Breaking News

Furar Danko 80

 

 

80

 


……..Shiru kamar Lulu bazatace komai ba, sai kuma taÉ—an taÉ“e baki da É—age kafaÉ—a. Cikin rashin damuwa da kallon abinda zatayi É—in a wani abu ta kwashe komai dangane da auren contract da Uncle Yousuf ya sanar mata saboda kar Baba yay mata auren dole ta sanarma Dada. Ta kuma faÉ—a mata ita babu abinda Aliyu yama taÉ“a nuna yana so a gareta, shiyyasa ma take É—an ganin girmansa”.

 

Salati Dada keyi a zuciya tana tsinema Uncle Yousuf, wato sunyi hakanne dan kar Lulu ta auri jikanta dake gadon asibiti. To lallai idan sun san wata ai basu san wataba kuwa. A zahiri kam bata nunama Lulu komai ba, tunda dama dai bugar cikinta take. Abinka da tsohuwar mace gashi taji abinda batai zato ba, Lulu kuwa har yanzu yarinya ce fa, dan ma ALLAH ya bata ilimi da kaifin basira, sannan ga yanayin rainon data tashi irin waɗan nan makirce-makircen na tsoffin matan ƙasar hausa ba gane kansu take ba. Sun cigaba da hira da Dada data ajiye maganar Smart har sai da Baba ya farka suka fito, Lulu taje ta dubashi. Ta jima a wajensa kafin ta tafi dan tana son komawa office. Mai Napep ɗin nan da yay zaman jiranta dan Uncle Yousuf ya bashi napep ɗin ne domin kawai bibiyar Lulun. Smart ya kirashi har sau biyu amma yana sanar masa tana a ciki bata fito ba. Da ta fito kuma yay kiransa ya gaya masa. Hakama da suka koma office. Ta sake zaman kusan awa biyu a office kafin ta fito Zainab biye da ita d kayayyakinta. Bayan ta saka mata ta sanar da ita gobe ta fito da wuri dan akwai wasu baƙin da take saran zasu zo nemanta. Da girmamawa Zainab ɗin ta amsa mata, ita kuma ta shiga mota sai gida. Sai dai ta tsaya wajen wani mai bread ta saya. Koda mai napep ya sanarma Smart bai kawo komai a ransa ba game da sayen bread.

 

(Ni dai nace Humm lulun mu fa ta wuce da saninka Smarty 😂😜).

 

★★★……

 

Tun shigowarsu cikin Saloon É—in nata tai kamar wadda ta suma. Ba ita kaÉ—ai ba hatta matan dake wajen ana musu ayyuka mabanbanta kallon mamaki suke musu dan kowa dai yasan anan mata kawai akema aiki banda maza. MM Atik Kumo ya katsema Nadiya tunani da faÉ—in, “Hello girl”.

 

Nannauyan nufashi ta kawo da dubansa, cikin Æ™arfin hali da in ina ta ce, “Ranka ya daÉ—e lafiya dai?”.

 

“Ita ta kawomu. Ko zamu iya ganinki a waje?”. Asim ya bata amsa kai tsaye. Ƴan shagon ta duba, ganin duk sun zuba musu idanu yasata cewa, “Okay muje”. Su suka fara fita sannan tabi bayansu tana jan Æ™aramin tsaki da gargaÉ—ar yaranta su cigaba da ayyukan gabansu. A cikin motar su ta samesu, MM Atik dake zaune mazaunin driver yay mata nuni da ta shiga ciki itama. Batai musu ba ya buÉ—e ta shiga, bayan ta rufe ta gaishesu. Asim ne kawai ya amsa mata MM Atik kam tambaya ya jeho mata na cewar “Yaya Æ™awarki?”

 

Numfashi ta É—an furzar da gimtse fuska, a taÆ™aice ta ce, “Ban san yaya take ba dan bama tare yanzu. Tun a waccan ranar bamu sake kasancewa tare ba”.

