Breaking News

Zafin Kai 88


88
Suna barin kofar gidan da mota gidan wutar gidan ta sake kamawa sosai yan anguwa da tsirarru wainda ke kusa suka fara ankara da gobarar gidan Amma da yawa suka qi tahowa kawo dauki sbd Ababa da baya mutinci ko gaisuwar mutunci ma bayayi da mutane,hakama baka Isa ya Rabi ko katangar gidansa ba sai yace kana leqa masa ta da ‘yaya akan wannan kawai sai yakai qararka acika tarar kudade ba dalili tsaban zalinci da mugunta,
Hakama Sam baya muamala da kowa bakuma yabari ayi da iyalinsa.

Wannan yasa da yawa suna ganin wutar suka fara nesa da gidan Dan kallan iKon Allah.

Kukan dabbobinsa ne Daya fara tashi sosai sbd zafin wutar Dayake kokarin Kai musu Dan haka sbd dabbobin gidan kawai yasaka mutane Kai dauki suka shiga aka Sako dabbobin tareda gargadosu waje sunata fitowa da gudu suna Kuka.

Raguna ne sosai da Shanu harma da akuyoyi da kaji masu yawan gaske.

Duk dahun magrib da yayi ana iya ganin yawansu Dan haka tini jamaa suka ringa taruwa Dan kawo dauki dakuma samun rabonsu.

Wainda sukasan halin Ababa sune suka Tara masa kan dabbobinsa guri Daya akai nesa dasu can Wani gidan da baa gamaba aka barsu Nan kafin ya iso.

Wainda basusan halinsa ba kuwa haka Suka ringa Satan kaji da raguna cikin hayaniyar da Taron mutanen suna guduwa dasu.

 

Naseer kuwa Kai tsaye Asibitin Kaantes ya nufa da motar Dayake ja cikin Wani shegen gudu sbd rayuwar hande dake cikin mummunan hadari Dan jini ne sosai yake fita ta hancinta sbd ita Kai tsaye qwayoyin sukai cikin kanta Dan jininta bazai iya daukaba,hakama kan nata bazai iya daukaba Dan haka Suka Huda jijiyoyinta Kai tsaye tana fidda jini sosai.

Suna Isa sbd DD ne da Kansa ya saka Kai tsaye dole aka amsheta Akai sama da ita sbd Bata taimakon gaggawa Dan Muni abin yake dada Yi.

Ana karbanta aka tabbatarwa DD cewan zaa dubata da kyau komai zaije daidai Kila.

Da wannan ya Dan samu Daman Jin Kansa dake tsananin juyawa ya Dan rage Dan haka Kai tsaye Asibitin suka bari suna kama hanyar zuwa highbridge.

Suna Isa bayan Naseer yayi parking juyowa yayi ya Kalli DD zaiyi magana D din ya katsesa da Bude baki cikin danyan Kai yace masa ya hada masa dakin kudi yanzu a cikin gidan.

Murmushin mugunta Naseer yayi tareda gyada Kai Yana Bude motar ya fito Yana nade hannuwan rigarsa Datake long sleeve.

Kai tsaye cikin gidan ya nufa Bai tsaya Palo ba ya wuce babban store Room din Dayake kitchen take ya hau fitarda kayan dasuke ciki Daman ba wasu masu yawa bane.

Yana gama fitarwa dakin yakoma zallan fili fes babu qazanta Amma duk da Hakan Saida ya Kuma tsaftacesa tsaf ya fito ya nufi dakin DD cikin closet inda wata mahaukaciyan katuwar boyayyar safe locker take cikin bango baa ma ganinta sai Wanda yasan da ita.

Password ya saka ya Bude take wasu mahaukatan kudi suka bayyana a Jere masu shegen yawan gaske tin daga kan nairsa har dollars da pounds akwai.

Haka Naseer yafara fiddosu Yana zuwa qatuwar jaka Yana Kaiwa storeroom din Yana dawowa Yana sake diban wasu Yana Kaiwa.

Saida yakai kudi me yawan gaske kafin ya dakata akwai rechargeable fans kusan guda uku manya manya acikin kayan Daya cire daga store din Dan haka ya daukosu gabaki Daya ukun ya kunna tareda bin kudin Nan Yana zazzagewa wasu suna Yana fasa bunch nasu wasu Yana barinsu a daurensu,
Babu tsoffi acikin kudin suka sabbi ne fil Dan haka tini fankokin suka fara daga kudin sama cikin dakin take dakin yakoma kaman ana ruwan kudi sbd gudun fankokin dakuma yawan kudin dake watse.

