Breaking News

Tsutsar nama 48

 *_Typing📲_*









   *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*

             _(Itama nama ce)_






_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_




_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕_


___________


_Koda kuɗinka sai da rabonka. Ka gani su birgeka, ka saya ka birge mai kallonka. Albishirin ku ƴan kasuwa da masoya. Kuna ina? Ina kuka shiga? Maza ku garzayo kantin sauƙi da rahusar ingantattun kaya na kasarku dama ketarenta. Bari na kaiku, *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING* ke muku sallama irin ta addinin musulunci da babban albishirin shiryawa tsaff domin kawo muku kayayyakin buƙatunku na yau da kullum. Tun daga kan irinsu, atamfa, lasses, shaddoji, materials, abayas, takalma, handbags na zamani, vails ƴan yayi. Hijjabai. Sarkoki da dangoginsu. Kayan shafe-shafen dana kwalliye fuska. Agoguna harma dasu eyeglasses na manyan mata. Kai kai Karfa na cikaku da zance, dan zaku iya ganin komai a *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING* domin farin cikinku. Kayan yara harma dana maza ba mata kawai ba. Ba'a sayen ɗai-ɗai zamu tsaya ba harda sari ga mai buƙata zamu bada in sha ALLAHU kuma akan RAHUSA mai sauƙi da kaima zaka samu naka rabon. Zakuma mukai maka kaya a duk inda kake a *NIGERIA* in sha ALLAHU. Ƴan kasuwa masu sari da masu sayen ɗai-ɗai ku garzayo nan domin gani da ido in sha ALLAHU. Ka gani su birgeka, ka saya ka birge masu kallonka sai a *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING*👇_



https://chat.whatsapp.com/Cce1etNkvVKCBlgSqXa4Ek


___________



........Kai tsaye ɗakin Yaya Musaddiq na nufa. Bayan na gaishesa ya ɗan tsokaneni nai masa zancen da naji ana tsogumi ɗazun a kai. Murmushi yay min da faɗin, “Kandala ƙyale batun mutane da halinsu. Dan su basu iya komai ba daman sai gulma kawai. Yanzun nan babu jimawa muka rabu da Mansoor ɗin ma, dan munje can gidan nasa ne da kafintan da yay kayanki saboda zasu kaisu da sassafe gobe in sha ALLAHU. Ya kuma min batun kayan sai gobe in sha ALLAHU zasu kawo wata ƙanwar Mamynsu ce da zatazo da ga Dubai a yau da dare ake jira dan akwai wasu kaya a hannunta, amma shima yana cikin damuwar rashin kawo su shiyyasa ma ya kasa neman ko Hafizzullah a waya ya haɗaku dan kunyarki yake ji”.

     Ajiyar zuciya na sauke a hankali. Dan nama san ƙanwar Mamyn tasu, yasha bani ita muyi waya. Murmushi yay min yana kai ma kaina rankwashi da faɗin, “Sam yanzu Kandala baki da kunya. Yanzu ni kike zuwa tambayar batun kayan aurenki ma”. Hannu na saka na rufe fuskata ina dariya. Shima dariyar yake yi. A dai-dai nan Hafizzullah ya shigo ɗakin da sallama. Dan tun washe garin da aka ganni yazo gida dama. Ledar hannunsa na warce ina faɗin, “Zaga gari mi kuma ka samo anan?”.

      Ƙoƙarin warce ledar shima yake a hannuna yana hararata. Ban yarda masa ba har sai da na buɗe. Ganin awara yasa na taɓe baki ina miƙa masa. “Oh oh kwantar da hankalinka ashema naman talaka ce”.

         “Oho dai, kema naga ci kike”.

     “Ai ni in naci ba komai bane. Amma kamarka dai saurayi mai hurama ƴammata hanci abin kunya ne. ALLAH yau da ina da waya saina ɗauki hotonka nasa a status ƴan matanka sun gani”.

     Dariya ya sanya da yimin gwalo, ya ce, “Ai sai ki samama kanki lafiya tunda baki da. Kuma sai na zuga Yaya Mansoor kar ya saya miki waya har sai kin shekara a gidansa”.

        “ALLAH sarki jiki duk baƙin ciki su Hafizu. Aiko zakasha mamaki, kafin rana ita yau kasa a ranka na mallaki waya”. Na ƙare maganar ina kai masa rsankwashi a kansa.


