Breaking News

Auren Shehu Book 2 Page 10

*Khadija Sidi*
Auren Shehu 2 

10

A hankali ya kwantar da ita tare da mata matashi da daya daga cikin kullin rawanin sa, ya mata addua ya tofe ta. Cikin sanda kar ya tashe ta ya wuce fada da niyar sauraran korafe korafen jama’ar Rugan Shehu kafin Zainab ta tashi.


Be yi cikakken minti ishirin da tafiya ba kukun daya daga cikin shanun gonar ya dami Zainab har ta kai ga farkawa. Duk wanda ya saurari yanda saniyar ke kuka dole ya gane ta na cikin azaba. Tun Zainab na iya jurewa a tunanin ta Usman na tare da shanu, har ta kasa ta fito, Nan ta ci karo da abin da ba ta taba gani ba tun da ta zo duniya, ba ga bil adama ba bare dabba. Saniya ce ke kai kawo, ta baro cikin yan uwan ta shanu zuwa farfajiyar bukka, duk sanda ta taka daya biyu sai ta tsaya ta na mai fitar da sauti yayinda wani farin abu ke kokarin fita daga jikin ta.

Ganin haka Zainab ta ja da baya a tsorace har ta na shirin rugawa duk da dai sam ba ta jin dadin jikin ta, kiran sunan Usman ta ke bilhakki yayinda ta duba lungu da sako na gidan gonar babu Usman babu alamar sa.

Jiki na rawa ta kara dawowa ga saniyar, sai sannan ta gane wannan farin abun mai yauki yauki ba komai ba ne fyace dan saniya ne ke kokarin fiitowa, Saniyar nan dai nakuda ta ke. Hankali Zainab ba karamin tashi yayi ba musammam yanda ta ga wajan na kara budawa duk sanda Saniyar ta dan tsaya tare da durkusar da kafafun ta na baya, haka kuma ta dan tasa sai ta cigaba da takawa, da ke dabba dabba ce ciwan da take be hana ta cin ciyawa ba duk sanda ta gifta ta gaban sa.

Kamar yanda Saniyar ke kuka haka Zainab ke taya ta, haka kuma ita ma ba ta fasa safa da marwa ba ta na mai bin sahun Saniyar. Usman tafe tun kafin ya iso gidan gonar ya ke jiyo kukan Saniyar, tsoran kar ta cutar da Zainab ya sa shi karasawa da gudu.

Sa kafar sa gidan yayi daidai da lokacin da saniyar ta durkusar da kafafun ta na baya, kamar mai Shirin zama kasa ta sullubo yar saniyar ta akan idanun Zainab. Idanun Usman kan Zainab, tashin hankalin da ta ke ciki be boye kyawun halittar ta ba, dan kuwa Usamn zai iya rantsewa tun da ya zo duniya be taba ganin bafulanar da kayan saki ya mata kyau ba kamar yanda yayiwa Zainab, rigar ya saukar mata har ciki, abun ku da mai hips sai zanin ya zauna mata a kugu ya mata cif cif.
“Abu…”
Usman ya kira sunan ta cikin wani irin yanayi, hakan ya sa Zainab juyowa da sauri dan sam ba ta lura da shigowar sa ba saboda idanun ta na kan saniyar nan da ke kokarin lashe abin da ta haifa. Ganin sa da gudu ta nufe shi, cikin kuka ta shige jikin sa hakan ya sanya Usman runtse idanun sa, kan ta bisa kirjin sa yayinda ta ruke sa gam ta ke fadin

“Haihuwa ta yi, a gaba na ta haihu! Wallahi ta haihu!”

Usman na mai shafa bayan ta cikin rarrashi yayi karfin halin furta

“Yi shiru bar kuka Abu, kin ga baki da lafiya, ai ta riga ta haihu ni ma kin ga wata rana haka za ki haifo min diya mai kama da ke…..”

Cikin sauri ta zare jikin ta daga nashi, cike da tsiwa ta furta

“Allah ya sauwake na haihu da kai gwara….”

