta gaggaurawa Suwaiba mari ganin yanda take kokarin bata al'amari wannan ai cin fuskane take a matsayin ta na mace mai hankali dattijuwa bai cancanta tayi irin wannan maganganun ba.


Da gudu na fad'a dakin nayi kwance kan bed rumutse idona nayi da k'arfi hawaye suka fara gudana a fuskata Shikkenan Amjad ya gama zubar mun da mutumcin na, a duniya ni kuwa me nayi wa mutumin nan me zafi a duniya ya b'ata min suna gurin jama'a a takaice ma yanzu na rasa wane irin kallo jama'ar gari suke yi min. Innalillahi wa'ina ilahi raji'un. "!!!! Bude kofar dakin aka yi, nayi saurin goge hawayena domin na dauka granny ce.... A hankali ya k'araso har bakin bed din hannunsa cikin aljuhu ya tsaya a kanta k'ikam!!! Yafi minti biyar yana kallonta kana ya sauke ajiyar zuciya hade da Jan siririn tsaki yace." Kukan me kike yi."!!!? Shiru babu amsa.. K'afar shi guda ya Dora kan bed din ya d'ago fuskata da hannun shi, da sauri na kwace ina kauda kaina... Murmushi ya saki ya shafa sajanshi As'usuel yace." Saboda kawai Inna ta tace min in kara aure shine kika rugu daki da gudu kina kuka kome.? Shiru nayi masa ina jin wani irin tafasa da zuciya ta take, a halin yanzu idan nace zanyi magana ba mai dad'i bace domin zai iya zaginsa wallahi saboda yanda nake jin wata irin muguwar tsanar sa cikin zuciya ta bayan haka kuma nasan yana a matsayin mijina yanzu kome nayi masa za'a rubuta min lada da zunubi ne, shiru yafi amfani a gare ni..... Kasa yayi da muryar shi yace." Ki koyi mu'amula dani idan kuma kin kasa zaki sha wahala a gurina zanyi aure idan Allah ya hukunta hakan a tare dani saboda haka kar kisawa zuciyar ki cewa dake kadai zan zauna." Hannu na daga masa da sauri bakina na rawa na ma rasa me zan ce masa.!! Kafarsa ya dire a kasa har yanzu hannunshi yana cikin aljuhun sa yana mata wani irin kallo Wanda shi kadai ne yasan ma'anar sa. 

Kasa cewa komai nayi kawai na sauke hannuna kasa ina kokarin mayar da hawaye na domin na tsani yaga kuka na gudun raini daga gare shi. Cikin wata dakilalliyar murya yace." Kin bude baki kina so kiyi magana kuma kin kasa kawai ki fada kar ta kashe ki.""""" Ni kuma ina sauraron ki.... Kaina na a kasa nace"Kome kayi min na barka da Allah ka b'ata min suna a duniya kowa na ganina kamar wata  mai yawon ta zubar a Shikkenan. "!!  Yanda ta fadin maganar hakan ya Sosa masa rai sosai amma sai ya basar duk da ya kara cusguna mata ya zauna kusa da ita yana k'wakumar ta sosai.. Asma'u a karshen gado take tsoro ya kamata yunk'urin tashi take ya hana faruwa hakan k'irjinta yake kallo da lumssasun idonsa yace." Yanzu zan gwada miki wani Abu in yaso sai ki barni da Allah kamar yanda kika ce duk abunda nayi miki kin barni dashi.""  Kafin ya Ankara ya haye jikinta ta inda tayi plate kam bed dama jiki duk babu kwari gajiyar buki fa fargaba. Sosai ya sake mats nauyin shi yana wani irin Abu da idonsa. Asma'u ta shiga wani hali na Neman dauki domin ta San halin rashin mutumcin guy babu abunda bazai iya yi mata ba.... Hannunta ta sanya tana dukan kirjinshi hade da ture shi. Ko gezau yak'i yi sai ma rike hannunta guda da yayi ya kaishi kasan wandon sa, yana cusawa sa, still idonsa tsaye a kanta. A wannan lokacin Asma'u ji tayi kamar ta nutse saboda kunya domin zahiri tana jin joystick dinshi a hannunta. Sai tayi saurin dunkule hannun nata, amma duk da haka bai fasa wasa da hannunta a gurin ba.... Dan kanshi ya curee hannun NASA hade da d'aga ta yans watsa mata wani irin kallo yace." Yanzu ma sai ki barni da Allah  kinji ko."! Rigar shiri ya sakko da ita ya gyara sosai ya kama hanyar futa.

Asma'u suman kwance tayi a gurin domin ta kasa motsa ko k'aramin Dan yatsan ta saboda yanda gab'obinta suka shika tsigar jikinta duk ta mike Wani irin sanyi sanyi take ji a fatar jikinta, wandon ta kuwa tuni ya jike da ruwa Yo dama haka kurrum take zubah to balle wannan *Majnun* _(Sunan littafi na me zuwa)_  Ya kusan ce dole taji abunda ya fi haka ma, rintse idonta tayi tana cije lips dinta cike da wata irin sha'awa take matse cinyoyin ta, tafi minti ashirin cikin wannan halin kafin ta fara jin sassauci ta mike zaune idonta duk fad'a kokarin Mik'ewa take ta shiga toilet ta tsarkake jikinta. Ya shigo dakin a karo na biyu wannan karon bakin kofar ya tsaye yana sanye da Shadda galila 'yar gaske dark blue wannan ma dinkin Muhammad Abacha me har kasa tasha wani irin aiki na maza Wanda suka amsa Sunan su. Hular kanshi zanna buka 'yar gasken yau Amjad ya futo bahaushe sosai kuma ango. Kauda fuskar ta tayi cikin fad'uwar gaba tana tunanin me ya dawo dashi dakin kuma..... Babu yabo babu fallasa yace." Kowa ya hallara ke muke jira OK." Yana gama maganar shi ya fuce daga dakin babu abunda ya dame shi.....









*3/12/2019*

[12/4, 10:26 AM] .: *Babban Yaro*

*08089965176_07084653262*







*73*








Yana futa na mike da mataccan jiki na shiga toilet ruwa na hada mai zafi nayi wanka sosai sannan yayi wankan tsarki na futo jikina daure da towel mai d'an fad'i kofa na nufa na kulle da key na barshi a jiki gudun kar ya kara fad'o min daki kamar yanda ya saba, zama nayi kujerar mirror ina goge fuskata tunani nake yi wace irin kwalliya zanyi ma gashi ni ba gwanar kwalliya bace domin ban iya ba, mai na shafa a jikina shafa farar hoda kwalliya na xizara na gyara girata kana sanya man lebe Mik'ewa nayi na zazzage kayan dake cikin ledar. Wani irin material ne roba-roba Kalar shi Orange yana da wayan stones a jikinsa birjiki dinki petad gwon ne  sai site din takalmi da jaka iri d'aya wani k'aramin akwati na bude naga wani irin sarkar gwal hade da a warwaron ta guda shida manya manya sai zubuna hudu sai shek'i suke yi sunyi bala'in burge ni da sauri na sanya rigar jikina kamar a jikina a dinka min sai da bayan a bude yake sosai kuma tudun nonowana duk sun fito, gashin kaina da yayi tozo na gyara sosai na dauki wane irin net golden da nagani na Dora a kaina take na fara wani irin shek'i da walwali na gwal dama ga fatata tayi luwai-luwai tsayuwa nayi gaban mudubi INA kara duba kaina ni da kaina nasan mayi masifar kyau na kadan ba, duk da babu wani kwalliya na fuska amma zahirin kyawuna ya futo, takalman na dauro a k'afafuna na rike pose din.. Ina tunanin futa a haka domin ni kaina nasan kayan sun matse ni dama haka nake kome nasa sai ya fito min da kira kuma material din Roba ne shiyasa abun yayi tsanani. Motsin bude kofa naji gabana ya fad'i sai na tuna na kulle kofar a jiyar zuciya na sauke, babu kuzari na karasa jikin kofar na Mirza key din kana na matsa gefe shigowa yayi idonsa tsaye a kanta... Sai da yayi ta maza tukkuna domin ji yayi kamar zai fad'i yayi gyaran murya yana bin ta da kallo cikin nazari.... Bata fuska yayi yana wani ya mutse ta yace." Kinyi kyau sosai amma wannan kayan sai kin cire su Wallahi." Kallo na bishi dashi cikin mamaki nace"A kan me."? Hararata yayi yace." Ni ba lusarin Namiji bane da zaki burtsu nono waje ki nunawa wasu dole inyi kishin aurena."" A hankali nace "Ba laifina bane dinkin ne haka." Cikin dakin ya shige yana fad'in "Zancan kike so shiyasa Mimi take burge ni ita duk rintsi bata nuna tsaraicin ta." Shuru nayi masa saboda ba naso inyi magana me zafi yayi min wani abun nasan halinsa. Ina tsaye jikin kofa ya karaso gurin hannunsa rike da wata atampfa ruwan ganye cikin wata farar Leda ya warware sosai ya mik'o min tare da fadin sanya wannan yafi mutumci." Cike da mamaki nace "Ina ka tab'a ganin anyi party da atampa." A kaurare yace

" wannan na party bane Walima ne Wanda Annabi ya koyar... Karbar nayi nace"Jeka waje in I shirya." Hannunsa ya zuba Cikin aljuhu yace." Baki isa ba ina tsaye a gaban ki ki shirya mu futa me kike nufi ne."?Yanzu nana kaunar yi masa musu saboda ina jin tsoron abunda yayi min d'azu, sai na fara kokarin kwabe doguwar rigar dake jikina na dawo daga ni sai brz da k'aramin shiket iya gwiwa bayan pant dina na ciki.. Rigar atampar nake kokarin sanyawa ganin yana ya k'urawa k'irjina ido... Fuzge rigar naji anyi na tsorata matse ta yayi jikin kofar ya zura hannunshi ta bayan ta ya rike kugunta sosai! Kanshi ya cusa tsakanin breast dinta yana murzawa cikin futar hayyaci k'amshin turaran ta ya dagula masa lissafi wani irin nishi yake saki yana gogo fuskarsa a gurin. Asma'u ta dinga jin ta kamar tana yawo a gajimare tsigar jikinta ta dinga mekewa wannan salon da yake mata zai zautata gashin shi na fuska sai tsikarin ta yake a k'irjinta sai taji kamar anayi mata susa take nipple dinta suka kumbura suka fara k'yakyayi.. Ajiyar ,zuciya take sauke wa ba tare da tasan me take yi ba ta rungume kanshi dake k'irjinta tana lumshe ido. Daukarta yayi kacokan ya nufi bed da ita plate tayi ta kasa motsa Dan yatsan ta guda... Shi kuma yayi tsaye a kanta hannunsa cikin aljuhu kallon kurrula yake mata sosai itama shi take kallo da lumssasun idonta lokacin ji tayi kawai tana bukatar taji shi a jikinta yana mata wasa da Brest domin sun dame ta da kyaik'ayi..... Idonshi ya Dan sauya kala amma ba sosai ba yace." Tashi ki sanya kayan ki.""" Tsabar bakin ciki da takaici ya sata fashewa da kuka!! Murmushi yayi yace." Me nayi miki kuma." !? Da sauri ta mike ta dauki pillows ta fara jifan sa dashi tana kukan takaici.



     Komai ya hallara kowa yazo hatta da 'yan gidan su Asma'u an dauko su kwansu da kwarkwatar su, Malami mai jawabi yazo Amarya da Ango kawai ake jira har yanzu nasu fito ba, Jahid ya kira wayar Amjadu din yafi sau biyar bai dauka ba a zahiri kuma yaga lokacin da ya shiga dakin Asma'u domin zuwa da ita kamar yanda ango da amarya suke futowa tare.....Cikin gidan ya koma yana tambayar Granny ko Amjad ya futa ne bai sani ba, tace." Yana cikin dakin matar shi k'ato da Neman fitina maza buga musu kofa mutane na jiran su......... Jahid yaji wani Abu aran sa, amma take ya fara addu'a hade da danne zuciyar sa, ya karasa jikin kofar yana bugawa.



   Lokacin da Amjad yayi nasarar kwace pillows da Asma'u take jifan sa dashi ya rike ta a jikinsa har sai Da dawo nutsuwar ta sannan suka ji bugun kofa sakin ta yayi da sauri! Jin muryar Jahid din yana fad'in "Ka futo don Allah Ku aje jira." Itama Asma'u jin muryar Jahid din tayi saurin saka rigar ta d'aura zanin atamfar,  net din ya mik'o mata bayan ta d'aura d'ankwalin ta Dora a kanta.. Takalmin ta ya gyara mata sosai ta sanya ya nuna mata hanya da hannunsa, itace a gaba shi a bayan ta suka futo.


Babu kowa a parlor domin granny da Iyami ma duk suna waje daf da zasu futa ya rike hannuna cikin NASA.. Kwata-kwata baya son kusancin sa da ita saboda k'amshin ta yana gigitashi daurewa kawai yake yi, tun daga futowar su har zaman su jama'a suke musu htona da wayoyin su kai harda masu vedio ma masu camera man suna ta aikunsu mutane da dama suka dinga mamakin Wannan hadin Fari da bak'a wasu hadin yayi musu wasu kuwa gani suke Amjadu yayi wauta da ya karb'i auran Asma'u wadanda kuma suka San meye kyau suna yaba wa gami da ganin nagartar Asma'u.. Zama sukayi cikin kujerar su Anutse sannan guri ya nutsu  Malamai kusan hudu ne dukaninsu sai Da suka yi tambihi kan zaman aure da rayuwar yau da kullum sannan akayi addu'a aka fara ciye_ciye da rabon kaya abun gwanin sha'awa dama su Jahid sun shirya tsaf........ Alina na zaune kujerar baya tana jin kamar ta cakawa kanta wuka ta mutu da ganin Wannan bakin cikin  wai me yasa ta ko wane fanni Asma'u take nasara a kanta gashi dai dalilinta har suka San Amjad din,, Mimi ta aure shi tana zaune yanzu kuma Asma'u lokacin da suka ji labarin faruwar hakan ta girgiza ta shiga halin damuwa da tashin hankali daurewa kawai take yi don kar ta nunawa kawayen su halin Da take ciki har suka zo gurin Walimar a lokacin aljanun ta ma sun so su buge ta Allah ya takaita.


 

   Hafsa kuwa kyashi da bakin ciki ya hanata cewa komai mutumin da ta kwallafa rai a kansa shine ya auri Asma'u tasan yayi mata nisa dole tayi kokarin cire shi cikin zuciyar ta ko da kuwa hakan zai zama shine silar mutuwar ta... Hafsa da Alina daurewa kurrum suke yi har aka tashi daga gurin walimar Su Jahid suka fara sanya mutane jikin mota...... Alina ta karasa kujerar amarya da ango cikin daure wa tace"Sugar boy inayi maka fatan alkairi. """ da murmushi a fuskarsa yace." Nagode Alina." Amjad duk Cikin 'yan matan shi yafi sakin jiki da Alina saboda ta iya mu'amula da kisisina shine dalilin da yasa ma yaje birth day dinta... Wayar ta futo da ita ta tsaya kusa dashi tana d'aukar su hoto shi kuwa sai murmushi yake yi.... Ta matso gurina zata daukeni hoto wata banzar harara na maka mata nace"Matsa daga kaina."! Alina tasan jarabar Asma'u murmushi tayi me ciwo ta kauce daga gurin... Asma'u yake kallo a fakaice yaga tasha kunu girgiza kansa yayi kawai yana mamakin kishinta a kansa... Su Maryam ne suka karaso gurimu ko wacce rike da k'atuwar waya suna ta d'aukar mu hoto, yak'e kurrum nake yi zuciya ta duk babu dadi....... Ganin sun cika gurin ya sanya ya mike ba tare da ya kalli inda nake ba ya bar gurin  shima Cikin abokan shi ya shiga.



    To sai daf sallahr magariba sannan taro ya tashi kowa ya koma gida rike da k'atuwar Leda me hoton ango da amarya da kayayyaki a ciki abun burge wa sai muce Allah ya sanya alkairi.Misalin 11:00 na safe aunt Hauwa suka iso gidan ita da k'awarta Zainab, granny da Iyami suka samu a parlor suka gaisa da ita cikin mutumci nan ta nuna musu dakin Asma'u take suka mike aunty Hauwa tana rike da wata Leda me Zane- Zane suka shiga dakin.


   Ina zaune kasan kafet ina shirya baby domin a gurina ta kwana taki yadda da Iyami ko kadan suka shigo jin muryar aunt Hauwa yasa na dago da sauri ina amsawa suka karaso dakin nace"Aunt sannunku da zuwa.. Zama suka yi bakin gado na juyo muna gaisawa nace"Aunt Ina Umammu Ashe dama hak...... Katseni tayi da sauri tace"Yanzu maganar k'orafi da tashin tashina ta kare tunda dai gaki jikin gidan sai kiyi hakuri k'walla nagoge kawai ina gyada kaina cike da takaici,  tace." Ba zama ne ya kawo mu ba matso inyi miki bayani." Juyowa nayi ina kallonta aunt Zainab tace"Ni banga abun kuka da damuwa ba ke da Allah ya mallaka mi miji na tsrewa sa'a." Da sauri nace"Aunt Zainab auran irinsu abban baby had'ari ne wallahi ki dubi yadda rayuwar Mimi ta kare duk a kansa." 



   Aunt Hauwa tace"Ke bana so shirme itama tata kaddarar kenan kowa da tashi dama Allah yayi Mimi ba me tsawon kwana bace, kema kika iya zama dashi zaki dauke hankalinsa daga kan ko wace mace shiyasa ma nake kokarin gyara ki. Kuma wallahi banda gaddama gurin shimfid'a abunda yake tunzura zuciyar maza kenan har ta kaisu ha Neman Matan waja." Aunt Zainab tace"Hakane kawata yaran yanzu sun kasa fahimtar hakan wai idan mijinki yayi miki laifi sai ki kaurace masa a shimfid'a to ba haka ake hukunci ba. Idan kikayi fada da mijinki kar ki FASA yi masa duk wani Abu da kika saba yi masa kawai idan kina so ki ga gazawar sa to ki rage walwala a gida ki rage fara'a ki kama kanki, Tom shi kuma a lokacin zai shiga halin damuwa zai San abunda yayi miki ne, kuma zaki bashi tausayi ki kara shiga ranshi, dalili zaiga dukkanin wani hakkinsa kina sauke masa, take idan me tsoron Allah ne zai zo ya baki hakuri to Kinga ko tanan kinyi winning d'inshi." Aunt Hauwa aunty Zainab suka d'age suna kara wayarwa da Asma'u kai kan zamantakewar aure, kana suka fara yi mata bayanin yanda zata yi amfani da kayan mata 'yan gaske Wanda da Kansu suka hada mata domin nemo mata martabar ta a gidan miji suka yi mata bayani sallah dallah suka mike da niyyar tafiya Kuka ta sanya tana fad'in sai kace wata mara galihu daga zuwa zaku tafi haba aunt Hauwa. "!!!


Cikin tsokana aunt Zainab tace"Aikuwa dai Gaskiya Dole muci kazar amarci gaskiya." Hararata aunt Hauwa tayi tace"kin zama babbar kwabo wallahi idan ya shigo ya ganki kice me." ? Da sauri na mike na bude wani firji dake can gefa Leda na ciro nazo na aje gaban su na Ciro robobin yugut da biyu masu sanyi aunt hauwa tace"Baki da hankali Asma'u waye zai ci wannan kajin da sanyi a jikinsu.."! Aunt Zainab ta bude ledar tana dubawa lafiyyayn gassasun kaji ne sunji kayan had'u guda uku sai dai babu wacce aka gutsira sunyi sanyi kadan dalili frijin ba a kunne yake ba... Zainab tace"k'aryar ki ta sha karya kawata inke baza ki ci ni zanci domin nasan wannan kajin karshen su zubar wa da kyawun su, nuna min kicin in shiga in gasa yanzu... Nace"Naga kamar akwai k'aramin kicin a parlor na bayan na babban parlor tace "muje ji nuna min." Futa mukayi na nuna mata aunt Zainab ta kunna oven ta gasa kajinan tsaf sai kamshi da turiri suke ta zubo su k'aton plate ta futo take kamshi ya cika dakin nima naji mi yau na ya tsinke, kawai sai na zauna cikinsu muna ci muna hira, domin dama ko da na tashi ban karya ba, duk da cewar ga kayan karin nan a je... Fula's din tea na jawo na hada tare da fad'in "Aunt ko in hada muku tea din."? Gyada kai kurrum sukayi tare da fadin wannan ma ya isa... Kurbar ruwan shayin nake ina tunani Amjad tun a gurin Walima rabona dashi har yanzu banji motsin sa ba.......












*4/12/2019*

[12/5, 7:50 AM] .: *BABBAN YARO*





*74*







Aunt Hauwa sauri sauri take cin kazar a cewar ta wai bata so Amjad din ya shigo ya ganta sai yaga kamar rashin hankali, aikuwa kafin su gama ci muka ji alamun bude kofa aunt Hauwa ta zabura! Da sauri ta gyara zama ta koma gefan gado tace"Tashi maza ki tare shi daga parlor mana." Ganin yanda tayi maganar babu wasa a fuskarta yasa na mike sa sauri Baby ta sanya kuka dawowa nayi na dauke na bude kofar.. Ina budewa na ganshi tsaye a gurun hankalin sa na kan wayar shi kome yake dubawa oho! Saurin kauda kaina nayi tsigar jikina na Mik'ewa take naji sha'awar shi ta kamani yana sanye da wata d'amammiyar vest ash color had'e da 3Queatr  mai aljuhu na gaba da baya, fatar shi tayi wani fresh kwantaccan gashin da yabi lafiyyar fatar tashi shine yake gigita ni yake samun sha'awar shi... Baby ce take zillo sai taje gurin sa. Ya zura wayar cikin aljuhu ya karb'e ta daga hannuna yana dariya kamar bashi ba, sai wasa yake mata tana dariya, sai da suka gama sannan ya kalle ni babu yabo babu fallasa yace." Kun tashi lafiya."!? Kunya naji kadan abunda ya kamata ni in fara gaishe shi. Nace"Lafiya k'alau kaifa." ?



   Baby yake wa wasa bai ce min komai ba, sai nayi nufin komawa dakin. Gyaran murya yayi na juyo a hankali ina kallonsa yace." Ke da waye ciki naji kamar sautin maganar mata a ciki." Kai tsaye nace "Su Aunt Hauwa ne." Wacece ita."? Ya fada cikin rashin sani. Na Dan ji babu dad'i ganin yanda yayi maganar babu walwala a tare dani nace"Aunt Hauwa zakace baka sani ba."? Jim! Yayi daga bisani yace. " Sorry nagane ta a maimakon kimin magana nazo in gaisa dasu sai kiyi shiru wato da ban tambaye ki ba baza ki fada ba ko."



   Ajiyar zuciya na sauke nace"Zan fada mana yanzu ma na mance ne." Shuru yayi min yana kokarin shiga dakin. Naji kamar in jawo shi in hanashi shiga ciki dakin Saboda yanayin kayan jikinsa, wani irin kishin sa nake ji bana so ko su aunt Hauwa su ganshi haka.


   Sakin fuskarsa yayi sosai suka gaisa dasu aunt Hauwa kana ya futo ya same ni inda nake. Bai ce min komai ba ya bar gurin kafadar shi sab'e da baby... Jikina babu kwari na koma cikin dakin inda na har sun mike suna shirin tafiya kamar in sanya kuka haka nake ji. Nayi diriduri Neman abunda zan basu nake na rasa da sauri na bude wardrobe din da naga ya bude jiya na fara bin cikin ta da kallo. Wasu dogwayen riguna na ciru a daure  na Ciro Mayafai biyu Leda na sanya na biyo bayan su da sauri. Nan na Tarar suna sallama da granny na bi bayan su INA mik'a wa aunt Hauwa abunda ke hannuna. Karba tayi mukayi sallama idona cike da k'walla nace aunt ki gaida min da Umma don Allah.


 Tana tafiya tace"Zata ji insha Allahu. " Rambo ne yayi musu magana yana nuna musu mota kai tsaye suka nufi inda motar take suka shiga Doh-doh yaja motar suka futa daga gate din... Ciki na koma zuciya ta babu dad'i kwata-kwata.... Na parlor na zauna kusa da granny dake kallon tashar sunnah tv malam Umar Sani fagge ba tambihi... Tace"Wannan yayyun naki suna da hankali da nutsuwa Asma'u. " murmushi nayi kurrum ta cigaba da cewa"Dama inaso in kara kwantar miki da hankali cewar don Allah kar ki d'aga hankalin ki kan abunda kika ji Suwaiba na fad'a jiya kiyi hakuri da abunda tayi kinji ko."! Murmushin takaici nayi nace "Babu komai granny Wallahi ni zuciya ta fes take wallahi ban sanya abun a raina ba, duk abunda ya faru dani nasan kaddara tace." Granny taji tausayin yarinyar ya kara shiga ranta tace"Yawwa haka ake son mutum me saurin fahimta." Sake wa nayi da granny muka dinga hira nake tambayar ta baby tace"Tana gurun babanta irin wannan lokacin suke bacci mutukar yana gida, shuru kawai nayi na kamo wani zancan.. Iyami CE ta shigo tana tambayar granny me za"a girka na abincin rana Granny tace." Ga matar gidanan Ki tambaye ta mana."

Dariya granny ta bani jin abunda tace, nace" Lokacin da banzo gidan ba ku ne kuka tsara abunku yanzu kuma sai ace a tambaye ni." Cikin bada kulawa tace"ai hakkin ki ne dole a tambaye ki, don ta k'ato ne mai sauki ne ba komai yake ci a gidanan ba dama kece zaki koya masa cin abunci a gida. " nace "Wallahi nima komai a dafa zanci." Iyami ta bar gurin tana mana dariya....... Kiran sallahr azuhur ne ya tada mu daga gurin kuma har lokacin su baby basu tashi daga bacci ba... Wanka na soma yi na dauro alwala na futo tsane jikina nayi sannan na shafe jikina da humra wacce k'amshin ta ya Riga ya kama jikina, duk kayana na gidanmu har da Wanda na dinka na futar buki don haka sai na rasa Wanda zan sanya.... K'atuwar wardrobe din dai na bude na fara dube-dube idona ya sauka kan wasu d'aurarraun Pakistan, da sauri na jawo su ina kwance wa Allah yayi ni da son Pakistan sosai da dogwayen riguna  wani ne ya bani sha'awa pink coulor ya sha ado da stons  sai daukar ido yake take na cire shi daga ledar shi na sanya a jikina gaban mirror na tsaya ina duba kaina, wallahi ni kaina nasan nayi kyau sosai ya kamani daga k'irjina dai-dai kuguna ya bude dalili akwai tsaga gefe-da gefe duk da wando k'ato ne bai hana bayyanuwar hips d'ina ba, sumar kaina na taje na hade ta tsakiyar kaina tayi tsini sosai sai na Dora net din da nayi futar buki dashi....jikina na kara feshewa da turare ko da wasa banyi wani fente-fente ba a fuskata saboda nasan ba kasafai nake yin kyau ba fuskata duk sai ta dame.... Futa nayi kafata sanye da wani takalmi plate, granny na samu zaune kan kujera da carbi a hannunta.



    Ina zama tana shafa addu'ar ta tace"Ca nake bak'uwa mukayi daga k'asar Hindu ." Dariya NASA ina rufe bakina tace"Kinyi kyau Maman baby sai kace yarinyar nan ta hindiya ya ma take da suna."? Wai ni take tambaya Dariya kawai nake mata ganin da gaske take maganar.... Iyami ce ta shigo tace"Yauwa Iyami yama sunan yarinyar ta wannan film din mai yawan fara'a."!? Take Iyami tace"  Johi chaula." Yanda Iyami ta fad'i sunan yayi mugun bani dariya dake wa kawai nayi nace"Granny ina ni ina wannan tsohuwar matar." Tace"Ai dama ba cewa nayi sa'ar ki bace cewa nayi kuna kama ko ba haka ba Iyami."? Iyami tace"Hakane Hajiya nima yanzu naga kammanin sun futo Sosai.."! 


   Ni dai ban San sanda na fashe da dariya ba take dimples dina duk suka futo Iyami tace"Wallahi har irin dariyar su ma gashi kumatunta yana motsawa." Ni dariya granny dariya nace"Ni kam Iyami ki daina had'ani da wannan tafi ni kyau nesa ba kusa ba ina ni ina ita ki duba da kyau don Alla.....Maganar tawa ta katse ganinshi ya futo daga bedroom din shi nayi saurin gintse fuskata ina kokarin kama kaina.. Iyami kuwa cigaba da k'od'a ni take wai nayi kyau har da rantse wa.

