Breaking News

Furar Danko 65

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠

 

🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗


 

 

 

𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

 

 

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣5️⃣

 

 

 

……..Cike da matuƙar ɗoki Asma’u ta isa gida, kusa da Ammah ta zauna da ke kallonta ganin yanda take ta faman washe haƙora. “Auta lafiya kuwa irin wannan washe baki haka ko suruki na samu?”. Adda Sa’adah ta faɗa cike da zolaya. Su Adda Suwaiba da ke ta shirin wucewa gidajensu suma dai duk idanu suka zubawa Asma’un. Dariyar ta sake faɗaɗawa tana ɓoye fuskarta a jikin Ammah da faɗin, “Kai Gwaggo nifa ba haka bane, zan faɗama Ammah albishir ne”.

“A to muma sai a faɗa duk muji ai”. Cewar Gwaggo Sa’adah. Asma’u dai na dariyarta ta ce, “Gwaggo dama fa zan sanarma Ammah ne matar Yaya itace lawyer ɗin da take so ɗin nan mai taimakon mutane musamman akan harkar fyaɗe”.

Kallonta Ammah tai da sauri, dan haka cike da zumuɗi Asma’u ta sake faɗin, “Wlhy Ammah da gaske nakeyi. Barrister Mawaddat Jiƙamshi ce matar Yaya, dama tun shekaran jiya nake ta mamaki dana ga kamanninsu yayi yawa duk da ban taɓa ganin waccan a zahiri ba sai a tv, sai banyi magana ba sai yau dana tabbatar”.

Wani irin abu ne mai sanyi ya shiga ratsa zuciyar Ammah ta shiga sake tsarkake sunan ALLAH maji roƙon bayinsa. Tun a randa ta fara ganin yarinyar nan ana hira da ita a gidan tv akan wani case data cimmawa na fyaɗe har yarinyar ta kamu da cuta mai karwa garkuwar jiki da wanda yay mata fyaɗen ya goga mata a ranta taji inama ace ɗiyarta ce ita, ko kuma Aliyu ya sameta a matsayin mata. A ranar tai addu’a da fatan idan hakan zai iya kasancewa kuma ya zama alkairi ALLAH ya tabbatar, idan kuma har matarsa ce. Amma da ga baya sai ta cire hakan a ranta sakamakon jin yarinyar ɗiyace ga babban hamshaƙin mai arziƙi nan Alhaji Isma’il Ibrahim Jiƙamshi. Ta cigaba da ƙaunarta kawai a ranta da mata fatan alkairi a rayuwa. Tuna wannan al’amari ya sakata jin ratsawar wannan al’amari mai sanyi har zuciyarta na harbawa da sauri-sauri, tabbas wannan shine ɗaya da ga cikin alkairan son mutum domin ALLAH, dan ita kam taso yarinyar nan domin ALLAH ne……

 

 

★★….

 

Tunda Mommy ta fara magana Uncle Yousuf ya zuba mata idanu kawai yana kallonta har sai da takai aya. Ta ƙare da faɗin, “Gaskiya Yousuf zuciyata ta fara raya min wani al’amari mai girma. Anya kuwa babu lauje cikin naɗi a wannan al’amarin. Kasan mu mata munada wani hali na rufewar ido a duk sanda muke son ganin buƙatarmu ta biya akan abinda muke so. Ka tuna randa marigayiya ta fara ganin Yaya kuna tare, kuma kaine da kanka ka sanar min tunda yay mata kallo ɗaya ya watsar da lamarinta har kuka baro gidan a wancan lokacin bai sake kulata ba”.

“Tabbas anyi haka aunty Kareema, amma miya alaƙanta wannan abin kunyar da yake yi yanzu da wancan?”.

“Ba zamuce sunada alaƙa ba, ba kuma zamuce basu da shi ba. Amma inaji a jikina wannan soyayyar mai zafi da yakema Mawaddat bata lafiya bace.”

Murmushi Uncle Yousuf yay da gyara zamansa. Ya ce, “Aunty Kareema ban katseki ba ko ƙin fahimtarki anan, amma ina roƙonki karki sakama zuciyarki komai game da abinda Yaya keyi da tunanin wani. Lafiyarsa lau ya kuma san mi yake yi sarai. Akwai dai abinda yake ɓoyewa shiyyasa yake kaffa-kaffa da Mawaddat, dan ba wai tsantsar soyayyar bace ba kawai. Abu na biyu tausayin rasa mahaifiyarta tana laɓuɓuwa ma ya taka rawar gani a kansa. Kin san mu maza munada wani abu akan ƴaƴan mu musamman idan ya kasance mahaifiyar yaro bama tare da su, sai mu dinga jin wadda ke riƙe da su zata cuta musu ne kawai. Shiyyasa zakiga maza da yawa suna samun saɓani da matansu akan ƴaƴan da uwarsu ta fita a gida, kota rasu ta bari.”