Cike da danasanin furucin sa da ya ja masa rage jin dadi ya furta

“Don Allah kar ki karasa! Kin ga dai muna da mai jego be kamata mu na hayaniya gaban yar jinjira ba! Bari na taimaka mu su”

“Mtswww”

Amsar da Zainab ta bashi kenan yayinda ya wuce ta ya na mata dariyar kyeta. Sai da ya cire rigar sakin sa da rawani ya rage daga shi sai dogon wando sannan ya shiga taimakawa saniya. Bini bini sai ya kama Zainab wacce ke zaune bisa kujerar tsakar gida daga gefe ta na satar kallan sa, daga sun hada ido ta yi saurin kau da kai gefe.
Cikin ranta mamakin kyau da kyan sura irin na Usman ta ke, lalle Usman ya isa wannan kalmar ta “Man” dan kuwa da a ce wayayye ne da Zainab ta yi alfahari da shi, duk abin da ta ke mafarki na kyawun da namiji Usman na da shi, gaba daya sai ya dishashe mata duk wani kyan Sudais da ta ke gani, sai dai Usman kauyenci ya masa kan ta.

“Ina ma a dauki wayewar Sudais a bawa Usman”

Cewar Zainab cikin ran ta, gaba daya ta shagala cikin tunani sai tsuntar idanun ta tayi cikin na Usman, hakan ya sa ta kawar da kai cike da jin kunya. Usman na murmushin jin dadin yanda matar ta sa ke satar kallan sa ya ce

“Babu komai Abu ki kalle ni da kyau, ai ni mijin ki ne lillahi warasulihi! Jira na ke ki shirya na fara biyan bashin sadakin da na mora!”

Cike da jin kunyar ya kamata a karo na farko Zainab ta nemi amsar da za ta bashi ta rasa, ta tsinci kan ta tana mai tambayar

“Mace ce ko namji?”

Cikin rashin fahimtar abin da ta ke tambaya ya ce

“Me fa?”

“Abin da ta haifa, mace ce ko namji”

“Oh mace ce”

Ya bata amsa a taikaice yayinda ya ke duban yar jinjirar saniyar, har lokacin saniyar na lasar abar ta.

“Wani suna za a sa mata?

Zainab ta kara tambaya zuciyar ta daya. Usman na mai darawa ya bata amsa da

“Har wani suna na musammam ake sakawa dabba? Kai wani abun sai yan birni, toh wani suna ki ke so a saka mata?”

“Halitta!”

Cewar Zainab kai tsaye. Yanda ta fada da iya gaskiyar ta da kuma yanda ta yi mirsisi da fuska ne ya sanya Usman fashewa da dariya mai karfi har yana jefa kai baya. Yanda ya ke dariyar ya sa Zainab saka dariya. Sai ga su duka biyun suna dariya har Usman ya kare ta sa dariyar Zainab ba ta dena ba tsabagen na ta na muguntar ta ga yar saniyar ta mata kama da kanwar ta ta Halitta.

Tsayawa Usman yayi ya na kallan ta cike da sha’awar yanda fara’a ke yiwa Zainab kyau, tun da ya ke be taba ganin ta cikin annushuwa haka ba. Ko da ta ankare da kallan da ya ke mata nan ta ke ta tsuke fuska, Usman na murmushi ya ce

“Fara’a na mi ki kyau Abu, MashaAllah ki na da kyau”

Shiru ne ya biyo baya na dan wani lokaci, kafin daga bisani yayi gyara muryar ya ce

“Allah sarki Halitta, mace ce ta gari mai tsoran Allah…..”

Wani irin bakin kishi ya taso ya tukare kirjin Zainab musammam da ta ji Usman ya kara da

“Darajar ta ya wuce a saka ma saniya sunan ta, ki bari idan ki ka haifar min diya a saka mata Halitta….”

“Aikin banza aikin wofi! Toh da ka san ita ka ke so ai da ka fadawa Daddy da be yi kuskuran aura maka macen da ba ta gari ba! Ka ga ita ba ma sai ka sato ba! Amma ka yi kum aka daura min auren masifa! Ka rabo ni da uwa ta, da yan uwa na! Da wayewa! Da makaranta ka kawo ni duhun daji bayan ka san natsane ka! Ran da na fara ganin ka na tsane ka! Har wata mace ta gari! Me ya sa ba ka aure ta ba! Allah ya isa wallahi!”

Ta wuce jiki da suri gudun kar hawayen da ke idanun ta su kunyata ta su zubo gaban Usman. Cike da mamakin me ya fada har ya tunzura ta haka ya bi ta da kallo dan sam be kawo a ran sa kishi ba ne. Zainab kuwa zubewa ta yi bisa tabarma ta sha kukan ta, wato ko a kauyen ma sai Halitta ta daga mata hankali, ta na can Saudia tare da na ta mijin amma ga Usman nan sai yaban ta ya ke.
Usman kuwa nan ya yi zaman sa sai da ya killace saniyar sa tsaf, har ya samu karamar ta fara shan nono, sannan ya nufi bukkar dauke da damammiyar furar da aka aiko masa da shi bayan Zainab ta shige ciki.

