Breaking News

Ameenatou 36

 *_Arewabooks@Mamuhgee_*

36

Ameenatou na islamiya ya dawo Dan haka bayan yayi Sallah abinci yaci ya kwanta Dan samun baccin da tinda yake Lagos harya baro Bai wani samuba.


Shima siddeeq hutun ya kwanta ya samu kafin yamma.


Karfe Biyar da mintina ya tashi daga babbacin na awa Daya da Yan mintina San Saida yayi laasar ya kwanta.


Wanka kawai yayi ya shirya ya karbi ke din mota daga hannun siddeeq da kansa yaja ya nufi makarantarsu Ameenatou Kai tsaye.


Yana Isa ana tayar dasu Kuma Hafiz ma Yana Isa daukota Dan haka Koda ta fito cikin doguwar hijabinta akansa idanuwanta suka fara sauka Yana tsaye jikin motarsa Yana waya ahankali kaman mara lafiya kyakkyawar fuskansa ta fada kadan gaba Daya ya juyo hankali da idanuwan duk Wanda ya fito makarantar dama masu wucewa akansa sbd ganin bature tsaye bakin makarantar tasu.


Waya yakeyi Amma Shima tinda ta fito idanuwansa na kanta yanajin jikinsa na mutuwa zuciyarsama sanyi tayi Dan baisan wane irin so ne yakewa Ameenatun ba.


Ganinsa itama ya Sakata sakin kyakkyawar murmushi tana Dan dauke idanuwanta daga kansa Dan kuwa Jin tayi ganinsa ma gaba Daya ya Sakata Jin wani farin ciki me yawa gashi tana son tayi murna sosai a fili Amma batason Yan makarantar Susan shi zata aura su fara kalle mata shi Dan gulmansu.


Nufosu tayi zata Bude Baki tayi magana Hafiz ya jefa mata wani kallan Daya sakata nutsuwa tana hadiye zancen Daya fadawa Haroon na kewan datai masa me tsanani.


Kashe wayarsa yayi Yana kallanta fuskansa daukeda murmushi Mai bayyanarda farin ciki yace


"Barka da fitowa Budurwan Babbah"


Wani sabon farin ciki taji ya rufeta sedai narke fuska tayi tana qasa qasa da murya kada Hafiz yaji tace masa


"Yanzu ba budurwan Babbah bace ai na sauya suna"


Mota ya Bude mata ya shiga ya rufe mata Saida ya zagaya ya shiga ya zauna Hafiz ma ya shigo kafin ya kalleta Yana tayar da motan yace


"Yanzu yar budurwan Barrister ce ko??


Wani sabon dadin taji Yana hararan Hafiz da Shima ita yaketa harara kaman idanuwansa zasu fado Amma taqi kallansa bare taga kwabar dayake mata ya ido sbd sakarcin Data Saba yi musu hadda Haroon din kada tayi a gaban makarantar cikin bainar jamaa.


A hanya kafin su Isa gida guri uku tana sakawa ana biyawa sbd siyan wani littafinta na islamiya da zata dashi gobe kafin suka Isa gida anata kokarin shiga sallan magrib Dan haka Haroon din Bai shiga ba alwala kawai sukai a waje suka wuce masallaci ita Kuma ta shige gida.


Saida sukai ishai suka shigo gidan anan Haroon yaci abincin Dare tareda su Babbah na tambayar yanda ya baro mutanen gida.


Irin son dayake mata itama take masa basa buqatan ma wai saisun kebe sbd a jininsu suke jinsa shiyasa duk firar da sukeyi anan dai tareda kowa tsakar gida ake yinta Kuma ahakan suke soyewansu a gaban su Babbah Dan shi Kam idanuwansa ne basa iya kaucewa daga kallanta matiqar tana gurinda yake ita kanta kallansa shine ke sake sakawa duk tana sake shagwabe masa ko agaban su Babbah ne kuwa sai idan Hafiz ya gaji da sakarcin ya dinga fada kenan Yana hararta idan Haroon din ya tafi.