 Kallonta yake tun daga samanta har kasan ta, tabbas ba karya Iyami tayi ba shima ya gani dressing din ya karb'a ta bai San me yasa pink din Abu yake mata kyau ba.. Sosai kwalliyar ta ta bashi sha'awa amma ko a fuska bai nuna ba, ya tsaya bakin k'ofa yana fad'in"Granny me yasa baku tashe ni ba gashi har lokacin sallah ya wuce uhumm!." Tace"Wallahi yanzu nake tunanin ince Asma'u ta shiga ta duba Ku Ashe baka tashi ba sai yanzu." Girgiza kansa kawai yayi ya koma ciki dakin jikinsa duk ya mace jin masifaffan k'amshin yarinyar. 



  Granny tace" Maza tashi kije ko da akwai abunda zaki masa." Mik'ewa nayi babu kuzari a jikina na nufi dakin... Wani irin sanyi da kamshin dad'i suka bakunce ni. Duk da cewa ba yau ne karon farko da na fara shigowa dakin ba, sai da gabana ya fad'i dana tuno abubuwan da suka faru tsakanina dashi shekarun baya..... Baby na kwance kan bed tana bacci na karasa Cikin dakin sosai zama nayi gefen bed din ina jin motsin zubar ruwa a toilet din... Wanka yake yi bed din nake kallo duk ya ya mutse ga baby a kwance bare in gyara masa, can na hango wani k'aramin frem hannu nasa na dauko ina dubawa.. Mimi ce tana dariya Lokacin tana da cikin baby  da alama shine ya dauke ta a wayarsa don shi din take kallo tana dariya lokacin tayi wannan ramar da haske amma tayi kyau sosai..... Hoton na rungume a k'irjina  hawaye suka fara zubo mun nace da na sani ban shigo dakin ba..kuka nake sosai domin na ma mance a inda nake jin motsin bude kofa yasa nayi saurin goge fuskata Ina kokarin mai da hoton in da yake Cikin tsautsayi ya fad'i kasa take ya tsage gida biyu... Wanda yayi dai-dai da futowar sa daure da towel ido muka hada dashi.  Nayi saurin sunkyar da nawa saboda ganin yanda ya futo.. Hoton nake dubawa gabana na fad'uwa. Karasowa yayi kusa dani bai ce komai ba ya sanya hannu ya karb'i frem din yana dubawa naga ya b'ata fuska cikin tuhuma ya kalleni kana yace." Meye dalilin ki da zaki tsaga min hoto. "? Tambayar shi ta bani mamaki K'warai nace" Kamar yaya."!?



    Babu walwala a tare dashi yace." Ina tambayar ki kina tambaya ta. Duba b'arnar da kika yi min lokaci guda shekarar abina guda babu abunda ya same shi sai dalilin ki."! Raina ya b'aci amma sai na danne zuciya ta kawai na mike da niyyar tafiya domin nasan laifina ne da na shigo masa daki har na dauki abun shi.. Tsaki naji yaja kasa-kasa yace." Ke akan kowa ma sai kin gwada kishi." Sai da na futa daga d'akin tukkuna na fara tunanin me maganar shi take nufi? Ni a kan kowa ma sai na gwada kishi! Idan na fahimce shi yana nufin kishin Mimi ne ya sanya na fasa hotonta Ikon Allah."!! Abun ya bani mamaki matuka Mimi ko tana raye a duniya Allah ya hada mu auran Namiji daya bazan yi kishi da ita ba, to ko zanyi kishi a kansa sai inyi da Wanda bana ganin shi baya Raye a duniyar ma gabaki daya.

Nafi minti a shirin ina tunanin wannan al'amari daga bisani na share maganar kawai domin dai ni nasan Mimi tafi k'arfin komai a gurina kuma ina zargin domin ya kuntata min yayi min wannan maganar.... Parlor na futo domun bana son tsohuwar ta fuskanci wata matsala amma nayi alk'awarin guy nan ya shigo gona ta zan gasa shi kamar yanda yake min wulakanci son ranshi, Granny tace"Dama yanzu nake tunanin kiran ki ki futo muci abunci ." nace gani na futo granny Daining muka nufa Ni da Ita. Ko da wasa ban kalli shi ba na fara hadawa kowa nashi.. Yana zaune da airpix s kunnen shi baby na jikin shi tana wasa tana ganina ta dinga kokarin saukowa granny ta dauke ta tana fad'in"Bari taci abunci tukkuna." Kuka tasa nace"Baby rigima Bari in gama zan dauke ki." Cikin sauri na had'a mishi abunci na tura gaban shi granny tace"Dauke ta ni na hada da kaina." 'Yar dariya nayi nace "Bari in karasa lada na." Lokacin kuwa baby har ta fara kuka abunda baya so kenan a rayuwar shi kukan baby  a kufule yace." Malama ki dauke ta ki k'yale cin abunci mana dole ne."!! Granny tace"A'a!!! K'ato bana son son Kai ba, ji wani magana da kake cin abunci Dole ne mana idan bata ci ba ta yaya zata yi maka rainon yarinyar... Wayar tashi ya aje  kan teble din yana kokarin karb'ar baby dake zillo sai tazo gurina, yaro kenan duk yanda take da Dadyn ta taki yadda dashi. Yaji kamar ya tashi ya gaggaura wa Asma'u mari a hasale! Yace." Asma'u wai ba dake nake ba ne."!? Idona na d'ago na kalleshi babu yabo babu fallasa nace" To." Daga haka nayi shiru ja goge hannuna da tissues na karb'i baby daga hannun granny barin gurun nayi raina duk babu dad'i tsaki yaja ya cigaba da danna wayarsa ko kallon abincin banyi ba... Parlor na zauna cikin kujera da baby granny ta biyo da plate din abincin a hannunta tana ta faman mita "Ni wannan rashin. Kawaicin naka akan baby shine yake bani haushi dai kai wallahi duk yanda mutum yaso ya kyauta ta maka sai ka kaishi k'arshe ka canza halinka Haba! Ina dalilin Wannan Abu."!!







*5/12/2019*

[12/6, 12:51 PM] .: *BABBAN YARO*

*75*



Shi dai shiru yayi mata yana latse-latse a waya ranshi nayi masa zafi domin har yanzu baby kuka take yi taki yin shiru Mik'ewa yayi ya karasa kusa dasu baby ya karba daga hannunta har

 Hannunsu har yana had'uwa  jikinta ya tab'awa yaji alamun zazzab'i, zama yayi kan kujera yana kokarin cire mata Riga jikinta ya kalli Asma'u da ta zuba musu ido shi da babyn yace." Ki duba dakin kan drowar akwai maganin ta dauko min." Asma'u ta mik'e jikinta babu kuzari, baby yake hurawa kunne yana rarrashinta granny tace"Zazzab'i ne yake damunta ko."? Gyada kansa yayi kurrum. Tace"Hak'ori zan sa Iyami taje ta had'o mata dauri tunda ga ba nono take sha ba ballanta yayi mata magani... Ina mik'a masa kwalbar maganin na bar gurin.  Kuma har yanzu yarinyar bata daina kuka ba fafur taki karb'ar maganin daga hannunsa sai bugewa take duk jikinsa ya b'aci granny tace"Wacce dai ka karaina kake wa tsawa da nunawa iyaka ita din dai zaka je ka nemi taimakon ta domin nima kasan baby ba yadda take dani ba."



    Shiru yayi mata yana matsawa baby tasha magani tana buge-buge dole dai ya mike da ita a kafad'a ya nufi dakin Asma'u da ita.... Ina zaune duk abun duniya ya dame ni ga kukan baby na damuna ka bakin cikin abunda yayi mun a kanta cikin wannan hali ya shigo dakin.



    Kauda kaina nayi daga kansa domin wani irin haushin sa nake ji, Mik'o min ita yayi ba tare da tace min komai ba." Danne zuciya ta nayi nace"Me zanyi mata."? Kai tsaye yace." Ki bata magani tasha.'' Babu sauki s muryata nace"Kai da kake Ubanta baka bata sai ni 'yar karo."'" Hannu ya daga min da sauri yace." Ban nemi wata magana daga gare ki ba. Yarinyar nan tun da ta tashi bata yi kuka ba sai da kika zo gurin, duk kece sila kina ji ta fara kuka me yasa baza ki bar abunda kuke yi ba ki dauke ta, kece kika tunzurata take kuka har zazzab'i ya kamata."!! Cikin mamaki nake kallonsa ganin da gaske yake maganar nace"Kana nufin nice na d'ora mata zazzab'in kome. "? D'ora min ita yayi a jikina yace." Nifa ba haka nake nufi ba yanzu dai bata maganin sai muyi magana." Tsaki nayi niyyar inyi masa ganin rainin hankalin sa yayi yawa sai kawai na fasa na rike baby dake zura hannuta cikin rigata kamar me son tasha nono tana kuka da makyarkyata ban tab'a jin tausayin yarinyar ba irin na yau take wasu zafafan hawaye suka soma zubo min.......... Nace"Baby sannu kinji maganin ya mik'o min yace." Bata mu gani." Karba nayi na fara kokarin bata ta datse bakin ta.... Hannu na sanya na bude bakinta da sauri na d'ura mata maganin ta had'iya d'aga ta nayi ina girgiza ta sai shashsheka take yi ns rungume ta kam a jikina.


Yana tsaye a kanmu har Lokacin da nasamu baby ta sauke ajiyar zuciya bacci ya dauke ta, lura da yayi da hakan ne ya zare hannunsa daga cikin aljuhu ya fara kokarin d'aukar yarinyar dake rungume a jikina tana sakin ajiyar zuciya... Rike ta nayi kam a jikina ina hararasa Hankali nace "Zata tashi fa......... Bai ce min komai ba ya bar dakin na bishi da kallo cikin jin haushi kwantar da baby nayi na gyara ta sosai kana mike a hankali na shiga toilet domin dauro alwala,  sallah nayi na kwanta kan daddumar bacci me nauyi ya dauke ni, Lokacin Amjad ya shigo ya tadda duk suna bacci daga ita har babyn sun bashi tws


 Tausayi sosai Asma'u ya dauka kamar wata jaririya ya kwantar da ita kusa da baby hijab din jikinta ya ke kokarin cire mata ta bude idonta da sauri!! Mik'ewa tayi zaune tayi tana kallon shi. Ita yake kallo babu yabo babu fallasa yace." Ki huta kema naga kin bacci a kasa ne." Hannunsa ta kalla dake rike da hijab dinta yak'i saki..... Kauda kanta tayi tana kokarin sauka kasa dawo da ita yayi da hannunsa yana fad'in "Ina zaki je? Babu fuska tace" Zan shiga band'aki ne." Sakin ta yayi ita kuma ta sauko band'aki ta shiga cikin rashin sanin abinyi, kawai sai ta tsiri wanka, shi kam cikin shiri yake domin futa amma ganin yanayin Asma'u ya tada masa da sha'awa yana jin ko ya futa bazai iya komai ba dama daurewa kawai yake yi domin kar ya nuna mata zulamar sa... Zama yayi yana jiran futowar ta



   Asma'u ta manta d'auka ya futa daga dakin sai ta futo daure da guntun towel iya cinya hankalin sa nakan wayarsa yaga futowar ta ta kasan idonsa da yanda tayi saurin komawa da baya.. Girgiza kansa yayi kurrum ya cigaba da latsa wayar sa. Kayan ta tayi saurin mai dawa ta futo tana b'ata fuskar ta... Hankalinsa kan wayar shi yace." Wanka me kikayi da rana haka." Shiru nayi masa kawai ni so nake ya bar mun dakin naga ma futa zaiyi daga gidan dama duk a takure nake zaman shi a gidan kwana biyu kacal. Yace."ko mafarki kikayi."?



   Sarai na fahimci inda maganar sa ta dosa share sa nayi na zauna kujerar mirror a takure aje wayar yayi ya karaso gurin, k'amshin turarasa ya dabaibayeni rumfa yayi min hade da tsare ni da idonsa yace." Ina tambayar ki. "? Shiru nayi masa ina jin fad'uwar gaba.... Sunkuyowa yayi ya talfamo fuskata cikin tafin hannuwan sa ya kura min ido, ni kuma sai kauda kaina nake cike da fargaba. Bakinsa yake kusantowa dashi fuskata na rintse idona da k'arfi na mike, shima Mik'ewar yayi da sauri ya rike hannuna yana ya mutse fuska yace." Meye haka? Kike wani furgita da abunda kin San shi." Nace"Wai ba futa zakayi bane don Allah kayi tafiyar ka idan zakaje ni Wallahi na kan rasa inda ka sanya gaba ka k'yaleni mana. "



   Miskilin murmushi yayi yace." Futa zanyi amma na fasa kuma kece kika hanani futa." Da gefan ido na kalleshi ina kokarin kwace hannuna a hannunsa, fuskarsa ya kara kusantowa da tawa nace "Wai meye hakane."? Cikin shakakkiyar murya yace." Sha zanyi.!!!!!! Yanda ya fad'i maganar zaka tabbatar bashi da kunya.. Nace" me zaka sha."? Bakina yana nuna da idonshi! Ban San sanda naja tsaki ba ina kokarin fuzge hannuna cike da takaicin sa kamar ba d'azu yaga yimin rashin mutumci ba.



    Bude idonsa yayi sosai ya zuba su a kaina! Nayi kasa da nawa ganin yanda NASA suka yi ja gasu sunyi kananu dasu yace." Nu kike wa tsaki kan nace zan sha bakin ki."!! Shiru nayi kaina a kasa zuciyar na wani irin bugawa.!



    Gyad'a kansa yayi yace." Kinyi dai-dai Zan sha karshen ki yanzu kin jawowa kanki."!!! Kafin in Ankara ya dauke ni cas bed din ya cilla ni na mike da sauri ina nuna masa baby dake bacci da hannuna... Ko a jikinsa yayo kaina zai danne Allah ya bani sa'a na mike da sauri na dira kasa kofar futa na nufa kafin in bude ya kama ni ya matse jikin kofar rigar jikina ya sabule daga tsaye yayi min rik'on tsauri!! Shanyayyun idonsa ya zuba min  tsoro ya shige ni domin nasan kaina bana so ya  gano a matse nake dashi yasa na dinga kauce wa shi kuma yana kara kusan to ni har ya samu nasarar kama bakina ya fara tsotsa kamar Wanda ya samu sweet


 Jikina nane yayi bala'in mutuwa  jin yanda yake tsotsar harshe na hade da leb'una na ban San sanda na bude masa bakin gaba daya ba na cigaba da hadiyar yawun shi da ba tare da nasan a wace duniyar nake ciki ba. Gaba ki daya ya gigita min lissafin domin tuni ya cire min brziya inda yake wasa da hannunsa a guda a k'irjina yana fidda wani irin nishi!!!! K'afafuna suka tsami sun gagara daukata sai na fara kokarin fad'uwa k'asa tare muka zube dashi, nayi plate kasa shi Kokarin cire rigar jikinsa yake da ta fara ya mutse wa dake shadda ce  ya jefar gurin k'afafun sa ya raba a kaina ya rankafo sosai Brest dina guda ya kama da bakinsa yana tsotsa d'ayan hannun kuma yana Mirza d'ayan.... Wani irin hali na shiga mai mutukar wahala rintse idona nayi tam! Domin bana so na bude na kalleshi saboda kunya  na lura bashi da kunya ko guda ganin yanda ya wani k'aramin shu'uman idonsa yana kallona ga beast dina a bakinsa yana Mirza guda na kasa hanashi..... Hannuna guda ya rike a nashi yana sakin wani irin nishi kafin in an kara naji tsinin a barshi a jikina da k'arfin ta tsorata nayi sosai na bude idona sai na ganshi daga shi sai gajeran wando duk ya cire kayan jikinsa, kamar in kurma Ihu naji ganin baya cikin hayyacin sa yasa na tattaro k'arfin da yayi min saura na kwace kaina, fad'uwa yayi gefe na mike da sauri.... Hannunsa ya sanya ya jawo kafata na fado kanshi.... Idonsa ya rufe tsam!! Yak'i kallona matse ni yayi a jikinsa yana sakin ajiyar zuciya... Mintuna goma muna haka sannan  ya sake ni Mik'ewa yayi yana hararata ya shige toilet  cikin wata irin tafiya. Ni kuwa da sauri na kauda kaina ganin yanda wani Abu ya mike cikin wando sa duk na tsorata. Yana shiga toilet din nayi saurin Mik'ewa kayana na sanya da sauri na futa daga d'akin.







*6/12/2019*

[12/7, 7:46 PM] .: *BABBAN YARO*

*76*







 Ido muka had'a da granny dake zaune a parlor tana gyara carbin ta, kallo ta bini dashi cikin zargi.. Take naji kunya ta kamani saboda nasan dole ta fahimci wani Abu aikuwa tace"Lafiya kika futo a gigice."! Karasa nayi kusa da ita jikina babu kwari Sam naki yadda na kalleta nace"Lafiya Granny ." kallona dai takeyi tana gyara carbi ni kuma kunya duk ta ishe ni, tace" Ina Abban baby." Yana ciki." Abunsmda nace kenan nayi shiru.



   Minti biyar tsakani na dai-dai ta hankalina tace"Nasan abunda ya koro ki a guje daga daki." Kasa kallonta nayi ina mamakin tsohuwa da sa'ido, ta cigaba da cewa"Har 'yar Uwar ki ta kare rayuwar ta ban tab'a gani ta guji mijinta ba ke meye dalilin ki."? Nace"Granny ban fahimci abunda kike nufi ba."!



   Hararata tayi tace"Ni ba yarinyar bace Asma'u kin futo daga d'aki kina haki! Da zare ido kice min babu komai. Me kike nufi."? Kallonta nayi ganin yanda ta fututtuke fuska ! Bude baki nayi zanyi magana ta d'aga min hannu babu wasa a fuskarta tace"Tashi ki koma gurin shi.""! Baki na rawa nace"Ina...in ai futa zaiyi."  


  

  Tace"Idan baki tashi kinje ba Allah yana fushi dake wallahi mala'iku na tsine miki Ko mu da muke mutan da ba muyi gudun miji ba sai Ku 'yan zamani ni d'in nan da kika ganni kullum sai na bawa mijina hakkinsa har sai ture ina so kiyi koyi dani ko mijin ki bai neme ni ki ki mik'a masa kanki."



   Dariya tsohuwar ta bani ni kam ina ganin duk irin tsananin sha'awar dake damuna bazan iya Neman shi ba, tace"Ki tashi ki koma dakin wannan guje-gujen da kikayi ya nuna min har yanzu wani abun bai afku ba. Ke dashi, Saboda haka maza so nake ki samu cikin 'yan tagwaye." Sosai naji kunyar ta jin abunda take fad'a narasa me yasa tsoffafi basa jin kunyar fad'ar magana.


 Kafin nayi wani yunk'uri ya fito daga d'akina fuskar shi a had'e! Kai tsaye bedroom dinshi ya nufa granny tace"K'ato zo nan." Tsayawa yayi daga bakin kofar yana kallonta, tace"Kazo nace" babu fara'a ya karaso gurin  tace"Meye ya faru naga ta futo tana nishi

"! Tambayar granny ta bashi mamaki k'warai murmushi yayi cikin zuciyar sa, kana ya kalli agogon hannunsa yace." Neman ta nayi a shimfid'a taki."! Kai tsaye ya fad'i maganar kunya da takaici kamar su kashe ni.... Granny tace"koda naji dama  nasan hakane to koma ciki gatanan." Dariya yasa yace." Ni na fasa dama futa zanyi sai na dawo." Kokarin tafiya yake granny tace"Kayiwa Allah ka koma ciki yanzu zanturo ta." Yana dariya yace." Nafasa fa domin wannan maganin da kika bani ya daina mun aiki." Granny tace"Zan nemo maka wani insha Allah ai duk laifin ita Asma'u ne da ta hanaka.""" Tab'e baki yayi yace." Rabu da ita granny ina ganin zan bi sha'awar Inna Suwaiba ne." Granny ta kalleni tace"Kinji ko."? Tsabar bakin ciki da takaici yasa na mike na bar musu gurin da ita dashi duk na lura basu da kunya hummm.


   Amjad kaya ya sanja domin dai shaddar dake jikinsa duk ta ya mutse ya futo cikin suit granny na zaune a gurin tana sakawa da kwance wa yayi mata sallama daf da zai futa tace"K'ato don Allah kar ki bi matan banza ka rike sha'awar ka har ka dawo gida ga iyalinka insha Allahu zan yi mata fad'a." Sosai tsohuwar ta bashi tausayi Sam bata son ta ganshi cikin damuwa yace." Kar ki damu granny insha Allah zan kiyaye sai na dawo." Tace"Ubangji Allah ya tsare min kai duk inda kake ya kare ka daga sharrin mahassada da magauta." 


    Rambo ne ya bude masa mota ya shiga ya zauna ya zauna kusa dashi doh-doh yaja motar suka futa daga gidan.....Gabakid'aya ma'aikatan shi sun hallara  a gaban shi mutum guda ake jiran zuwan shi wato Bashir Manager har yanzu bai zo ba zargin da ake masa ya tabbata kenan Amjad duk wani bunkice ya gama shi kan abunda ya faru a company sa wattanin baya da suka wuce,al'amarin ya faru ne da saka hannun Manager wato Bashir da hadin bakin k'ananun ma'aukats Wanda sune suka ji tsananin azabah da horo suka fad'a.... Amjadu yayi mamaki wannan al'amari Babu abunda baiyi wa Bashir ba na rayuwa Da abunda zai saka masa kenan take police din dake tsaye a bayan shi da 'yan jarida suka nufi gidan Bashir din cikin motar su, sunyi alk'awarin duk inda yake zasu nemo shi dole yazo ya fad'i wad'anda suka sanya shi aikata wannan mummunan aiki.


Ko da suka isa gidan Manager sun taddashi cikin tsananin damuwa da tashin hankali ga ciwo yana fama dashi a kwance yake magashiyan ga iyali ga rashin abinyi babu abunci hakkin Allah da Amjad ya kwantar dashi da ciwon zuciya... Babu imani police din nan suka tasa k'eyar sa gaba 'yan jarida na ta faman daukar shi a hoto, tun a mota yake kukan takaici da nadama da yasani bai aikata ba gashi kud'in da ya karba gurin aikata abun 'yan fashi sun shigo sun kwashe domin shi yana ganin kamar da hadin bakin Mai citta gurin zuwan 'yan fashin gidan sa yayi biyu babu uku ba ko daya bashi ga tsuntsu bare tarko hausawa suka ce idan kace tukunyar wani bazata tafasa ba tom kaima taka baza tayi ba..... Kafin kace komai har jama'ar gari sun fara taruwa a kofar  rujajan company da ya Riga ya mutu babu mamora du suna dauke da abubuwan duka suna jiran  Manager su sambade shi... Labari ya watsu a gari dalili wasu kafafen yad'a labarai da suka fara maganar... Haka a ka shigo da manager a rirrike 'yan sanda na kare shi saboda dukan da jama'a suke kai masa da gorori duk da haka sai da suka fasa masa kai jini ya dinga d'iga a goshin sa duk yayi wiki-wiki suka isa dashi gurin mai gayya mai aiki wato Amjadu Mainasara.



    Mai girma governor tsaye  a parlor shi hankalin shi a mungun tashe jin abunda yake faruwa a gari, shifa ya dauka yaron ya hak'ura Ashe kwance-kwance yayi musu sai da suka saki jikinsu mutukar sunan shi ya futo cikin wannan badakalar to babu shakka yasan ya gama amfani a garin kano yasan jama'ar gari sai sun kusa kashe shi da iyalinsa gashi daf ake da zab'e bayan nan kuma yasan daga sama gurin shugaban kasa sai ya fuskanci hukunci mai tsanani watak'ila ma sai ya daure shi.... Kaiwa yake yana kawowa cikin tunanin Neman mafuta.



   Matar shi ta futo cikin kwalliya ta tardar shi cikin wannan halin nan take tambayar sa duk ya warware mata komai murmushi tayi tace"ka kwantar da hankalin ka mijina Kaine dai akan mulki kana da damar da zaka iya sawa ka hana kuma insha Allahu mulki sai ya dawo hannunmu mune zamu maimainta zama kan kujera daram!! Ka sanya su Lauje da fafake Kumurci tare da police suje su tashi taron idan ta kama ma su saki harbi da tiyagas tom zakaga kowa na kokarin guduwa domin ceton ransa. Nan su Lauje sai su dauko manager din su zo dashi mu kuma mun San inda zamu yi dashi ka San dai karshen zancan."



   Take governor ya yarda da sha'awarar matar shi ya tashi tsoffafin ya ranshi da police na gidan gomnati suka nufi  gurin domin  tashin taron da tarwatsa jama'a



  Wani irin mari Amjadu yake kifawa Bashir yana tambayar shi dalilin da ya sanya ya aikata wannan mummunan aiki Bashir sai da ya suma sau uku domin Amjadu zagewa yayi ya dinga labta masa wata murtykekiyar bulala yana fad'i "Bashir baka da amfani a duniya nan tunda dakai za'a had'a baki ayi wa Allah da manzon sa izgilanci kai cire ta tawa ni me sauki ne tunda bawa ne makaskanci irin ka, da iyakar ni kuka tsaya abun bazai dame ni ba, dani da Ku kunje fa mu cikin masifa da tashin hankali da fushin Ubangji ko ka fad'a min wad'anda suka sanya ko baka fad'a ba min ba ni na sam su kuma karshen su yazo da izinin Allah."!!



 Manager ya fad'i a gurin yana wani irin nishi! Mai wahala kafin kace kwabo ya kara suma take Amjad din ya kwara masa ruwa sanyi karara ya mike a zabure!Wanda yayi dai-dai da sakin harbi a gurin ji kake tas!tas! tas! Kafin kace kwabo gurin ya hargitse!! Hayakin tiyagas ya d'ume gurin sai atishawa ake ana Neman d'auki!! Wannan ya basu damar shiga ciki Amjad na ganin su sun shigo a guje ya sanya su Rambo su dauke manager su b'oye ko ina ne domin yasan shi suke nema..... Bindiga suka saito dai-dai kanshi zasu harbeshi yayi saurin sunkuyawa!! Take suka wuce da gudu!!! Rambo dake sab'e da manager a kafad'a ya fara kokarin haura Katanga!! Lauje ya  hango shi da sauri ya fuzge bundigar hannun wani d'an sanda ya saita k'afar Rambo ya bashi harbi take Rambo ya fad'o kasa shi da Maneger dake a sume!! Ihu Doh-doh ya kurma!! Yayo kan Rambo yana duba k'afar shi dake zubar da jini!! Ganin Lauje da wani d'an sanda sun yanko da gudu gurin ya sanya Doh-doh daukar Manager a kafad'a cikin jarumta ya fara kokarin haure Katanga... Lauje! Ya duba hannunshi, Ashe lokacin da yayi harbin jefar da bundugar yayi a gurin!! Da gudu ya juya da baya domin d'aukota! Amjadu ya soka masa hancin ta a k'irjinsa fuskar sa a mutukar murtuke!!! Lauje ya d'aga hannunsa sama! Cikin saranda! Amjad ya hade hannunwan sa biyu cikin jarumta ya murde su ya rike tamau! Suka fara tafiya har suka karasa inda Rambo yake kwance cikin jini yana nishi lokacin kuma Doh-doh ya samu nasarar dirga da Meneger k'asa ya nemi mab'oya Ashe bai tsira ba 'yan jarida da sauran police d'in gidan gomnati sunga shi take suka rufa masa baya..... Wani d'an jarida shi ya fara isa gurin ya ji lokacin da menegar yake cewa"Duk wannan abun da ya faru daga gomnati ne me girma governor shine da wasu 'yan kasuwa suka tilas tani tare da bani makudan kudi miyan goma sha biyar kan in b'ata sana'ar Amjadu domin ya durkushe a cewar su bashi da amfani kuma Asali shi din ba Dan Asalin najeria bane babu yanda za'ayi yazo ya dinga cin moriyar kasa saboda haka Dole a rusa company yaje kasarsu su ya gina musu shine ni kuma nazo muka hada baki da wasu daga cikin ma'aikatan company muka futar da kaya masu dauke da sunayen Allah da manzon sa." Manager yana kuka yake maganar ya rike Doh-doh sosai yace." Ka nemar min ga fara gurin ubangidan ka nasan mutuwa zanyi ko na rayu nasan governor bazai barni inji dad'i ba. Aikuwa wannan d'an jaridar ya gama nad'e maganganun manager a na'urarshi.. Manger ya fara wani irin tari kafin me ya amsa kiran ubangiji bayan yayi Kalmar shahada Allah kenan manager ya mutu da kalmar sha hada a bakin sa.



Ganin Police din gidan gomnati sun kusa iso wa gurin yasa wannan d'an jaridar Neman mab'oya wani siririn guri ya shiga ya b'oye yana gyara na'urar shi inda ya saita camera shi dai-dai gurin yana daukar duk abunda yake faruwa a gurin.... Menegr suke kokarin kwace wa daga hannun Doh shi kuma ya rike gawar tamau yak'i sakinta domin yana hango zuwan Amjadu gurin Wanda yake rike da Lauje!! Sai da suka iso gurin sannan doh-doh ya sakar musu meneger Amjad ya buga masa tsawa akan me!! Yace." Sir Allah yayi masa rasuwa yanzu."" 