Ko da ya shiga ya aje kwaryar yayi gefe ba tare da ya tanka mata ba, yana kokarin saka riga ya ga ta ja kwaryar da kan ta, ta bude ta fara shan furar. Cike da mamaki ya ce

“Yau kuma yunwa ake ji Abu?”

“Na ga alamar so ka ke ka kashe ni, gwara na ci na koshi ko na sami damar yakar ka”

Cewar Zainab yayinda ta ke hadiyar furar da ko sukar babu, ta karfi da yaji ta ke sha. Be bata amsa ba sai da ya sanya rigar sa tsaf, ya zo ya zauna kusa da ita, hakan ya sanya Zainab matsawa da sauri gudun kar su hada jiki. Sai a sannan ya lura da idanun ta da yayi jajur, da alama kuka ta sha. Be tambaye ta dalili ba, Hannu ya kai goshin ta domin ya ji ko zabin da jikin ta ya kara raguwa dan dazu da ta rungume shi be ji zafin sosai ba. Da sauri ta buge hannun ta na mai kokarin kwada masa lodayi, ya janye hannun tare da fadin

“Na zaci mutuwar ki ke so ki yi ai? Me m ki ka ce? ”
Ya fada cikin kokarin tuno kalaman Zainab, ya kara da

“Yauwa ka kashe ni ko na kashe kai na….”

Zainab ta masa banza ta cigaba da shan furar ta, har ya fitar da ran za ta kara tankawa sai ji yayi ta ce

“Wannan wani irin rayuwa ne a ce babu asibiti? Yanzu wannan dabba ce ta haihu fa, ina ga mutum?”

“Mu na da unguwar zoma”

Ya bata amsa a taikaice. Cikin rashin gamsuwa Zainab ta furta

“Idan kuma haihuwar ta zo da tangarda fa? Unguwar zoma ta iya tiyata ne? Sauran rashin lafiyar ina ake duba mutum bare a san cutar da ke damun shi a bashi magani?”

Shiru Usman ya mata yayinda ya ke tuno haihuwar Cangwai da ya zo da tangarda har ta kai ga rasa ran ta, haka ma na wasu dirgaggu da ba zai iya mantawa ba. Daga bisani ya furta

“Abu?”
“Uhum”
Ta bashi amsa baki cike da fura.

“Ya jikin ki?”

“Da sauki, wannan maganin da bani ya taimaka min”

Usman na gyada kai ya ce

“Kenan muna da magani mai kyau ko? Muna shiga dawa mu samo Allah ya mu ilimin, sarrafa su kamar yanda yan birni su ke sarrafa shi ne ba mu iya ba, shi ya sa na ke mana kwadayin sayasar tallfin ruga da shugaban kasa ke san kawowa”

“Ruga settlement policy?”

Zainab ta tambaya. Ya girgiza kai tare da fadin

“Haka na ji ana ce masa a turance, Allah ya sa dai ba zagin mu ku ke ba”
Zainab na mai murmusawa yayinda ta rufe kwaryar furar ta na kokarin aje ludayi Usman ya karbe, ya ja kwaryar gaban sa, maimakon ya dau nasa ludayin, sai ya ki da na ta ludayin ya fara sha yana mai sai ta daidai in da Zainab ta sanya na ta bakin, ita kanta Zainab ta lura da hakan dan kuwa ta ji wani irin yar har tafin kafar ta. Shiru ne ya biyu baya kafin daga bisani Usman ya ce

“Abu ina neman alfarma, me zai hana ki na dan koyar da yaran Rugar nan boko….”

“Gidan fa? Na ce da kai ka mayar da ni gida!”

Zainab ta katse shi cikin bamnami. Kai ya girgiza mata alamar “ah ah” ba tare da ya tanka ba. Tashi ta yi za ta fita har ta kai kofa sai ta sake dawowa ta ce da shi

“Dajin nan ba su iya hausa ba kuma ba sa ji, ni kuma ba na jin fulatanci, ban iya ba, ta yaya ka ke so na koyar da su?”