Ajiyan zuciya Naseer ya sauke bayan yagama wannan aikin kafin ya fito Kai tsaye mota ya nufa ya Bude Booth yaga har lokacin Ababa a some yake Dan haka kaman Wani Barawo haka ya cakumosa ya cirosa daga motar ya nufi cikin gida dashi.

DD dake Palo zaune Yana amsa waya daga Asibitin juyowa yayi yaiwa Ababan Wani mummunan Kallo sbd Jin Abinda ake sanar dashi daga Asibitin cewan irin munanan qwayoyin da aka samu a jininsa sune a jinin Hande Kuma nata jinin bazai dauka ba ko kadan han haka akwai yiyuwar Wani mummunan Abu ya sameta.

Kashe wayar yayi zuciyarsa na qara daukan nauyin Abinda aka fada din sbd idan mahaifiyar Bena ta rasu duniyar Bena dinsa zata tsaya ne.

Shin Ina ta hadu da wannan qwayoyin?
Waye ya Bata?
Ta Ina aka samesu?
Meya hada gidan Ababa da wainndan qwayoyin?
Tin farko ma meyasa ya fito ze gudu bayan daga cikin gidan ya fito yaga wuta naci hakama yaga halinda Annen take ciki,
Idan ze gudu ne to tabbas shine ya Bata wainnan qwayoyin,
Idan ma ba shi bane tabbas yasan inda suka fito Kuma idan yasan inda suka fito to yasan Shima waye ya Basa wainda yasha Shima.

Naseer Kai tsaye dakin ya nufa da Ababa Yana Isa ya Bude store din Daya koma dakin ruwan kudi ya tsaya daga kofa ya daga Ababan sama ya Jefasa cikin dakin kan kudade

Mummunan jefawan da Akai masa ya sakasa farfadowa agigice cikin azababbiyar azaban qafarsa Daya data Kaye take
Cikin radadi da taurin Rai ya Bude idanuwansa da tini sukai ja sbd tashin hankali da mamakin Ina yake?

Kudi yaga suna yawo a saman dakin da koina cikin dakin suna tashi sosai.

Da sauri ya sake rufe idanuwansa ya Budesu Yana Jin azabar qafarsa har lokacin da fara kallan dakin yaga koina kude a kwance da masu tashi kan iska,

Hannuwansa dake Dafe da qara ya kalla yana juyawa da Kansa Yana kallan inda yake kwance.,
Daloli ne da pounds da Bema sansu ba yan dubu dubu yake kwance akansu kaman shimfa.

Sake rintse idanuwansa sosai yayi wannan Karan ya Budesu da kyau ga tabbatarda kudine yake kwance Akai,

Tashi zaune ya sake Yi Yana kallan Naseer dake kofa zuciyarsa na mummunan bugawa sbd wainnan kudin Bai taba ganinsu ba a ruyuwarsa hakama baisan dalilinsu na Daukosa ba su kawosa gurin wannan kudin,
Sake kallan Naseer yayi zaiyi magana Naseer ya katsesa da cewa

“Kudin da duk kake buqata a rayuwarka har karshenta wainnan zasu isheka,
Bakasu zaayi,babu duka ba zagi ba komai zasu zama naka ka gudu inda kayi niyar guduwa kayi rayuwarka babu ruwanmu da abubuwan daka aikata ko kake aikatawa,
Duka wannan kudin zaa baka su ne a sirrance babu Wanda ya sani ko zai sani,
Duka duka Abu biyu mukeso daga gareka Wanda kana bamu su shikenan ka kwashi kudin Nan ka tafiyarka,Amma sharadin mu na farko shine duk tsanani kada dd babba ko kowa yasan min hadu dakai har munyi Wani boyayyan Hulda,.ka yarda da Hakan?????

Duk da Ababan na cikin radadin kafarsa hakama zuciyarta na cikeda tsoro,mamaki,shakka, fargaba da wasi wasi akan komai Dayake faruwa a Nan din Amma Jin cewan basason dd babba ya sani ya sakashi Jin shiga tinanin idan har basason dd babban ya sani to kenan da gaske boyayyan Hulda zasuyi dashi da gasken.