"Hahahahaha"!!! Yaran gidan gomnati suka kwashe da dariya take suka saki gawar maneger ta fad'i a gurin.... Kumurci ya nuna Amjadu cikin tsageran ci yace." Abunda kake son ji daga bakinsa baza kaji ba!! Ko bai mutu ba mu zamu kashe shi!!! Mu kaishi lahira! Hahahahaha!! Kai da kake D'an karoro d'an gudun hijira kazo garin mutane kana mana mulkin mallaka wallahi idan kayi wasa sai mu maida ka garinku na gado tsirara.!!! Amjadu yaji zuciyar sa na wata irin tafasa ga takaicin manager ya mutu bai fad'i komai ba ga takaicin maganganun da kumurci yake yab'a masa, cikin zafin zuciya ya saki Lauje! Da ya galabaita ya fad'i gurin kan Kumurci yayi cikin jarumta ya Kai masa naushi!!! Kafin kace kwabo fad'a ya hautsine tsakanin Amjad da Kumurci, fad'a da gabb'ai! Ba da makami ko bundiga ba............




*Tofaaa*

Ran maza ya b'aci









*7/12/2019*

[12/7, 8:59 PM] .: *BABBAN YARO*


*77*






Sosai ake bata kashi tsakanin Amjad da Kumurci sai tada k'asa suke yi a gurin, Kumurci dake mak'ale da wata matsiyaciyar wuk'a mai mugun kaifi a jikinsa ya fuzgo ta da sauri ya d'aba ta kirjin Amjadu!!! Cikin zafin nama ya k'wace kansa daga rik'on da Amjad din yayi masa suka bar gurin a guje!! Doh-doh yayi kan ubanginsa da da gudu ya d'ago shi cikin tsanani. Tashin hankali jini tuni ya b'ata masu jiki, cikin tsananin jarumta Amjad ya mike tsaye hannunsa dafe da k'irjina da yake jin wani irin zafi da zugi a gurin ya rintse idonsa ya bud'e su kan Doh-doh yace." Rambo yans cikin halin taimako. "!! Cikin tashin hankali doh-doh ya kamshi yana fad'in" Sir kaima a halin yanzu taimako kake nema, mubar gurin nan domin ns lura mutanan ran ka suke buk'ata!!!


 Amjad ya mike tsaye a daddafe jini duk ya bata masa hannu Doh-doh us rike shi suna kokarin futa cikin jama'a, da sauri d'an jaridar nan ya futo daga mab'oyar sa ya k'araso gurin tare da kama gefan kafadar Amjad din yana masa sannu kana yace." Yallab'ai insha Allah Kaine kake da nasara kuma insha Allah karshen mutananan yazo domin duk abunda ya faru a gurin nan ina dashi cikin na'ura ta insha Allah sai mun tona musu asiri."! 



   Amjad yaji dadin wannan Abu take yaji k'warin a jikinsa duk da cewa yana jin jiki domin ba k'aramin suka wuk'ar tayi masa ba daurewa kawai yake yi suka futa cikin dandazon jama'ar gari dake ta hatsaniya da ta kura sai rigima suke  da yaran gidan gomnati, futowar Amjad din ce ta dauke musu hankali, su kuma suka samu nasarar guduwa bayan sun faffasa galashin motar Amjad yayi raga-raga!!.... Sam wannan bai dame shi ba, burinshi kawai mai girma shugaban kasa ya San abunda yake faruwa a jahar kano domin daukar mataki akan governor bisa wannan danyan aikin da suka yi.



    Wasu matasa ya sanya suka dauko Rambo suka sanya shi a mota Rambo saboda tsabar galabaita da yayi Sam ya kasa magana sai gumi yaki ga jikinsa yayi bud'u-bud'u!!! Shi kanshi Amjadu din Jikinsa bud'u-bud'u da k'asa saboda tumurmuson da sukayi a kasa!



     Yini nayi cikin zullumi da fargaba da fad'uwar gaba misalin biyar da kwata muna zaune a parlor ya shigo gidan, sallamarshi muka amsa dukaninmu muka bishi da kallo, wata irin fad'uwar gaba ta rikito min ganin shi cikin jini a jiki duk k'asa!! Salati nake a zuciya ta na mike zumbur!! Granny kuwa ai kafin ya karasa shigowa ta riske shi bakin kofa ta fashe da kuka tana fadin "Dama fad'uwar gaban da na yini ina kenan innalillahi wa'ina ilahi raji'un."!!! Kuka take sosai ta rirrike shi kwata-kwata ta hanashi magana "Hatsari kukayi kome!? Ooh ni jikar mutum biyu, Asma'u kinga abunda na yini ina fada miki ko watak'ila tunanin abunda kikayi masa ne ya sanya a ransa don Allah ki kula da mijin ki." Yanda Granny ta hakikance tana magana ne zaka fahimci ba a cikin hankalin ta take ba kuka take yi ya samu ya shige bedroom d'insa ba Tare da yace mana komai ba.

Kallo na bishi dashi jikina na rawa!! Granny tace"Kinyi tsaye a gurun baza ki bishi kije meya faru ba."!? Kafin ta rufe baki har na bud'e d'akin na shiga. Yana tsaye tsakiyar dakin yana kokarin cire rigar shi na karasa gurin da sauri! Nace"Abban baby men..... Meya faru wai."!!! Shiru yayi min. Yana cire rigar shi na fasa wani ihu! Ganin naman kirjin shi a waje fatar ta kwailaye jini jazur Ashe suit din jikinsa shine yake tsane jinin yana cire wa ya fara kwatanya a jikinsa yana d'iga k'asa." Hawaye shab'e-shab'e a fuskata nake nuna gurin da hannuna na kasa cewa komai!



    Wuce ni yayi zai shiga toilet na bishi da sauri rike hannunsa nayi nace"Kana ganin yanda jini yake zuba a jikin ka ko ka damu abban baby ba a wasa da rai kaji tausayin tsuhowa kaji tausayin baby wacce bata San meye rayuwa ba, don girman Allah ka daina wasa da ranka."!!! Cikin dauriya yace." Yanzu me kike so ayi miki."!? Ina zubar da hawaye nace "Ka bari a duba gurin nan kar ya zama matsala."!! Murmushi yayi me ciwo yace." Zanyi dressing gurin da kaina kar ki damu." Girgiza kaina nayi nace"Ka Bari a kira Jahid ya duba sosai wai kai baka ganin yanda jini yake zuba ne."!!! Kallonta yake cike da mamaki ganin yanda take hawaye duk ta tada hankalin ta yace." Mik'o min wayata gata can." Da sauri na mike na d'auko.


   Jahid ya kira a waya  tun kafin ya fada masa komai yace." Ganina akan hanya Aboki duk ina da labarin komai innalillahi wa'ina ilahi raji'un. "!!? Daga haka ya kashe wayar tasa......shuru dakin yayi, k'irjinsa na zubawa ido inda ciwon yake ina ji kamar a jikina na mike da sauri ina neme-neme a dakin dankwalina na cire da sauri na d'ora kan ciwon sam bana son gani.



  Wani irin d'as!d'as!d'as! K'irjinsa yake hakan ya tabbatar min Yana cikin tashin hankali da fargaba na kalleshi sai akayi sa'a shima ni yake kallo mun fi minti uku muna kallon juna daga bisani nace" Abban baby meye faru don Allah ka fad'a min. "!?


     Idonshi tsaye akaina yace." Tsautsayi ne kawai amma dai da da karar kwana da sai dai kuji mummunar labari." Naji fad'uwar gabana ya karu "Hadari kuka yi da mota."!? Girgiza min kai yayi alamun a'a! " To menene. "!? Nafada Muryata na karkarwa." Kai tsaye yace." Magauta ne suke so suga bayana."!! Kuka nasa nace"Allah ya fisu kaima ka daina biye musu idan naso kake mu rasaka ba, kamar yanda muka rasa Mimi." Shiru yayi mata kawai yana kallonta had'e da mamakinta sosai lallai yau yaga tsantsar sonsa a kwayar idonta.

[12/8, 1:16 PM] .: *BABBAN YARO*

*78*


Wallahi har ga Allah a lokacin na manta 'yar tsamar dake tsakaninmu dashi, hankalina ya tashi da yanda naga jini na zuba a jikinsa kuma bai damu ba.. Dankwalina Dana sanya a gurin ya jike da jini na sanya hannuna na daine gurin hawaye na kwaranyo min, yace." Wai kukan me Kikeyu ne."? Rasa abunda zance masa nayi kuma ban fasa shashshekar kukan ba, ina jinsa ya sauke ajiyar zuciya yace." To idan kuma akace miki na mutu yaya zakiyi ? Ki daina min wannan kukan bana so kina k'aramin zafi cikin zuciyata domin zubar hawayen ki a gabana babban tashin hankali ne."


   Shuru nayi masa dai ina kokarin maida hawaye na gefe guda kuma ina tunanin maganar da da yake cewa kukana nayi masa zafi cikin zuciyar sa...... 10 minutes Jahid ya shigo gidan iya parlor ya tsaya ya kira wayar Amjad din. Mik'ewa yayi zai fita na bishi a baya cikin mutuwar jiki. Jahid nata zayyanewa Granny abunda ya faru, ita kuma sai salati takeyi cike da tu'ajubi tace"Shikkenan da da karar kwana sai da akawo mana gawar sa, innalillahi wa'ina ilahi raji'un." Kuka ta fashe dashi sosai da taga Amjad din ya futo duk jini a jikinsa ta dinga fadin innalillahi wa'ina ilahi raji'un." 



   Zama yayi kusa da jahid din dake kokarin futo da kayan aiki yace." Granny please wannan abun fa bana kuka bane ko na tashin hankali don Allah kiyi min addu'a na yarda dukkanin abunda ya samu bawa daga Allah ne don Allah Ku daina daga hankalin Ku." Tace"Dole ne nayi kuka k'ato kai kadai nake gani a duniya inji dad'i narasa iyayan ka kaima bana so na rasa ka."!! Girgiza kansa kurrum yayi, Jahid ya soma yi masa dressing din gurin ciwon yana kara kwantar wa da granny hankali.



   Shuru parlor yayi minti goma ya kalleni dake tsaye kanshi, kasa nayi da kaina zuwa yanzu na fara dawowa nutsuwa ta yace." Kunna min TV nan ."  Cikin sauri naje na kunna masa kamar yanda ya umarce ni..... "Mik'o min romot d'in mu gani." Yafad'a yana Dan ciji lips d'insa saboda yanda yake jin zafin ciwon Ga Jahid ya dage sai wanke gurun yake da magani.



    Hannuna rike da romt din na karasa gurin na mik'a masa tare da matsawa daga gurin domin ji nayi tsigar jikina na wani irin tashi gani Kwata-kwata bana son ganin tashin hankali a rayuwata.  Tashar *NTA NEWS* Ya kunna dai-dai lokacin da suke yin labaransu na k'arfe shida cikin turanci suke fad'ar abunda ya faru a jahar kano tsakanin governor kano d'in da Amjadu *Young millionaire* hoton governor da Amjad  suka hasko lokaci guda suka cigaba da hasko badak'alar da ta faru a rujajjam company inda mutanan mai girma governor suka dinga b'arna da sakin harbi hade da tiyagas, da inda suke kokarin k'watar manager , kai har dambe  tsakanin Kumurci da Amjadu sai suka hasko dukanin abunda ya faru da inda Kumurci ya dab'awa Amjadu wuk'a a k'irji. Da kuma lokacin da suke dariya har suka samu nasarar guduwa bayan sun jikkta mutane tare da ragargaza gilashin motar Young millionaire. "

 Tsakanin ni da granny ban San Wanda yafi wani tsurewa ba ganin hatsaniyar da ta faru lallai kam da da k'arar kwana da sai dai a kawo mana gawarshi. Iyami ce ta shigo da baby a hannunta, karb'ar yarinyar nayi na rungume a jikina  ina kokarin danne hawayen da suke kokarin zubo min ayya nawa nake cikin zuciyata da ya mutu Shikkenan baby ta zama marainya gaba da baya zata taso bata San iyayen ta ba, naji tausayin tsohuwar data kwallafa ranta a kanshi.... Gabana ya fad'i  cikin zuciya ta nace idan ya mutu ke wane halin zaki shiga? Ni kaina nasan ina masifar son guy mussaman yanzu na San mallakina ne kawai ina share shi saboda sanin halin shi, nake tunanin gwara in kama kaina tun wuri amma ina ganin dole in sauke nawa in kula dashi idan ba haka ba abun zai yi masa yawa ko ina babu sauki duniya ga uban makiya Allah ka tsare min shi. Abunda nake fada kenan cikin zuciyata.


   Baby ta dinga yunk'urin sai ta sauka taje gurin shi ina riketa Hannunsa guda ya miko min wai in bashi.... Nace"Ta yaya zaka iya daukar ta sai ta dauje maka ciwon ."" a hankali yace." Ke dai ki bani ita nace, kar ki bari tayi wannan kukan ranki zai b'aci. "!  Gurin na karasa muka had'a ido da Jahid kunya ce ta kamani don Wallahi shaf na manta ban gaishe shi ba, nace" Jahid munyi lafiya yasu Salim." ? Murmushi yayi kad'an yace." Lafiya lau Salim nan lafiya zan kawo miki shi." Nace"To ina jira." Daga haka nayi shiru ina mik'a masa baby. Kallon fuskarsa nayi naga ta sauya karb'ar baby yayi ya rike ta da hannu d'aya, yarinyar ta dinga kokarin kai hannunta gurin ciwon tana so ta jawo bandejin da Jahid yake nad'a masa a gurin. Granny tace"Dama ganganci ne yasa ka karbeta kasan yanzu hannunta yayi ido komai kamawa take yi." 

Wasa yake da baby din bama ya sauraran abunda granny take fad'a. Duk hankalinsa na kan 'yar tashi.


 *****


A ranar kiran gaggawa ya samu governor dashi da Amjadu  daga fadar shugaban kasa, hankalin shi ya kai k'oluluwar tashi  yasan halin mai girma shugaban kasa da zafi da daukar Serious ba tare da b'ata lokaci ba ya nufi babban birnin tarraya abuja, cike da ta tsantsar tashin hankali da nadama.... Lokacin da sak'on shugaban kasa ya samu  Amjadu sam ba nuna wata fargaba ko tashin hankali ba, tabbas yasan gurin da zasu je ba gurin wasa bane dole yaje da shirin sa duk wasu matakan kare kansa ya tanade su hade da shaidu, yana jin jiki ya kira doh-doh a waya Wanda yake can asibitin malam Aminu yana kula da Rambo yace." Yazo yana Neman sa, a daran aka kira Ali wannan d'an jaridar shima Dole zai zama shaida a gurin duk da ba kutu zasu shiga ba amma yana ganin tafiya dasu tana da amfani...... Nan parlor muka kwana ni dashi da baby domin  babu yanda banyi dashi ba kan ya tashi mu koma daki yak'i hakanan na zaune kasan kafet shi yana saman kujera a kwance baby gefan hannun shi inda babu ciwon ko kadan ban rintsa ba kamar yanda bai rintsa ba. 


  K'arfe hudu na asubah ya mike yana kokarin dauke baby a jikinsa mik'ewa zaune nayi da sauri na dauke baby na kwantar kan kujera, ya mike zaune,  hannun shi na rike hade da tsira masa ido... A dake yace." Menene. "!? Hawaye ne suka fara sintiri a idona nace" Wallahi ina jin tsoron zuwan ka abuja nan."


   Tsaki ya ja k'asa-k'asa yace." Jiya kin kwana kina kuka ga rashin barci  kan abunda bai shafe ki ba, na fad'a miki tun jiya wannan kukan da kike yi bashi da amfani Sam na tsane shi."

 Hannunsa na saki na hade kaina da gwiwa sosai nake zubar da hawaye ni kadai nasan irin fargaba da take damuna akan wannan al'amarin gani nake yi idan ya tafi kamar yanda ya fada jiya za' muji mummanan labari!!! 



   Shashshekar kukan ta ne ya dame shi! Dafe kansa yayi ya yunk'ura ya mike tsaye cikin k'arfin hali ya tsuguna gabanta tare da d'ago kanta suka fuskanci juna..... Kallon-kallo muke ni dashi!! Ga hawaye shab'e-shab'e a fuskata.... Fuskarsa yake matsowa da ita, nayi saurin rintse idona hawaye suka zubo, harshen shi naji kan kuncina yana lashe ruwan hawayen. Nayi saurin bude idona ina kallonsa shima ni yake kallo kuma bai fasa lashar fuskata ba. Naji wani irin Abu a jikina lokacin babu abunda nake so illah in jini a jikinsa babu hali da babu ciwo da babun abunda zai hana na rungume shi. Sai da ya lashe ruwan hawaye na tas! Sannan ya mike a nutse ya shiga toilet din parlor.



    Jiki a mace na bishi da kallo har ya shige dakin , kwanciya nayi a gurin ina zubar da hawaye ni kaina kukan da nake yi ya ishe ni..... Alwala ya dauro a gurguje ya futa k'arfe biyar da rabi ya dawo gidan kai tsaye dakin shi ya shiga ya sanya Riga da dogon wando jins shart din mai botira ce kuma bata da nauyi sosai saboda ciwon sa, a gurguje yake yin komai har ya kammala ya futo hannunsa rike da wayoyinsa yaji dad'i da ya futo ya tadda Asma'u ba tashi daga parlor baby dake bacci kan kujera ya mannawa kiss a kumatu yayi saurin futa saboda jin tsoron rigimar granny.. Yana futa Doh-doh da Ali na tsaye, take Ali ya bude masa mota ya shiga shima ya zauna kusa da doh-doh yaja motar suka futa daga gidan. Kai tsaye airport suka nufa.

[12/9, 11:02 AM] .: *BABBAN YARO*




*79*




 Gabakid'aya wad'anda suke fad'a aji k'asar najeria sun hallara a d'akin meeting na fadar mai girma shugaban k'asa, Amjadu ne kawai mai k'ananun shekaru a cikinsu, duk sun girmeshi nesa ba kusa kai harda wandanda suka girmi mahaifin sa a cikinsu kuma dayawa daga cikin su k'abilu ne saboda haka suke komai cikin hikima da nutsuwa, duk wani bunkice mai girma shugaban kasa ya gama yi kuma ya tabbatar governor Alkanawi shine bashi da gaskiya duk wani dauki ba dad'i da ake da a jahar kano ya sani kuma shine ya haddasa ta, bayan yayi rantsuwa da alkur'ani gaban bainar jama'a zai yi kula da jahar sa zaiyi mulki tsakani da Allah amma ya karya doka, babu shakka a abunda yayi ba k'aramin Abu bane ya wuce gona da iri ta inda mai girma shugaban kasa yake ganin dole a hukunta shi, kuma mulki ya bar shi har abada domin a doka ta siyasar kasa duk governor da aka samu da cin amanar kasa za'a hukunta shi kuma  ya bar siyasa har abada don haka 'yan majalisa da hukumomin zab'e suka yanke shawarar juyin mulki ga mai girma governor Alkanawi domin su nawa jama'ar kano damar zab'o Wanda suke so ya mulke su daga nan zuwa wata biyu lokacin zab'e kenan.... Bayan nan kuma mai girima shugaban k'asa ya sanya dole hukumar  Efcc ta tsaurara bunkice a kansa domin alamun rashin gaskiya sun bayyana a fuskarsa. Wannan shine hukunci da aka yanke ga mai girma governor Alkanawi... Bayan nan kuma  Mai girma shugaban kasa da shauran k'ososhin k'asa suka jinjinawa Amjadu *Young millionaire* bisa ga NAMIJIN kokarin sa bisa kawo wa k'asar shi cigaba da jikinsa da kud'in sa da lafiya hak'ika idan k'asar najeria tana alfahari dashi da wannan aikin nasa. Nan mai girma shugaba ya sanya hannu a wata ta karda dake gaban shi, ya mik'awa na kusa dashi shima ya sanya hannu haka har sai dai mutum goma suka sanya hannu a wannan takarda kana takadar tazo gaban Amjadu shima ya karb'a ya sanya hannu ba tare da ya fahimci me takardar mecece ba.... K'arshe ta kardar ta koma gaban governor Alkanawi, hannu na rawa ya sanya hannu zufa suk ta jika jikinsa shaddar jikinsa duk ta jik'e yana sanya hannu wani soja dake tsaye kusa da shugaban kasa ya dauki takardar ya ajeta kusa da shugaba shi kuma ya had'ata da wasu takkadu ya rufe!!!


   Ambassador Aminu Ahli shine ya kalli Amjadu cikin turanci yace." Duk wani Abu da zaka yi a jahar kano Wanda kake ganin zai kawo cigaban kasa da talakawa mu zamu mara maka baya kaje kayi kanka tsaye zamu tallafa maka ni cikin asusuna na cire 50 Million's na baka domin kaje ka k'ara farfad'o da harkokinka da company ka da suka rusa, take jama'ar gurin suka dinga ma Amjadu kyautar ta bangirma Shi kanshi shugaban kasa sai da ya bashi 50 Millions.....*Innalillahi wa'ina ilahi raji'un* wanin hanin ga Allah baiwa ne *Amjadu Young millionaire* Ni Binta na taya ka murna hak'ika babu abunda yafi gaskiya a duniya dad'i wani lokacin akan yi maka Abu domin a kuntata maka amma daga k'arshe sai ya zame maka alkairi, Fad'ar irin mak'udan kud'in da Amjadu ya samu a gurin b'ata lokacine. Mai girma governor Alkanawi kamar ya mace saboda bakin ciki.Take Sojoji suka tasa k'eyar Alkanawi suka futo  dashi 'yan jarida da suke zaune a reception suka mik'e dama duk abunda yake faruwa suna kallo ta CCTV Camera aikuwa suka yi caaaa! Kan alkanawi suna so suji ta bakinsa, ido jazur yace." Sharrin shad'ain ne kawai da zugar mutane gashi sun kaini sun baro da k'arshe ina Neman afuwa ga al'umar jahar kano bisa ga abunda ya faru."!! Daga haka yayi shiru idonsa yayi wani irin jaaa sojoji suka tasa shi a gaba.


   To hakace ta kasance kan Amjadu manya manyan 'yan jarida suka sanya shi a gaba dole sai yayi magana , babu yanda ya iya cikin turanci yace." *Hak'ika wannan ranar bani da kamar ta a duniya saboda Allah ya nuna min gaskiya ga gaskiya CE, Allah ya wanke ni bisa ga zargin da jama'a suke min Na tabbata ubangiji baya bacci kuma shi sharri d'an aike ne  sunyi nufin cutata ubangji ya mayar da abun kansu saboda bani da hakki a Kansu nagode wa Allah da na tsalle ke wannan sharrin nasu kuma ina jinjina ga me girma shugaban kasa tare da mataikan sa hak'ika sun cancanci yabo da godiya a gare ni nagode k'warai da hallancin su a kaina."*

Abunda ya iya fada kenan ya wuce masaukin sa tare dasu doh-doh da Ali da yake cikin farin ciki da murna domin yana ganin dole ma ayi masa Karin girma gurin aikinsu saboda namjin kokarin da yayi.


   Kafin kace kwabo garin kano ya hargitse da Sowa da murna gari ya hautsine da hayaniya kowa na fad'ar ra'ayin sa kan abunda ya faru, matasa dattijai duk sunji dadin wannan hukunci da shugaban kasa ya dauka dama sun gaji da mulkin Alkanawi don haka sai suka yanke shawarar tsayar da Amjadu a matsayin mai mulkar jahar su, take wasu suka futar da hoton shi a matsayin governor mai jiran gado nan da wata biyu suka dinga bin jikin gidaje da kan titina suna manna kasuwanni da shagunan mutane suka dinga manna hotonan amjadu a matsayin governor.


   Duk abunda yake faruwa mun gani labarai Ya Aminu ya kirani a waya yana fad'amin min wai nasan abunda yake faruwa kuwa nace"Gani a labarai Ya Aminu ni bana son siyasa nan fa." ! Yace." Kiyi hakuri ki taya shi addu'a kinji ko."! Ni dai shiru nayi kawai hankalina duk a tashe burina kawai ya dawo gida gashi na kira wayarsa ya kai sau ashirin bai d'aga ba..... Daki na shiga nayi kuka na mai isata na futo na tadda Granny ta jurawa TV ido inda suka nuno Amjadu lokacin da yake bayanin godiya a fadar me girima shugaban kasa. Ta kalleni idonta ya Tara k'walla tace"Zo kiyi min bayani me suke cewa ne naga sojoji sun kewaye shi, ga mutanan masu nacin tsiya sun kewaye shi da na'ura fadamin me yake ce musu jikina duk yayi sanyi.."! 


Nace"Granny suna so ne ya zama governor kano babu wani damuwa sai Karin daukaka da ya samu kuma shine yake da nasara a tafiyar wannan 'yan jaridar da kika ga sun kewaye shi duk murna suke taya shi suna so su ji ta bakinsa ne."


 Granny tace"Alhmdullahi Allah nagode maka dama nasan addu'a ta baza ta fad'i 'kasa ba nasan 'kato bashi da hakkin su amma ni kam bana sha'awar siyasar nan akwai zube war mutumci da dai su k'yale shi kawai." 


Nace"Wallahi nima haka granny bana so amma gashi tun bai dawo garin anji ta bakinsa ba jama'a sun fara fidda hotonan sa a matsayin d'an takara governor ." Granny ta sauke ajiyar zuciya tace"To Ubangji Allah ya dawo dashi lafiya muji ta bakinsa ni dai sanin da nayi wa 'kato baya sha'awar siyasa ban sani ba ko yanzu." 



Shiru nayi mata zuciya ta nacan tunanin wani Abu. Mik'ewa nayi na koma bedroom dina waya ta na d'auka ina 'kara kira shi cikin sa'a ya d'aga, ajiyar zuciya na sauke cikin damuwa nace"Abban baby sannu."! Muryar shi bata futa sosai naji yace." Yawwa ya gida babu matsala ko."? Nace"Eh nayi ta kiran wayar ka kana gani ka'ki dagawa." Ajiyar zuciya yayi yace." Sorry  sai yanzu wayar tazo hannuna mybe lokacin da kika kira tana gurin Doh-doh."""" Shuru nayi yace." Shikkenan ko."!? Da sauri nace"Amma yau zaka dawo ko."? Kai tsaye Yace."A'a."!  'Kasa nayi da murya ta nace"Meyasa kasan fa ba lafiya gare ka ba." Kwanciya yayi kan bed yana lumshe ido yace." Menene damuwar ki da lafiya ta bayan idan ina nan d'in bakya kula ni. " Naji wani sanyi na shigata jin yanayin yanda yayi magana nace"Baby na kuka abbanta." 


'Karya kike yi sai dai idan kece kike kuka kina so in dawo ai na gane. " ya fada yana siriryar dariya , cikin jin nauyi nace"Da gaske nake don Allah yaushe zaka dawo."? Ajiyar zuciya ya sauke yace." Idan na dawo d'in me zaki bani. " ? Shiru nayi masa, yace." Ok bari in kashe wayata." Da sauri nace"Sai dai ka dawo d'in komai kake so." 

'Yar dariya yayi yace." Kinyi alk'awari ko." ?  Lumshe idona nayi ina jin wani fleengs nace"Eh" yace." Ok sai jibi zan dawo zan huta anan tukkuna hayaniyar gari tayi sau'ki kinsan in na shigo gobe zasu takura min ko baki San abunda yake faruwa bane."!?


Nace"Na sani munga komai a labarai Abban baby na taya ka murna kuma ina maka fatan alkairi har 'karshen rayuwar ka."!. Sosai yaji dadin addu'ar ta yaji yarinyar ta 'kara samun wani matsayi a zuciyar sa yace." Thank you my wife I will not leave you forever."!


Naji dadin abunda yace cikin jin kunya nace "Thank u my life patner."!! 'Kit!!! Na kashe wayar cikin jin kunya gabana sai dukan uku-uku yake ina mamakin yanda na sake har nake magana dashi haka.... Nashi 'bangaran kuwa rike wayar yayi yana sakin wani irin murmushi Wanda shi kad'ai yasan ma'anar shi, ya mike da kuzari a jikinsa ya shige toilet domin gasa jikinsa saboda wani irin ciwo yake masa ni kam nace" Dole ne ko don dambe da kasa kai da Kumurci!