Jin haka Usman har da kwarewa, ta na kallan sa ya karaci tarin sa babu ko sannu, bayan da ya gama ya dago ya na duban it bakin sa kunshe da dariyar mugunta ya ce

“Kar ki damu ai da na ce mu su da ga yau kun iya hausa kawai za ki ji sun yi”

Yanda ta yi da fuska ta na kallan sa ya sa shi kasa daurewa sai gashi na ya na dariya sosai, hakan ne ya kara tunzura ta ta furta

“Na dade ban ga azzalumi irin ka ba Usman!”

Ta fice cike da fushi, Usman kuwa be dena kyakyacewa ba.

Sai da Zainab ta kwana uku ta na jinya sama sama sannan ta sami sauki. Wata ranar lahadi da safe, Usman na shirin tafiya fadar Shehu Zainab ta ce da shi ta amince za ta koyar da yaran Rugar sa. Jim yayi ya na mamakin amincewar ta dan kuwa sam be yi zato ba. Cike da mamakin yanda Zainab ta ke canza masa ya ce da ita ta bari idan ya dawo za su yi maganar.

Ko da ya dawo ya kara tambayar ta, ta jaddada masa eh da gaske ta ke Usman yayi murna kwarai. Sai dai duk yanda ya ke jin dadin zaman gidan gonar daga shi sai Zainab dole ya mayar da ita cikin alhalin sa. Cikin lallami ya sheda mata, nan ma mamaki ta ba sa dan kuwa nuna masa ta yi ta na maraba da hakan dama ta gaji da zaman kadaici duk sanda ya fita hakan nan ta ke zama daga ita sai shanu da tsintsaye.

Usman be mayar da Zainab ba sai da ya tabbatar ya gina mata bandakin kara na ta ita kadai, duk da dai shi ma din ba masai gare shi ba sai dai duk sanda tutu ya matso ta shi da kan sa ya ke raka ta daji. Ba Usman ba hatta su Iyalle sun yi mamakin sauyin da su ka gani tattare da Zainab, haka kuma Usman ya ba da umarnin a ringa yiwa Zainab hausa hakan ya ba ta damar koyawa yara har da yan mata karatu, matasa maza ne dai Usman ya hana saboda kishin kar su na kalle masa Zainab. Duk sanda wani daga cikin yan rugar ta yiwa Zainab hausa sai ran ta ya sosa, wato da gaske dai sun iya hausan, kawai mugunta ya sa da ba sa kula ta. Ta sha alwashin sakawa Usman da daidai yanda ya mata ta hanyar da be taba tsammani ba.

Inda kowa ke nan nan da Zainab, Raqeeba da Rahila kuwa bakin ciki ne ya maye zuciyar su, musammam Rahila wacce ta riga ta yiwa mijin ta Tanko alkawarin kawo karshen Usman ta hanyar Zainab, da kuma samin damar cafkar ita kan ta Zainab hankali kwance, gashi duk yanda ta so ta dan kyebe da Zainab ko ta dan zuge ta abin ya gagara.

Babban tashin hankalin ta shi ne yanda Usman ke nan nan da Zainab, babu wanda be lura da yanda ya canza ba, walwalar shi ta karu, haka ma yawan zaman shi cikin gidan. So tari sai ya faki lokacin da Zainab za ta koyawa yara karatu sai ya kirkiri wani aikin da zai iya zama tsakar gidan yanda shi ma zai samu ya dan tsinci darasin, ya na so ya ce ta na koyar da shi amma ya na tsoran harshen Zainab.

Haka rayuwa ta cigaba har tsayin sati biyu, Rugar Shehu kaf maganar Zainab ne a bakin su domin kuwa jan su jikin ta ta ke sosai, haka ya sa Usman fara sakin jiki da ita, duk dai har lokacin ta ki yarda ya fara biyan bashin sadakin ta, duk sanda ya zo da batun ta tashi su yi karatu ya fara sauke nauyi sai ta ce bacci ta ke ji.

Misalin shadaya da rabi na dare Usman na zaune bakin kofar bukkar sa, tunanin duniya da yanda zai yi da Zainab ne ya addabi zuciyar sa, haka kawai ya ji zuciyar sa na kwadaita masa san ganin ta. Tun yana iya jurewa ya kasawa yayi, cikin himma ya tashi ya shige bukkar.

