Breaking News

Tsutsar nama 50

 *_Typing📲_*










   *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*

             _(Itama nama ce)_





_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_




_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒇𝒕𝒚_


_______________


_Koda kuɗinka sai da rabonka. Ka gani su birgeka, ka saya ka birge mai kallonka. Albishirin ku ƴan kasuwa da masoya. Kuna ina? Ina kuka shiga? Maza ku garzayo kantin sauƙi da rahusar ingantattun kaya na kasarku dama ketarenta. Bari na kaiku, *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING* ke muku sallama irin ta addinin musulunci da babban albishirin shiryawa tsaff domin kawo muku kayayyakin buƙatunku na yau da kullum. Tun daga kan irinsu, atamfa, lasses, shaddoji, materials, abayas, takalma, handbags na zamani, vails ƴan yayi. Hijjabai. Sarkoki da dangoginsu. Kayan shafe-shafen dana kwalliye fuska. Agoguna harma dasu eyeglasses na manyan mata. Kai kai Karfa na cikaku da zance, dan zaku iya ganin komai a *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING* domin farin cikinku. Kayan yara harma dana maza ba mata kawai ba. Ba'a sayen ɗai-ɗai zamu tsaya ba harda sari ga mai buƙata zamu bada in sha ALLAHU kuma akan RAHUSA mai sauƙi da kaima zaka samu naka rabon. Zakuma mukai maka kaya a duk inda kake a *NIGERIA* in sha ALLAHU. Ƴan kasuwa masu sari da masu sayen ɗai-ɗai ku garzayo nan domin gani da ido in sha ALLAHU. Ka gani su birgeka, ka saya ka birge masu kallonka sai a *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING*👇_



https://chat.whatsapp.com/D1Ki9jt2lNkKVetOWNuFN5


_______________


.......Har muka iso kuka nake sosai, haka dai aka fita dani kaina a lulluɓe. Ina jin mutane nata yaba gidan. Hakan baisa naji wani abu daban ba saboda nasan gidan Mansoor kam tabbas yayi ƙyau da tsari. Sannan babu laifi babbane. Da addu'a na shiga kamar yadda Gwaggo ta bani umarni. Dan motar da aka ɗakkoni ce kawai dama ta shigo har cikin gidan. Sauran duk a waje suka tsaya. A falo aka ajiyeni kamar yanda Inna Magajiya tace. Mutane suka ɗan shishshiga kitchen da inda ba'a rasa ba. Bedrooms dai a rufe suke duka biyu dake a gidan kamar yanda naji suna faɗa. A karan farko na ɗan ji mamaki, dan nasan bedrooms huɗu ne a gidan Mansoor. Amma dai banda tacewa, bayan mutane sun gama zazzagawa suka fita dan dare ya farayi za'a maidasu gida. Sai da kowa ya fita sannan Gwaggo ta kama hannuna ta kaini bedroom da naji tana faɗa bayan ta buɗe da makulli, anan ne na gane ashe keys ɗin na hannunta sune dai suka hana mutane shiga wai dan kar a ɓata tunda dare yayi babu damar zama a gyara min. A bakin gado ta zaunar dani, tana sake jaddada min kalmar haƙuri, haƙuri dai da duk abinda zan gani, dan shi aure ibada ne bawai wasan yara ko nanaye kamar yanda mu yaran yanzu muke tunani ba. Ni dai kuka kawai nake zabga mata. Tadai samu ta zame jikinta ta gudu ta barni. Kuka na sake fashewa da shi irin mai cin rai da zuciya ɗin nan, harna zame na kwanta a gadon batare dana sani ba na cigaba da kukana.