Washe gari ne zaa tafi da Ameenatou Abuja gurin rubuta jamb nata Daman hadda shi ne ya Saka Haroon din dawowa da wuri Kuma kaman yanda yaso university na Lagos aka cika Mata Dan haka tin 6 da mintina ya iso gidan da motarsa Daman Abdul tini ya shirya itama duk rigimarta Saida aka lallabata tayi wanka tin asuba ta shirya dadah ta shirya mata abincin karyawa da wuri Babbah ma sai addua yake binta da ita Yana cewa saita cinye har marking din Daya wuce Wanda akeso.


Abuja zatai jamb din Dan haka Babu Bata time suka fito itada Yaya Abdul da Haroon din suka kama hanyar Abuja idanuwan Haroon na cikin mirror Yana kallanta itama shi take kalla suna jifan juna da murmushi tana masa magana kadan kadan kaja Yaya Abdul din yaji Mai take fada masa batasan Yana ganinta ba yayi mata banza sbd yasan ma maganar idan yayi Bata bakinsa zaiyi Dan haka yayi kaman ma baisan me sukeyi ba fatansu dai kar Haroon din ya jefar dasu gurin wannan mayen kallan nasa da kullum sai Babbah yace tsoron yakeyi Haroon din ya cinye masa ita da ido ta rame kafin a tashi auren.


Sai 3 suka dawo gida a gajiye budurwan gidan ta dawo harma da zazzabi sbd kaf rayuwarta Bata taba Shan wahalan tafiya ko wata yar gwagwarmayar ba sai yau duk da komai na gata Akai mata Dan kuwa ko Rana Haroon dinta Bai bari ta shiga ba Saida zata shiga exams din ta fito mota hakama bayan fitowanta lafiyayyar tsadaddiyar restaurant yakaisu sukaci abinci Amma Sam Bata iya cin wani abincin ba sbd gajiya gida kawai takeso karshe ma haka suka koma daga shi har Abdul din suna lallabata har aka iso gidan.


Haroon ajiyesu kawai yayi ya wuce Shima Dan haka wanka dadah ta taimaka mata Tayo ta zo ta kwanta take bacci ya dauketa sedai Koda yamma tayi zazzabi sosaine ya rufeta Dan haka hankalin dadah ya Dan tashi zuwa dare Saida aka Kaita chemist kafin su dawo zazzabin ya Dan saketa Se zuwa dare ya sake dawowa.


Koda gari ya waye Haroon Bai Isa gurin aikinsa ba Jin rashin lafiyanta Kai tsaye gidan ya taho karshe dai asibiti aka kwasa aka Kaita duk da narkewanta ne yake Saka ciwon zama wani babba.


Suna zuwa haka aka kwantar da ita sbd ganin yanda hankalin duka ahalin ya tashi hakama Haroon seelah din.


Kwananta Daya a asibitin aka sallameta bayan Haroon yagama lalacewa akanta tareda mantawa da aikin dayake gabansa Wanda duk iya kokari da sadaukarwan siddeeq gurin ganin project din ya tafi daidai ko kadan ne Hakan Bai faru ba Dan haka yake cikin tashin hankali da rashin nutsuwa.


Aikuwa Haroon na dawowa hayyacinsa ya nutsu ya fahimci gagarumar tashin hankalin Dake gabansa take ya shiga firgici Shima Dan tini ma sbd sakacinsu aka sace plans da komai da komai na project din.


Wannan mummunan tashin hankalin ya kusan Sakasa zaucewa Dan kuwa Yanke jiki yayi ya Fadi Saida siddeeq da sauran ma'aikatan suka taresa sedai gaba Daya Jin yayi Yana fita hayyacinsa kansa na Neman Juyewa hannuwansa na rawa.


Gaggawan mayar dashi hotel siddeeq yayi Shima nasa hankalin baa kwance ba Dan kuwa yasan ko Dad yaji wannan zancen sake samun hawan jini zeyi gashi Babu ya yanda zata yiyu cikin qanqanin lokaci su hada sabuwar plan din dazata sakasu Kai labarin wannan project da aka fara.


Haroon Neman zaucewa yafara yi zuciyarta na tsananta bugun Daya wuce misali hakama baisan ta inda zai fara ba.


