Breaking News

Ameenatou 19


 *_AMEENATOU_*

_Mamuhgee_

#Arewabooks@Mamuhgee



19

Haroon duk yanda yaso sanar da Jamaal kasawa yayi sbd shigarsa a aikin site din bazaiyiba tinda kwata kwata bayason aiki guri Daya da Jamaal inde na kulawa da harkokin Dad dinsu ne Dan tsoron bawa Jamaal daman fahimtar wani abin Koda tsautsayi ne Dan haka yauma hadiye zancensa yayi Yana dawowa Palo ya zauna a daya daga cikin lafiyayyun kujerun palon Yana cewa


"Amma yau din a gida zaka kwana tinda tafiya ka dawo ba buqatan zuwa asibitin ko?"


JEEY din baice komaiba Saida ya karasa shenye abinda yake hannunsa ya ajiye gwangwanin E-Bull din ya juyo Yana nufar hanyar bedroom dinsa Yana gyara towel dinsa kadan Daya kusa zubewa a qasa ya Bude Baki Yana cewa


"Inada patients Dake jiran dawowana na dubasu,

And inada ma da surgery da zanyi so meyasa zanyi kwanciyana a gida?

I can't even sleep or have a rest if ba hospital din naje ba you know that"


Yana kaiwa Nan ya shige bedroom dinsa Dan shiryowa.


Bai wani jima sosai ba ya fito shirye cikin farar freesize Casablanca hoodie rigar data bayyanarda freshness dinsa sosai

 sai half trousers fari Shima da slippers din Bally a kafarsa da haskenta da tsaftanta kaman ba akai yake tafiya ba.


Qamshin turaren Allure ne na Chanel ya gauraye palon gabaki Daya daga fitowarsa Wanda ya tabbatarwa da Haroon ya fito ya Dan dago nasa fararen idanuwan Shima ya kallesa Yana ajiye remote dayake hannunsa Yana sauya channel Yana duba time na agogon dayake daure a hannunsa yace


"Please kayi dinner damu mana to kafin ka tafi asibitin,Dad yayi tinanin zuwanka da Rana Kaci abinci tareda mu amma baka fito ba."


Zama yayi kusa da Haroon din Yana kunna wayarsa da tinda ya shigo gida ya kasheta Dan samun hutun dayake buqata.


Zamansu guri Daya ne kadai wasu lokutan yake taimakawa kowa ganesu da tareda banbance waye Jamaal waye Haroon sbd fatarsu Daya Dan banbanta sai Kuma halayya da yanayi Amma suna rabewa basa guri Daya shikenan gane waye wannan waye wancan zaiyi matiqar yin wuya har Dad dinsu kuwa musamman idan zaiyi maganar Sirri da Haroon ya ringa kokarin tantancewa kenan kada yaje yayi da Jamaal ya lalata aikin shekara da shekaru.


Cikin sauti me nutsuwa da Kwanciyar hankali ya Bude Baki yace


"Idan na tsaya Kaine zaka kaini asibiti bazan driving ba ka yadda da Hakan?"


Murmushi me kyau da nutsuwa Haroon ya sake Yana gyada Kai da cewa


"Har bakin office ma kuwa zan kaika DR JAMAAL SEELAH."


Murmushi Shima ya saki Yana kallan Haroon din Dake Dora masa da bayanin yanda Dad zaiji dadin Hakan Dan farin cikinsa a rayuwa ya zauna table cin abinci da gabaki Daya iyalinsa.


Kiran sallan magrib ya Saka Haroon miqewa ya nufi hanyar Daya bedroom din dayake palon na Jamaal Yana cewa 


"Kayi magana da mum kuwa?takira dazu tana buqatan sanin yanda ka dawo wayanka is off."


Shigewa yayi bedroom din batareda yaji amsan JAMAAL din ba,

Toilet ya nufa Kai tsaye yayo alwala ya fito suka fito tare zuwa masallacin gidan da suke sallah a ciki tareda su Dad da masu gadinsu da securities.


Tareda iyayensu sukai sallah suna gamawa sukayo ciki gaba Daya Banda Dad Lameenu daya fita tareda drivernsa zuwa wani gurin.


Dad cikin kulawa ya Kalli Jamaal Dake cika masa ido tamkar bashine ya haifesa ba ya tambayesa yanayin aikin Nasarawan Dan kuwa ba qananun dukiya zuka zubawa wannan aikin ba Wanda idan bakiyiba zasu tafka asarar da jijjigasu matiqa Dan haka Koda wasa bari kowa ya Saka hannu a aikinba sai Jamaal ne kadai project din da komai da komai yake hannunsa.


Cikin nutsuwa suke tattaunawa har suka Isa cikin main palon mansion din inda yake tsare da luxuries na Jin dadin rayuwa da asalin Hutu.


Hanyar dining room suka nufa dukkaninsu daidai fitowan mum Atey da itama Hutu da Jin dadin rayuwa yake bayyane a tattareda ita.


Tana ganin Jamaal ta washe Baki cikin kulawa tana cewa


"Dr jeey tin dazu nake cewa kana hutawa baka fitoba bare muyi Maka barka da dawowa"


Dan kallanta tayi a gazarce Yana Dan sake fuska kadan batareda murmushinsa ya bayyana ba ya amsa da


"Eh na gaji ne Koda na iso Ina buqatan ishashiyan Hutu,.thank you"


Fitowan Ayesha 'yarta ne ya sakashi Dan daga girarsa Daya sama Yana Dan  dauke kallansa daga gefen kwata kwata suna cigaba da magana da Dad akan abinda suke tattaunawa.