       Tun ina darzar kuka da tunanin Mansoor zai iya shigowa har al'amarin ya fara bani tsoro. Dan gari yay wani irin shiru sai kukan karnuna amma babu Mansoor babu labarinsa. Kai komai ya fara canja min daga yanda nake tunani da hasashensa. Dan daga jiya zuwa yau komai da nake gani ba irin tsare-tsaren Mansoor ɗina bane. Komai yana zuwa min a banbancin abinda muka tsara. Mi hakan ke nufi, Mansoor ne ya canja komai a yanda na sanshi ko yaya al'amarin yake ne?. Banda mai bani amsar ko ɗaya daga cikin tambayoyi na. Dan haka na cigaba da kwanciya a wajen ga ciwon kai mai tsanani na ratsani, kafin ma wani dogon lokaci na fara rawar sanyi. Ina jin yanda wata iskar hadari ke tasowa da ƙarfin tsiya amma na kasa ko motsi. Haka na cigaba da kasancewa a wajen na tsawon lokacin da ban san adadi ba har barci yay awon gaba dani batare dana farga ba....


        Hasken rana irin mai kashe idon nan ne ya addabi fuskata. Dole na buɗe idanuna da sukai min wani masifar nauyi saboda kukan da nasha. Ganin a inda nake nada banbanci da inda na saba ya tuna min da mike faruwa. Zumbur na miƙe zaune ƙirjina na luguden daka. Ɗakin na shiga bi da kallo, madaidaici ne ba wani ƙato ba can. Sai dai kayan sun masa ƙyau cas. Abu na farko dana fara lura da shi sam ba irin fentin gidan Mansoor bane ba, kuma bedroom da Mansoor ya nunan a matsayin nawa randa mukazo ƙatone sosai. Ƙirjina yay wata irin girgiza. Sai dai tunawa da banyi sallar asuba ba yasa na tattare komai zuwa gefe na miƙe. Ƙofar da na gani da nakema zaton bayi ne na nufa. Nan ma dai ba irin toilet ɗin gidan Mansoor bane. Kai ƙwalwar kaina fa na neman juyewa. Amma dai na sake ƙoƙarin dakewa nayi alwala na fito. Akwatin dana gani saman bed side drawer na buɗe, na samu hijjab kamar yanda nai fata, dan haka na nutsu domin gabatar da salla..

       Ina idar da sallar na miƙe kamar zararriya, dan kaina gaba ɗaya a juye yake da komai. Fitowa nai gaba ɗaya daga bedroom ɗin. Ganin wani dake a kusa da shi yasa na buɗe na shiga nan. Gabana ya faɗi. Dan babu komai a ciki sai ƙatuwar katifa irin wadda ba'a sanyawa a gadon nan. Sai wani ɗan ƙaramin akwati mai shegen ƙyau. sai takalma haif cover suma dai masu ƙyau sosai, a saman katifar da agogo da waya kusa da shi, sai can gefe kaya ne da aka cire shadda honey color data ciza sosai. Ga wani ƙamshi na musamman dake tashi har ina jin kamar nasan ƙamshin, amma dai na hana zuciyata hasasowa. Fitowa nai ƙwaƙwalwata na sake birkicewa. Falo ne dake tsaka tsaki, shima dai yayi ƙyau da kayan da aka jera masa, saukar idanuna akan wanda ke zaune daga can cikin ɗaya a kujerun dining ya saka zuciyata wata irin girgizar da ya rage kaɗan ta biyo ta bakina ta fito. Karkarwa jikina ya shiga yi, irin wadda bamma san na cigaba da tafiya ba cikin matuƙar sassarfa. Har na iso gaban dining ɗin bai ɗago ba. Yanata danne-dannesa a laptop hankali kwance. Ga mug dake ta turiri alamar shayi ko coffee a ciki.

     “Wanene kai? Miya kawoka nan? Ina ka kaimin mijina?”.

   Tambayoyi uku a jere suka fito a bakina dake rawa. Kamar baima jini ba, ko nace bai san da zuwana wajen ba. Dan ko motsi baiyi ba balle ya ɗago ya kallan, aikinsa kawai yake hankali kwance cike da ƙwarewa.

          A matuƙar harzuƙe hawaye masu zafi na rige-rigen sakko mini cikin daka tsawa na ce, “Da kai nake magana malam!!”.