 ********


Washe garin ranar Innah Suwaiba ta dira cikin gidan ita da 'yar ta Hafsa had'e da 'kullikan kayan su wai sun dawo gidan da zama domin labarin duk abunda yake faruwa ya isa gareta don haka arzikin d'anta ne tunda d'an 'yar uwarta ne itama ta dawo kusa a ci da ita.... Mamaki kamar ya kasheni na dinga kallon matar na marasa a wane matsayi zan aje ta, gaisuwar da nayi mata ma a banzace ta amsa, Hafsa kuwa ido ne tsakanina da ita granny tace"Haba Suwaiba ai ko wani kika kawo cikin gidanan kikace yana so ya zauna zai zauna saboda darajar ki ba sai kin dinga tashin hankali ba don Allah ki dinga yin komai cikin nutsuwa da fahimtar juna." Wannan magana da granny ta fad'a sai Innah tace"ai ta fad'a mata ba'kar magana ta inda take shiga ba tanan take futa ba. K'arshe dai granny bar mata parlor tayi domin baza ta iya da jarabar Suwaiba,  dakinta na bita na tadda ta a zaune nace"Granny wannan matar tana so ta d'aga mana hankali a gida." Tace"Sai hakuri Suwaiba taki sanin abunda ya dace Wallahi kiyi hakurin zama da ita ni kam 'kato na dawowa zan tattara in tafi inda nafi kauri."



Nace"Babu inda zakije granny kina gidanan domin ni dake zan zauna gaskiya. " tace"Yanda nake da matsayin a gidanan haka Suwaiba take dashi domin a matsayin uwa take ga mijin ki saboda haka ki kula da kyau." Kuka NASA nace "Wallahi kin San Allah bazan zauna da ita ba sai dake domin ina ganin idan ta cigaba da yimin wannan halin nata watarana zan rama ko in zage ta."



Ganin ina kuka yasa granny fadin "Shikkenan kiyi hakuri mu Bari tukkuna mai gidan ya dawo sai muji ta bakin sa." Hawaye na nagoge nace"Me zan girka miki na rana." ? Tace"ki bari Iyami sai tayi ke kije ki huta mana." Nace"A'a ki fad'a min dai." Tace"yi min towon alkama da miyar kuka." Nace" Tom" futa nayi daga d'akin na tadda  Innah Suwaiba ita kad'ai ta d'au 'kafa daya ta d'ora kan d'aya kicin na wuce ta Bini da banzan kalo tana Jan tsaki .!!



Me zan gani Hafsa na tsaye ta kunna gas sai fasa 'kwai take yi gefe ga Uwar doya nan ta tsame ta cikin wani kwando ta d'ora mai zata fara soyawa..... 'Bata fuska ta nayi nace"Hafsa meye haka kikeyi min a kicin duba don Allah gurin a gyare duk kin bi kin zubar da 'bawon 'kwai da doya Haba don Allah."!!



Hafsa da ada take bala'in tsorona itace yanzu ya juyo tayi min wani banza kallo ta d'auke kanta daga kaina ta cigaba da abunda take..... Wani irin zagi na kurma cikin zuciyata amma a zahiri nace"Ko bakyajin abunda nace ne."!!! A wula'kance tace"Ina ce da akwai me aiki da zaki wani dame ni da surutu, idan na gama aikina sai ta zo ta gyara." 



Gyad'a kaina nayi nace"Yayi kyau."! 'Karasa wa nayi kusa da ita kawai na murd'e gas d'in na kashe had'e da dauke man da take soya na aje kaskon gefe kana na kalleta fuskata babu annuri ko na kwabo nace"Futa ki bani guri in gama abunda zanyi in yaso sai ki dawo kiyi kome Nene. """


"Baki isaba."! Tafad'a kanta tsaye gashi ta tsare ni da ido har da ri'ke 'kugu gaskiya nayi mamakinta nace" OK sai inga yanda zakiyi min iko a gidana."!

Wata irin shewa ta buga tace"Masu gida manya, hahahahaha da dai bamu San komai bane sai kice wani abu, to mun San komai aure ne akayi shi dake da My love d'ina bisa 'kaddara da har zaki dinga wani famkama da hura hanci kin auri me kud'i tom bari kiji ba a sanja 'yan uwa har karshen rayuwa ke kuwa fa my love zai iya sanja ki har abada ya kawo wata saboda haka ni nan da kika ganni jinin mu d'aya da Amjadu za'a iya tsaga jikinsa a tsaga nawa a ga jinimu yazo d'aya saboda haka ki iya bakin ki Wallahi idan ba hakaba wannan gallafirin auran naki zamu iya yin sanadin sa."


Naji wani irin takaici ya rufe ni jin abunda Hafsa take cewa danne zuciyata nake yi ina kokarin hanata aikata abunda tayi niyya nace"Hafsa kin San halina ba tun yau ba bani da kyau ke kanki kin sani bana so muyi irin wannan zaman daku ki iya takunki ki bar shiga hurumin da bana ki ba, idan kin 'kiji zaki sha mamaki wallahi."!! 


A hasale tace"Ke kar ki kawo min maganar banza da wofi da dai da kikayi min abunda kike so a skull lokacin ki ne yanzu baki isa ba wallahi kutumar ubanki zanci la'ada waje kuma in zauna....... Kafin ta 'karasa na tsinke ta da wani irin gigitacan mari! Ta rike kuncin ta da sauri tana kallona da ido jazur tace" ni Kik....... Kafin ta 'karasa na kifa mata wani a d'aya kuncin nata, nace"Ina fatan yanzu kin tuno wacece Asma'u Sulaman 'yan a waki."!!! Ihu! Hafsa ta kurma ta d'auki soyayyan man dake cikin kasko ta watso min da sauri na kauce saboda nasan da zafin sa zai iya 'kona ni. Kaina tayo aikuwa santsin mai da 'bawon doya ya kayar da ita cikin man dake da sauran zafi kafin kace kwabo fatar hannunta ta kwailaye! Ina tsaye ina kallonta tana kuka.

Granny da Innah Suwaiba suka shigo kicin d'in hankali a tashe! Innah Suwaiba kaina tayo tana fad'in"Shine kika 'kona min yarinya saboda kina ba'kin cikin zata zama kishiyar ki shine tun yanzu kike so ki nakasta min ita Dan ubanki! Mari ta kai min a fusace.!!!









*8/12/2019*

[12/9, 10:38 PM] .: *BABBAN YARO*


*80*




 Nayi saurin dafe kuncina ina kallon matar cike da d'umbun mamaki! Ta cigaba da cewa"Shikkenan kawai saboda ta shigo tana soye-soye a gidan d'an uwanta sai ki 'kona ta da mai saboda sharri da ba'kin ciki to Bari kiji wallahi ki sanya a ranki sai kin zauna da ita a matsayin kishiyar ki, domin ita tudu biyu taci ga aure ga 'yan uwan taka."!

Ta 'karashe maganar tata cikin kumfar baki.


Hawaye masu zafi ne suke zurarowa a daga idona tace"Kina tsatsare mutane da idon ki na rashin kuny...... Kafin ta 'karasa granny ta katse ta ta hanyar fad'in"Wannan ba girman ki bane Suwaiba abunda ya kamata kiyi kafin ki yanke hukunci shine ki fara tambayar su me ya had'asu ba ki za'bi taki ba Asma'u ma 'yar ki tunda tana auran d'anki." Granny ta 'karashe maganar cikin sigar rarrashi.



Botsarewa tayi tace"Kina kallo fa ta 'kona mun yarinya wane irin ba'asi zan tsaya tambaya anan ga gaskiya a zahiri duk bakin cikinta baza ta ci arzi'kin ita kad'ai to kaji."!!



Cikin saurin na futa daga kicin d'in ina ji zuciya kamar zata fashe saboda takaici tabd'ija lallai akwai rigima mutu'kar matar nan tace zata zauna min a gida domin na lura bata 'kauna ta ko kad'an nima take naji wata irin tsanar ta ta shiga zuciya ta, zama nayi gefan bed ina tunani matakin da zan d'auka kan Hafsa babu shakka tayi ganganci tace zata had'a miji dani... Aure bazan hanashi yayi ba, kuma Hafsa 'yar Uwar shi CE bazan rabasu ba amma ko da wasa bazan d'auki raini daga gurin kowa ce shegiyar ba ciki kuwa har da ita Innah Suwaiba. 




Waya ta dake kan drawor ta fara ringing Sam banyi tsammanin shine ba ina dubawa nagan my one and only da abunda nayi serving d'in numbar shi kenan.


Murya 'kasa nayi sallama inajin ya sauke ajiyar zuciya kana ya amsa sallama ta, shiru nayi domin har yanzu akwai sauran 'bacin ran su Innah Suwaiba a tare dani.... Yace." Me kike cewa d'azu kika kashe min waya."?


Shiru nayi ina tunani nace" inajin shi yace." Kat ki 'kara kashe min waya daga yau." A hankali nace "Tom."!! Ina baby."? Ya fad'a cikin wani irin voice Wanda ya sanya ni jin wani yanayi nace" sun futa cefane da Iyami. "


Yanayin yanda yayi magana ya nuna min ransa ya 'baci yace." A kan me za ki bari a futa da ita kasuwa dole ne cefe nan." ! Na sassauta murya ta tare da fad'in"Dole ne mana tunda bamu da wasu a bubuwam a kicin Rambo bayan nan, Doh-doh kuma kun tafi tar...... Kafin in 'karasa ya katse ni a hargitse yace." Kada ki kuskura ki 'kara bari a tafi min da yarinya kasuwa ko ina gari ko bana gari Wannan si shirme ne ita Iyami me yasa baza je ita d'aya ba."


Cikin zuciyata nace "Ikon Allah ."! A zahiri kuwa ha'kuri nake bashi ina fad'in " Baby ce take kuka  dole sai Iyami taje da ita." Aiko saurara ta baiyi ba ya kashe wayar sa......

 Wayar nake bi da kallo cike da mamakin hakinsa Sam shi idan ya d'auki zafi baya tsayawa ya saurari mutum... Na fi minti goma rike da wayar a hannuna, kana Naji motsin shigowar Iyami parlor na futo kamar babu abunda ya faru nace"Iyami kin dawo ne."?


Tace"Na dawo yanzu baby nayi ta min kuka s hanya." Nace." Sakkota mu gani." 'Kokarin sakkota take daga baya ta sanya kuka Iyami tace" barta kawai a bayan nawa." Nace"Ke da zaki shiga kicin yanzu." Tace"Hakane fa yanzu da na shiga kicin din aje kaya nace"Ba'ki mukayi a gidanan ken..... Innah Suwaiba ta katse ta ta hanyar fad'in"Mu ba ba'ki bane 'yan gidane sai dai kece ba'kuwa." Iyami tayi saurin fad'in"A'a sannu Innah Suwaiba Ashe kece." Banzan kallo tayi mata tazo ta zauna kan kujera hannunta rike da wani plate cike da doya da 'kwai ta zauna ta fara cin abunta.



Iyami kicin ta nufa ni kuma na wuce d'akina rungume da baby domin nayi alk'awarin banza 'k'ara shiga har Kar matar ba gaisuwa ma don ta zama dole ne."



Waya ta na d'auka ina kirashi tana ta ringing ya'ki dauka har ta katse na 'kara kira ta katse bai dauka ba, sai da na kira sau uku bai d'auka ba na hak'ura nace Fushi yake yi kenan take naji zuciya nima nayi min zafi nace karfa wannan guy ya samu hanyar wula'kantani don yaga na saki jiki dashi dashi har yake mun fad'a domin a rayuwata na tsani in kira mutum a waya ya kashe ko ya'ki dauka.... Wata zuciyar tace min Kin manta Irin zaman da sukayi da Mimi dama kuma granny ta fad'a miki shi mutum ne me d'aukar zafi amma bashi da rik'o, lokacin sai naji zuciyata tayi sanyi saboda nasan zuwa dare ya sakko dole zai nemi ya kira waya ko don yaji gwalantun babynsa da ya saba. Ranar haka na yini sukuku sai bayan sallahar Isha'i sannan na futo parlor. Granny Iyami Innah da Hafsa duk suna zaune suna kallo Cikin kwanciyar hankali abunsu.... Kai tsaye daining na nufa domin cin abunci granny tace"Kin futo kenan." Ina tafiya nace"E Granny sannun Ku da hutawa. " hankalinta na kan TV tace"Yawwa kinga hankalina ya d'auke gurin kallon Wannan wasa Dad'in mu ko dad'in kowa ina son kallon diramar nan. " ta k'arashe maganar tana dariya... Ina kokarin zama nace"Ba kya kad'ai ba granny  shirin dadin kowa ya shiga zuciyar mutane sosai." Hira muke tsakani mu Innah Suwaiba na makamin harara ko kallonta banyi ba nagama abunda nake yi na bar gurin bayan nayi wa Granny sallama.



Ko da na shiga d'akinta wanka nayo jikina duk babu kuzari na duba wayata ya Kai sau biyar banda ko misscal d'insa ba, haka dai nayi shafe-shafe jikina sanyi 'k'alau na shirya baby cikin kayan baccin ta kwantar da ita nayi  saman cikins na kwanta rigingine waya ta na d'auka na lalubo numbar Munnu wacce muka rabu da ita tun ana ya gobe d'aurin auramu.




Buga d'aya tayi ta shiga Munnu da zumud'i ta d'aga wayar tana fad'in"Sai yanzu kika tuna dani saboda kin samu duniya ko."? Nace"Munnu ke wannan ya dama Wallahi ni fargaba duk ta cika min ciki kinsan dai abunda yake faruwa ko."? Tace"Ya Aminu ya fad'a min INA muku fatan alkairi Asmy." Nagode Munnu kin San wani Abu."? Tace "Sai kin fad'a."


'Wallahi Yayar Mahaifiyar Abban baby  ce ta sanya ni a gaba masifaffiyar mata Babar du Hafsa mai warin.! " munnu tace"Ikon Allah dama fa naji labarin 'yan uwan sune." Nace "Babu wai a ciki Munnu a takaice dai matar ta tattaro kayanta ta dawo gidan da ita da Hafsa."


Salati Munnu take yi cike da mamaki tace"Kaji mu da mata 'yar rainin hankali." Nace"Wallahi munnu ni ba wannan ba ma da tazo da sigar son mu zauna lafiya sai mu zauna meye duniyar amma Baki ga irin abunda take min ba, ke d'azu fa har da mari."! Munnu ta rike Baki cike da mamaki tace"Akan me ta mare ki." Nan na kwashe abunda ya faru tsakanin da Hafsa na fad'a mata 



Munnu tace"Meyasa baki ci kutumar Uban Hafsa ba wato ita Dan bata da hankali tana ganin a haka Amjadu zai aure ta lallai bata da hankali wallahi.


Nace"Hafsa dole in kiyaye saboda na lura matar na da matsayi a gurin shi kuma kema kin San halin d'aukar zafin guy kin San dai irin zaman da suka yi da Mimi shiyasa nake bin komai a sannu.: Ajiyar zuciya ta sauke a hankali tace"Kina da gaskiya anan kiyi hakurin zama dasu kafin kiga irin matakin da zai dauka nasan ki da saurin hasala da rashin hakuri ki danne zuciyar ki ga duk abunda zasuyi.'!! Nace " Insha Allah Munnu." Na muka cigaba da hira inda take tsokanata wai sai ta rigani haihuwa tunda yayana ya takura mata kullum Abu d'aya, nace"Munnu duk dake kema kikaje kina bankar maganin aunty Hauwa Dole ya Aminu ya samu guri." 

Tace" kuma Wallahi da farko na ji zafi amma da yayi na biyu na uku sai na daina ji sai dad'i. " dariya nayi nace"Munnu baki da kunya wallahi bakin ki ya iya fad'ar dad'i. " tana dariya tace"Sai kin ji yaya yake sannan zakice baki bazai iya misaltashi ba." Ina dariya na kashe wayar ina mamakin futsarewar idon Munnu.




12:25 na dare ya shigo gidan ko ina shiru sai 'karan Ac kai tsaye bedroom d'insa ya bud'e ya shiga a hankali gudun kar wani yaji motsin sa, wayoyinsa ya zube kan drowar gefan bed, ya shiga toilet ruwa ya had'a mai zafi yayi wanka tsaf ya futo jikinsa d'aure da towel mai fad'i  da wani 'karami a hannunsa yana goge jikinsa sama-sama saboda raunin dake kirjin sa don ma ya sha magani gurin ya dusashe don ba yayi masa ciwon komai yanzu sai dole bazai sanya Riga mai nauyi ba gudun ta Sosa masa ciwon.....wasu irin kayan bacci ya sanya a jikinsa irin na maza blue colour rigar mai mad'aurai daga gaba sai dogon wando har 'kasa bai daure igiyoyin ba ya bar k'irjinsa a bud'e, turare ya fesa a jikinsa kana ya gaye bed cike da gajiya bacci yake ji sosai. Shiyasa baya bukatar damu dukanin su har babyn da safe sa had'u yasan dai duk zasuyi mamakin dawowar sa yau din bayan yace sai gobe.


Ko minti goma baiyi da kwanciya ba bacci ya dauke shi mai nauyin gaske!!  Mafarki yake gashi na sex sosai da mace ya kasa gane ko wace yarinyar ce cikin mafarkin nasa yana ji kamar Asma'u amma yarinyar taki bashi Samar ganin fuskarta, a jigace! Ya farka ya duba jikinsa duk yayi kaca-kaca da bed d'in ga girman sa ya mi'ke sosai, babu nutsuwa a tare da shi ya bud'e kofar dakin NASA ya futa domin a lokacin ji idanunsa ya rufe  sosai yana tunano irin dad'in da yake kwasa cikin baccin sa don bai so ya farka ba, kai tsaye bedroom d'in Asma'u ya nufa sai aka yi sa'a 'kofar a bud'e take.





Anzo gurin.......







*9/12/2019*

[12/10, 10:12 AM] .: *BABBAN YARO*

*81*











 Fitilar d'akin ya kunna haske ya gauraye d'akin, can ya hango ta kwance kan bed ta rungume baby a jikinta suna bacci, cikin nutsuwa. Kashe Fitilar yayi ya 'karasa  bed d'in zama yayi a hankali yana janye blanket d'in da ta rufe 'kafafunta dashi ya fara shafa cinyoyinta da ya gani muraran kasancewar rigar dake jikinta iya gwiwa ce, sosai yake shafa cinyoyinta yana cije lips d'insa Joystick dinshi na 'k'ara mik'ewa.... Asma'u cikin bacci taji sanyi-sanyi na damun ta gashi kamar ana yi mata susa a jikinta, sosai take jin dad'i don dama dakyar bacci ya dauke ta saboda shauki taso Amjadu ya kirata a waya ko ta rage abunda yake damunta amma be kiraba da kyar bacci ya d'auke ta..... Bed din ya haye sosai a hankali ya d'auke hannunta da d'ora ma baby ya dauke baby a gyara mata kwanciya can 'karshen bed kana ya matso kusa da Asma'u da ta bud'e idonta a tsorace jin motsin kan bed din.


Cike da tsoro ta mike zaune tana fad'in "Waye."!? Cikin sha'kakkiyar murya yace." Nine."! Idonta ta bud'e sosai tana kallon inuwar shi, babu shakka shine Ashe ya dawo? Take tambayar kanta... Ajiyar zuciya ta sauke.... Matsowa yayi jikinta sosai ya d'ora ha'barshi a kafad'ar ta,, yana sakin wani irin numfashi! Muryar ta bata futa sosai tace"Yaushe ka dawo." Shiru yayi mata yana laluben jikinta da hannunwan sa, ta dinga jin tsigar jikinta na mi'kewa lumshe ido tayi hannunta ya kama ya rike cikin nashi kana ya tsira mata idonsa masu bala'in kashe mata jiki yace." Ina alk'awarin mu." ?  gabanta ya fad'i jin yanda yake magana a sha'ke! Kauce-kauce take yi ya juyo da fuskar ta suka fuskanci juna... Hucin nuffashi sa shine yake kokarin kassarata kusancin su yayi tsanani....... A dashe yace." Ko kin manta..gani na dawo kamar yanda kika ce kin al'kawarin kome yi sai ki bani za'bi."!!! Cike da fargaba nace"Abban baby kayi hakuri ka samu nutsuwa tukkuna gobe mayi maganar, kaga dare ne yanzu kar mu tashi baby daga bacci."



Idonsa a lumshe yace." Uhumum!!! Ni babu ruwana da dare baby kuma yanzu zan d'auke ta daga d'akin.kawai ki bani za'bi." Ganin yanda yake gogo min k'irjinsa a nawa yana d'a min hankali nace"To....me kake s....... Kafin in 'karasa ya zura hannun sa 'kasan rigata  da wata irin murya yace." Wannan nake so."! Tsigar jikina ta mike jin yanda yake wasa da hannunsa a gurin. Tuni jikina yayi laushi, lura da yayi da haka ne ya sanya ya d'aga ni. Baby ya d'auka a hannunsa ina kallonsa ya futa daga d'akin.



Zuciyata na ayyana min kawai in tashi in kulle 'kofata don har ga Allah tsoro nake ji, wata zuciyar tace"Kar ki aikata haka Asma'u kiyi 'kokarin sauke hakkin da yake kanki.......ina nan kwance ya dawo d'akin key ya sanya ya kulle kana ya kula haske yace." Tashi kiyi alwala muyi nafila. " Babu kuzari a jikina na mi'ke toilet na shiga minti biyar na futa yana tsaye kan dadduma ya mik'o min duguwar rigata da nake sallah da hijab na sanya ya tada sallah.



Raka'a biyu mukayi ya dafe kaina sosai yayi addu'a don har na dinga mamakin sa Ashe yana da ilimin addini me zurfi haka bayan ya gama ya shafe fuskarsa nima nafi kamar yanda yayi mik'ewa nayi ja koma bakin gado na zauna duk tsuro ya cikani.

 Ina kallonsa ya kashe Fitilar dakin cikin duhu ya 'karaso kusa dan.... Mikar dani yayi ya zare hijab din jikina da kanshi ya d"age duguwar rigar ya cire min babu brziyya a jikina sai pant........ Ajiyar zuciya mai zafi ya saki!! Hannu na sanya na rufe kirjina cikin jin kunya shi kam Amjad baya cikin hayyacin sa Brest dinta sunyi bala'in gigita shi ta inda ya kasa sarrafa kansa ko kad'an fuzgota yayo tafad'a jikinsa ya  haye kanta sosai yake zuba mata wasu lafiyyayun kissis masu bala'in zafi...... Harshen sa ya zura cikin ramin cibiyar ta yana wasa da gurin. Asma'u ta bud'e masa jikinta sosai tana karb'ar sako sai fidda numfashi take yi lokacin ita kadan tasan halin da take ciki.... Jikinta tuni ya Riga ya gama jikewa.... Amjad hannunta ya ri'ko guda d'aya ya cusa cikin wandon shi da yayi saura a jikinsa, a sark'e yace." Kiyi min wasaaaaah!!! Wani Abu ta rike mai tsayi da kauri gashi sai motsi yake mata a hannu  ta fara murzawa tuni taji shi ya fara sakin nishi!! Yana samtabu, breast dinta guda ya cafka da bakinsa ya hau tsotso a kamar yaron da ya kwana ya yini bai tsotsi nononar Uwar shi haka Amjad yake shan nono Asma'u yana wasa da d'ayan..... Ita dashi duk basa cikin hayyacin su domin ita bata San me dame take yi a cikin wandon sa,  tasan dai hannunta har yanzu na ciki.... Hankalinta ya d'auke mutuka bata San sanda ta saki abunda yake hannunta ta damk'i gashin kansa tana sakin wata irin 'kara jin bakin shi a headquarter yana tsotsa!!! Duk jagwalin ruwan da yake zurara Gogan Ku ya tsotse tas!! Yana wani irin rawar jiki ya cire bakinsa daga gurin ya zura Babban yatsansa ciki!!!! "Ahaaaaa!!! Ita dashi suka saki nuffashi Asma'u bata sanda ta bud'e masa cinyoyinta ba shi kuma ya shiga tsakanin sosai yake wasa da yatsayan a gurin , ita kuma ta sakin wani irin nishi had'e da shafa kwantacciyar sumar kansa, wasu irin hawaye na zubo mata ko na meye oho.....



Sai da ya tabbatar ya samu hanya kana ya cire hannunsa daga gurin.... Zare dogon wandan sa yayi ya d'aga kafarta guda tayi sama d'ayar tale sosai gwiwar sa duk biyun ya dire kan katifar ya saita Jijiyar sa, babu sauki a tare dashi ya Danna!!!!.


A zabure! Tayi yunk'urin mik'ewa ya mai da ita da hannun daya ya safe k'irjinta tare da tsira mata idonsa lumsassau itama shi take kallo, tana cije bakinta cikin jin zafin abunda yake mata ta bud'e bakinta da yayi mata bala'in nauyi zata yi magana ya kwanto kanta hade da da had'e bakinsu guri guda tare suka saki numfashi, Ya Fara tsotsar bakinta cikin wani irin salo. Gefe guda kuma yana can yana kokarin shigar da jijiyar shi rijiyar Asma'u da take cike dam da ruwa da santsin amma a tsuki  duk 'kokarin shi ko rabi ya shiga abun ya fassakara ga wani irin ruwa me d'umi da yake ji a jikinsa..... Bakinsa ya cire daga nata jikinsa na kyarma yace." Ki bud'e min jikin ki kin matsa ni." Asma'u da take jin wani irin zafi a 'kasanta tace"Wan...wani irin na matse ka... Nifa da zafi Wallahi duk ka yanke min guri kad'a gani haka." Ya tsansa guda ya zura a bakinta yana lumshe idonsa bai ce mata komai ba ya cigaba da 'kokarin shi, yana mamakin tsukewar yarin duk inda mace mai ni'ima take yarinyar ta kai amma guri a tsuke tsam!! Sai ya tuno Lokacin Mimi bai wani shawahala sosai ba, yanzu Rabin jijijyar shi ya ki shiga.

 Jiki na kyarma! Ya cire jikinsa, ita kuma ta samu damar mik'ewa zaune da sauri zata sauka domin ji tayi kamar an sanya reza an tsatstsaga mata gabanta yanzu ta daina jin zagi sai rad'ad'in azabah!!! A gigice ya damkota bakin shi na rawa yace.'' Ina zaki je."? Kokarin kwace kanta take yi ganin shi duk a burkice, abunda ta gani yayi bala'in furgita ta da tsorata joystick dinshi k'atuwar gaske ta wani mike duk da a cikin duhu ne tana jin motsin ta a jikinta...... Jikinsa sai rawa yake yi yace." Tunda kinki sakar min jikin ki tom kiyi min kokari na samu biyan buk'ata ina cikin halin damuwaaaa."!! Nace"Nima gaskiya bazan iya ba domin da zafi tun d'azu kakayin Abu daya kaki ka daina."!! 


A gigice yace." Nifa ba laifina bane naki ne kawai kin bi kin matse kanki nima ai kinji min ciwo."!


Zumb'ura baki nayi na yunk'ura zan mike rike ni yayi yana wani marairaice fuskarsa duk da a cikin duhu ne na hango tsantsar sha'awa a tare dashi.... Tsoron yanda naga idanunsa sun koma Naji nace"Tom me zanyi maka yanzu..... A sark'e yace." Kece kike da abunda zakiyi min tunda kuwa kin San dole ne kuma Alk'awari kika min."!!!! Jawo ni yayi jikinsa ya cigaba da ya mutaani fargaba duk ya cika ni....... Muryar shi naji k'asa kasa yana fad'in "Me kika fiso in miki." Shiru nayi masa, idona a lumshe ina jinsa ya bude min cinyoyi kamar d'azu ya kafa kanshi sosai yake tsotsar gurin lokacin hankalina ya dauke har ya cire bakinsa ya maida joystick d'insa gurin ban sani ba saboda yanda yake wasa da ita a gurin cikin hikima da santsin ruwan ni'imar da yake zubah ya samu ya danna ta da mugun k'arfi Wanda shi kanshi sai da yaji kamar ya keta wani Abu kafin ya shiga... Ni kam ihu! Na kurma sosai na dinga dukan shi da hannyansa jin da nayi gudundumemen Abu ya huda ni.... Amjad ya zauce ya gigice domin bai San wane hali Asma'u take ciki ba shi dai tunda ya samu ya shiga sosai ya fara safa da marwa yana sakin nishi daki-daki!

 Sosai yake amfani da ita tamkar Wanda ta saba da al'amarin haka yake mu'amula da Asma'u Lokacin ta jigata ta Kai makura gurin galabaita tsananin azabah da zafi ya hana komai sakar masa jikin kawai tayi yake budurin sa dai da zai kawo ne ya dinga sakin wani irin ihu! Kamar mahaukaci yake kara 'kaimi akan ta sai dukan katifar gadon yake da hannunsa biyu yana wani irin kuka mai shashsha'ka!! Kirf! Ya rufu a kanta had'e da 'kank'ame ta 'kam!!!!! Yana sauke wata irin zazzafar ajiyar zuciya!.