“To haka ɗinne kuma. Amma inaga ya kamata ace munsan abinda yake ɓoye manan ko hakan zaisa mu fahimcesa”.

“Karki damu zamu sani, lokacin mu sani ɗinne dama baiyi ba, ina kan bincike yanzu haka ma”.

“To Alhamdullah ALLAH yasa muji alkairi.”

Da Amin ya amsa mata, da ga haka suka cigaba da tattauna al’amarin Daddy ɗin har zuwa wani lokaci kafin tai musu sallama ta koma gida. Ta samu Daddy na ramuwar barci da ya gagara yi daren jiya, bata tashesa ba har sai da ya tashi da kansa sannan ta labarta masa abinda ya sakasa nutsuwa kamar yanda suka tsara da Uncle Yousuf. Murmushi yay da faɗin, “Ashe yaron nan nada hankali har haka”.

Dariya Mommy tayi kawai batace komai ba. Shima sai bai sake bi takanta ba ya tashi ya shige bayi fuskarsa ƙawace da murmushi…

 

__________★

 

Gab da Azhar Smart ya tashi a barcin da yay, yaji daɗin yin barcin kuwa sosai, dan haka ya watsa ruwa da ɗaura alwala yasa jallabiya ya fice massalaci batare daya nema Lulu ba. Sai da aka idar da salla ya dawo gidan sannan ya nufi ɗakinta. Baccinta take hankali kwance, beauty face ɗinta ta sake yin wani fayau kasancewar babu ɗigon kwalliya, hatta lips ɗin ma yanzu babu ko lipgloss ɗin a jikinsa. Samun kasan yay da tsira mata idanun nasa na tsawon mintuna, tabbas ita ɗin ƙyaƙyƙyawace, sannan tana cikin jerin mata masu tsananin kula da jikinsu ta hanyar gyarashi kwaf-kwaf a kowane motsi. Ga izza da gayu da duk wani cikakken namiji bai isa mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa ba, “Sai dai akwai kauɗi da masifa kuma ba” ya faɗa a fili yana ɗan taɓe baki da ƙarasawa gaban gadon ya tadata. Idanunta ta buɗe a hankali ta saukesu kansa. Yanda ya ɗan ranƙwafo kanta ya sata zabura, dan yanayin ya mata kamar wani abu da ya shuɗe a baya. Tashi yay shima tsaye da kyau yana girgiza kansa. Fuska ba wasa ya ce, “Tashi kiyi sallah”.

Harararsa tai kamar zatai magana sai kuma ta fasa saboda yanda yay masifar kafeta da idanunsan nan da bata ƙaunar ya zuba mata su, dan duk wani ƙarfin gwiwar ta sai ya sare taji komai ya kufce mata. Dama fitsari take ji dan haka ta sauka a gadon tana wani yamutse fuska ta nufi bathroom ɗin. Sai da ya bata ɗan lokaci sannan yabi bayanta, anyi sa’a kuwa zata fara alwala.

“To alwalan ma a gabanka zanyi?”.

“Haka ya kamata, ya kuma dace, dan hakki ne a kaina sanin ibadarki da komai naki a yanzun”.

“Kai a wa?”.

“Mijinki”.

“Kana son shigarmin rayuwa da yawa”.

“A ciki nake tsunduma ma ai”

“Mafarki kenan”.

“Ni da ke duk a ciki muke, mai rabo a cikinmu sai ya fara farkawa ya fuskanci reality. Yi alwala lokaci na tafiya”.

“Al….”

Sai kuma ta kasa ƙarasawa saboda tuno abinda ya faru ɗazu a ɗakinsa saboda faɗar sunan nasa. Sai kawai ta ɓige da maka masa harara cikin ƙunƙuni ta furta “Zan koya maka hankali sannu-sannu”.

