Breaking News

Ameenatou 22

 *_Arewabooks@Mamuhgee_*

22


Fadila da tinda aka fara wannan tashin hankalin ta shiga nata tashin hankalin Mai tsananin gaske da damuwa tareda janyewa daga kowa Dan kuwa tasan bama zata taba samun Jamaal ba yaudaran kanta takeyi data bari ta jefa kanta a duniyar da Bai kamata ace ta jefa kanta ba.


Ummanta da baban damuwa suka shiga Suma gashi damuwan yafara tabata yau lafiya gobe ciwo harta Kai oxygen ma wasu lokutan da dama tana zarewa kanta batareda saninsu ba saidai su sameta tana kokarin rasa rayuwarta suyi gaggawan Kiran Dr Jamaal din Wanda Shima tini kansa ya fara daukan caji Dan kuwa sosai take kokarin rasa rayuwanta a lokuta da dama idan Hakan ta faru.


Zafi sosai kansa ya dauka kaman yanda iyayenta Suma kansu ya dauki zafi daga karshe batareda sanin Jamaal din ba baba yaje har office din Alh Lameenu seelah yayi magana dashi bayan dogon jiran Daya Sha da bin dokoki sbd baida appointment dashi.


Bayani da nasihu yayi masa akan su hakura subar yaran suyi aure tinda suna son juna Kuma ya sake Basu tabbacin yarsa batada wata tarbiya mata kyau ko halayen da zasu sakasu Jin Dana sanin barin dansu ya aureta ciwonta Kuma kaddara ce da Allah yafi kowa sanin dalilinsa na yinta a Hakan.


Harya gama bayaninsa da nasihunsa Harma da waazinsa Dad Lameenu baice komaiba sai daga karshe yayi masa Godia fuska a sake Yana nuna ya gamsu da bayaninsa Kuma insha zasu tattauna da Dan uwansa zasu taho da jamaarsu maganar neman auren.


Bayan tafiyar baban  numfashi Dad Lameenun ya sauke Yana Jin gwara su bari ayi auren idan har sunason riqe Jamaal a hannunsu batareda ya barsu ba.


Da daddare suna tareda Mam a office dinsu na gida yayi masa bayanin komai Wanda kusan Shima Mam din shawarar Daya Yanke kenan ganin Jamaal din yafara Shirin barin kasar da gaske barinsu zeyi Wanda yafison ya rasa wani bangare na dukiyarsa me yawa Daya rasa Jamaal a bangarensa.


Ranarda Jamaal yagama samarwa fadila Visa auren kawai za'a daura musu ya tafi da ita Dad dinsa akan dining gurin cin abinci ya sanar dashi ya amince da auren idan har zai zauna dashi bazai barsa ba har abada sedai mutuwa.


Wani sanyi ne ya fara cike zuciyar Haroon kafin mum Atee data sakin hamdalan farin ciki hakama Ayesha data shiga damuwan tafiyarsa.


Shikuwa dagowa yayi ya zubawa Dad din fararen idanuwansa batareda yayi masa alkawarin dayace yayi masa dinba Dan kuwa baiyi alkawarin barin mahaifiyarsa har abada ba haka Kuma idan ya daukota daga qasarta ya dawo da ita kusa dashi baiyi mata adalciba shiyasa Bai taba gwada cewa zai dawo da ita kusa dashi ba kwata kwata duk yasan idan yace ta dawo kusa dashi din zata dawo Amma dai bayason yi mata Hakan Dan qasarta itace Kwanciyar hankalinta da nutsuwanta.


Murmushin yaqe Dad din ke sakewa na yake Yana nunawa Jamaal din ya amsa fadilan dari bisa dari.


Numfashi Jamaal din ya sauke Yana Dan lumshe idanuwansa tareda Jin wani nauyi dayake kirjinsa ya sauka Dan kuwa Koda ya tafin zuciyarsa bazata taba samun wannan nauyin ya sauka ba tinda bawai baya kaunar mahaifinsa bane Yana tsananin kaunarsa fiyeda tinani kawai dai shi ya iya boye Abu ne dakuma yawan samun sabanin raayin dayake samu da Dad din ba kaman Haroon ba da duk abinda Dad yafada masa yayi me kyau da mara kyau to ya zauna.