*Tofaa kanwa ta kar tsami kwarnafi ya kwanta🤭😋*


Yafi minti goma a kife a kanta sannan ya dawo nutsuwar shi ya d'ago jirkitattun idanunsa yana kallonta... Rintse idona nayi da sauri ina jin wani irin mugun haushin sa ya dinga wani Abu sai kace mahaukaci wani irin azabar radadin zafi nake ji a kasa nasan da kyar in ba ya ji min ciwo ba.

 Bakina yake kokarin kamawa da nashi nayi saurin kauda fuskata wasu hawaye masu zafi na zubo min.


Harshe ya sanya yana lashewa ya tsira min jirkittatun idanunsa masu kashe min jiki..... Hannunsa na dauke da ke kan cikina ina kokarin mik'ewa zaune ya mike tare dani a jikinsa..... Cije bakina nayi cikin jin azabar radadin zafi nake kokarin komawa na kwanta domin wani irin jiri naji dakin yana juyawa dani.... A hankali yace." Sorry! Zafi ko."? Ji nayi kamar in kifa masa mari wai tambaya ta yake yi da zafi."! Ganin irin hararar Dana ke masa ne ya sa ya dauke ni cak ni dashi duk babu kaya a jikin mu toliet din ya bude..... Yana rungume dani a jikinsa ya hada ruwa cikin kwami  ya sanya ni a cikin ruwan zafin, a hankali yace ki gasa jikin ki zaki ji sauk'i!! Ko kallonsa banyi ba.... Da niyyar shiga yayi cikin ruwan da take sai ya fasa ganin idan ya shiga din zai iya dawowa ruwa shiyasa ya hada wani ruwan yayi wankan tsarki yanayi yana kallonta yana mamakin baiwar da Allah yayi mata  gaskiya 'bakar mace tayi a rayuwa  lokacin Mimi lanjare masa tayi gashi bata da wani kuzari da dauriya sai aikin kuka, Asma'u ma dai duk da tayi kuka Amma tayi jarumta sosai don ba ko wace mace ce zata iya yin jarumtar da tayi ba duba da yanda ya zage kwanjinsa a kanta ya dinga sasakar ta kamar ba budurwa ba.







*10/12/2019*

[12/10, 9:05 PM] .: *BABBAN YARO*

*82*


Sai da na tabbatar ya futa daga toilet d'in sannan na saki jikina nasamu damar bud'e 'kafafuna sosai ruwan zafin na shigata yanda ya kamata rintse idona nayi jin wani irin zafi 'kasa na daurewa kawai na akeyi amma Sam bana so na motsa jikina bacci me dad'i ne ya fara fuzgata cikin ruwan, muryar shi naji sama-sama yana kiran sunana.



Cike da bacci na bud'e idona ina kallonshi yana sanye da jallabiya me 'karamin hannu. Yace." Kinyi wankan tsarki. "  ? Gyada kaina nayi ina yunk'urin mik'ewa.. Ya rik'o hannuna na futo daga cikin kwamin, ruwa ya had'a min yace." Yi wanka ki futo muyi bacci." 

Futa yayi daga toilet d'in. Ni kuma nayi wanka tsarki kamar yanda addini ya tana da, yana zaune gefan bed na futo daga toilet d'in ya taso da sauri ya rungume ni a hankali muka karasa bakin gadon ina cije baki. Zaunar dani yayi kana ya warware towel d'in jikina babu kunya ya fara 'kokarin sa min riga kallonshi nake yi cikin takaici da mamakin rashin kunyar sa gurin saka rigar duk sai da ya ta'be min nono wai ni zai mayar shashasha don yaga na k'yale shi. Kwanciya yayi rigingine ya d'ora ni saman shi bargo ya sanya ya rufe mu, hannunsa guda ya sanya a kan mazaunai na yana wasa dasu cikin 'kwarewa!



Muryarshi a sha'ke yace." Wai kurma kika zama ne uhumm."!? 


Lumshe idona nayi kawai saboda bani da abunda zan ce masa.... Cikin kyakyawan lafazi yace." Asma'u. " bude idona nayi amma ban kalle shi ba.


Ya cigaba da cewa "Ha'kika babu abunda zan ce miki sai dai nace Allah yayi miki albarka  Allah yayiwa iyayan ki albarka da dukanin wadanda suka baki tarbiyya kika kawo min budurcin ki gidana kin shayar dani ni'imar da bantab'a sha tunda uwata ta haife ni..... Ina fatan auranmu dake yayi albarka Allah ya azurtamu da zuria dayyiba Babu shakka ina alfahari dake, kinzama wani jigo na rayuwa ta."Ban ta'ba tsammanin futowar wannan maganar daga bakin shi ba sai na dinga mamakin Ashe yana da saukin Kai da iya mu'amula mutukar ka fahimce shi, jin addu'ar da yake min yasa naji saukin zuciya tayi sanyi Kwata kwata na daina jin haushin abunda yayi min.... Luf nayi a jikinsa bacci na fuzgata gefe guda kuma ina jin hannunsa na yawo sassan jiki, share shi nayi kawai har bacci ya dauke ni.



Amjad kuwa daurewa kawai yake yi domin wani sabon fleengs din ne ya taso masa jin fatar Asma'u da tudun Brest dinta a jikinsa ya kara dilmiyar dashi, gaskiya kome za'ayi bazai tab'a iya rabuwa da ita ba... Ashe haka yarinyar take da baiwa iri-iri bai sani ba tabbas ya gode Allah da bai sa ya yi mata wani abunba lokotan baya da ya samu dama akanta.



Idonsa biyu har aka fara kiraye-kirayen sallahr asubah lokacin jikin Asma'u ya d'ume da zafin zazzab'i  jikinta sai rawa yake yi tana datse hak'oran ta.


Gogan naku duk ya burkice a gurguje ya d'aura alwala ya nufi masjid hannunsa rike da carbi.... Ana idar da sallah ya shigo gidan kai tsaye d'akin Asma'u ya koma, bed din ya nufa da sauri ya cire bargon dake jikinta, tattaro ta Yayi gabad'ayan ta ya sanya a jikinsa yace." Kinyi sallah ko."? Girgiza Kai tayi tana cize baki... 'Kokarin zame jikina nake yi daga jikinsa ya rike ni tam! Hade da tsira min ido duk ya koma wani abun tausayi nace"Ka bani Paracetamol kawai zazzab'i sauka." Jiki na kyarma ya cikani ya mike da sauri ya futa. Kallo na bishi dashi cikin mamakin rawar jikin da yake yi.


Yana futa suka  ci karo da granny tace" kai 'kato ka dawo Ashe." ? Yana 'kokarin kar'bar baby dake kuka yace." E nadawo jiya kuna bacci nine ma na aje miki baby kusa dake."



Granny tace'' Haba ni nayi mamaki dama ya akayi baby ta dawo gurina. Cike da zargi tace"Ina Asma'u take." ? Kai tsaye yace." Tana ciki bata da lafiya."? Granny ta fahimci kome ye ganin shi a hargitse yana wani sinne Kai. Kai tsaye ta shige dakin bata re da tace masa komai ba.


Simi-simi ya wuce da baby dakin sa domin dauko magani duk jikinsa yayi sanyi zazzab'in nan ya mugun bashi haushi shifa so yake yi ya 'kara wani sex d'in ko gurin ya washe sosai, shiyasa duk jikin sa yayi sanyi zuwan zazzab'in ya 'bata masa rai sosai, babu kuzari ya shiga dakin  a hannunsa rike da maganin


 Granny na tsaye hannunta rik'e da jibgegen zanin gadon da ya cukurkude yayi kaca-kaca da jini kamar an yanka lafiyayyar kaza ma jini a jika! Sai fad'a take yi kamar ta ari baki tace" in banda rashin imani irin na 'kato fisabillahi sai ya kamaki ya kwana a kanki yana Abu d'aya duba don Allah jini kamar an yanka kaza ai komai a sannu ake binsa."



Ya tsinci kadan daga cikin surutan da take yi don haka ko da ya shigo 'bata fuskar sa yayo don ma kar ta kawo wargi. Ya bude firji hade da dauko goran ruwa Mara sanyi ya nufi gurin Asma'u.  Granny ta kalleshi cike da takaici tace"Ka dawo cikin dare kamar wani munafiki ka haikewa yarinyar mutane don rashin imani ba dole tayi zazzab'i Haba! Sai ka yi mu'amula da ita a hankali cikin laluma tunda bata saba ba ni wallahi wannan jinin ya bani tsoro ! Yo ko mu da muke mutan da ai bamu zubar da Wannan jinin ba daran farkon mu."!!


Bai kulata ba, ya d'ago Asma'u da kunya ta kusa kashe ta a gurin yana kokarin bata magani Granny ta kwa'be hannunsa maganin ya zube kasa.!


Hararasa tayi tace"Baza ta sha d'aci ba da safiyar nan ka gama wajigata zaka dauko kayan d'aci ka bata to da sake."!!!


Dariya ya 'kunshe wa yace." Wai ke granny meye ruwan ki ne ? Wannan fa sa'ido ne tsakanin mata da miji ki daina shiga ki k'yale mu, kome ma nayi aike ce kika bani maganin 'karfi."


A hasale! Tace"Dana baka maganin 'karfi sai nace kayi wulakanci son ranka tou Shikkenan tunda ka samu lafiya bazan kuma baka ba balle ka cutar musu da yarinya."



Dariya yasa sosai yana mamakin granny da 'k'arfin halinta... Ganin ya mai da ita shashasha yasa ta futa daga dakin hannunta rike da bedshirt din tana ta faman fad'a kamar ta ari baki.!



Kallonshi nayi a fakaice naga sai dariya yake yi da annushuwa ni ya barni da wahala da cizon leb'e a hankali nace"Kaje ka 'karbo bedshirt din can don Allah."



Ido ya tsira min hade da d'age gidansa guda Yace." Saboda me."? Kauda kaina nayi nace"Bamu kad'ai bane a gidan nasan halin granny zata nunawa mutane." 



"Mu da suwaye a gidan."? Yafad'a yana me tsurawa k'irjinta ido kamar wani tsohon maye sai cizar lips d'insa yake. Lokacin shi kadai yasan halin da yake ciki.


 A hankali nace" 'Baki muka yi jiya da yamma, Innah da yarinyar ta." Shiru yayi yana tunanin wace Innah take nufi." Yace." Wai Innah Suwaiba ce." ? D'aga masa kai nayi kurrum. 

Shiru na minti biyu yana kallona yace." Yanzu wane irin yanayi kike ji a jikin ki."?


"Zazzab'i" na fada ina lumshe idona.... Koka rin shigowa bargon yake yi yana fad'in"Bari kiga abunda zanyi miki yanzu zaki daina jin sanyi.... Rigar ta yake kokarin cirewa na buge hannusa da sauri nace" Don Allah k'yaleni ni kam  ka k'yaleni da rigata.!!! Tsaf na fahimci wayon sa tunda naga ya tsira min idona yana cije lips nasan abunda zaiyi..... Da siriryar murya yace." Ni kika bugewa hannu." ? Baki na zumb'ura nace"Yi hakuri ba da gayya nayi ba."


A sake yace." Ok bari in miki fiffita nasan kina jin zafi har yanzu. " kafata guda ya d'aga sama! Na rintse idona cikin jin a zaba nace"Please Abban baby don girmar Allah ka k'yaleni wallahi ni kadai nasan abunda nake ji."""  Amjad da ya fara hawa network yace." Ki bari min ki fiffita a gurin zaki ji sauki ko kuma ki bari in 'kara wani shikkenan kin wuce komai kin dawo babbar mace, yanzu ma don farko ne."


Cikin zuciya ta nace"Wallahi komai nacin ka dole ka rabu dani a zahiri kuwa kuka nasa masa ina bashi hakuri domin na lura da gaske yake...... Da kyar na samu ya bar d'akin.. Yana futa ya tadda granny Innah Suwaiba A tsaye a parlor granny hannunta rike da bedshirt tana wassafawa Innah Suwaiba abunda ya faru kamar wacce aka yi a gabanta take fad'in"Ni yarinyar ta burge ni wallahi na Dade banga budurwar da ta kawo 'yan cinta gidan miji ba.


Fad'ar wannan magana da Granny tayi sai Innah Suwaiba ta tsargu tace." Insha Allah zaki ga budurcin wacce tafi Asma'u daraja a gidanan." Karaf a kunnan sa, sai ya fara mamakin wace macece ce wacce zata fi Asma'u shi daraja a gidansa










*10/12/2019*

[12/11, 1:09 PM] .: *BABBAN YARO*

*83*





 Cikin tafiyar sa ta jarumin namiji ya 'karaso tsakiyar parlor inda su granny suke tsaye suna mai da magana. Ina Suwaiba tace." Ka futo yaron kirki."? Zama yayi cikin kujera yana fad'in"E Innah yaushe kika zo gidan." ? Washe Baki tayi tace." Jiya muka zo da yamma ai bani Kad'ai bace tare muke da 'k'anwar ka Hafsa." Yace." Duk ya mutan gida da sauran 'yan uwa."? Tace"Kowa lafiya Lou kuma suna taya ka murna da farin ciki Ubangiji Allah ya taya ka rik'o ." yace." Ameen Innah nagode k'warai. " mik'ewa yayi zai wuce ta dakatar dashi ta hanyar fad'in"Nace dama ai mun dawo kusa dakai da zama duk inda zaka shiga muna 'kungun ka ko da ko gidan gwamnatin ne, arzikin mu ne."



Dariya Ta bashi don haka sai da ya dara tukkuna sannan yace." K'warai kuwa innah amma fa ni wannan mulkin ba son shi nake ba, don dai jama'ar gari sun matsa ne." Tace" A'a mu kam muna so zamu yi ta taya ka da addu'a. " yace." Nagode Innah.''


Yana 'kokarin shiga d'akinsa tace" baka tambayi 'yar Uwar taka ba." Ajiyar zuciya ya sauke al'amarin Innah ya soma bashi haushi yace." Tana ina."?


Tsaki ta buga tace"Tana cikin d'aki kwance jiya daga zuwan mu matar ka ta 'kona ta da soyayya man 'kuli.''


Juyowa yayi cike da mamaki yana kallon Innahr tasa. Granny tace"Haba Suwaiba a dinga Sara ana duban bakin gatari mana, ki bar shi yaje ya kwanta ya huta tukkuna kome sai a ayi ki duba da kyau ki gani yana tare da gajiya ga bacci jiya ya kwana yana ibadar aure."!


Ya'ke Innah tayi tace"K'warai zance ki haka yake ka shiga ka kwanta ka huta Idan yaso in ka tashi sai muyi maganar dole ka jawa matar kunne ta ga mutumcin mu domin mune kai baza ka tab'a janza mu ba."



Amjad ya 'bude dakinsa ya shiga yana mamakin maganganun Innah Suwaiba idan ya fahimci maganar ta tana nufin sun dawo gidan shi da zama kuma tana so ta cusa masa 'yar ta bayan haka kuma yanda ya fahimta tana so ta tayar masa da hankali a cikin gida, sai babban abunda ya d'aga masa hankali shine wai Asma'u ta 'kona Hafsa da mai a gaban granny Tayi maganar yaga bata musa ba tabbas zancan haka yake yi, dole ya sanya ido kuma ya tsawatar matsayin matar shi daban matsayin dangin sa daban amma Sam bazai lamunci zaman Innah Suwaiba cikin gidan shi ba yasan halin matar muguwar 'yar rigima ce.

[12/11, 10:30 AM] BintuUm@rAbb@le: Wayoyin shi dake kan drwoar ciki ya d'auki guda ya kunna tun jiya suke a kashe saboda yasan mutukar ya barshu a kunne babu shakka jama'a zasu dame shi shiyasa ya kashe su, yana kunnawa messages suka dinga shigowa ya aje ta  kan bed d'in bathroom ya shiga ya had'a ruwa sosai yayi wanka ya futo daure da towel a kungun shi,  ya zauna yana duba sa'konni mutane wasu ma Sam bai San su ba, suna yi masa fatan alkairi, sa'ko har daga  Garin mahaifin sa Chadi ya duba iya Wanda zai iya ya aje wayar kwanciya yayi rigingine yana tunanin ta yaya za'ayi ya sallami Innah domin gaskiyar magana sun ta kura masa da sa ido mussaman granny yanzu da babu kowa cikin gidan yasan suna tare da matar shi amma parlor d'aya duk abunda zai yi idonsu na kai. Tsaki kawai yake ja..... Kira ne ya shigo wayar sa, yana dubawa ya numbar Ali 'Dan jaridar nan Ali ya wuce komai a gurin sa ya d'auki wayar had'e da sallama.



Suka gaisa cikin girmama juna Ali yace." Yallab'ai muna Neman alfarma a gurin ka idan zamu samu." Yace." Ali fad'i kome ye."! Ali yace." Muna so zamu yi hira dakai a gidan redion mu yau da misalin 'karfe takwas na dare."


Jim! Yayi yana tunani yace." Babu damuwa insha Allahu zan amsa gayyatar Ku. " Ali yayi mamakin saurin amincewar sa, murna ya yi sosai yayi masa godiya kana suka yi sallama. Aje wayar yayi gefan sa yana lumshe ido, minti biyu tsakani kira ya 'kara shigowa ya bude idonsa had'e da kallon fuskar wayar.....Hibbah  sunan da ya gani yana yawo kan screen din wayar, tsaki yaja kawai ya share wayar har ta katse. Wani kiran ya 'kara shigo ..... Dauka yayi ya k'ara a kunnesa ba tare da yace." Kome ba, ita kuma jin ya d'auka yasa ta ma'ke Muryar ta tana fad'in"Zumana ka ya dani ko."? Yana sane yace." Wacece ke."? Hibbah takaici ya ishe ta tace." Nice Hibbah mayar ka, duk wulakancin da zaka mun bazan yi zuciya ba  ina sonka ina 'kaunar ka." Idonsa ya 'bude sosai yace." Ke baki da hankali ko bakin San abunda ubanki yayi min ba ne." ? Take tace" Nasan kome zumana, kuma mahaifina a halin yanzu yana cikin tsananin tashin hankali da nadama shine dalilin ma da yasa na kira ka a waya ina me baka hakuri ko don darajar son da nake maka ka YAFE masa domin yana cikin halin damuwa. Amjad yaji zuciyar sa nayi masa zafi da maganganun da take yi masa na shirme yo shi ina ruwan sa da Alhaji Hashimu mai citta can gasu gada kuma Allah ya raka taki gona, don haka a kaurare yace."  Hibbah kike ko meye? Ki kula ki kama kanki daga yau sai yau kar ki kara yimin magana makamanciyar wannan duk wata ukuba da mahaifin ki ya shiga shine ya jawa kanshi, ki dauka a rayuwar ki kamar baki ta'ba sanin Amjadu ba a rayuwar ki kuma ki fad'awa ubanki cewa ko da wasa kar ka kuskura ya shiga hurumi na idan bai wasa ba wallahi sai na d'aure shi."!



Hibbah ta fashe da kuka tace"Ni kaka fadawa wad'annan kausasan maganganun naka don kayi sabon aure kuma zaka zama governor shine kake min wulakanci kar ka manta da cewar Kaine ka fara keta min rigar mutumci na wallahi Idan bakayi wasa ba sai na tona maka asiri domin duk abunda ya faru a tsakanin mu dakai INA  da pictures d'insa a waya ta."



Yace."Hibbah Idan baki fasa tona min asiri ba bakya 'kaunar Allah da manzon sa kije duk inda zakije ki fad'a cewa ni fasi'ki ne kuma nine na fara sanin ki 'ya mace wannan ba damuwa ta bace taki ce duk abunda zaka yi kije kiyi kanki zaki 'batawa suna a duniya."!! Yana gama fad'in maganar shi ya kashe wayar zuciyar sa na yi masa mugun zafi haka kurrum yana cikin farin ciki da annushuwa Hibbah ta 'bata masa rai da Safiyar Allah.


******



Aunt Hauwa ce  tayi sallama cikin gidan su. Umma na zaune a rumfa tana lissafin 'kudi tace." Kece da yamman nan." Aunt Hauwa ta zauna kusa da mahaifiyar ta suna gaisawa tace"Wallahi daga kasuwa nake sai da na fara zuwa gida na aje kaya san nayo nan."


Umma tace"Hakan yayi kyau ai.... Aunt Hauwa tace"Jiya Aminu yaje min da wata magana wacce ta d'aga mun hankali mutuka." Umma tace" Humm al'amarin mutane na da ban mamaki wallahi mutuwa she kara goma sha biyar amma saboda rashin imani da tada zaune tsaye suka 'bullo mana da wannan maganar."



Aunt Hauwa tace"Ni wallahi abun yayi mugun daure min kai ayi abun nan tare da sanin shaidu da sanya hannun kowa amma daga baya a sanja magana."



Umma tace"Duk Ku kwantar da hankalin Ku insha Allahu kamar yanda suka buk'ata din zamu tashi mu bar musu gidan su ko hayane mu kama ai Shikkenan. " 


Aunt tace"Insha Allah ba zamuyi haya ba Umma zanje gurin Kawu Yunusa tunda akwai gurare cikin gidan shi ko d'aki guda ne ya baki ki zauna a ciki kafin mu San abun yi."



Umma tace"A'a ni bazan je gidan Yunusa ba kun San halinsa nayi sa dashi ma ban tsira ba balle INA kusa dashi ai har dukana ma sai yayi, Aminu yace." Inje gidan shi in zauna dakin nam na tsakar gida ni kam bana sha'awar zama da suruka gwara inje in biya 'kudina in San na biya babu me yi min wulakanci." Umma ta 'k'arashe maganar ta tana goge hawaye

Aunt taji zuciyar ta nayi mata zafi sosai tace"Umma me za'ayi da rashi talauci baiyi ba a rayuwa amma dole ne in Sanar da Asma'u halin da ake ciki a halin yanzu itace take da dama a hannu kuma mijinta yana da rufin asiri ko sa wani taimako da zata yi mana." 



Umma tace"Kul! Kar ki fara domin yin hakan zai zama kamar ro'ko me Asma'u take dashi da zata taimaka Idan ba so kike yi ki koya mata ro'ko ba zamu tashi daga gidanan ba tare da ta sani ba, Shikkenan daga baya sai taji kome ye."



Aunt Hauwa tace"Umma nifa bana sha'awar ki zauna gidan haya wallahi ki bari ayi wa Asma'u magana nasan insha Allahu a siri zai rufo." Umma ta futtuke bata so Dole aunt Hauwa ta hak'ura amma ji take kamar taje ta ciwo bashi ta siyawa Ummsn su gida su huta da ganin wannan bakin cikin.



To 'bangaran Ya Aminu ma tun da ya futa da safe take fafutukar gurin ganin ya samu gurin da Ummansu zata zauna abun ya fassakara da kyar wani abokinsa ya samo masa gida a kurna shima daki daya ne gidan mutum uku ne Umma ce ta hudu tace"Taji ta gani haka zata zauna.



Aunt Hauwa kamar ta mutu don bakin ciki haka ta tattara yana ta yana ta ta bar gidan zuciyar ta nayi mata suya.



****


*Assalamu alaikum jama'a kamar yanda muka shaida muku tun da safe cewa yau zamu yi hira da shararran kuma sanannen mutumin nan da kuka sani a jahar kano  wato Amjadu AbulAbbas mainasara Wanda kuka fi sani da Young millionaire gamu tare dashi a yau zai fad'e mana biri har bindinsa zamu ji komai daga bakinsa."* d'an jaridar ya 'kare maganar sa yana gyara wa Amjadu Abun magana dake ma'kale a jikin rigar shi.


Amjad yayi sallama cikin dakakkiyar muryar shi ya gaida jama'ar jahar kano sosai kana d'an jaridar ya d'ora da fad'in" Yallab'ai jama'ar jahar kano suna 'bukatar ka zama shugaban su kamar yanda maigirma shugaban kasa ya basu damar za'bar governor su saboda abunda ya faru, d'umbin masoyan ka suna so suji ta bakin ka suna so suni ra'ayin ka kan hakan."



Amjad yayi gyaran murya a nutse yace." Alhmdullahi Allah ne abun godiya hak'ika babu abunda zance da masoya da jama'ar jahar kano babu shakka sun nuna mun 'kauna ta hak'ika ta inda nake ganin bazan ta'ba bujerewa bukatar su ba, babu shakka na karba kuma zan tsaya ra'ayin daka kan jahar kano domin in kawo cigaba mutukar na zama shugaba a cikinta duk wani 'k'aramin ma'aikici zai samu promotion zan dauki sabbin ma'aikata da suka dace masu bukatar tallafi da kowa ne b'angare gwamnati na zata tallafa musu , zamu yiwa matasa aure zamu basu sana'ar yi kana zamu ya'ki da 'yan daba gami da 'yan Sara suka zamu sanya ido sosai a jahar kano zamu sanya jami'an  tsaro ta ko wane fanni zamu kula da marasa lafiya gami da nakassasu zamu yi yak'i da cin hanci da rashawa mutukar Allah ya bamu mulki zamu tsaya mu kula da hakkin Al'umma da izinin Ubangiji. "

 Cikin nutsuwa ya 'k'arashe maganar sa.


 Jama'ar hajar kano suna ma'kale da redio mussaman matasa sai ihu suke yi jin cewar za'ayi musu aure ayi musu lefe kuma a basu abunyi babu shakka baza su taba mancewa da guy nan ba, ma'aikata kuwa babu Wanda ya kaisu murna jin abunda amjad din yace, wadanda suka aje takkadun su tuni suka fara murna  zasu samu aiki da basu samu ba Kai yara da manya dattaija har da mata na cikin gida murna suke yi jin cewar Amjad din yace." Suma zai basu tallafi na sana'oi iri-iri..... Tambayar 'karshe da ta bawa kowa mamaki har shi Amjadu din inda d'an jarida yake tambayar sa da cewar"Yallab'ai munji wani labari daga majiya me tushe   shine muke so muji daga bakin ka shin hakane ko ba haka bane ko kuma sharrin magauta ne wai da gaske ne  Matar da kake aure a yanzu cikin gidan haya ta 'kare rayuwar ta har ka aure sannan a halin da ake ciki yanzu Wanda suke hayar a cikin gidan ya basu notis domin su tashi su bar gidan hak'ika wannan labari da muka samu ya bamu d'umbun mamaki ta inda muka k'aryar ta hakan saboda sanin da makayu maka cewar kai mutum ne mai taimako da tallafawa Wanda yake dashi hakikanin gaskiya baza ka bar iyayen matar ka cikin gidan yaya ba, yallab'ai muna so muji komai daga bakin ka, sannan muna Neman afuwa  a gurina saboda mun San dole ranka ya 'baci dalilin wannan tambayar."



Amjad yayi shiru na tsawon mintina biyar kana ya sauke ajiyar zuciya yace." Wannan maganar da kayi ba gaskiya bace, babu shakka akwai abunda yake rufe Wanda ni dakai da su da kuma ita wife dina bamu sani ba, So nasan dai gidan da suke ciki cikin unguwar Gigiginyu na company ne Wanda ya mallakawa mahaifin ta tun yana raye had'e da shaidu da sa hannu yau shekara goma sha hudu kenan da rasuwar sa wannan shine abunda na sani, amma dole zan bukince kan maganar taka."



'Dan jaridar yace." To babu komai Yallab'ai mungode mutuka da samun damar hallatar mu da kayi muna maka fatan alkairi a rayuwan ka Allah yayi maka jagora ya taya ka rik'o." Amjad yace." Amin suma amin." 


Nan D'an jaridar yayi sallama kana ya rufe kayan aikinsa........ Amjadu tun a mota zuciyarsa take masa wani irin ciwo ranshi ya gama 'abaci da abunda Asma'u tayi masa domin shi yana ganin duk laifin ta ne har akazo wannan jalli tabbas ya Dade da sanin mecece siyasa a rayuwa babu sauki a al'amarin duk inda zaka wa mutum baza ka futa ba dole sai ya San yanda yayi ya bata maka rai! Yana mamakin Gidan  haya Asma'u suke zaune amma bata ta'ba fada masa ba dole ya nuna mata 'bacin ransa..









*12/12/2019*

[12/11, 10:37 PM] .: *BABBAN YARO*

*84*




Sai wajan 'karfe goma ya isa gida, Parlor babu kowa duk sun gaji sun tashi mussaman Hafsa da akaci Uwar kwalliya kamar matar gida ana jiran sa ya dawo ya gani k'arshe sai ta 'buge da gyangyadi, gefe guda kuma 'konar ta na yi mata zugi da rad'ad'i! Babu arziki taje ta kwanta, Inna ta bita a baya tana mita......granny kuwa Dariya take musu tare da fad'in kwaji dashi haka kurrum saboda daukar dala ba gammo Ku gayyato jiki Ku dawo gidan mutane  nima barin gidan zanyi sai ku 'k'arata Ku kad'ai."