******Dad Lameenu Dake zaune tareda Mam a palonsu na office suna magana wayarsa ce tayi ringing Ya juya ahankali ya Kalli sunan me Kiran yaga BB ne Dan haka Kai tsaye ya dauka tareda Kai wayar kunnensa Yana cewa


"Yes BB"


Bayanin komai daki daki BB ya fara korowa tin daga kan sunayen ahalin gidan Babbah da Kuma yanda Haroon gaba Daya rayuwarsa ta mace akan yarinyar gidan da Baya gane komai ba a yanzu idan ba abinda ya shafeta ba harma da bautawan dayake musu da gagarumar tsautsayi da aka samu akan project din....


Dad Lameenu Bai gama Jin karshen zancen ba wata mummunan zufa ta tsinke masa Yana cewa


"What???

Yaushe wannan babban balain ya samu??

Ina Haroon din yake yanzu??


Mam na Jin Hakan ya ajiye wayar hannunsa Daya karanta wani article da aka rubuta gameda rushewan da SEELAHs keyi a boye batareda sun bari duniya ta saniba.


Ajiye wayar yayi Yana Dan rintse idanuwansa da suka fara sauyawa Dan kuwa Yana fatan ba abinda zuciyarsa ke Saka masa bane zaiji daga Lameenun.


Cikin tashin hankali lameenu ya buqaci ganin BB yanzu yanzu Dan zuciyarsa bugawa zatai idan Yana sauraron wannan mummunan tashin hankalin ta waya.


Kashe wayar yayi Yana kasa kallan Mam da shima ya kasa tambayar Lameenun komai BB din yake Jira yaji komai Dalla dalla daga bakinsa.


Kafin BB ya iso daga Mam har lameenu da jininsa ya Dade da Hawa Dan tini aka kirawo likita Yana cikin auna BP dinsa BB ya iso take ya sallami likitan akan saisun gama magana.


iPad din hannun BB ya fara kamo hotunansu Hafiz da Yan gidan kaf ya ajiye ipad din gabansu bayan ya kamo hoton Ameenatou datake sanye cikin hijab dinta na islamiya tana murmushi asalin kyanta da kuruciyarta a bayyane tana kallan gefe Dan kuwa batasan ana daukanta hoton bama.


Bayani Daya bayan Daya a tsanake BB yafara jerowa Wanda yayi mugun girgiza su musamman Mam Dan kuwa Bai taba tinanin Shima Haroon zai fada irin kaddarar Dan uwansa ba ta yiwa mace son da Bai kamata ba adaidai lokacinda suke buqatan nutsuwansa da hankalinsa tareda sadaukarwansa fiyeda komai a duniya yanzu.


Ameenatou dukkaninsu suka zubawa idanuwansu da sukai jajir,


Tayaya Haroon zai bari zuciyarsa ta mutu akan mace bayan yasan Menene a gabansu,

Tayaya Haroon zai bari mace ta shiga zuciyarsa,

Tayaya zasu iya samun yanda suke so daga zuciyar Daya mutu akan mace.


Kenan shi tasa mummunan kaddarar akan matan da yayansa suke so ne ko me?

Shima Haroon macen ce zata shiga tsakaninsa da ita?

Ta Ina zai fara karban wannan kaddarar ta Haroon bayan haryanxu Bai fito daga baqin ciki da radadin ta Jamaal ba.


Wani nauyi kirjinsa yayi Yana tafasa da wani irin zafi da radadin da baisan mezaiyiba akan Haroon din Daya kashesu da ransu a Rana tsaka.


Lameenu da tini jininsa ya sake hayewa akan babban tashin hankalin da Basu Saka masa Rana ba da sauri aka sake dawo da likita.


Da sauri likita ya dawo Yana cewa a kwantar masa dashi flat.


Mam tsaban tafasa da qunan da zuciyarsa keyi Jin yayi Haroon baida sauran amfani a garesa ko kadan Dan haka take ya Bada umarnin a Siya masa ticket a ranar zashi Nasarawan.


Lameenu na Jin Hakan yaso wartsakewa su tafi Amma Ina hawan jinin ya sharbesa da kyau Dan haka Yana ji Yana Gani Mam din ya tafi.

##MAMUH#

#DR JEEY

#AMEENATOU

#MAM SEELAH

#BABBAH



*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*

_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*

_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*

_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*

_Miss xoxo_


Guda Daya 400

Guda biyu 700

Guda uku 1k

Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

No comments