   Cak ya tsaya daga danna keyboard ɗin laptop ɗin da yake yi. Nasan kuma yanda nai tsawar ne da matuƙar ƙarfi ga jikina na girgizar tashin hankali da ɓacin rai. Na sake zabura zan masa wata tsawar ganin nan ma bai amsa min ba yay wata irin juyowar da ta saka ni yin tsalle a lokaci guda da zuciyata saboda tsabar kiɗima. Sai gani rijif a ƙasa wanwar.

       “Ba'a min tsawa”.

    Ya faɗa a dakensa cikin silent voice ɗin nan nasa na gadara babu alamar damuwa da halin da yaga na shiga kuma. Sai ma ɗauke kansa da yay ya sake maidawa ga screen ɗin laptop ɗin. Yaraf kake jina na ƙarasa zubewa ƙasa gaba ɗaya. A hankali sai kaina ya fara juyawa, yayinda lips ɗina ke wata masifaffen rawa ina nunasa da yatsana da shima ke rawar. Tun ma ina banbance tsakanin haske da duhu har hakan ya fara neman gagarata. Tuni na tafi luuu ƙasa gaba ɗaya alamar ina neman suma. Daga haka ban sake sanin mike faruwa ba sai farkawa nai na sake gani na a inda na faɗin yashe. Da ƙyar na iya miƙewa hannuna dafe da kaina dake faman juya min. Kai tsaye inda nasan yana zaune na kai idona. Wayam babu kowa daga shi har laptop ɗin nasa. Sai mug ɗin nan na shayi kawai ajiye. Falon na juya ina sake ƙarema kallo. Yanzu kam ni kaɗaice a cikinsa da alama, sai zuciyata ke ayyana min kodai mafarki ma nake yi ne? A gaskiya sai dai mafarkin kuwa, dan wanda idona ya ganarmin a gidan nan nafi fatan ya kasance a mafarkin ne. Kasa daurewa nai, cikin layin juyewar kai tamkar wata ƴar maye na nufi ƙofar da nake ƙyautata zaton hanyar fita ce. Da ƙyar na iya lalubar handle ɗinta na buɗe, cikin yanayin dishi-dishi na dinga bin harabar gidan da kallo, ba wata babba bace dan bata wuce ɗaukar motoci uku ba suma a ɗan takure. Motar da nake ƙyautata zaton an ɗakkoni a ciki jiya kawai ce a ajiye. Saukar idanuna akan buzun dake zaune a gate yana fifita wuta alamar shayi yake dafawa yasa ni jin ƙarin gwiwar nufar can. Sai dai ina kai rabin harabar wani mahaukacin farin kare mai kama da tumakin turawa a gashi ko nace zaki a ƙarfi da girma ya wani irin zaburowa kaina daga inda yake kwance a saman motar yana haushi na hauka ga harshensa waje. Daburcewa nai na rikice dan na tsani kare. Balle irin wannan mara ƙyan gani da suffa, sauƙinsa ɗaya daya kasance fari. Ganin yana gab da iskoni na ƙwalla ƙara ina durƙushewa a wajen na ƙanƙame jikina dake rawar mazari.

       “Laalah!”. 

     Aka faɗa a ɗan tsawace, sai dai hakan bai hana fitar muryar tasa acan ƙasan maƙoshi ba. Sannan karen ya tsaya cak bai ƙaraso inda nake ba. Sai kallonsa da yay yayi haushi sau biyu yana kallona kamar mai son masa ishara dani. Da alama ya fahimci mi karen ke nufi, dan a daƙile ya sake faɗi, “leave here”.

     Abin mamaki tinƙas-tinƙas karen nan yabar inda nake ya koma saman motar daya taso yay kwanciyarsa kamar bashi ba. Sai lokacin na samu damar sake fashewa da kuma. Ganin ya juya abinsa zai koma inda ya fito na miƙe a zabure nima. Kusan atare muka shigo falon. Batare dama nasan mi nakeyi ba a tsawace na furta, “Ina ka kaimin mijina? Mi kayima Mansoor ɗina? Miya kawoka gidan aurena? Yanzun ma kidnapping ɗina kayi?”.