Asma'u kuwa komai cikin d'aki Tayi shi saboda yanayin da take tafiya babu sauki shiyasa ta kulle kanta Har baby ta gaji da kukan ta ta ha'kura.... Yini tayi babu abunda yake cikinta sai yughot da granny ta tilas ta mata dole tasha kwata-kwata bata jin test a bakin ta.... Sallah ma da k'yar! Tayi ta jikinta ciwo kawai yake yi cikin wannan halin ya shigo ya same ta.



Tana kwance kan dadduma da ta idar da sallahr Isha'i ya shigo ya same ta, sama-sama taji muryar shi ta bud'e idonta da suke cike da bacci.... Mik'ewa tayi zaune tana mutsike ido zatayi magana ya Riga ta ta hanyar fad'in.


"Tashi zamu yi magana." Yanayin yanda ya fad'i maganar ne yasa ta bud'e idonta sosai tana kallon fuskarsa taga ya wani murtuke fuska, gabanta ya fad'i sunkuyar da kanta tayi 'kasa.




A hasale yace." A rayuwata na tsani rufa-rufa Asma'u a yanda na d'auke ki a zuciyata Sam bai kamata ki rufe min sirrin cikin gidan Ku ba yau da  tun farko kin Sanar dani cewar gidan da kuke ciki ba naku bane ni mai mallaka mu gidane tun kafin azo ga jallin tonan asiri! Ina fatan kin saurari hirar da akayi dani a tashar freedom redio."



Cikin rashin fahimta nace"Abban baby ban fahimci maganar ka nifa tunda ka futa ina kwance ina bacci in banda yanzu da na tashi nayi sallahr Isha'i wallahi ban saurari komai ba, kuma naji kana wata magana kamar ta cikin gidanmu ka Sanar dani kome ye."!? Baba walwala a fuskar shi yace." E maganar cikin gidanku ce ko bata shafe ni bane."!? Ya fad'i maganar cikin gatse! Kallonsa nayi naga ya tsura min ido cike kamar wacce tayi masa sata!!! Gyada kaina kurrum nayi takaicin halayen sa ya soma damuna Sam shi baya daukar Abu da sauki! Sai yayi dakawa mutane tsawa! Mik'ewa nayi  ba tare da nace masa komai ba. Na cire hijab jikina toilet na nufa cikin yanayin tafiya kamar me koyo..... Muryar shi a sama! Yace." Ko bakya ji ne wato ina miki magana kina tafiya kamar wani sa'an ki, ki bar ganin jiya na kwanta dake Wallahi kika raina ni sai na baki mamaki."!

Cikin fada yake maganar



Hawayen dake kokarin zubo min nake mayar wa a zuciya nace wai dame zanji ne Da bala'in sa ko da haibaicin da Innah sa ta yini tana yi min ko kuma da ciwon jikina zanji.... "Abban baby Allah ya baka hakuri maganar da kake wallahi ban San da ita ba." Toilet din na shige ban San saurari abunda zai ce min ba... Ruwan zafi na hada na kara shiga tsawon minti goma sha biyar na futo daga ciki, wanka nayi tsaf na futo daure da towel na rofu jikina da wani jin wani irin sanyi na shiga ta Nasan zazzab'i ne har yanzu bai tafi ba.



Yana zaune inda yake na  jikina babu kwari na lalubo kayan bacci cikin Kayana gaban dressing mirror na tsaya na shafa mai sama-sama humrar gurin aunt Hauwa na shafe jikina da ita sannan na zura kayan baccin masu Riga da wando rigar mai siririn hannu ce shi kuma wando iya gwiwa yaje gashin kaina na tubke sai na d'aura d'ankwalin abaya a kaina... Kai tsaye bed din na nufa.... Amjad da tunda ta futo daga toilet yake binta da wani irin kallo sai da yaga ta juyo ne yasa ya dauke kansa da sauri hade da kara hade fuskar sa, sai da ya bari ta kusa karasowa ya sanya k'afarsa ya tade tata ta fado kansa



'Dankwanlin a bayar ya cire ya jefar kasa ya rike tarin gashin ta da tayi parking dinshi tsakiyar ka, jansa yayi da k'arfi yace." Ina a matsayin mjinki kina kin daukar magana ta da muhimamci Asma'u magana ta dake ta farko ta k'arshe shine ki kira Yayan ki Aminu cewar insha Allah gobe yazo ina Neman sa maganar zaman gidan haya ta 'kare in dai ina Raye a duniya."


Cikin kuka nace"A rayuwata na tsani mutum mai saurin daukar zafi da rashin fahimta nifa Wannan maganganun naka Sam ban fahimce su ba kamata yayi daga shigo sai ka warware min kome cikin ruwan sanyi amma kazo kana tayi min masifa ko tunanin halin da nake ciki baka yi."



Sassauta rik'on gashin yayi yace." Kece kika jawa kanki da ki'ki tsayawa ki saurari maganata." Nace'ta yaya zan saurare ka kazo kana yimin hayaniya.!" Duk ina hawaye nake maganar tsira min idonsa yayi yana kallona yace." Kiyi kokarin hana hawayen ki zubowa  bana son ganin su." Jikina na fuzge da k'arfi nace"Ni ka k'yaleni ko waye yace maka haya muke yi a gidanmu karya yake yi."


Yace." Nine makaryaci kenan." Banza nayi masa na shiga cikin bargon ina share hawaye.... Mik'ewa yayi ya futa daga d'akin, ni kuma na shiga tunanin maganganun shi.



Amjad na futa parlor ya tadda Hafsa a zaune ta k'urawa kofar dakin Asma'u ido, cikin mamaki yace." Ke Lafiya me kike yi bakiyi bacci ba."? Furgitt Hafsa ta dawo hayyacin ta. Sai ta hau ya 'ke da kame-kame yace." Tashi kije ki kwanta dallah." Cikin tsare gira yayi maganar! Hafsa ta mike simi-simi ta shige daki gwiwar ta duk ta sage, Amjad yana yi mata mugun kwarjini a rayuwar ta ta inda ko muryar shi taji sai taji gabanta ya fad'i  kusa da mahaifiyar ta ta kwanta cikin sarewa dà  al'amarin shi ta fashe da kuka me cin zuciya.


Bedroom dinshi ya bude ya shiga yana Jan tsaki in banda abun Innah yana da Asma'u a gidan sa me zaiyi da wata Hafsa a halin yanzu Sam babu maganar aure a tare dashi domun yana ganin Asma'u shi ta Tara dukanin abubuwan da yake so matar auran shi ta kasance dasu.

A gurguje Yayi ya wanka yana tunani k'amshin jikin Asma'u da yanda yake jin wani sihirtaccan kamshi na futa daga sumar kanta. Lumshe idonsa yayi ya nufi d'akinta cikin karsashi da k'warin gwiwa.

[12/12, 10:04 AM] .: *BABBAN YARO*

*85*





Cikin bargon ya shiga yana laluben ta... Hannunsa na ture lokacin Dana ji yana 'kokarin kama Brest dina tsigar jikina duk ta mike saboda yanayin jikinshi sanyi ruwan da yayi wanka take na fara sauke ajiyar zuciya.. Birkitoni yayi muka fuskanci juna dashi ya kura min idanunsa masu mugun kashe min jiki sai wani lumshe so yake yana cizar lips d'insa, nagane shi mutukar zai yi futuna zai dinga lumshe min ido yana lasar leb'e kamar wani yaro.... Cikin wani irin voice yace." Ki d'auka a ranki kin zama ni na zama ke a duniya bani da wacce zan kawo wa matsalata sai ke ina so kema idan wani Abu na damun ki naki ko na cikin gidanku ki fad'a min insha Allah zanyi iya iyawa ta akai, ina fatan kin fahimta." Duk wannan maganar da yake yi yana yi yana shafa min jiki da hannunsa hade da goga min fuskarsa a wuyana, bakina na rawa nace"Nima ban 'b'oye maka komai ba wallahi abunda kake tuhumata dashi ban sani ba ina jin bayan barina gidan abun ya faru, amma mungode sosai da wannan karamcin naka ubangji Allah ya kara maka suttura."


'Kasa kasa yace." Amin." Ya cigaba da ya mutsa min jiki daurewa kawai nake yi don kar yaga gazawa ta amma fa gabana sai fad'uwa yake yi ina jin tsoron yace zai 'kara wani sex din dani don ko yanzu dana shiga ruwan zafin banji wani sauyi ba gurin har yanzu rad'adi yake min.



Hannunsa ya zura ta bayana yana kokarin cire min Riga.. Nace." Abban baby ban... Maganar ta katshe lokacin da naji saukar fuskar shi tsakanin Brest din yana gogo min gurin.... Naji wani irin  Abu jikina yayi hannuna na sanya ina kokarin ture kanshi murya na rawa nace "Bani fa da Lafiya ka bar...kabari don Allah."!!

" Uhum-Uhum."!! Ya fada kamar wani yaro 'karami wannan salon NASA yana mugun kashe min jiki... Na dinga motsi da kafafuna ina ture shi. Da kyar ta d'ago kansa yana kallona da idanunsa da suka sauya yace." Ki Bari in 'kara wani zaki ji dad'i Wannan karon kuma baza kiji zafi kinji."!? A shagwabe Yayi maganar, zuciyata ta 'kara dilmiya a cikin kugin son sa.... Rintse idona nayi saboda bana so ya fuskan ci wani Abu daga gare ni fuskarsa ya matso da ita daf da tawa yace." Me kike so in miki." Shiru nayi masa gabana na fad'uwa in San samu ne zance masa ya tsotsi Brest d'ina domin ina mugun jin dadin haka, amma kunya baza ta barni ba



Cikin wata kasallaliyar murya yace." Ki insha nan."? Yafad'a yana 'kokarin zare min dogon wandon jikina, kara runtse ido nayi ina turje k'afafuna domin hanashi aikatawa, cikin zuciya INA fadin "Sam bashi da kunya wallahi.... Duk abunda take yi da k'afafunta sai da Yayi nasarar zare wandon dama babu 'k'aramin a jikinta, wata lafiyayyar ajiyar zuciya ya sauke jiki ns kyarma ya kafa kansa s gurin..... Asma'u ta saki a jiyar zuciya me k'arfi ita da take turje-turje tana hanashi sai gashi ta bude masa 'k'afafu sosai tana saki nishi hade da shafa sumar kansa


 *Zaku ga ina rubuta abubuwa masu tsauri cikin littafin, ina in fahimtar daku abunda yake faruwa tsakanin ma'aurata, rashin sakin jiki da juna gurin mu'amular aure tana kawo na'kasu da koma baya kan zamantakewa aure yana da kyau ace ma'aurata su amince da junansu gurin auratayya su dunga 'kokarin farantawa junansu  mata muna da wasu abubuwa da yawanci maza basa so shine gidadanci da kunya mutukar akace wannan mijiki ne kun Riga kun zama d'aya ke dashi ki saki jiki dashi ta ko wane fanni ki kula dashi mussaman a shimfid'a duk abunda kika lura yana so gurin mu'amular Ku ta aure kiyi masa zaki samu BABBAN matsayi a zuciyar sa kuma zaki samu lada gurun ubangiji, amma abun mamaki shine zakiga namiji ya zake yana miki wasa gurin sex kina jin dad'i amma shi da yace yimin kaza Ku tab'a mun nan ko kuma tsotsar min nan sai ki hau no'ke-no'ke wai ke kunya dan rainin hankali wasu suce 'kyamkyami wato shi baya jin 'kyamkyamun naki yake tsotse ki, don Allah mata mu ringa ma mazan mu adalci Wallahi mafi a kasari wasu matan ne suke jawo mijin su shiga bariki ko kuma in yaga 'yan mata ya dinga rawar jiki ko dako a gabanki ne, ke kuma kiyi ta jin haushi gashi dai Matsalar daga gurin ki ne kin kasa gyarawa. Wallahi maza suna son jarumar mace wacce zata iya daukar dukanin futunar su idan sunzo da ita ko wane sitayal mijin ki yace." Zai yi dake gurin sex kar ki Gaza ki bashi hadin kai koda Ku ke kina jin zafi ne ki barshi yayi domin ya samu gamsuwa dake ko ya futa bazai ji sha'awar matan waje ba, ke ko yaji sha'awar ma yasan idan ya dawo gida yana dake bashi da matsala. Yawancin maza suna son matansu suyi masu goho domin su kadai suke jin dadin da suke ji gurin hakan, mafi a kasarin mata mu kuma bama son wannan gohon saboda zafi gashi babu wani dadin kirki, ki saka a ranki  don ki faranta masa rai kikeyi ki Bari tukkuna ya samu nutsuwa dole kema zai biya miki taki bukatar, akwai matsaltsalu sosai a zamantakewar aure mussaman gurin sex yana da kyau matan da mazan kowa ya gyara domin kawo zaman Lafiya a zamantakewar auran gaba daya.... Nasan cikin gruop din nan akwai 'yan mata sosai akwai kuma iyayena akwai wa' yanda na girma suka girme ni  duk dai matane mu ina fatan wannan tunasarwar da nayi ta amfane mu gabadaya ubangji Allah yasa mu dace*


****


A ranar Amjad da Asma'u rayuwa suke yi me dad'i da sanyaya zuciya duk wani takaicin da ya shigo dashi gidan ji yayi ya yaye domin Za'kin Asma'u ya mantar dashi komai ita kad'ai yake gani a halin yanzu ko wace gaibu ce indai da Asma'u a rayuwar shi,  Asma'u ta ji dad'i aure domin ta faskanci mijin nata jarumi ne kuma jajirtacce sai da ya tabbatar ya gamsar da ita sannan ya saurara mata, suka rungume juna suna sakin numfashi cikin gamsuwa.



Da asubah tare suka yi wanka tsaf Asma'u take tafiyar ta domin wannan tale-tale da take yi ta daina yi sai dai yanayin jikinta da Yayi sanyi wannan kuwa dole ne tunda an yage mata wannan tantanin na budurci hak'ika budurcin 'ya mace yana da mutukar daraja a tare da ita Wannan zai siya miki daraja da martaba gurin mijin ki zai ta gani kimarki saboda yasan shine ya fara sanin ki to hakane ya kasance gurin Amjad wani irin 'kimar ta yake gani yana sawa iyayenta albarka da shi kanshi Jahid din da ya sadaukar masa da Asma'u


***


Yana kwance kan bed yana bacci sosai Asma'u ta gama shirnta tsaf ta tsaya kanshi kura masa ido tayi tana kallon fuskarsa ganin yanda take futar da wani irin annuru gaskiya ta more miji kyakyawa me kyawun zuciya uwa uba kuma jarumi cikin maza dole ta dage a kansa.. Ajiyar zuciya ta sauke tana tuno al'amarin da faru tsakaninta dashi jiya, murmushi kurrum tayi da ta tuno irin sambatun surutun da ya dinga yi mata k'arshe sai da ta rufe masa baki sanin cewar basu kadai bane a gidan.  A hankali ta runkufo kansa ta sakar masa kiss a kunci karaf! Ya rike ta tsira mata rikitattun idonsa yayi yana kallonta.... Duk sai ta diririce ta fara kame-kame! Ya mike zaune sosai hade da sanya ta s tsakiyar k'afafun shi yana shakar kamshi jikinta sai wani lumshe idonsa yake jikinsa har ya soma kyarma!  A sark'e yace." Zaki sumbace ni ki gudu to na kama ki idona biyu kiyi min yanzu Ku kuma in 'bata wannan kwalliyar."



Asma'u ta diririre "Ni fa b... ba wani Abu Zan.... Maka ba." Tafad'a cike da kunya.


Yace." Ok zaki gyaramin kwanciya ne kika rankwafo kaina kome ."? Cikin sigar tambaya ya fada."


Kunya duk ta isheta fuskarsa ya cusa tsakanin wuyanta yana gogo mata gemunsa tuni tsigar jikinta ta fara tashi da kyar tace." Abban baby ka bari ba babu dad'i Wallahi."



A hankali yace." Kike rantsewa babu dad'i.'' Daga kanta tayi a shagwabe!! Babu zato taji ya damk'i dukkanin Brest din nata da hannunsawa biyu yana murzawa yace." To Wannan fa."!!.  Hannunsa take kokarin cire shi kuma yana kokarin d'age rigar Yana so ya zura hannusa sosai yaji laushinsu cikin hannunsa duk ya wani burkice mata kokari kurrum yake ya kwantar da Ita ita kuma ta turjewa.... Da kyar ta samu ya sake ta ta mike da sauri tana gyara rigar Dan har biriziyar ta balle  daga baya.... Hararsa tayi kasa-kasa ta zumb'ura bakinta hanyar futa ta nufa yace." Kizo kar ki futa nace." Kin zuwa tayi ta bude dakin ta futa da sauri tasan halin futunar shi jiya idan ba matantawa tayi ba sai tace sau kusan uku yana  yin rileazing a jikinta da ya kawo  yake 'kara wani 'k'arfin kamar wani doki



Kicin ta nufa tana baza kamshinta mai dad'i gaske Innah Suwaiba da Hafsa ta Tarar a tsaye suna yiwa Iyami masifa kamar wasu iyayen ta







*12/12/2019*

[12/12, 10:23 PM] .: *BABBAN YARO*

*86*





'Kamshin turaran ta ne dauki hankalin su, suka juyo da sauri suna kallon bakin 'kofa. Asma'u ta hade fuska sosai domin taga irin kallon da Innah ta watsa mata, cikin ladabi tace"Innah kin tashi lafiya." ? Innah Suwaiba tace"Da ban tashi ba zaki ganki, don baki da kirki zakiyi min irin wannan gaisuwar kamar wata sa'ar ki, ko kuma shi mijin naki bai fad'a miki matsayi na a gurin shi ba." ? 


Cikin kwantar da harshe nace"Inna kiyi hakuri don Allah ba sai Abban baby ya fad'a min matsayin ki a gurin shi ba na sani dani dashi duk muna karkashin ki kuma ke a matsayin mahaifiya kike a gurinm...... Inna Suwaiba ta katse ta hanayar fad'in.

"Ke bana son kinibibi da iya samun guri da kin dauke ni a matsayin uwarki ai baza kiyi min irin wannan gaisuwar ba."!



Shuru nayi mata ganin yanda take magana a hasale bana so ina fada tana fada babu mutumci yin hakan.....Iyami na kalla cikin taushin murya nace" Iyami me ake had'awa na kalaci."? 



Iyami tace"Yanzu dai zan fara aikin." Cike da mamaki nace"Yanzu kuma."? Tace" E wallahi na shigo kicin din ne nagansu suna aiki shine kika shigo wai bazan ta'ba komai ba sai sun gama."



Raina ya 'baci sosai Iyami macace mai 'kokari da ganin girman mutum Sam bata raina mutum tana da mutumci bazan so abunda zai "bata mata rai ba. Nace''Innah da kinje kin huta Iyami zata hada komai na kari kamar yanda ta saba kome kike so ki karya dashi ki fad'a zata miki."



Hafsa ta hasalo! Ta inda take fad'in"Babu wata banza da zamu tsaya ta yi mana iko da abunda muke da iko dashi ke kibar wani hura hanci a gidanan kina wani baza 'kamshi ke kanki mu muke da iko dake saboda haka ki iya takunki."



Duk 'kokarin danne zuciyarta da nake yi abun ya faskara na kalli Hafsa fuskata a had'e nace"Kiyi shuru tunda ba dake ake ba."! Innah tace"Baza tayi shurun ba sai ta saka baki domin itama watarana mai bada doka da oda ce a gidanan."" 



Na bude baki kenan zanyi magana granny ta shigo kicin din tana fadin"Hayaniyar me nake ji ne a gidanan da safiyar Allah." ? 'Kasa nayi da kaina INA 'kokarin mayar da hawayen da suke 'kokarin min...... Innah tace"Yarinyar 'kankanuwa ta tsaya a kaina tana 'kokarin zagina da safiyar."! Granny ta kalleta cike da mamaki tace"Asma'u baza ta zage ki ba Suwaiba don Allah mu zauna lafiya ki k'yale yara suyi abunsu."




Innah Suwaiba ta hau matse hawaye tana fad'in " Yau kam zan bar gidanan domin yafi k'arfin na duk da ina da iko da meshi kin nuna min ni bani na haifi Amjadu ba, Aisha ce Uwar shi abunda baki sani ba kuwa shine abunda yayi Aisha shine yayi Suwaiba. "!! Ni da granny muka bita da kallo cike da mamaki! Ta futa daga kicin din tana kuka. 


Hafsa tabi bayanta bayan ta gama watsa mana mugun kallo dani dasu granny da suke tsaye suna mamakin wannan al'amarin..... Granny tace"Asma'u ko kinki ko kinso Dole yau in bar gidanan domin ni bazan zauna in tayar miki da hankalin gida ba dama dalili ne ya kawo ni gidanan saboda haka na bar zaman shi daga yau.''.


Hawayen da nake 'kokarin danne wa ne suka zubo min na kasa cewa komai har granny ta futa daga kicin din..... Innah Suwaiba kuwa tana shiga parlor suka yi kicibus da Amjad ya futo daga dakin Asma'u yana dauke da baby a hannuna ganinsa sai ta 'kara rururcewa da kuka tana fadin "Dole in bar gidanan yau domin an nuna min matsayina a cikinsa, kamar ni Suwaiba 'karamar yarinya ta nemi fada min magana."! Ta k'arashe maganar cikin kuka.



Amjad yace." Inna wai me ya faru ne kike kuka kiyi shiru ki fada min." Karaf Hafsa tace"Asma'u ce ta zage ta wai akan me zamu shigar mata kicin."


Wani irin kallo yake watsa Hafsa kana ganin kallon kasan na tsana ne yace." Yi min shuru ke na tambaya ko ita."? Hafsa tayi 'kum! Da bakinta tana sinne kai wani irin bala'in kwarji guy yayi mata take jikinta ya fara kyarma!



Inna kuwa jin tsawar da ya dakawa Hafsa yasa ta 'kara kyami gurin kukan tace"ai ba karya Tayi maka ba, matar ka dai zagina tayi kuma a Gavan granny ta zage ni ta nuna mai aikin gidan ka tafi ni daraja dole in bar gidanan yau.



Amjad yaji kansa. Yana Sara masa Sam ya tsani hayaniya a rayuwar sa shi da zata tafi ta bar masa gidansa ma yafi son haka.. Amma don ya kwantar mata da hankali yace." Innah kikace Asma'u ta zage."!? Tace"Ba wai kuma babu karya a ciki naga ka tsaya kana mamaki dama yarinyar bata da tarbiyya shiyasa kowa yake gudun hada jini da ita."



Karaf a kunne na, raina yayi mugun b'aci sosai jin irin kazafin da Innah take min har kokarin 'bata suna idona ya rufe Sam na manta wacece ita, da kausarshiyar murya nace"Kiji tsoron Allah baiwar Allah sai fad'a kike yi na zage ki da girman ki da kome karya dai haramun ce babu kyau a cikinta na d'auka dani da Hafsa duk d'aya muk.........."Asma'u. "!!!  Cikin tsawa ya katse ta yana mata wani irin kallo fuskar shi a mugun had'e!!



Innah Suwaiba tace" Koda naji ka gani ai a gabanka dai Yarinyar nan bata duba furfura ta ba take cewa ina 'karya oh! Duniya kenan Nasan inda ta dauke ni a matsayin uwarta bazata fada min haka ba, hummm ko da yake duk laifin ka ne da baka nuna mata matsayina ba, Innah Suwaiba ta kare maganar tata tana me rurucewa da kuka. "!!!!


 Asma'u ma hawaye ta fara sharewa tana mamakin wannan masifar daga yin aure yau kwana uku Shikkenan ta kasa samun nutsuwa wai yaya zata yi ne."!?


A kausashe taji Muryar sa yace." Ki bata ha'kuri yanzu."!


Kallon fuskar sa tayi ta ganta a murtuke! Ya wani tsatstsare ta da ido, granny tace"Ba wai zan hana ta tabata hakuri bane amma ina so kafin ka yanke hukunci ka dunga bunkice ni dai da kunne na banji lokacin da Asma'u ta zagi Suwaiba ba, amma tunda abun ya zama haka ke Asma'u bata hakuri domin a zauna Lafiya. "!  Hannu nasa na goge hawayen fuskata na kalli Innah Suwaiba dake zaune cikin kujera tana matsar hawaye nace" Innah kiyi hakuri don Allah." Tace." Oh-oh aike zan bawa hakuri ke da akazo gidan ki za'a takura miki." Amjad yace.'Innah mu bar wannan maganar don Allah Insha Allah Zaku koma gidana dake Rijiyar Lemo da zama na bar muku kome kike bukata kiyi mun magana ni dan ki baki da banbanci da mahaifiyata Kuma Asma'u ma 'yar ki ce tunda iyalina ce don Allah kiyi hakuri magana ta wuce."



Inna Suwaiba bata so haka ba amma babu yanda ta iya tace"To nagode K'warai da gaske Allah yayi maka albarka ya jikan mahaifiyar ka, amma da nake cewa ko zamu je gidan gomnatin tare ne."! 



Cikin 'kosawa yace." Innah ki bari tukkuna in zama governor din sai a shirya shawarar abunda zai faru yanzu dai idan anjima zan sanya Doh-doh ya kaiku can gidan akwai kome a ciki babu abunda zaku nema." Inna sai was he baki take yi tana shi masa albarka tace"To kafin mu tafi INA so muyi muhimiyar magana dakai.".



Yace. " tom Shikkenan ni dai burina ki kwantar da hankalin ki kuma ki dauki Asma'u kamar ni." To Dan albarka kome ya wuce a gurina...... Ni kam tuni na bar musu gurin zuciyata kamar zata tsage saboda takaicin su gaba dayan su.... Kuka na zauna naci sosai a dakin.. Kafin ya shigo cikin shirin futa. Dauke kaina nayi daga kansa har ya karaso kusa dani ya sanya hannu ya dago fuskata hade da tsira min idonsa, lumshe idona nayi hawayen da nake makalewa suka zubo ..... Tsugunawa yayi ya tallafo fuskata ya fara aikunshi sai da ya tabbatar ya lashe ruwan hawayen da suke zubo min a fuskarta sannan yace." Nasan Halin Innah Suwaiba da tada futuna Asma'u inaso kiyi hakuri da ita kamar yanda nake yi da  ita ki dauke ta a matsayin uwa kinji ko kiyi min wannan alfarmar don Allah duk abunda zata tayi miki ki daina mayar mata da magana."!!!



Rungumeshi nayi sosai ina jin wani irin tausayin shi nace"Abban baby kayi hakuri don Allah Wallahi raina ne ya 'baci shiyasa na mayar mata da magana amma insha Allah bazan sake ba."!! Bayan ta yake bubbugawa cikin sigar rarrashi yake fada mata kalamai masu sanyaya zuciya har ya samu tayi shuru kana ya fada mata abunda zai futar dashi yanzu.... Asma'u tayi masa addu'a da fatan alkaro hade da samun nasara a rayuwa, bai futa daga dakin ba sai da ya ya mutsa mata jiki da salon soyayarsa ya futa ya barta da kewar sa.




****

Amjadu ne tare da dumbun jama'ar gari suke zagaye a birnin kano da kewayen ta dukanin wasu local goment da suke karshin jahar kano sai da suka zagaya   yawon kamfen alhamdullahi babu wata local goment da   shiga a ka jefe shi ko aka yi masa ihu! Ko wace local goment sun bada goyon baya, cike da samun nasara suka dawo gida.










*12/12/2019*

[12/13, 10:14 AM] .: *BABBAN YARO*

*87*





Amjad bai shiga gida ba sai da ya tabbatar da komai ya kammala a cikin gidan da ya mallakawa Mahaifiyar Asma'u  gidane plate mai kyau sosai ginin zamani gida cikin jama'a kuma 'yan boko dama yana da ire-ire wannan gidan yake ginasu saboda mabukata to gaskiya Wanda ya saka Umma a ciki nagani na fada ne komai na jin dadin rayuwa akwai shi a cikin gidan sannan yayi musu sallama Umma albarka kawai take shi masa ko a mafarki bata ta'ba tsammanin zata zauna irin wannan gidan ba na wane da wane, yanzu sun ringa sun gane cewar magauta ne hade da 'yan siyasa masu Neman kujerar governor suka had'a wannan kutungwilar domin a tozarta Amjad din, a cewar su idan jama'ar gari suka ji cewar iyayen matar shi na yawon yaya zasu zage shi, to shima Amjad din tun kafin aje ko ina ya gane sharrin abokan adawa ne.



A ranar bai shiga gida ba sai kusan sha daya na dare domin sai da yaje ya dubo Rambo dake kwance asibiti yana samun kulawa sosai kuma bashi da wata matsala tunda Amjad din yana tsaye a kansa.



Yana shiga parlor yaga mace a zaune kan kujera tayi kirif da hijab! Ya tsorata domin baiyi tsammanin ganin kowa ba sanin da yayi dare yayi dukanin su basu yi bacci Ba.