 

“Saboda mi?”.

 

Cewar MM Atik É—in yana jiyowa gaba É—ayansa gareta. “Hummm saboda naje da su Alhaji Baita wannan get together É—in fa. Kasan na faÉ—a maka Lulu ta tsani maza, shiyyasa nake kallon kamar aljani ya aureta ne shiyyasa. Yanzu haka ma zancen bikinta sai gani nai an É—aura mata aure wai da driver É—in nan nata a tv, hakama dinner É—in ta gani kawai nayi ana nunawa duk da kuwa na bata haÆ™uri ta waya da duk hanyar data dace amma taÆ™i saurarena”.

 

Murmushi MM Atik yayi damin hango irin ruwan bala’in datai masa a randa ya fara ganinta. Nadiyar ya kalla da faÉ—in, “Ai masifa bata mata wahala. Bar batun auren driver dan kuwa muna ganin da manufa tayisa, sakamakon son gujema auren Hon. Nakowa da wannan É—an uwan nata Tajuddeen Sulaiman Garko. Ba ita kawai ba nima naji haushin ganinku da tsoffin nan a wancan ranar, kawai dai na miki shiru ne”. Shiru Nadiya batace komai ba akan hakan, shima sai ya cigaba da faÉ—in, “Manta abinda ya faru ya faru ya wuce, yanzu sabon dil nake son mu Æ™ulla”.

 

“Nami kuma kenan?”.

 

“Akan Æ™awar taki dai, dan bazan iya haÆ™ura ba.”

 

“Abu mai wahala kenan, dan ta yanke alaÆ™armu, tare da gargaÉ—in nisantar ta. Nasan halinta kuma sarai idan ta faÉ—i abu har cikin ranta ne. Abu ne mai matuÆ™ar wahala Lulu ta sake kallona balle har na shiga jikinta”.

 

“Zamu iya amfani da wata ai, amma ya zama ke zakina controlling nata”. Cewar Asim.

 

Kai Nadiya ta jinjina da faÉ—in, “Wai babbar magana. Na fahimci bakusan wacece Lulu ba. Kubar ganinta haka batajin magana tasan mitakeyi. Sannan koni kaina nasha wahala kafin mu fara abota gaskiya, dan bata da saurin sakewa da mutane, sannan ba kowa ke iya haÆ™uri da halin Lulu ba”.

 

“Karki damu inhar aka jajirce wannan ba komai bane ba. Sannan kema fa akan aikin nan zakija manda. Dan a yanzu haka zamu sauke miki miliyan É—aya kafin ma aikin ya fara”.

 

Sosai Nadiya ta zaro ido waje, ranta fal farin ciki ta ce, “Yanzu yaya kuke so ayi?”.

 

Kallon juna sukai da murmushi, kafin Asim ya miÆ™a mata card da faÉ—in, “Ki samemu a wannan address É—in zuwa anjima”.

 

“Wannan yafi komai sauÆ™i”.

 

Ta faÉ—a tana amsar card É—in……..

 

_______________★

 