         Bai ko kallan ba ya cigaba da tafiyarsa zuwa bedroom ɗin nan mai katifa. Ai bamma san lokacin dana daka wani uban tsalle ba nabi bayansa nima. Dan amsoshin tambayoyina kawai nake buƙata. Dole kuma ya bani, inba haka ba kuwa zaiga tsagwaron tashin hankali, kuma a wannan karon saina tabbatar masa da kaidin mace, dan ko dare bazan sake kaiwa a gidan nan ba. Ina isa ƙofar ɗakin yana rufota bamm, handle ɗin na kama da rawar jiki na fara murɗawa da jijjiga ƙofar amma ko motsi batai ba alamar ya kulle ta ciki. Wani irin kuka mai tsuma zuciya na sake fashewa da shi ina cigaba da jijjiga ƙofar da bugata a haukace amma mutumin nan ko tari baiyi ba. Galabaita ta sakani silalewa jikin ƙofar zuwa ƙasa wasu zafafan hawaye na rige-rigen sakkomin da masifar gudu. Cikin jin karaya da sarewa na shiga furta, “Awwab why? Why Maash? Why zakamun haka a ranar da tafi kowacce rana muhimmanci a garemu. Mike shirin faruwa? Ina mijina Mansoor?!! Miyyasa ka sake satoni zuwa nan a ranar auren...” kuka ya sarƙeni na kasa cigaba da maganar✍️


 

🤔🤔🤔😞


Alhamdullah 🙏. Anan zamu dakata a book one na wannan littafi mai suna TSUTSAR NAMA. sai kuma ALLAH yasa muna da rabon kaiwa bayan salla.


★Tofa masu karatu yaya take ne?.


★Mike shirin faruwa?.


★Ina Mansoor ango?.


★Miya kawo Maash a madadinsa?


★Kidnapping Sam-G ya sake yi kamar yanda take tunani itama kokuwa yaya al'amarin yake?


★Waye yay kidnapping Sam-G a farko tunda Maash ya tabbatar mana bashi bane?.


★Waye Maash ya kashe ma wai?


★Wake amfani da sunan Samraah wajen amsar kuɗi maƙudai haka a wajen Maash? Tunda tace ba ita bace.


★Maash zai samu nasarar amsar videon a wajen Sam-G kuwa?


★Magana fa ake ta an kawo amarya gidan mijinta amma ango ya rikiɗa zuwa wani daban.


★Hhhhh masu karatu akwaifa gurmi. Gurmi gagarumi ma kuwa na musamman. Dan littafin nan ɗauke yake da nasa salon shima. Hargitsi da cakwakiyar dake cikinsa kuwa. Hhhhumm ba'a magana, dan bama mu fara komai ba sai a book 2 da zai zo bayan salla, kuma komai da kuke buƙata yana a cikinsa ne.


★Dan shi kansa Maash fa akwai wani ƙunsashen al'amari a tashi duniyar dako fara taɓota bamuyi ba. 


★Kai kar dai na cikaku da surutu, ku shirya kawai tsaff zuwa bayan salla idan ALLAH ya kaimu da rai da lafiya domin samun duka wannan amsoshin a TSUTSAR NAMA BOOK 2 har ma da wanda baku sani ba.


★Ya rabbi ka karɓi ibadunmu, ka gafarta mana ka yafe mana kurakuran mu. Ƴar uwa! Ɗan uwa! Duk wanda naima ba dai-daiba ya gafarceni. Nima na yafema kowa. Kada ka bari ko ki bari ku zama cikin jerin mutanen da zan iya kaima UBANGIJINA kuka a kansu a acikin wannan watan mai tunkaromu. Wannan shawara ce. Dan nima bazanyi fatan nazama cikin wanda kuma zaku kai ƙarata wajen UBANGIJINA ba. Fatana kumin addu'ar fatan alkairi nima na muku tare da iyayenmu baki ɗaya.



Taku har kullum👎

    BILKISU IBRAHIM MUSA

            (Bilyn Abdull 💞)



(C)2024.



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._



_GUDA DAYA:400_

_BIYU:700_

_UKU:900_

_HUDU: 1200_


_BANK NAME:KEYSTONE_


_BANK ACC NO:6019473875_


_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_


_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_


__

_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_


*09033181070*


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*



_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

No comments