Cikin farin ciki me tsanani da Jin dadi Haroon yayiwa Dad din Godia Yana bayyanarda Jin dadinsa ga sulhun da aka samu tsakanin Dad da Jamaal din Dan idan Jamaal ya tafi ya barsa baisan wace rayuwar zai fuskantaba a gurin Dad din idan Jamaal Baya nan hakama yasan bazai taba iya musu ayyukan nasarorin da Jamaal yake musu ba musamman bangaren manyan harkoki da baida sani ko kadan akansu.


Jamaal ma Jin yayi tausayin Dad din nasa ya shigesa sbd ya amince ne da auren yasani Badan har dari bisa dari din Daya fada ba Yanason auren sedan Yana tsananin sonsa fiyeda nasa farin cikin bayason rabuwa dashi.


Godia yayiwa Dad din cikin nutsuwa da kulawa tareda bayyanar masa da kaunar da Dad din ke tsananin son Gani daga garesa.


Hakan da yayi ba qaramin Saka Dad din farin ciki me girma yayi ba Wanda harya bawa Haroon tausayi sbd idan akwai abinda Allah ya jarabta Dad din dashi shine Jamaal da kaunarsa.

Ko Alh Lameenu lokuta da yawa shi kansa Yana tsoro da shakkar yanda Mam ke tsananin son Jamaal Dan haka yake gudun kada Hakan ya zama raunin Mam su samu matsala sosai me girma tinda Jamaal din kwata kwata ba page Daya suke dashi ba akan abinda suke aikatawa Dan ma Allah ya rufa musu asiri ba shine lawyer ba Haroon ne da kashinsu ya Dade da bushewa duk power dasuke riqe da ita suna juya sharia yanda suke so da sai Jamaal ya tabbatarda sun rasa komai.


A Daren ranar firan da suka jima a tsakaninsu basuyiba Saida sukai shida Dad ciki kulawa da kauna har tsawon dare kafin ya fito ya wuce part dinsa tareda Haroon da Shima ranar kaunar Yan biyunsa ta motsa a part din zai kwana.


Bedroom dinsa ya wuce Kai tsaye ya fada wanka zuciyarsa na samun nutsuwan dayake buqata wadda ya rasa a kwanakin sbd rigimansa da Dad.


Haroon ma Dayan dakin ya nufa wankan yayi ya fito Kai tsaye ya nufi bedroom din Jamaal ya Bude closet dinsa ya dauko kayan bacci black ya Saka ya fito yaje kwanta,sai a lokacin Jamaal din ya fito ya shirya cikin fararen kayan bacci ya kwanta tareda dauko wayarsa Yana Kiran fadila a natse.



*******Amincewan Dad shine babban abinda yayiwa kowa dadi da farin ciki har bangaren su fadilan wadda batada wani qwari ko kuzari Amma tayi murna sosai.


Babu Bata lokaci Jamaal ya buqaci ayi auren Dan kuwa a yanda yake sane da ciwonta yayi tsanani sosai Dan kuwa yanzu lungs dinta sunyi Nisa sosai oxygen ma Neman gagara riqesu yakeyi Dan haka yake buqatan auren zai fita da ita yaga wasu likitocin da zasu duba case dinta sosai tareda shi.


Bai sanarwa kowa ba har iyayenta matsalanta yayi muni sedai daga su har fadilan jikinsu yayi sanyi sosai Dan sosai kullum take sake zama weak numfashin ma ahankali ahankali take iya shaqarsa.


Hakanan suke lallabawa Dan asamu ayi bikin,


Fadila da kanta ta cire Rai daga rayuwa a yanzu Amma dai babban fata da burinta shine ta samu zama matar Jamaal kafin Allah ya dauki ranta,

Tanason cika masa burinsa na son ganinta a matsayin matarsa mallakinta kafin ta koma ga Allah Dan haka take fata Dan rokon Allah ya Bata qwari da qarin kwanakin da zata  cika masa wannan burin.