Kwanaki uku kenan da fara fitar Lulu aiki, kullum kuma Smart ke kaita office da safe sannan shima ya koma gidan yay shirin tashi fitar a Napep. Idan ko fita ta kamata a yinin mai Napep É—in nan da bata san da shi ba na biye da ita. Duk kuma inda ta saka Æ™afa ana sanar masa. A lissafinsa dai babu wani abu dake faruwa, dan ranar farko ta sayi bread wanda bai san a tsakkiyarsa aka saka mata kayan shaye-shayen ta ba, kamar yanda takeyi sai zata kwanta tasha hakan tayi, shiyyasa bai gane komai ba sai ya É—auka kawai gajiyar aikin data koma ce tunda tayi Æ´ar zirga-zirga. Washe gari dai yaga ta tashi a tsayenta bakamar kwana biyu datai wani sukuku ba. Rana ta biyu ma sai da tai amfani da dabarun nasu ta amsa, hakama jiya. Yau cikon kwana na uku yaso ya É—an fara tsarguwa, amma dai baice komai ba. Yana son mata tambaya akan zuwa gidan su Sa’id sai kuma dai yay shiru. Sai kuma gashi a yau yana tare da Coach kira ya sameshi da ga Ammah wai yazo da sauri idan yana kusa. Ya Isa gidan da tunani kala-kala sai ya É“ige da samun mahaifiyar Sa’id da wasu Æ´an uwanta maza uku dan dangin mahaifinsa sun rantse bazasu zo ba, ita data É“ata taje ta gyara sun dai zo na farko. Ba Smart kaÉ—ai ba kowa ma na gidan nan yau mamakin jin maman Sa’id wai sunzo bada haÆ™uri ne da neman afuwar Hawwah dan ALLAH tai haÆ™uri ta koma yake. Smart yace shifa Æ´ar uwarsa bazata koma wannan gida ba, anyi kenan takardar saki kawai yake buÆ™ata Sa’id ya kawo, dan suna sonta baza’a kashe musu yarinya ba. Sosai Maman Sa’id ke faman magiya akan wancan ma daya faru tsautsayi ne da munafuncin munafukai, amma yanzu ta gane gaskiya. Ankai ruwa rana matuÆ™a kafin Smart ya haÆ™ura zata koman amma ba wannan gidan ba. Da sauri Mama tace ta yarda, Hawwah ta zaÉ“i duk inda take so a gidajensu a gyara mata. Wannan abu yaba kowa mamaki, Umma na son magana tana tsoron ta tanka Maman Sa’id tai mata bankaÉ—a tunda taji tana shaguÉ“e akan munafukai, ba kowa kuma ne mai zuwa É“ata Ammah da Hawwah a wajenta ba sai ita dama. Bayan wucewarsu kowa ya shiga mamaki, Abba ya tsare Smart akan miya ma maman Sa’id É—in har tai irin wannan sakkowar lokaci É—aya. Ya tabbatar musu bashi bane, dan shi target É—insa akan jiran dawowar mahaifin Sa’id ne ai. Yana son kawo Lulu a ransa wani gefe na zuciyarsa na musa masa. Amma dai duk da haka bayan ya koma gida da daddare sai da ya kasa haÆ™uri yay mata tambaya. Dariya kawai tayi taÆ™i faÉ—a masa komai, hakan ya tabbatar masa itace kenan tayi koma miye. Sai kawai ya zuba mata ido yana jin wani abu mai girma na Æ™ara ratsashi a kanta. Jin kaifin idanunsa a kanta ya sata dakatawa da ga abinda take a system ta É—ago, harararsa tai da faÉ—in, “Malam wannan kallon fa? Ni fa bana son kallo”. Ta Æ™are maganar da murguÉ—a baki. Murmushi ya saki mai sanyi batare da ya janye idanun ba, sai ya samu kansa da furta, “Kullum sake mamaye komai da komai kike yi”. Bata fahimci ina ya dosa ba, sai dai yanda yay maganar a Æ™asan maÆ™oshi da tausasa fitar sautin matuÆ™a ya sata tsayawa kallonsa, “Lafiya kake kuwa? Kodai kaima ka fara ban sani ba?”.

 

“Na fara mi?”.

 

“A hawa network mana”.

 

Ƙaramar dariya yay yana girgiza kansa. “Tom maybe na fara amma nawa ba irin naki bane gaskiya. Kema fata nake ki daina wannan ai ki dawo wannan irin nawan”.

 

Nan É—in ma dai ba fahimtar tai ba, dan haka ma ta taÉ“e baki da miÆ™ewa tana faÉ—in, “Ai kai kam wani lokacin kamar mai aljanu. Dolene na sanarma Ammah ta fara maka addu’ar su ko ka kwaso a drivern cin ba’a sani ba”. Daga haka ta wuce bedroom ta barshi yana murmushi………✍️

No comments