💥💫💥💫💥💫


     Kamar yanda Mansoor ya faɗa hakance ta kasance. Dan washe gari misalin sha biyu na rana ƴan kawo kayan nan suka iso gidanmu su uku. Zuwa lokacin baƙi sun ƙaru. Dan wasu matan ma a cikin ƴan Gwarzo ma sun iso. Tuni Aunty Zakiyya ta shiga maƙwafta tai kiransu dan Mum taki aikawa a kira kowa aiki. Sai ma yi take kamar wadda ta ruɗe. Dan ma ƙanwarta na tare da ita tana saitota. Baby kam ban san ina ta tafi ba dan tun jiya da yamma ban sake ganinta a gidan ba kuma. Waɗan nan kaya sun matuƙar girgiza sukata. Dan da gasken gaske Mansoor da ahalinsa sun nuna bajinta. Duk da ba fariyya akayi ba komai na nan dai-dai misali amma kuma na bajinta da zai tabbatar maka an kashe kuɗaɗe sosai. Dan komai acan-acan ko maƙiyi yasan kaya sunyi ga kuma kayan lefe da dama sun riga sun kawo. 

     Har aka gama karɓar kayan ni dai ban ko leƙo ba sam. Sai da dangin Mansoor suka wuce sannan aka maido kayan nan ɗakin da muke da su Gwaggo Gudidi sannan su Asiya suka tsareni sai na gani harda Aunty Zakiyya. Na ɗan kalla sama-sama na rufe akwatin ni dai. Har raina ina sake jin kima da girman Mansoor matuƙa dama ahalinsa gaba ɗaya....


   

           💦💦💦💦💦💦💦


      “Aunty dan ALLAH ki kwantar da hankalinki ni banga aibun yarinyar nanba sam wlhy. Ga danginta mutanen kirki. Karfa kiga irin tarbar da akai mana ta girmamawa wlhy.”

         “Humm Anesa ni fa bance tanada aibu ba. Amma ya kamata ku fahimci abinda nake nuna muku. Yanzu dan ALLAH da kikaga yarinyar tayi kama da wadda akai kidnapping na tsawon sati biyu da wasu kwanaki? Nafa fiku son yarinyar nan, kuma har yanzu ina jin sonta a raina”.

     “Aunty wlhy ni ban ganta ba.”

“Humm to ai naso ki ganta da kin tabbatar. Amma al'amarin da mamaki ace ai kidnapping yarinya budurwa ƙyaƙykyawa kamar wannan wai ta tsallake tarkon namiji. Sannan kuma basu nema kuɗin fansa ba saboda sun sami abinda yafi kuɗin kenan. Ya kamata kowa ya gane maganar matar kawunta da abar a duba ce fa. Dan dolene ɗayan biyu a samu ɗaya. Kodai da ƙafarta tabi wanda suka sacetan nan zuwa wani hotel ko guest house. Ko kuma wanda sukai kidnapping ɗin nata sun samu abinda yafi kuɗi a jikinta. Wai Kinga kuwa yanda ta ƙara wani fresh na haske da laushin fata tamkar wadda ke rayuwa a ac. Ai bana jin ko kafin a sacetan jikinta yay wannan luf-luf ɗin. Amma da yake yaron nan ya makance da shirme shi ko sau ɗaya bai zauna yayi tunanin komai ba. Na rasa mike damun kan Mansoor ne. Ga ubansa shima yama ƙi ya sauraran balle ya gane abinda nake nufi. Kema kuma gashi kina nuna bazaki fahimceni ɗin ba”.

         “A'a Aunty, ba fahimtarki ne bazanyiba nikam. Abinda kawai nake son ki duba bakin alƙalami fa ya riga ta bushe. Tunda gashi yau har sauran kayan lefe mun damƙa musu. Sannan Mansoor ya sanar min sun kai kayansu can gidansa wasuma a dangin nata na jerensu yanzu haka. Sannan Aunty gobe ne fa ɗaurin aure. Kuma kin ce Abban Attahir ma yaƙi fahimtarki balle ma shi Mansoor ɗin da kin gagara tunkararsa da batun, to tayaya kike tunanin zamu iya wani abu a ƙurarren lokacin nan?”.