Su kansu iyayenta duk yanda jikinsu yayi sanyi ga yanayinta a yanzu ta Basu qwarin gwiwan karban kaddararsu,

Suma a yanzu fatansu ta zama matar Jamaal kafin Allah ya dauki ranta

Idan hakan ta faru zasuyi farin ciki ko bayan ranta sbd burinta ya cika Kuma Jamaal ya zama sirikinsu baiyi musu wahalar banza a banza ba.


Jamaal kwanakin auren na sake kusantowa Amma kwata kwata kansa ya dauki zafi baida lokacin komai bayan tattaunawa da Neman yanda zaiyi ya kawowa fadilan sauki ta samu shakar numfashi me dadi da nutsuwa Dan lamarin yafara karya masa zuciya Amma Koda zaiyi yawon duniya da kasashe ne zai Nemo mata lafiya idan har Allah yayi zata warke din.


Kwanaki na sake kusantowa na auren fadila na sake zama weak sosai Dan yanzu gaba Daya tayi fayau kaman Babu jini a jikinta hakama sai qanqancewa takeyi tana rama da komawa karama.


A daidai wannan Gabar iyayenta sunyi kuka harsun godewa Allah sbd tinda take fama da ciwon tsawon shekaru Bata taba komawa Hakan ba sai yanzu gashi ita kanta wannan Karan ta fidda Rai daga rayuwa adaidai lokacinda taso ace ta rayu Dan bawa Jamaal farin ciki.


A rayuwar seelahs Babu Wanda ya taba tinanin zaa samu Jamaal a hali na fita hayyaci sbd kwallafa Rai a Abu sai yanzu.


Duk yanda su Dad suka dauki matsayi da girman yarinyar a zuciyarsa abin ya wuce Nan Dan haka hankalinsu yasake mummunan tashi akan lamarin auren.


Gaba Daya Jamaal ya aje komai ya tattara hankalinsa gaba Daya akan Neman mafitan ciwon fadila,

Kai tsaye ya ajiye komai har aikin asibiti sbd gaba Daya ta koma a kwance take rayuwa a kwanakin ga oxygen din kwata kwata kaman ya Dena mata aiko Dan haka take ya fasa jiran sauran kwanakin auren yace a daura kawai zai fita da ita waje mum dinsa ma tana Jira zasu taru da wasu likitocin su duba matsalanta Daya kasa Ganowa.


Babu Wanda yayi musu da maganar auren nasa dayace a matso dashi Dan Babu wani biki ko hidiman ma da zaayi tinda amaryan a kwance take tana Neman numfashinda zata shaqa ma ta rayu.


Haroon baitaba sani ko ganin haka asalin so yake ba sai akan Dan uwansa Wanda Bai taba Ganin abinda Jamaal yaso fiyeda komai ba bayan iyayensa dashi sai Fadila,


So ne me tsafta da karfin gaske da Allah ya jarabcesa dashi na yarinyarda ba lallai ta rayu ba Dan koshi da ba likita ba baiga alaman tashi ga fadila ba sedai kwata kwata Jamaal ya kasa yarda da fadilan bazata warke ba ta tashi ta basa 'yan biyun datai alkawarin basa Shima yayi alkawarin ita kadai ce zata zama uwar yayansa,

Ita kadai ce macen dayake son ta Haifa masa wasu Jamaal and Haroon Kokuma Mamman da Omar.


Tausayinsa sosai Haroon yakeyi tin yanzu Daya kasa gane komai ya jinginar da rayuwansa kwata kwata akan fadila da iyayenta da suka koma sune masu basa hakuri da qwarin gwiwa.

#MAMUH

#SEELAHS

#AMEENATOU BABBAH

#LOVE

#HOTLOVE



*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*

 _Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*

_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*

_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*

_Miss xoxo_


Guda Daya 400

Guda biyu 700

Guda uku 1k

Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

No comments