Cike da mamaki yake kallonta yace." Innah bakiyi bacci b." ? Hamma! Ta buga Muryar ta da alamun bacci tace"ta ina zanyi bacci ina jiran ka ka dawo muyi muhimiyar magana wannan yaron yazo ya matsamin da lallai sai nazo mun tafi sabon gida wai Kaine ka umarce shi yazo ya dauke mu." Amaj ya zauna cikin kujera cikin gajiya yace." Nine nace Yazo ya kaiku gidan tunda mun gama magana dake tun da safe."



Inna Suwaiba ta gyara zaman ta sosai tace"Har ka manta maganar da nace zamuyi da Kai ko." Sosa kansa yayi yace." Wallahi na manta Innah kin San abun da yawa kiyi hakuri."



Tace"Ai ya wuce kam har kullum muna yi maka fatan alkairi da zamowa shugaba me adalci." Yace." Godiya nake Inna."



Cikin kwantar da murya Innah tace"Dama Alfarma ce nake nema a gurin ka wacce nasan kana da damarta sai dai Idan baka yi NIYYA ba ko kuma matar ka ta hana ka amma abunda nake nema a gurinka Allah da manzon sa sun hallata maka shi kuma Kai kan ka zaka kara yin kwarjini ka zama cikkakan namiji mussaman yanzu da nauyi zai hau kanka yana da kyau  ka amin cewa 'bukata ta "





Cikin. "Kosawa sa maganar ta yace." Innah idan muna magana dake tsakanin mu ne don Allah ki daina sako iyalina a ciki Asma'u bata isa ta sani nayi abunda ban yi niyya ba wannan tsakanina dake ne ji fad'i ko wace irin alfarma kike so insha Allah idan da hali ni zan miki alfarma innah ke kin wuce ki nemi alfarma a gurina." Innah Suwaiba ta saki fuskarta sosai jin abunda Amjad din yace Tace." Dama ina so ka auri 'yar uwarka Hafsatu insha Allahu baka da matsala da ita nayi mata tarbiyya sosai zasu zauna lafiya da ita Asma'u mutukar wata futuna ta 'bullo to babu shakka daga 'bangaran ita Asma'u ne domin ni nasan yarinya ta me tarbiyya ce , bayan haka kuma Hafsa a kanka ta'ki sauraron d'imbun samarin ta da suke sonta da aure Tace dole kai take so, lokacin babu irin magiyar da banzo nayiwa kakar ka ba a kan mu hadaku aure ta bujere tare da fadin"Ita baza tayi maka dole ba katsaham! Muka samu labarin auran ka da wannan yarinyar me rasuwa ina nufin mahaifiyar baby 'alamarin ya 'bata mana rai sosai ganin muna a matsayin iyayen ka, ka kasa zuwa ka sanar mana shiyasa muka yi fushi muka koma gefe guda hade da zuba muTo.  ido sai bayan ta mutu kuma shima katsaham! Muka ji auran ka da ita wannan d'in to da nayi bunkice sai na tabbatar da cewar kaima baka sani ba Allah ne ya nufin haka, to sai muka dauki abun a matsayin kaddara yanzu dukanin abunda ya faru a baya mun YAFE maka."!

Ta k'arashe maganar ta ta tana sauke ajiyar zuciya.



Dama tun kafin ta fad'i maganar ta ya fahimci inda ta dosa, don haka bai wani furgita ba yace." Innah idan muna magana dake a tsakaninmu ne don Allah ki daina sako sunan kowa ciki naji kina maganar cewa granny ta hanani auran Hafsa ki gafarce ni anan wallahi ba laifin ta bane granny tayi iya bakin kokarin ta gurin ganin ta 'kulla auramu Allah bai nufa ba, idan tuhuma zakiyi to ni zaki tuhuma domin ni na nuna bana ra'ayin yarinyar Sam bana sha'awar auran zumunci, kiyi hakuri don Allah ki bar zancan ni Hafsa a matsayin 'kanwa na dauke ta, insha Allah zan tsaya mata a kan kome idan ta samu miji zan yi mata aure kuma zan gantata amma maganar aure tsakanina da ita ki aje ta gefe.




Innah Suwaiba ta fashe da wani *Mashahurin* kuka tana fyace majina tace"Ta tabbata bani na dauki cikin ka ba yau tabbata ta bani ce na tsuguna na haifeka yau ta tabbata bani ce na shayar da Kai ba! Yau ka nuna min *Aisha* ce uwarka domin nasan ita baza ta ta'ba umartarka da abu ka bujere wa bu'katar ta ba, Alhmdullahi Allah yasa nima na Haifa da yau nasha takaici."! Cikin kuka me futar da sauti ta 'karasa maganar.



 hankali a tashe yace." Innah! Yi shiru don Allah ki daina wannan kukan da kike yi bana so, wallahi dukan abunda kika fada ba haka bane na fada miki a Yanzu bani da wata uwa da ta wuce ki kiyi hakuri kiyi shuru muyi maganar please."!!! 



Inna Suwaiba ta fyace majina kamar ba dare ba sai d'aga murya take yi ta cigaba da cewa"Idan da ka dauke ni a matsayin uwa ai baza kayi min musu a kan magana ta ba hummm."!! 



Amjad yace." To kiyi shuru muyi maganar kinga dare ne kar ki tashi mutan gidan kiyi shuru don Allah." Innah Suwaiba ta goge hawayen ta tana fad'in "To kai nake saurare."!?



Ajiyar zuciya ya sauke ya dafe kansa mintu biyu tsakani yace." Bukatar ki kawai in auri Hafsa ko.? Ko numfasawa bata bari yayi ba tace" Shine bukata ta yaron kirki." Kallonta yayi idonsa yayi ja yace"Shikkenan Allah ya sanya alkairi. " washe baki tayi tana zabga masa godiya tare da fad'in"Insha Allahu zaka yi alfahari da wannan auran tunda kayi min biyyaya."



Mik'ewa yayi  yace." Innah ya kamata kije ki kwanta Shikkenan magana ta wuce na amunce. " innah ta mike tana fadin "Allah ya tashe mu lafiya kaji yaron kirki gobe sai kara tusa maganar da tsayar da ranar d'aurin aure."



Wuce wa yayi ba tare da ya tanka mata ba yana mamaki ta sosai shi yanzu babu maganar aure a gabanshi sai bayan za'be tukkuna kome ye sai ayi ya amunce mata ne kawai domin a zauna lafiya sosai yake mamakin rigimar mata.



Ina jin motsin shigowar sa 'karamin Parlor na nayi saurin hayewa bed wasu masifaffun hawaye masu tsananin zafi suka kwaranyo min a fuskata.



Asma'u yini tayi cikin fargaba sanin da tayi cewar mijinta ya tafi yawon kafen dole tasan akwai ma'kiya da suka saka shi a gaba mafi a kasari ba'a futa a dawo Lafiya shiyasa ta yini tana yi masa addu'a samun nasara da dawo wa lafiya hankalin ta bai kwanta ba sai da taji shigowar motar sa gidan sannan ta saki ajiyar zuciya taje ta d'aga labulen window tana le'ken sa har sai da ya shigo sannan ta sauke ajiyar zuciya ta zauna tana jiran sa ya shigo shuru har kusan minti ashirin tayi tunani ko yana d'akinsa zai yi wanka mik'ewa tayi da nufin zuwa kawai ta zo bude kofa taji maganganun su da Innah Amjad yayi wa Innar sa alk'awarin auran Hafsa auran ta dashi tun baije ko ina ba zai yi mata kishiya ita kuma tata 'kaddarar kenan haka Mimi Tasha wahala akan shi itama gashi ko sati bata cika a gidan sa ba abubuwa sun cakud'e ta mata Innalillahi wa'ina ilahi raji'un. "!



Cikin wannan hali ya shigo ya same ta fitalar dakin ya kunna yaganta zaune daram kan bed! Asma'u duk kokarin ta na hana hawayen ta zubawa ta kasa zuba kawai suke yi sharrrrrr! Zuciyar ta sa wani irin Tara tsatsin kishi take yi."!

[12/13, 9:32 AM] BintuUm@rAbb@le: Cikin yanayin tafiyar shi ya 'karaso kusa da ita sam bai fahimci kuka take ba sai da ya kusan ci jikinta sosai yaji shashshekar kukan ta.... Jikinshi na kyarma ya zube wayoyinshi gefen bed din ya rugumota jikinsa yana sauke ajiyar zuciya tare da tambayar ta kukan me take, shifa ya tsani ganin zubar haweyen ta.



'Kokarin kwace jikinta take shi kuma ya rike tam! Yana rarrashin ta Sam baiyi tsammanin taji maganar su da Innah ba tambayar ta yake yi me ya same ta take kuka.... Cikin zafin zuciya ta gartsa masa cizo! A hannu sosai yaji zafi a hannunsa ya ki sakinta  duk ya rikice! Da kyar ta samu ta bude bakinta tace"Ka k'yaleni ni, tunda na lura kai kan ka kawai ka san...... Katse ta Yayi ta sauri yana rawar jiki yace." Me nayi miki ne nifa bana son wannan kukan kiyi shuru ki min bayani ki daina magana kina kuka kinji."! Yana maganar yana goga mata fuskar shi a tata wannan d'abi'ar shi ce da alama shu k'okari ma yake ya had'e bakin sa da nata.



Tace." Duk maganganun da kuka yi da Innah naji su Kai ko kunya baka ji ba har da amincewa zaka auri hafsa wallahi bari in fad'a maka abunda baka sani ba zaka mai da gidan ka sansanin ya'ki domin tuntuni bama zama inuwa d'aya da wannan kucakar yarinyar me warin hammata! Ni kam na fad'a maka sai dai ka za'bi guda cikin mu ni ko ko ita domin wallahi bazan had'a miji da ita ba."!



Yanda take fad'an maganar zaka San da 'k'uruciya a tare da ita bayan nan Kuma tsananin kishi ya rufe mata ido Sam bata tunanin maganar da zata fad'a.



Maganar ta ta bashi dariya sosai amma sai ya dake baiyi ba sai ya sauya al'amarin ma ta wata sigar....... Haushi ya turni'ke ta tana yi masa magana yana wani Abu daban, ture shi take daga jikinta shi kuma yana 'kara sakar mata nauyin sa har sai da yayi nasarar danne ta gaba d'aya ya tsira mata rukittatun idonsa masu kashe mata jiki.



Kauda fuskarta take yi ganin yana shirin yi mata abunda ya saba lallai ya raina mata hankali, sai ta fara ya kushe masa jiki tana turje-turje da 'kafafun ta duk ta turje bedshirt din...... Yaso ya sanya mata 'karfi kawai sai ya k'yaleta hade da sauka daga kanta... Toilet ya nufa domin yin wanka yana mamakin tsananin kishin ta a kansa.




Jikinsa daure da towel ya futo ya tsaya gaban dressing mirror ya feshe jikinsa da turare kana ya sanya Riga mai gajeran hannu..... Asma'u har yanzu tana zaune ta hade kai da gwiwa tana kuka, bai CE mata komai ba ta futa daga d'akin...




Mintuna biyar yayi ya dawo hannunsa rike da 'karamin Cup Wanda yq had'o coffee a ciki ya zauna kusa da ita yana kurba yana latsa wayarsa.




Haushin sa kamar ya kashe ta wato ba zai rarrashe ta ba ma balle yayi mata musu akan maganar da ta kawo masa wayar shi ma yake dubawa ta tabbata kenan abunda kunnen ta yaji ye mata gaskiya ne.





Zuciya ce ta ciyo tace"Wallahi INA sane da masu sona da wa'inda basa so na Ni a rayuwata babu abunda zan cewa granny domin ta nuna mana 'kauna dani da  'yar uwata Mimi Allah ya. jikanta, duk abunda wannan matar take yi min baka cewa komai babu irin 'kazafun da bata yi min ba dukol kayi shiru. To ni kuma nace bazan zauna da 'yarta ba wallahi sai dai ka zab'i guda cikiin mu kuma duk wani Abu da take min taje na barta da Allah zai saka min."

[12/13, 10:03 AM] BintuUm@rAbb@le Fuskar sa a had'e ya d'ago kansa yana kallonta "Kina da hankali kuwa Asma'u? Innah kike kokarin fad'awa magana a gabana uhumm."!? Ya fad'a muryar shi babu dad'i!



Ba tare da na damu ba nace" Ai itace ta jawo meye ruwan ta dani a gidan mijina a matsayin ta na babba bai kamata ta shiga hurumin da bana ta ba tun da tazo gidan nan take zagina." Cikin kuka take maganar....



Ido ya tsira mata fuskarsa babu wasa yace." Ke Matsalar ki kenan tsaurin ido! Shiyasa kowa ya tashi zai fad'i aibunki ke baki bar yara ba baki bar manya ba uhumm ? Idan da mutumci ya dace ki fad'awa Innah Suwaiba wannan maganar ko da kuwa cewa tayi in auri mata uku a lokaci guda ai tana da iko dani ne."



Asma'u taji kamar ya watsa mata barko no a ido idonta a rufe tace." To sai me idan tace ka auri Hafsa bayan ita ka 'kara da wasu biyu ko a kwalar rigar Asma'u wallahi ni dai nasan ta siya maka tashin hankali a cikin gidan ka, Wanda nasan idan  Maman ka ce ita ta hak'ika baza ta so kayi rayuwa cikin tashin hankali ba, ita dai akwai wata manufar ta ita kad'ai ta sani."!!! Sama-sama take maganar....



Babu wasa a maganar shi yace." OK da kike yin wannan fuffukar kina tunanin zaki hanani abunda nayi niyya ne? Ko kina tunanin zan bujerewa maganar Inna Suwaiba akan taki, Wallahi ki shiga hankalin ki ni nan da kika ganni bana daukar raini gurin ko wace mace zan 'bata miki rai Wallahi! Daga yau sai yau ki San irin maganar da zata dinga futowa daga bakin ki akan Inna domin duk rintsi Uwata ce ke ma haka dole ki girmama ta kamar yanda nake yi  "you have to be serious."! Ya fad'a  cikin 'bacin rai!



Asma'u kuka kawai take yi cikin zuciyar ta kuwa babu irin addu'ar da bata yi wa Innah Suwaiba Allah yayi mata katangar k'arfe da sharrin ta ubangiji Allah ya rusa maganar tun kafin aje ko ina ita tana ganin idan abun ya tabbata to babu shakka Zama Lafiya ya 'kare tsakaninta dashi tana mugun sonsa Wanda shine ya jawo mata tsanin kishin sa.




Sosai take kuka Yana jinta Yayi mata shiru kurbar Coffe dinshi yake gefe guda kuma yana latsa wayarsa a zahiri ka kalleshi sai kace kukan NATA baya cin ransa cikin zuciyar sa kuwa shi kadai yasan yanda yake jin zafi da kukan ta, ranshi ya 'baci ne da jin irin bak'aken maganganun da take fad'awa Innah Suwaiba ko kunyar idonsa bata ji ba, idan da zai bude mata zuciyarsa ta gani zata yi mamakin girman son ta da kaunar ta a ciki kawai yana dannewa ne saboda sanin halinta, shafa ya amsawa Inna ne kawai amma Sam bai shirya auran Hafsa ba yanzu bai sani ba ko nan gaba.




Asma'u ta gaji da kukan ta bacci me nauyi ya d'auketa cike da mafarkin 'yan gidansu musamaman Ummansu ta ganta cikin farin ciki da walwala.



Jin saukar ajiyar zuciyarta ya gane tayi bacci shima ajiyar zuciyar ya sauke kana ya kashe wayar sa toilet ya shiga ya wanke bakinsa ya  futo kai tsaye bed din ya nufa ya kwanta hade da shiga blenket din ya rungume ta jikinshi yana sauke a ajiyar zuciya k'amshin da jikinta yake futar wa ne ya gigita shi tuni ya fara ya mutsata yana kaiwa ko wanne shashe na jikinta kisses masu zafi! A rikice yake kokarin cire mata Riga... Furgit ta bude idonta ta ganshi yana kokarin hawa jikinta da sauri tayi nufin tashi ya mai da ita da hannu daya daya hannun kuma ya zare mata rigar jikinta tuni ya gigice ganin lafiyayyun Brest dinta masu gigita shi take ya rungume ta a jikinsa yana sauke ajiyar zuciya.

Asma'u duk buge-bugen da take yi. Sai da Amjad yayi nasara a kanta ya samu biyan bukatar shi.










*13/12/2019*

[12/13, 10:27 PM] .: *BABBAN YARO*

*88*




Haka suka tashi da safe ita dashi kowa na d'acin rai! Tunda ta gaishe shi bata 'kara kula shi ba shine ma yake janta da hira tana basar dashi haka suka had'u suka yi breakfast  har shi uban gayaar ya d'ora baby a cinyar sa sai shirme suke yi shi da ita ya koma kamar wani 'k'aramin yaro yana biye mata sai faman dariya suke kyalkyalawa.



Granny bayan tagama karyawa mi'kewa tayi ta nufi d'akin da take suka bita da kallo Sam basu kawo komai ba, minti biyar tsakani sai gata ta futo cikin shiri ta yafe jikinta da mayafi kirif tayi hanyar futa ba tare da tacewa kowa komai ba." 



Da sauri na mike naje na tari gabanta ina marairaice fuska nace"Granny ina zakije inace jiya mun gama magana dake kince kin fasa tafiya."



Jin abunda Asma'u take fada ne yasa shi mik'ewa da sauri ya karaso gurin yana tambayar menene."? 



Granny tace"Dama yau na shirya tafi gidana." Amjad ya 'boye dariyar da take 'kokarin subce masa yace." Wani abu aka miki a gidan. " ? Gyada kai Tayi tace"Ba'ayi min komai ba kawai zan baku guri Ku wataya."


Dariya yasa ya kama hannunta guda yace." Rayuwata baza ta tafi dai-dai ba idan babu ke a gidan uwargidana ta kaina idan mun yi miki laifi ki hak'ura. "



Granny tace" babu laifin da kuka yi 'k'ato nice naga ya dace in tafi." Amjad yace." Ni kuma ban sallame ki ba sai kiyi hakuri idan kuma kika ce dole sai kin tafi kin San kina futa zan sanya a saki karnuka sai muga ta inda zaku tafi."



Cikin sababi! Granny tace." Sai kace zaman nawa dole ne iyi yanzu nace nafi son zama a gidana nagaji da jin iface-iface! Cikin dare."


Saurin barin gurin nayi ina mamaki tsohuwar ko me take nufi oho.! Ina Juyawa Inna Suwaiba ta watsa min mugun kallo tana gyada kanta... Bedroom dina na shige ina fadin"Allah Yayi min gatangar k'arfe da sharrin ki."



Kwanciya nayi kan bed din ina sa'kawa da kwance wa har bacci me nauyi ya d'auke ni.....a takaice dai ban San sanda su Inna Suwaiba suka bar gidan ba domin bacci na shirga sai daf da sallahar azahar na tashi a gurguje nayi wanka da alwala na futo simple make up nayi na zura doguwar Riga mai hula humra na shafa a jikina sannan na hau dadduma na tada sallah


 Ko da na futa parlor granny kad'ai na gani zaune suna hira da Iyami na saki wata irin ajiyar zuciya mai sanyi, yanzu na tabbata Innah Suwaiba sun bar gidan cikin zuciyata nace mata 'yar bala'i kurrum tazo zata d'aga mana hankalin gida. Zama nayi cikin kujera cikin sakin fuska na dinga sanya musu baki a hirar tasu  kafin mu zauna cin abunci granny kam cewa tayi Iyami ta had'a mata ta kawo mata inda take domin baza ta iya zaman daining ba. A cewar ta 'kafar ta tsami take ni da Iyami muka sanya mata dariya... Yanzu wani irin nishadi nake ji a zuciya idan na tuna cewar me takura min tabar gidan wallahi d'an zaman da Tayi na kwana biyu jina nake yi a takutey gefe guda kuma idan na tuna al'kawarin da Abban baby ya daukar mata sai gabana ya dunga fad'uwa.




*******

Al'amura sun tsananta ga me girma governor gobe wato *Amjadu AbulAbbas mainasara* Yanzu kwata-kwata baya zama a gida kullum suna can suns taron siyasa  ya tsai da mataimakin sa Engineer Jabir Hamid shine ya yarda da alkairin sa da kulawar sa kana da yanda ya tsaya tsayin daka akan jam'iyyarsu tabbas Engineer Jabir Hamid tsohon d'an siyasa ne Wanda yake da a 'kida Amjad tun yana da 'kananun shekaru yasan da mutumin domin. A haife ya haife shi idan kididdiga ma za'ayi ya girmi mahaifin shi, to dashi ya yarda ra'ayin shi shi jama'ar jahar kano suke bi lokaci guda al'amura suka dai-dai ta yayin da 'yan bakin ciki da hassada suka 'kara yawaita sharri kullum yin sa ake yi ga amjadu amma yak'i tasiri jama'ar jahar kano sun Riga sunyi nisa a 'kaunar sa, Nima nace tabbas zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana muzuru ana shawo sai yayi Amjadu sai dai fatan alkairi




Kullum zai dawo gida cikin dare a gajiye amma saboda tsabar futuna komai baccin da Asma'u take yi sai ya turme she ta ita kuma tayi ta masa sangarta da shagwab'a salo-salo abunda yake 'kara gigitashi kenan yake 'kara dilmiya cikin kogin sonta, sun ringa sun saba ita dashi kullum sai sunyi sex kuma basa tab'a yin sau d'aya a rana duk rintsi kafin ya futa sai 'kara wani da safe ko da asubah.....aikuwa Asma'u tayi wata irin lafiyayyar 'kiba fatar ta murje sosai Sam bakye ce mata baka saboda tana samun kulawa kullum oga nayi mata feshi tayi 'kiba sosai ta samu Lafiya ita dashi duk sun mance da wani zancan Inna rayuwar su suke yi tsaftacciya....Asma'u da kanta ta fuskanci tana da ciki domun wata biyu kenan bata yi al'ada ba kunya ta hanata fad'a masa, shi kam gogon NAKU hankalinsa ya d'auke gurin harkokinsa Sam bai fahimci komai ba tabbas yasan dai Ta 'karayin Sugar ta inda Idan yana sex da yake iface-ifecn da ya saba Wanda Granny take 'k'orafi akai Asma'u ce take rufe masa bakin sa wani sa'in amma Amjadu hauka ne kurrum baya yi mata a gado.


****

Granny ce ta fahimci abunda yake faruwa aikuwa farin ciki duk ya isheta shiga futa d'ari sai tayi zancan ciki motsi kad'an Asma'u zata yi zata hau fad'a wai ta dinga yin komai a hankali da nutsuwa ita dai sai dai tayi dariya kurrum...cikin wannan yanayin za'be yazo gari ya hargitse ya hautsine ko ina ka duba police ne sosai aka sanya matakan tsaro a garin na kano,  ana ya gobe za'be  Alhaji Hashimu da Yarshi Hibbah suka shiga gidan redio domin ayi hira dasu. 


Dama tun safe ake maganar cewar za'ayi hira da tsohon d'an kasuwar nan Wanda yaga jiya yaga yau a fannin kasuwanci wato Alhaji Hashimu mai citta mutanan gari suka dinga dariya suna fadin ko me zai fad'a oho kowa ya 'kaugauta lokaci yayi ya saurari hirar har shi kanshi Amjadu wayar sa na hannun Rambo  yana jiran lokaci ya kunna masa.




Alhaji Hashimu mai citta ya zage yana shirya karya kan Amjadu har da fad'in  cewar mahaifin sa da bashin mutane ya mutu kuma bayan haka shi ba d'an gari bane yazo gari zai mulke su yana da kyau jama'ar kano su farka kar su zab'i bara gurbi Wanda zai tarwatsa jahar kano daga k'arshe ya koma garin su na gado maganar 'k'arshe da ta girgiza mutane shine abunda Alhaji Hashimu yace."Amjadu yayi wa yarshi ciki gashinan wata hudu a jikinta suna da shadar haka koda jama'ar gari zasu karya ta...... Wannan zancan ya jawo kace nace a garin inda kowa yake fad'ar ra'ayin da akan Amjadu dim wasu suna ganin hakan zata iya faruwa tunda dama tsohon Dan bariki ne yana da hotel har guda biyu tabbas ba asan iya adadin matan da ya lalata ba......wasu kuwa a take suka karya ta maganar tare da cin alwashin sai sun ragargaji mai citta shi da shegiyar yar tasa sai ta fada musu Wanda yayi mata ciki da bakinta, a rake su ka dauki gorori cikin shirin ko ta kwana suka nufi titin gidan redio na *Komai da ruwan ka* lamfu suka yi daga nesa suka hango motar Mai citta ta futo daga cikin gidan redio aikuwa suka futo da gudu suka tsaya kan titi... Cike da tsoro mai citta ya ci birki hankali a tashe! Yake kokarin bude motar ya futo  Hibbah kuwa har ta saki futsari a wando tsabar furgita da tayi kafin su Ankara suka ji taratsatsa!!!! Gilashin motar ya fashe d'aya daga cikin matasan ne yake dukan gilashin motar yana fad'in "Futo tsohon banza da shegiyar kilakin 'yarka ogon namu zakuyi wa 'azafi duk bakin cikin Ku k sai ya zama governor!


Mai citta ya futo daga mota a gigice! Yana sa'be babbar rigar shi da ta gama jikewa da gumi fad'i yake'" kuyi hakuri don girman Allah kar Ku tab'a min Lafiya ta kar ki dake ni don Allah kuyi hakuri."



Mari!! Wani daga cikinsu ya kaud'a masa! Cikin tsawa! Yace." Cire wannan babbar rigar ta jikinka ko yanzu muyi maka zigidir."



Da sauri! Ya cire babbar rigar ya jefar yana goge gumin fuskarsa, d'ayan yace." Yi mana tsallan kwad'o."! Babu musu mai citta ya dinga buga tsalle a kan titi shi kuma matashin na haurin sa da k'afar shi Mai citta sai zufa yake yi gwanin tausayi dukan shi yake yi a d'uwawu yana fad'in "Maza!!! Tsallan kwad'o da sauri! Allah sarki me citta ya dinga buga tsallan kwad'o yana nishi su kuma suna tayi masa dariya had'e da d'aukar shi vedio a wayoyin su domin sunyi nufin tozar tashi shi da 'yar shi mara tarbiyya........ Kasancewar jajiberan za'be ne yasa garin yake a hargitse babu Wanda ya fahimci abunda yake faruwa a gurin kowa na hidimar gaban shi dama kuma dare ne motoci jefi-jefi ne suke wucewa a titin sai da suka tabbatar da mai citta ya galabaita sannan suka k'yale shi suka dawo kan Hibbah da ta kusa suma saboda fargaba da tashin hankali..... Cikin iskanci suka jawo ta ta k'arfi ta fad'o kasan mota d'ankwalin ta ya kwance ta dauka zata d'aura suka take cikin tsawa dayansu yace." Ke 'yar iska ko wato kin shiga gidan redio zakiwa Governor mu k'azafi ko tom sai kin fada mana uban da yayi miki ciki kika lakabawa bawan Allah....... Hibbah tana kuka take basu hakuri babu Wanda ya saurare ta a cikinsu sai iskanci suke mata gashi suna kokarin yi mata tsirara a titi.



Cikin kuka tace." Don Allah kuyi hakuri zan fad'a muku." Take suka saurara mata mai babbar wayar ne ya sai ta camera  yana daukarta tace." Wallahi bashi bane sharri nayi masa domin. Ya aure ni." Suka ce tom ki fad'i sunan Wanda yayi miki cikin." Take tace" sharri ne ba gaskiya bane mun shirya maganar ne nida mahaifina muna ganin I Dan muka shiga gidan redio muka fada to zamu 'bata masa suna."



Mari suka dunga gaura mata suna harbin ta da k'afafun su... Daga bisani suka sakata tsallan kwad'o kamar yanda suka saka mahaifin ta..... Hibbah na kuka take tsallan kwad'o har ta isa gurin Baban nata da yayi mutukar galabaita tana kuka shi kuma yana share gumi.




Su kuwa matasan tuni sun bar gurin kai tsaye gidan redio komai da ruwan ka suka nufa domin. Kai musu rahoto suji kuma su gani duk maganar fa mai citta yazo Yayi karya ne...... Take suka fara turawa a wayoyin mutane a'lamarin ya watsu a media kafin Safiya kowa ya gane gaskiya mutane sai tur da Allah wadai suke yi da masu irin hallin mai citta.



A ranar Asma'u da Amjadu kwanan rigima suka yi gashi dai ranace ta farin ciki a gare su tunda Allah ya baiyana gaskiya.... Matsalar daga Asma'u ne ta inda take tayi masa shan'kam shi da yada masa magana cewar duk abunda ya faru laifin sa ne shine ya jawowa kansa raini da neme Neman matansa na tsiya...