Bisa gadon kara ya tadda ta kwance ta yi daidai ta na bacci, da ke garin akwai hasken wata be damu da ya kunna fitilar acibalbal ba. Sanye ta ke cikin kayan saki, ta dunkule jikin ta kamar mai jin sanyi hakan ya Usman dauko daya daga cikin haramin sa mai kauri ya rufe ta da shi, tare da mata addua ya tofa hannun sa sannan ya bi jikin ta ya shafe, ga mamakin sa sai ji yayi ta furta

“Usman”

“Abu”

Ya amsa ya na mai kokarin kallan fuskar ta dan a tunanin sa tashi ta yi. Ganin idanun ta rufe ya san bacci ta ke yi, cikin mafarki ta ke kiran sunan sa. Ya na mai shafa fuskar ta ya yunkura zai tashi Zainab ta ruko hannun sa, cikin magagin bacci ta ce

“Kar ka tafi, ka kwanta mu yi bacci”

Toh dama abin nema ne ya samu, ba musu Usman ya shimfide kusa da Zainab, yayinda ta yi saurin dora kan ta jikin sa ta na mai sakin ajiyar zuciya. Dama mafarki ta ke da Usman tun kafin ya shigo dan haka ba ta yi yunkurun hana shi aika mata sakonnin da ya fara da hannun sa ba, sai ma taya shi da ta yi ta hanyar masa sabon abun da sai da ya je birni ya taba gani turawa na yi a talabijin, wato “kiss” a baki, a hankali shi ma ya shiga mayar mata da martani. Can dai abu ya wuce gona da iri Zainab ta bude idanu, ta ga a zahiri Usman din ne ba wai mafarki ta ke ba, ta fara kokarin ture shi Usman na mai girgiza mata kai ya ce

“Kar ki hana mu abin da Allah ya halatta mana Abu, ni halak din ki ne ba a mafarki ba kadai, har a zahiri, ki bari na ba ki hakkin ki..”

Ta bude baki ta niyar magana yayi saurin katse ta ta hanyar rufe bakin ta da nashi. Ganin Zainab ta saki jiki har da ba da na ta gudunmawar na ja mu su assabari na yi gaba abu na, dan da alama yau soyayya za a sha.

Da sanyin asuba Usman ya sa Iyalle dora ruwan zafi. Cikin al’ajabin rashin kunyar da su ke gani kala kala Kado ta sanya Usman ya zama mara kunyar kamar ba bafulatanin usul ba ta dafa masa ruwan zafi, ita ta kaiwa Zainab har saban bandakin kara da Usman ya sa aka yi mata.

Tunda ta bude ido abubuwan da su ka faru tsakanin ta da Usman ya fara dawo mata cikin ran ta, ta tsani kan ta, duk yanda zuciyar ta ta kauracewa gangan jikin ta, sai da gangan jikin ta ya fi karfin zuciyar ta har ta kai ga sakarwa Usman jikin ta dan abin kunya. Allah ya so ta dama ba ya dawowa daga masallaci har sai gari ya waye sosai, kuma ko ya dawo din ma ba ya shiga bukkar ta, dan haka ta na idar da sallah ta yi kokarin komawa bacci, amma fargabar halin da tsinci kan ta ciki ya sa ta kasa komawa bacci.

Gari ya waye tangararan Zainab ba ta ko rintsa ba, ta na shirin tashi ta fara shiri kafin yan karatu su fara zuwa kamar daga sama ta juyo muryar Usman a tsakar gida ya na amsa gaisuwa, kafin ta ankara sai gashi ya shigo bukkar. Gaban ta yayi mummunar faduwa yayinda bugun zuciyar ta ya karu sa’ad da su ka hada idanu, ta yi saurin kawar da kanta, yin hakan ne ya sanya Usman tunanin kunyar sa ta ke ji, kenan Zainab ta na san sa tunda har ta kai ba iya hada idanu da shi. Ciki da jin dadi ya janyo ta jikin sa, hannun sa hagu sa zagaye da kugun ta ya furta

“Ina kwana Gimbiya Abu? Kunya ta ake ji haka?”

Cikin kokarin boye tasirin da ya ke da shi akan ta, ta furta

“Dallah Malam ka sake ni! Me zai sa na ji kunyar ka!”

Dariya Usman ya sa dan kuwa yau Abu ta na masa tsiwa amma ta kasa daga idanu ta kalle shi, hannu ya sa ya dago habar ta yanda zai iya sanya idanun sa cikin na ta, kamar mai rada ya ce

“Ki kalle ni toh, ki kalli idanu na ki min magana Abu….”