Duk da yaji bai tanka ba, dan ya gaji da magana haka nan. Itama sai tai ƙwafa ta juya ta fara alwala. Shi dai yana kallonta harta kammala zata miƙe ya ce, “Dakata. Mawaddat ba haka ake alwala ba sam. Akwai kura-kurai matuƙa a cikin wadda kikayi. Dan haka ina son ki bani hankalinki nan duk abinda nayi kiyi, yanda ake alwala shine. Da farko yin niyya a zuci sannan ki ce Bismillahi, sannan ki wanke tafukanki na dama da na hagu kowanne sau uku. Sannan ki ɗebo ruwa ki kurkure bakinki ki zubar da ruwan sau uku. Sannan ki ɗebo ruwa ki shaka a hanci ki fatar shi ma sau uku. Sannan ki ɗebo ruwa ki wanke fuskarka gaba ɗayanta sau uku, ki lura cewa wanke fuska yana farawa ne tun daga farkon goshinki har izuwa karkashin haɓarki, wato kusa da makoshi a tsayinta kenan, a faɗi kuma tun daga gefen kunnen dama zuwa gefen kunnen hagu. Sannan ki wanke hannu tun daga tafuka har zuwa gwiwar hannu na dama da na hagu shima sau uku. Sannan ki ɗebo ruwa ki yi shafar kai wato a tafin hannu ki shafo tun daga farkon goshi har ki kai ƙeya sannan ki sake dawowa farkon goshi. Sannan shafar fatar kunnuwa na dama da na hagu. Sannan ki wanke ƙafafu na dama da na hagu tun daga tafin ƙafa har izuwa gwiwar ƙafa. Ina fatan kin fahimta, amma zan fara sai kiyi duk yanda zanyi”.

Batace komai ba, sannan bata nuna zata ƙiyi ba. Dan ita dai tun maganarsa ta ɗazun akan mahaifiyar ta ya matuƙar sanyaya mata jiki, tsaf ta dingayin yanda yake yi har suka kammala, har cikin ransa yaji daɗin rashin gardamarta a wannan gaɓar. Dan haka ya ɗora da faɗin, “Akwai addu’a bayan kammala al’wala. Zan koya miki ita bata da wahala bata kuma da tsaho, sai dai ba yanzu ba sai na kammala shirina akan hakan. Muje kiyi sallarki”.

Komai batace masa ba yanzu ma tai wucewarta ta fita shi kuma yabi bayanta yana jin wani kaso na takaicin abinda ya faru daren jiya akan sayen magani na raguwar masa a zuciya. “Yanzu bamu da isashen lokacin da zan miki filla-filla akan yanda ake salla, amma zan nuna miki kaɗan a ciki kafin mu fara karatu na musamman akanta.” bai damu data amsa ba ya shiga nuna mata da faɗa mata abinda zata iya fahimtarsa a yanzun, nan ma dai batace komai ɗin ba har ya kammala ya bata izinin kabbara sallarta. Da ga haka ya samu waje ya zauna yana kallonta har ta idar. Ya dubeta zaiyi magana game da addu’a ganin har ta miƙe da ga sallamewa kira ya shigo wayarsa. Ahmad ne, dan haka ya ɗaga yana kaiwa kunne. Shaƙiyanci sosai Ahmad ke masa da ga can, har sai da ya sashi furta, “Ɗan sa ido ina ruwanka to. Kai ni karma kazo min gida ka tsaya nan nazo na sameka mu tafi”. Ƙaramar dariyar da ta saka Lulu kallonsa yayi kaɗan saboda jin abinda Ahmad ya faɗa da ga can. Sai kuma shima Smart ɗin da ya miƙe zai fice taji yana furta, “Irinku ne masu takurama sabbin aure da zarya har sai an cinye kayan gara da k….” daga haka ya fice bata ƙarasa ji ba. Baki ta taɓe kaɗan da ajiye sallayar tana sauke ajiyar zuciya da bata san dalili ba, da ga haka ta ajiye batunsa tai zaman dirshen a kan gado ranta fal tunanin cases ɗin dake gabanta. Dole ne ma gobe idan ALLAH ya kaimu ta fita office, kwana kusan tara yau fashin yayi yawa ai haba. Bata sake jin motsin Smart ba har sai da Mubarak ya kawo abincin rana. Lokacinne ya shigo ɗakin cikin shirinsa da alama fita zaiyi dan yaci wani faran shadda ƙal harda hula baƙa, ƙamshi yake mai sanyi ya fito a angonsa dai kai tsaye. Da ga bakin ƙofa ya dakata yana faɗin, “Ga lunch can an kawo ni zan fita su Ahmad na jirana”.

Baki ta taɓe kawai batare da tace komai ba. Shima sai bai sake cewa koman ba ya juya yay ficewarsa dan ya fahimci ƴan izza da masifar ne yanzu a kanta. Shi kuma bashi da wani isashen lokacin biye mata a yanzun……….✍️

 

 

 

 

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

 

*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*

 

FURAR DANKO

Billyn Abdul

 

-ZAFIN KAI

Mamuhgee

 

-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma

 

-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo

 

Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400

 

Pay at👇

 

1487616276

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇

 

09032345899

 

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070

 

 

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

 

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

 

Zafafa🫶🔥

 

 

 

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

No comments