 Amjadu kam lallab'ata yake mussaman da fuskanci tana da ciki Bini Bini sai ya bude cikin yayi ta mata sambatu wai nan hira yake da babyn shi addu'a kuwa kullum sai yayi Allah ya bashi da namiji shi idan San samu ne ma Asma'u ta haifi 'yaya uku lokaci guda.... Ni kuwa nace"Amjadu komai na Allah ne domin shine mai bayarwa da hanawa.






*13/12/2019*

[12/14, 11:48 AM] .: *BABBAN YARO*

*89_90*



Ga maibukatar cmplt. Sai same  ni a wannan numbars *08089965176_07084653262*





🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚



```Wannan pege d'in sadaukarwa ne ga duk wani d'an kwankwasiya Amana Mussaman Madugu uban tafiya Dr Rabi'u Musa kwankwaso```

⛑⛑⛑⛑⛑⛑⛑





Alhamdullahi anyi za'be an gama lafiya  yanzu sauran zaman jiran sakamako, to abun dai ba sai an futo an fad'a a zahiri  dai Amjadu duk yafi ko wane d'an takara yawan 'kuri'u jama'ar gari sai murna suke yi domin suna ganin sun Riga sun gama cin za'be, Amjad kuwa yana gida tun bayan da ya futa ya sanya 'kuri'ar shi ya dawo gida ya futini Asma'u yini yayi yana abu d'aya duk ya jigata ta, ya zamana da 'kyar take motsa jikinta aikuwa ta dinga kyalaya amai! na futar hankali Wanda tun da ta samu cikin ba tayi irin shi ba, granny ta dinga fad'a kamar ta ari baki, dama tun daga ya'ki futa take fad'a tana cewa"Shikkenan ya 'ki ya futo ya sanya yarinyar mutane a d'aki yana sasakarta ko tausayi babu." Ita dai Iyami dariya kawai take yi tace "In banda abunki granny yau sharabon da kika ganshi ya zauna a gida irin yau, yau d'in ma dalili ne kuma kinga baza ki hanashi ya kusanci iyalinsa ba." Granny tace"Duk da haka dai wallahi Iyami futunar 'kato yawa gare ta, ace ka shiga d'aki ka kulle tun safe Dan jaraba ko yunwar cikinka baka ji humm Allah dai ya kyauta."! 


Iyami dariya takewa granny ta 'mike tana fad'in "Granny kenan ko dai kishi kike yi ne." ? Da sauri Granny tace" Babu wani kishi ina tausayawa baiwar Allah ne." Cikin dariya Iyami tace"To ai aikin lada take yi kuma idan bazan manta ba kwanaki da bakin ki naji kina mata magana cewa ta tsaya ta kula da mijinta ta bashi hakkinsa saboda kar ya futa yabi matan bariki." 


Granny tace"Ai Ba irin wannan nake nufi ba Wato Iyami kema na lura kina goyon bayan 'kato ko."? Iyami tasa dariya tana fad'in"Dole ne in goyi bayan ubangidana shugaba mai adalci ubangiji Allah ya taya shi ri'ko yayi rik'o da hannayen sa Allah ya bashi ikon d'aukar nauyin jama'a." 



Granny taji dadin addu'ar Iyami shiyasa take sonta Iyami macace mai karamci da mutumci sun fi shekara goma a tare duk masu aikin da tayi tafi sha'kuwa da Granny kuma tafi sonta saboda tana kyautata mata, itama kuma tana kyauta ta mata gwargwadon iko idan Iyami zata je 'K'auyan su Shatara ta arzi'ki granny take had'a mata Iyami tayi buhu-buhu da kayan masarufi ta kaiwa 'yan uwanta na can da suke ganinta  da daraja saboda tana mutukar taimaka musu.


Iyami kicin ta nufa domin had'a sanwar dare ita kuma granny tayi zaune a parlor tana jiran futowar masu gidan, Baby ce ta  rarrafo tazo ta kama granny ta mike tsaye tana mata gwaranci Granny ta dauke ta tana fadin "Nasan Iyayen ki kike nema Yo idan suka ji kukan ki ai sa futo Dan dol... Kafin ta rufe bakinta baby ta tsandare da ihu! Tana nuna d'adin Asma'u da hannunta. 



Rarrashin ta granny take yi fafur yarinyar ta'ki yin shiru sai ya zamana ma kamar 'kara ingiza ta take yi.  Iyami ta futo daga kicin da sauri tana fad'in" Baby rigima ai tunda ta fara wannan kukan nata komai zai tsaya." Granny tace"Tayi min dai-dai Wallahi ke dai je ki cigaba da aikin ki." 



Iyami tace"Granny bari dai in tsaya in dama mata madarar ta kin san Abban ta baya son kukan ta abu komai a sannu dama Kuma yau ba abunci mai wahala zanyi ba."



Granny ta mi'ke tsaye da baby a hannun ta kai tsaye bedroom d'in Asma'u tq nufa tana fad'in"Iyami baza kiyi mana girkin dare ba mutukar kika tsaya rarrashin Wannan 'yar rigimar sai magariba tayi bakiyi komai ba, dole su futo haka." Iyami tabi Granny da kallo cike da mamaki.!



Granny kuwa dukan 'kofar d'akin take yi da hannunta tana fad'in"Kai d'an anace ka futo haka Haba! Wannan jaraba  dame tayi kama! Ni kam na tsani wannan d'abiar taka, ku futo Ku d'auki 'yar ku ta cika wa mutane kunne da kuka." ! Baby ta 'kara tsandara Ihu! Tana zillo dole sai ta sakko. 


Asma'u da Tayi mutukar galabaita ta kalli Amjad din da yake ta kyarma jiki yana 'kokarin sanja mata kaya bayan yayi mata wanka da ruwan d'umi tace"Abban baby don Allah ka bud'e 'kofar nan haka wai baka jin kukan da baby take yi ne tun d'azu." 



Shiru yayi mata kawai ya cigaba da sanya mata riga kamar yanda ya niyyata sai da ya shirya ta tsaf! Sannan ya nufi kofar futa, yana jin haushin abunda granny take masa a gidan duk ta saka masa ido, shi da gidan sa da komai bai isa ya shiga daki da matar sa zata hau 'korafi fa surutai! Cikin zuciyarsa yace ." Da ya sani ma lokacin da tace zata tafi ya barta tayi tafiyar ta ya huta da saka ido."




Yana bud'e kofar ya sha kunnu domin kar taga fuska ta kawo masa wata maganar.... Harara ta maka masa tace"Oho! dai ka futo kana muzurai da 'bata fuska bayan kagama turmshe 'yar mutane kagama iface-ifacen   ka na rashin imani! Irin naka baka  gani yarinyar nan ciki ne da ita sai ka dinga hawanta kamar wani doki Haba! Ina dalilin wannan abu." Ta 'karashe maganar tana mi'ka masa baby da take  mik'a masa hannu.


Hannu yasa ya 'karbi baby yana fad'in"Wai ke don Allah granny ina ruwan ki ne? Kin fiye sa'i do duk kin bi kin dame mu tun safe sai mita kike yi kin hanamu bacci sai kace an fad'a miki abunda kike tunani muka yi to ki shiga ki duba ki gani mana." Ya fada babu wasa



Granny taje "Oho! Kai ka sani ni babu wani shiga da zanyi in duba  domin ni ba yarinya bace, wai mutumin da zai dauki ragamar mutane sama da dubu d'ari shine yake ma'kale mace a jiki babu dare babu rana, itama Asma'u duk da laifin ta da take biye maka sai kaje ka baro ta tana fama da 'karamin ciki."



Dariya maganar ta ta bashi amma baiyi ba sai ma 'kara had'e fuska da yayi yace." Shikkenan kuma saboda zan ja ragamar jama'a sai in fasa more rayuwata kawai don in cutar da kaina bazai yiwu in takurawa kaina ba." Granny tace" Oh-oh! Kaje kayi tayi 'kato Allah ya bada sa'a kadai kiyaye da 'karamin cikin ta." Tana 'kokarin barin gurun take maganar...... Yace." Kinji ki kuma da wani magana granny ciki dai nawa ne kuma nasan takan komai. " Fad'ar haka da yayi sai ta fashe da kuka tana fad'in" Yanzu 'Kato ni kake wa wannan maganar? Ni zaka yi wa gori akan d'an cikin ka." Amjad ya saki dariyar da yake 'b'oye wa yaja hannun granny d'in da take ta faman kuka tana fyace majina sai surutai take yi wai yayi mata gori.



Yace." Nifa ba haka nake nufi ba Kuma ba abunda kike nufi nake yi ba to idan ma hakane ai ba haramun bane tunda ke da kanki kike cawa dani kar in bi matan banza kin ga idan sha'awa ta kamani dole in zo ga iyalina kiyi hakuri kinji Uwar gidana." Granny ta share hawayen ta tana fad'in"Yanzu ina Asma'u take."?



Yace." Tana ciki bata jin dad'i amai ma ta gama yi yanzu." Tace"Ai kaji abunda nake fad'a maka ka 'karya tani Hummm! Mik'ewa tayi ta nufi dakin Asma'u tana surutai kamar yanda ta saba. Shi kuwa Amjadu kallo ya bita dashi har ta bud'e dakin ta shiga sai a lokacin ya saki dariyar da yake 'boyewa yana mamakin 'karfin halin tsohuwar.





******

Alhmdullahi dukanin abunda aka ce Allah a rayuwa to an gama komai kuma zakaran da Allah ya nufa da chara ko na muzuru ana shawo sai yayi, hausawa suka ce hassada ga me rabo taki ce, Amjadu ya sha gwagwar maya a rayuwar shi kafin Allah ya tabbatar da mulkin jahar kano a hannun shi, hak'ika yaga dumbin masoya kuma yaga dumbin ma'kiya dasuke ta caccakarsa gami da zaginsa a gidajan redio dukanin su maganar guda ce cewar shi d'in ba d'an gari bane babu yadda za'ayi yazo ya mulki 'kasa saboda gudun kada ya gama cin albarka cin "kasa ya gudu k'asarshi ta gado *Chadi* to dukanin wannan surutun da suke yi babu mai sauraran su domin jama'ar jahar kano sun gama yin nisa  da 'kaunar Amjadu ta inda suke ganin zasu iya za'ben sa ya zama shugaban 'kasa mutukar yana nuna yana da ra'ayin haka su zasu Goya masa baya.

[12/14, 9:50 AM] .: Rayuwa kenan Asma'u a gidan gomnati lallai arzikin mutum a jikinsa yake Umma ko da wasa bata ta'ba tunanin zata haifi 'yar da zata auri kansila ba ma amma dake Allah Allah ne 'yarta Asma'u wacce take da 'karacin kyau a cikin 'yayanta itace take auran governor dole ta godewa Allah da wannan karamcin da yayi mata,  Amjadu ya d'ora Aminu kan harkokinsa da yake yi a da kuma a halin yanzu ana shirye-shiryen farfad'o da company da ya ruguje shekaru biyu da suka wuce. Umma kullum cikin sanya wa Amjadu albarka take yi saboda ya tsaya mata sosai su aunt Hauwa an samu abunda ake so kasuwanci ya k'ara bunkasa kudi ko ta ina suna shigo mata tunda yanzu Alhmdullahi jari ya fara k'arfi kuma Ya Aminu ya kama 'kasa duk ta dalilin Amjadu, Umma sai yanzu ta yarda da maganar hausawa da suke cewa sai kana dashi ake yi dakai ada idan ta shiga cikin dangin mijinta kallon arziki basa yi mata saboda bata da kudi bata da sutturar kirki yanzu kuwa har rububin gayyatar ta sabga suke yi shi kanshi Kawu  Yunusa kamar yayi mata sujjada Saboda tsabar ladabi da yake mata  kawai kallonsa take yi, saboda tsabar tsaurin ido irin nasa kuwa cewa yayi yana so ta auri Idiris Wanda ya kasance 'kani ga Baban su Asma'u Umma tayi mamakin jin Wannan maganar daga bakinsa kawai sai barshi  da halinsa tasan da cewar duk kwadayi ne ya jawo haka, duk da cewar suma Amjadu din yana tsaye a Kansu yana bukata musu sosai amma sun dauki ido sun 'Dora mata.



'Bangaran granny kuwa bayan za'be da wata biyu tuburewa Amjadu din tayi kan dole sai taje taga 'yan uwa suma da hankalin su na kanta tunda suka ji Amjadu din ya zama governor a jahar kano suke murna da yi masa fatan alkairi.... Amjad da yaga rigimar granny ta'ki karewa sai yace ta shirya insha Allah zasu je ranar Monday gabad'ayan su har Asma'u da cikinta yayi nauyi ga wata Uwar 'kiba tayi ciki wata biyar amma da kyar take cire 'kafa duk yabi nonowan ta da kwankwason ta shiyasa ta bude sosai bayan haka kuma da samun Hutu da cima mai kyau ga Ac ko ta ina ga kulawar ogo domin cikin NATA baya hanasu su more rayuwar su 'ka'ida ne sai sunyi sex dare da asuba abun ya zame musu jiki.



Duk da tarin ayyukan da suke gaban shi haka ya tsalle ke ya bar komai a hannun mataimakin shi Injiniya Jabir Hamid yasan mutumin jajurtacce ne akan komai yayi masa fatan dawowa lafiya  ya tattara iyalinsa suka nufi 'k'asar shi domin gaishe da 'yan uwa.




Satin sa d'aya yayi nufin komawa najeria saboda aikin da ya bari granny ta 'kekasa 'kasa tace ita ba yanzu zata koma ba tilas ya k'yaleta yace. " da Asma'u ta shirya su wuce Asma'u dama a takure take a garin saboda bata samun yanda take so gurin mijinta Granny ta sanya mata ido ita da sauran dangi sai kafkaf  suke da ita da cikinta ko da wasa basa Bari ta sake da mijinta shima haka zai gaji da mota ya kyalesu Dan dai ma aiki nayi masa yawa hade da dubba abubuwan da yake faruwa cikin system dinshi abunda yake dauke masa hankali kenan amma dai duk da haka daurewa kawai yake yi.

[12/14, 10:10 AM] .: Aikuwa granny tace"Asma'u baza ta bishi ba sai da ya bari sa dawo tare, tsakaninsa da granny aka dinga dauki babu dad'i da kyar wani yayan ta Wanda suke kira Malam Halilu yayi mata magana ta kyaleshi ya dauki matarsa ya tafi abunda take yi bai dace ba. 


Sai da ta bari Malam Halilu ya bar gurin ta dinga musu masifa mussaman Asma'u tace"Kije idan ya jawo miki najudar dole kanki kika jiyo ita dai Asma'u bata ce komai sai sinne kai take yi cike da kunya cikin zuciyarta tace"Granny kenan tsoguwa me rigima, ko da zasu tafi granny shigewa tayi daki tayi kwanciyar ta har suka bar gidan Asma'u ta yana da karamcin mutanan sosai suka sad'o ta da kayansu na can irin nasawa da abubuwan gurginsu kayansu na gargajiya duk da dai sun San tafi k'arfin abun Sam basu damu ba tunda Annabi ya fada cewa ka girmama bakon ka. Sai da suka shiga jirgi sannan 'yan rakiyar suka koma gida cike da kewar su. To suma nasu 'b'angaran sunyi kewar su sosai haka rayuwa take dama.



******

Granny sai da tayi wata uku sannan ta dawo lokacin cikin Asma'u ya tsufa haihuwa ko yau ko gobe a lokacin ne Kuma ayyuka suka tsananta ga governor domin ba k'aramin b'arna Alkanawi Yayi ba yanzu sun mai da hankali gurin ganin sun dai-dai ta komai a jahar kano.



Umma sau daya tazo gidan gomnati taga Asma'u ta sanya mata albarka tare da yi mata fatan sauka lafiya ta tafi cike da kauna da son yarta a zuciyarta



Aunt Hauwa kuwa ai tazo gidan yafi sau biyar duk da cewa akwai tsaro sosai amma babu yanda suka yi da aunt Hauwa domin wani sa'in gayya take yo wa ita kawayen ta lallai sai ta nuna musu itama babbar macace kanwarta tana auran governor.




Innah Suwaiba da Hafsa sunzo gidan ya kai sau goma securitys sun hana su ko da ra'bar gate din Saboda rashin sani har kuka sai da Innah Suwaiba tayi musu tana yi musu bayanin cewar ita mahaifiyar mai gidan ce suka ce basu San wannan tayi hakuri sai ya dawo tukkuna a lokacin suna Chadi....Haka suka koma gida jikinsu suk a mace zagi kuwa babu rij Wanda Innah batayi wa securitys din tana fad'in " Idan governor ya dawo zai nuna muku matsayi na a gurinsa shegu tsinannanu.!



Da ta samu labarin dawowar shi sai ta sanya Hafsa ta shirya sosai suka nufi government house din zuciyar cike da kudure-kudure a cewar ta sai ta sa Amjad din ya kori wannan masu gadin da suka yi mata wulakanci sannan ta umarce shi ya sanya ranar d'aurin auran sa da Hafsa.: Ko da suka isa gidan sai suka yadda securitys har sun fi na kwanaki yawa tabbatar cewar mai girma governor yana ciki bai futo ba, taje ta tsaya tana musu magana dukaninsu Hausa bata ishe su ba domin kadan ne daga cikinsu hausawa turanci suke mata suna zare mata ido! Inna ta tsorata sai ta koma gefe guda tana haraarau Hafsa da ta tsinci kad'an daga abunda suke cewa tuni ta tsure! Domin cewa suke maza su bar gurin idan ba haka ba zasu Zane su da bulala! Inna na gama jin abunda Hafsa take cewa kawai sai ta fashe da kuka Wanda yayi dai-dai da shigowar Aunt Hauwa cikin gidan cikin dalleliyar motar ta. Ga mamakin Inna taga aunt ta bude mota ta futo kuma kaitseye ta durfafi securities din babu wani fargaba ko tsoro sai ta dunga mamakin ita kuma wacece ita? Gani tayi suna gaishe ta suna mata magana da turanci hade da nuna su da hannu abunda suke cewa shine wai tasan da zuwan su Innah ko kuma tare suke domin sun San ta saba zuwa gidan da jama'a .


Juyowar da aunt Hauwa tayi sai da gaban Innah ya fad'i ganin suna kama da Asma'u a zuciyarta tace"Babu shakka wannan yayar ta ce   aikuwa hafsa tace"Yawwa inna ga aunt Hauwa nan sai tq shiga damu gidan." Innah Suwaiba Tayi sakato da baki har aunt Hauwa ta karaso gurin ta gaishe ta cikin mutumci sannan tace"Kuzo mu shiga ciki gashi munyi sa'a duka mai grima governor yana nan bai futa ba." Simi-simi suka bi bayan aunt Hauwa tayi musu jagora har katafaran parlor mai girma matar governor hamshakiya mandiya Asma'ulhusna. 



Suna zaune a parlor ita da granny suna shira granny na saman kujera Asma'u na kasa kan wani irin lallausan kafet ta mike k'afafunta Shi kuma ubangayyar yana matsa mata  granny tana fad'in "nauyin cikin ne yasa k'afar taki tayi kumburi nace anya kuwa Wannan cikin naki bana tagwaye bane." Fad'ar maganar granny tayi dai-dai da shigowar su Innah Suwaiba cikin parlor

 Innah Suwaiba tayi turus ganin abunda yake faruwa Amjad gurfane kamar wani bawa yana aikin mammatsa k'afafun Asma'u dake zaune da ciki turus a gaba daga ita har Hafsa jikinsu mugun sanyi yayi tuni Hafsa ta tabbatar wa da zuciyar ta cewar Asma'u tayi mata nisa kuma tayi mata fintikau ya kowa ne b'angaran tasan ko inna ta sanya Amjad din ya aure ta to tasan itace zata sha wahala a gidan Saboda tasan irin son da Amjad din yake wa Asma'u bana wasa bane jikinta yayi bala'in sanyi kamar yanda na innah yayi sanyi cikin sagewar gwiwa suka karaso cikin parlor granny tana musu barka da zuwa



Ita kuwa aunt Hauwa kunya ce ta ishe ta bata tab'a jin nadamar zuwa gidan ba irin na yau governor da kansa yana yiwa kanwarta tausa lallai babu abunda zasu cewa Allah tabbas  yanzu ta k'ara tabbatar da cewar kauna da so tsakanin kanwarta ta dashi Amjadu din ajininsu yake. Bayan sun gaisa da granny dashi kanshi uban gayyar ta wuce dakin Asma'u cikin kunya.



Ita kuwa Asma'u a ladafce ta gaishe da inna Suwaiba dake faman ya'ke tana satar kallonta a fakaice har ta samu damar mik'ewa tsaye a daddafe Amjad din yana taimaka mata sai da ya kaita kofar d'akinta sannan ya sake ta ta shiga gurin aunt shi kuma sai sannan hankalinsa ya dawo jikinsa ya dawo cikin parlor Innah Suwaiba tayi muzu-muzu tana jin Shakkar ta fada masa abunda ya kawo ta gidan saboda yanda yayi mata mugun kwarjini a ido haka suka gaisa dashi jikinta sai kyarma yake yi Hafsa kuwa ba yarda ta hada ido dashi ba. Saboda kwarjini gami da tsoro duk masifar da Inna tazo dashi ta neme shi ta rasa sai ta fara jan granny da hira cikin rashin abinyi Ita kuwa granny biye mata tayi suka dinga hira kamar wani Abu bai faru ba.... Sunanan zaune Amjadu din ya futo cikin shirin futa...ya tsa Yana fadin''Innah zan futa ofis babu wata matsala ko."! Baki na rawa tace"Babu komai Dan albarka Duk ka cika mu da abun alkairi wallahi bama bukatar komai mungode sosai Ubangiji Allah ya jikan mahaifiyar ka." Ya amsa da ""Ameen kana ya futa yana mamaki innah da bata yi masa wani k'orafi ba sai yaga ma kamar tsoransa take ji..shu kadai ya ke dariya cikin mota Rambo dake gefan sa yana taya shi murmusawa hummm Rayuwa kenan Amjadu bai zubar da bodyguard dinshi ba a yanzu ma sune suke take masa baya kasamcewar duk wata gwagwarmaya tare aka sha dasu.





******

Bayan shekaru hudu abubuwa da yawa sun faru ciki kuwa har da haihuwar Asma'u inda ta haifi twins duk maza masu kama da mahaifin su Allah bayanda baya al'amarin shi ana ya gobe suna Hassam din ya rasu sakamakon shakewar nuffashi dalili lokacin an haifi yaran da sanyi a jikinsu Amjadu sai da yayi kuka saboda ya yana son Hassan din kasamcewar ya Dan d'auko kamanin Asma'u kadan a lokacin sai Asma'u tafi shi dauriya. Hakadai ya 'karaci kukan shi ya gama ya barwa Allah to da yake ubangiji sami'uddu'ai ne sai ya kara bawa Asma'u cikin tagwaye lokacin Husaini na wata goma sha daya ta haife su duk mata kuma masu tsananin kama da ita sai dai daya tafi daya haske Hasana farace tas kamar ubanta ita kuwa Husaini kamar Asma'u tayi kaki ta tofar har yanayin jikinsu da saurin bakinta  gami da zafin nama irin na uciki Amjad ya Dora mata son duniya komai Husaina komai Husaina  gata da tsokana da Neman fada amma shi a gurin sa bata laifi idan Maman su ma ta tsananta sai su kwana su yini yana surfa mata masifa wani sa'in ma sai ya dauketa ma wuta ya daina kulata akan 'yayan sa sai taje tayi banbad'anci tukkuna zai dawo.... Lokacin baby ta girma  sosai yarinya me fara'a da hankali kamar uwarta yanayin baby sak da na Mimi domin wani lokacin Husaina tayi ta haike mata tana tsagalgale mata Saboda tasan tana da daurin gindi a gidan... Ko a gaban Amjadu din kuwa abun mamaki sai yayi shuru ko ya mai da abun wasa ita kuwa Asma'u sai bayan ta tabbatar ya bar gidan take kama Husaina ta zane tas! Ta kuna mata muhimamcin baby a gurinta abunda zai baka mamaki ga wannan family shine duk sanda Asma'un take dukan Husaina Saboda halinta babyn ce zata zo ta rugumeta ta kuka wai sai dai a Doke su tare Asma'u takaici duk ya ishe ta Tayi ta fada tana cewa  duk laifin baby ne da take wasa dasu..... Granny kuwa 'yar kallo tq zama a gidan domin Sam bata shiga har karsu Saboda sun gama raina ta Ubansu ya gama shagwaba su baby da Husaini sune c kawai take  mutuntata a gidan.




Tsakanin Amjadu da Jahid zumunci yayi k'arfi sosai Jahid ya aje aikin gomnati ya tsayawa Amjad kan harkokinsa na kasar waje abun sai son barka a lokacin ne kuma mahaifiyar jahid din ta tabbatar da cewar Asma'u mai k'ashin arziki ce a cewar ta da ta yarda jahid din ya aure ta da tuni shine governor😃



****


Umma ta samu wani alhaji dake nan unguwar da suke yana da mata biyu da yara bakwai sosai zuciyarta ta amice dashi ta yarda zata aure shi mutumin yasan abunda yake yi a rayuwa kuma yana tsaye akan iyalinsa sosai don haka akayi d'aurin aure Umma tq zauna cikin gidanta duk ranan girkinta Alhaji Ayuba nan yake zuwa.


Gaba d'aya iyalan Umma sunji dadin Wannan auran da tayi domin shine cikar mutumci ta a halin yanzu Ya Aminu yana da yara bakwai saboda shekata hudu da suka wuce ya kara aure Munnu ta gama boran ta ta hak'ura Yanzu suna zaman Lafiya da kishiyar ta mai suna Amina itama Aminar lallaba Munnu din take ganin yanda Ya Aminu yake kafkaf da ita.




****

Alina kuwa yawan bariki da shaye-shaye da take yi yasa ta zama kwarkwasino ita kad'ai sambatu take yi wai itama matar governor ce.😃



Hibbah kuwa wani tsohon saurayin ta ne ya ya amunce zai aureta bayan  taga yi masa magajiya da koke kike ya amunce bayan ya kafa mata sharad'ai.




Rambo da doh-doh kuwa dama tuntuni suka yi aure lokaci guda Amjadu ya mallaka musu komai na rayuwa suna zaune da iyalinsu cikin gidan gomnati.





***

Sai da Amjad yayi shekaru takwas kan kujerar mulki sannan ya sauka  ya d'ora Wanda yake ganin zai Dora daga inda ya tsaya a jahar kano an samu cigaba iri-iri an samu sauyi mutuka a jahar kano komai yayi sauki  ma'aikata da yan kasuwa suna harkokinsu yanda ya kamata  jama'a sai son barka suke yi masa tare da rokansa kan ya tsaya takarar shugaban kasa. Shi dai bai amsa musu ba kawai yana binsu da abunda suka zo masa dashi.





Rayuwa kenan komai yayi farko yana da k'arshe a yanzu Amjadu da Asma'u sun haifi 'yaya shida hudu mata biyu maza sai baby take cikin ta bakwai Idan ba fada akayi ba babu Wanda zai ce itama ba Asma'u ce ta haifeta ba saboda kulawar da take bata ma tafi ta 'yayan da ta Haifa a cikinta.

Rayuwar gidan Amjadu sai son barka nutsuwa da kwamciyar hankali a gidan babu maganar Karin wani aure a tare dashi duk ya aje gefe guda 'yayan shi ne kawai a. Gaban shi itama Asma'u sai  tayi da gaske sannan yake saurara ta gashi yayi mata mugun sabon da baza ta iya barinsa ba.


**** 

Suna zaune Innah Suwaiba tazo ta sanar dasu d'aurin aure Hafsa Amjad yayi mamaki sosai daga bisani yace." Duk wani Abu da ake bukata innar tayi masa magana zai tsaya akan komai aikuwa haka akayi bukin Hafsa na zuwa yayi mata hidima sosai da sosai kana ya mallaka mata k'aton gida hade da motar hawa lallai babban goro sai magogin k'arfe. Kyautar manya kenan



Bayan bukin Hafsa ne muka fara shirye-shiryen kaisu Baby da Husaini saudia  domin suyi karatu a can gaba ki dayamu har granny muka nufi kasa mai girma cikin aminci da yardar AllahAllah.







*Alhmdullahi*

*Alhmdullahi*

*Alhmdullahi*



Nan na kawo 'karshen wannan littafin mai suna babban yaro ina ro'kon Ubangiji Allah ya yafe min kusakuraina abunda na rubuta dai-dai Allah kamu ikon amfani dashi baki 'daya




Na gaishe ku  real fans d'ina na gruop din babban yaro yawan Ku bazai barni in rubuta sunan Ku ba ni Binta umar hak'ika INA alfahari daku wallahi nagode sosai da sosai da hadin kan da kuka bani har na kawo karshen wannan littafin nawa ubangji Allah ya sada mu da alkairin sa ameen




Sai mun had'u a sabon novel dina mai suna


*MASHAHURI*



_Taku......BintuUm@rAbb@le_

No comments