Maimakon ta kalle shi, ta tsinci kan ta tana mai lumshe idanun ta, hakan ya bawa Usman bin kyakkywar fuskar ta da kallo, yayinda ya tsaya daidai lips din ta. Murya kasa kasa ya furta

“A daren jiya kin koyar da ni wani abu da ban taba tunanin zan yiwa wata ba Abu, ina alfahari kan ki na koya, ina alfahari ke na fara yiwa….”

Ya na gama fadin haka ya fara kissing din ta, yanda ya ke saban shiga kuma bagidaje be kasa ruda Zainab ba, dan kuwa ta sha kissing samarin ta wayayyu, Amma babu wanda ya tafi da ita har ta kai ga mance in da ta ke face Usman.

Saukar assabari da alamar mutum ne ya daga yayi saurin saki ne ya dawo da su hayyacin su, yayinda Zainab ta yi saurin matsawa daga jikin sa. Usman kuwa juyawa yayi ya fice da sauri kamar yana tsoran abin d zaman sa dakin zai iya haifarwa.

Hannayen ta biyu rufe da fuskar ta ta zauna bakin gado ta na fadin

“Innalillahi wainnailaihi rajiun! Me ke damu na ni Zainab! What I’m doing to myself! This is not what I’ve been planning!”

Sallamar da ta ji an yi ya sanya ta daga kai ta kalli wacce ta shigo dauke da kwaryar nono. Yanda ta yi sin da kai ta gaishe da Zainab ba tare da ta bari sun hada ido ba cikin ta ya bata itace ta shigo dazu ta gan ta tare da Usman. Bayan ta aje kwaryar ta na shirin juyawa Zainab ta ce

“Rahila ki shedawa mijin ki Tanko na shirya! Na shirya damka masa Usman da Rugar nan mukar zai fitar da ni daga wannan kangin rayuwar!”

Cike da mamaki Rahila ta juyo ta na kallan ta ta na mai fadin

“Da gaske ki ke? Dama ba ki hakura ba? Yanda ki ka saki jiki da jama’ar Rugar nan har ki na koyarwa, na ji labarin Usman ya kauda budurcin ki….”

Zainab ta dago a razane ta na duban Rahila, wacce ganin haka ta girgiza kai cikin jaddawa ta ce

“Kwarai kuwa nan ya zo ya na fadawa kowa cikin fariya. Kuma yanda Raqeeba ta dawo jiki na rawa bayan ta ga Shehu ya na…..”

Nauyin maganar ya sa Rahila karasawa yayinda ta ke tuno fuskar Raqeeba sanda ta nufo ta jiki na rawa idanu na fito da kwalla ta ke fadin

“Rahila Kado ta maishe da Shehu dan iska! Wallahi ganin su na yi bakin shi cikin na ta kamar za su cinye juna….”

“Duka shiri na Rahila!”

Maganar Zainab ne ya dawo da Rahila daga kogin tunanin da ta ke shirin fadawa. Zainab ba ta gushe ba ta kara da

“Duka na yi ne domin Usman ya saki jiki da ni, Amma zancen budurci kwata yayi! Fyade ya min kuma ba zan taba yafe mi shi ba shi ya sa na yanke hukunci bullo masa ta wannan sigar, Rahila ki taimaka ki fadawa Tanko ni Zainab zan bashi gudunmawa dari bisa bisa dari domin kawo karshen wannan azzalumin!”

Dan farin ciki jikin Rahila har rawa ya ke yayinda ta yiwa Zainab sallama ta fita, dan kuwa Allah Allah ta ke ta kaiwa Tanko sakon Zainab, ashe dai yau Tanko zai yi alfahari da ita, haka kuma takusa zama matar Shehu, mijin ta Tanko zai haye kujerar Usman.

Zainab kuwa tun fitar Rahila ba ta motsa ba, babban fargaban ta shi ne yanda Usman ya fara tasiri akan ta, dan bayan fitar shi ta gane ba wai kawai gangan jikin ta kadai Usaman ya mallaka ba, ya na neman ya mallaki zuciyar ta wanda hakan ta ke gani ba za ta iya bari ya faru ba, nan kuwa ba ta san bakin alkalami ya riga ya bushe, tsanar da ta ke ikirarin ta yiwa Usman ne ya sa ta kasa fahimtar hakan.

No comments