         “Zamu iya kuwa Aneesa. Dan anma zauna a filin ɗaurin aure ya watse ballema wannan da sai gobe. Mansoor da kike gani sam bashi da wani isashen wayo. Wlhy koda yasan yarinyar nan bata ƙwarai bace zai iya shanyewa saboda son da yake mata na masifa da ni sai a yanzu ma zuciyata kemin wasuwasin bana lafiya bane. Dan abun yayi yawa wlhy. Wace soyayyar haukace haka kamar wani labaran littafin hausa. Ku shaida ne nima naso yarinyar nan a baya, dan ina gaba-gaba wajen shawo kan Abban Attahir harya amince da auren nan duk da fama da aka sha sosai saboda dagewar da yay akan sai Attahir ya fara aure sannan Mansoor ɗin yayi. Amma magana ta gaskiya zancen matar kawunta na jiya ya dawo dani a hankalina. Sannan ganin yarinyar a cikin hayyacinta fes saima ƙyau data ƙara shima ya tsaya mun a rai. Dan haka shekaran jiya nace Mansoor ya kamata ya nema likita yasa a mata gwajin ciki amma yaron nan sai ya koma min wani kalar tausayi kamar zai yi kuka, yana faman roƙona nabar wannan maganar dan ALLAH kada wani yaji, shi yasan wacece Samraah. Da ace wata matsala ta faru da ita acan sai ta faɗa masa bazata munafuncesa ba. Kajimin yaro fa dan ALLAH”.

         “Humm Aunty kar kiga laifinsa. Dan dama abin da kamar wuya ace ya fahimta kai tsaye. Amma dai kam al'amarin akwai ɗaure kai”.

       “Bana wasa ba ma. Inda shi wani ne dan ALLAH basai ya haƙuraba, idan ma ya matsune yay auren dole a goben basai a ɗaura da Waleeda ba. Nasan dai Daddynta bazai ce komai ba wlhy”.

      Idanu sosai ƙanwar tata ta waro waje. Sai kuma ta ɗan murmusa da faɗin, “Kai Aunty wannan ai babbar magana ce. Ni dai abinda nake gani anan kawai addu'a ce tafi dacewa. Sannan kisa a ranki in sha ALLAHU abinda zuciyarki ke ayyana miki bazai zama hakan ba.”

      Baki kawai Mamy ta taɓe batare data sake cewa komai ba.....


       💢💫💢💫💢💫💢💫💢


   *_RANA BATA ƘARYA BILYN ABDULL. MASU IYA MAGANA SUN CE SAI DAI WAI UWAR ƊIYA TAJI KUNYA_*. Na yarda da batun masu hikimar zance. Domin kuwa nima da kaina na yarda wannan rana tawace kam. Sannan in har Mum na amsa sunan uwa a gareni to taji kunyar kuwa. Dan halayyar da take nunawa yasa dangin mahaifinmu suka gagara haƙuri sai da suka yayyaɓa mata magana. Dan har Kawu Lurwanu na iƙirarin mata dukan tsiya. Yaya Musaddiq ɗin da take gani aba komai ba a gareta ne yayta basu haƙuri da kareta har aka samu ƙurar ta lafa. Gida ya gama cika danƙam da mutane. Dangi na kusa dana nesa sun nuna halacci. Ga abinci kala-kala anyo daga Gwarzo batare da an zaman jiran sauraren na nan gidan Abba da kunya ta sakashi kawo buhun shinkafa a jiya da dare ba, sai wasu ƴan kayan miya cakwat da nama a baƙar leda abin zakkunya dai.

        Kafin goma na fito shar dani a amaryata. Ga ƙunshin da ƙanwar mijin Aunty Zakiyya ta rangaɗa min a daren jiya ja da baƙi yay masifar fitowa kamar kaci. Duk da gyaran ƴan kwanaki akai mun na fito fes dani kamar fure a tsakkiyar lu'u-lu'u. Wani cotton lass ne a jikina lemon green ɗaya daga cikin kayan da suka kawo jiya aunty Zakiyya ta ciro min. Dan duk kayan da zanyi hidimar biki dama sai da Mansoor ya ɗaukan mukaje tela ya gwadani tun kusan wata biyu da ya shige. Aiko ɗinkin yay masifar zaunamin a jiki. Sai wata stones sarƙa mai ƙyalƙyali da walwali tamkar diamond na gaskiya. Awarwaraye zobba da komai sunji a hannayena. Ta sama gashina da a daren jiya shima yasha wanki daga ƙanwar mijin Aunty Zakiyyar dai dan aikinta kenan shima sai ƙyalli da ɗaukar idanu yake. Bayan ta gama tsaramin kwalliyar da naita zame-zame a farko aka naɗa min ɗauri na azo a gani. Nan take hasken camara na waya ya shiga kai-kawo a kaina. Nanfa wasu sukace sai sun turama ango fa. Ciki harda Hafizzullah. Ban tanka musu ba face murmushi kawai da nake yi........✍️

        



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._



_GUDA DAYA:400_

_BIYU:700_

_UKU:900_

_HUDU: 1200_


_BANK NAME:KEYSTONE_


_BANK ACC NO:6019473875_


_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_


_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_


__

_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_


*09033181070*


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*



_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

No comments