Gurin Haroon ta nufa tana sake fuskanta gaba Daya da farin cikin ganin Jamaal din tace


"Dr sannu da dawowa."


Batareda ya waiwayoba yanda ya kamata ya Dan juyo kadan yace


"Yawwa thank you"


Zama tayi a kujeran kusa da Haroon tana gaida Dad Shima kafin ta dawo da kallanta kan Haroon tana magana kasa kasa kada kowa yaji me take fada masa Yana dariya fuskansa a sake sosai sbd akwai shaquwa da kulawa sosai a tsakaninsu.


Mum kuwa gefen Dad ta zauna sai ya zamana gefen Jamaal din shi kadai ne Daman Hakan shine raayinsa Dan haka take masu aiki suka qarasa kawo abubuwan da Babu a dining din su ruwa da drinks da cutlerys Dan Basu gama hada table ba masu gidan suka hau.


Mum Atee sosai takeson samun shiga kamar me gurin Jamaal sbd tini ta gama da kame Haroon ta koma itace uwarsa komai da ita yakeyi a matsayin uwa shi kuwa Dr ko a mafarki ba'a Haifa macen da zata maye gurbi ko samun matsayin mahaifiyarsa ba bayan mum dinsa itace kadai tak dinta Dan haka duk tsananin dagiya da son nuna masa tsananin kauna da kulawa da mum Atee keyi Bata taba samun shiga yanda takeso ba Amma dayake ta iya naci da kisisina Bata Dena nuna masa kulawa da tattalin ba saima sake dagewa datakeyi Dan tagama fahimtar Dr din shine SEELAHs ma gaba dayanta yanzu da zuwa Nan gaba hakama Dr ne kadai zata kama ta kama dahir a zaman seelahs harma ta taka matsayin shugaba a cikin matan zuriar duk da akwai wainda suka rigata dadewa a family harda manyan Yaya Amma dai nata burin daban ne akan nasu Dan ita ba zaman auren kadai tazo yiba hadda nemawa Kai suka da matsayi.


Cikin nutsuwa da wayewa sukecin abincin da sakewa dukkanin kulawan mum Atee akan Jamaal take tana tura masa abubuwan datasan Yana ci tana basa tabbacin sbd shi Akai girkin.


Sun jima sosai gurin cin abincin kafin suka gama suka baro dining din Kai tsaye Palo suka dawo suka zauna harsu mum din suka zauna suna magana tsakaninsu ita Dan Haroon da  Ayesha shikuma Yana magana da Dad.


Anayin ishai suka fito Sallah suna gamawa Kai tsaye bangarensa ya nufa ya sauyo kansa daga guntaye zuwa dogon Riga da wando na Dior black ya  fito Yana qamshi ahankali wayarsa kawai ce a hannunsa sai laptop.


Haroon already Yana harabar gidan Yana waya Dan haka Yana ganin fitowan Jamaal din ya Bude motar ya shiga Shima Yana isowa ya Bude ya shige suka fice harabar gidan securities da suka San Dr Jamaal din ba dawowa zeyiba a Daren suna masa a dawo da safe lafiya.


A hanyar ta zuwa tinda suka fito Jamaal ya kira mum dinsa ya Saka handsfree ya ajiye a tsakiyansu suna magana da ita su duka biyun cikin tsananin kaunar datake musu da wadda sukewa junansu Suma.


Suna Isa Haroon a harabar asibitin ya ajiyesa ya juya ya fice sbd ana jiransa wani guri.


Shi Kuma Kai tsaye ya wuce office dinsa duk inda ya wuce ana masa barka da zuwa cikin girmamawa da kulawa harya Isa office ya Bude ya shige.


Laptop din ya fara ajiyewa da wayarsa kafin ya rage AC kadan sbd tin kafin ya iso ake sake tsaftace office dinsa a kunna AC dasu humidifier.


Ajiye remote din yayi bayan ya rage AC Yana nufar files din dayake kan desk dinsa Bai taba ba ya nufi toilet ya wanko hannuwansa ya fito bayan ya goge hannun da towel fari qarami.


Sensitizers ya fara shafawa hannuwansa kafin ya nufi files din ya fara dubawa.



FADILA ALIYU MUHD shine sunan dayake kan file din.


Budewa yayi cikin nutsuwa Yana dubawa tareda karanta dukkanin bayanan dake ciki.


Dr zayyan ne ya shigo office din bayan yayi knocking Yana sanyeda kayan theatr da fitowansa kenan ganin Jamaal ya sakashi sakin ajiyan zuciya da numfashi me sanyi sbd suna tsananin buqatansa akan patient din da aka juye masa file nata.

#MAMUH#

#DR JEEY SEELAH

#BARR HAROON SEELAH

#HASSAN AND HUSSAIN

#AMEENTOU

#FADILA

#LOVE

#ROMANCE

#CRAZYINLOVE



*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*

 _Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*

_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*

_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*

_Miss xoxo_


Guda Daya 400

Guda biyu 700

Guda uku 1k

Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

No comments