Lissafi yahau Yi akan yariga ya rasa komai,
Hande ta mutu,
Baida ‘yaya ko mata,
Ya rasa dukiyarsa suna can suna ci da wuta dabbobinsa da gidansa da Dan sauran arzikinsa dake gidan duk yasan ya rasa,
Yanzu Kuma gashi ya shiga hannun wainnan majiya qarfin dayasan ko dukan DD bazai iya dauka ba shi da yake da jikin Hutu kaman na Yara bare na Naseer Dayake kaman basamude ya tsane ruwan jikinsa tsam.
Dan haka babban fatansa da burinsa a yanzu ya samu Abinda zai gudu Yana tserewa komai da kowa,
Amma tinda boyayyan Hulda sukeso dashi zai risga dasu yasamu tserewa kafin asan meya kashe hande qaryarsa ta qare Dan kuwa ta tabbata su Safnah suyi galaba akansa kenan,
Da gangan suka yarda ledan robar qwayoyin gidansa Dan kawai su jaza masa masifar da shi duk taadancinsa baitaba sanin ya qwayoyin suke ba bare inda ake siyarwa Amma wlh bazai yarda ba mutuwar kasko zasuyi idan ma kamawa tayi Amma dai yanzu bari yaga yanda sukuma wainnan zasuyi dashi.

Gyada Kai yayi Yana kallan Naseer yace ya amince.

Ajiyan zuciya Naseer ya sake tareda Dan waiwayawa ya Kalli DD dake zaune Yana jinsu sai alokacin D din ya taso yazo gabansa ya tsaya Yana dauke kallansa daga Kansa sbd zuciyarsa zafi da radadi takeyi idan Yana kallan fuskan mutumin Daya haifi Bena Kuma mutumin Daya lalata rayuwarta ya reneta a gidansa kaman Dabba,
Da ba shine ya haifi Bena ba wlh da tin a jiyan zasu jefa shege cikin wutar dayaso barin Anne ta kama a ciki ko Rabin jikinsa ne ya kama kafin su fiddosa su miqawa jamaa shi akaisa Asibiti.

Tsanar kallan fuskansa yakeyi Dan haka Kai tsaye cikin kamewan murya da rashin Annuri ko kadan yace

“Duka wannan kudin zan baka inda Bena take kawai nakeson ji,
Kana fadamun bazaka fadawa kowa ka ganni ba bazan fadawa kowa na ganka ba.”

Dagowa Ababa yayi da sauri ya Kalli DD din sbd Jin tambayan da baimayi zatan ji daga Bakinsa ba sbd kenan tintini da Abbakar ke ce masa Bena tana Zurich tareda DD din qarya ake masa sbd ya kawo Kansa,
Kenan suma basusan inda take ba??
Da gasken kenan ta shiga duniya ta tafi???

Wani irin sanyi ne ya mamaye ransa sbd damarsa ta Kai su Safnah qasa ta dawo hannunsa,hakama kenan babu tabbacin shine ya kawar da Bena da Annenta zarginsa kawai akeyi hujja ake nema,
Hmmmnnn tabbas zai Bada hujja kuwa me kyau.

Dagowa yayi ya Kalli DD cikin marairaice fuska yace

“Daman Bena Bata tareda ku acan?
Nima zargin danakeyi tin ranarda Annenta ta bace na cewa Bena ta dauketa sun gudu Ashe gaskia ne…..

Wani Kallo DD da Naseer sukai masa lokaci Daya Jin Annenta ta Bata,
Naseer ne yayi saurin katsesa da cewa

“Wacece wadda muka sama a gidan to idan Annen Bata Nan??

“Hande ce, mahaifiyata,kakarsu Bena me tsananin kaunarsu,nayi kokarin cetan ta Amma nakasa sbd wutan shine na fito Neman taimakon masu kashe wuta asamu a fiddota shine Kuka taho Dani,
Meyasa Kuka taho Dani bayan mahaifiyata na cikin hadari”

Tsoki mara sauti DD yayi tareda gyara tsayuwa yace

“Ina Bena take?
Ina Annenta take?
Me ka sani game da tafiyanta da Annen tata?

Magana Ababa zaiyi sbd anzo inda yakeso yau Safnah zatasan shine uban ubanta a duk shedancin dasukeyi itada Nuratu, wayar DD ce tayi qara cewan yayi gaggawan zuwa Asibiti yanzun Nan.

Kashe wayar yayi tareda kallan Ababa yace

“Kudin gabanka basai na fada mata nawa bane Amma ka nutsu ka qirga miliyin Dari biyu ka ajiye mana sauran gefe,amsar da zaka bayar itace zata baka Daman daukan kudin ka tafiyarka”

Yana gama fadan Hakan ya juya ya fice
Naseer ma kofan dakin da Ababan yake ciki ya janyo ya rufe tareda saka key din kofar datake da masifaffen nauyi da qarfin masifa.

Suna rufesa gidan suka bari da sauri zuwa Asibiti.

Koda suka Isa Hande tayi Nisa bayan sunan Safnah da Ababa a bakinta babu Abinda take fizgota tana fada,

Wani jijjiga da wasu yawu masu jini jini take fitarwa.

Sunan Safnah datake fada ya saka DD da Naseer yin shiru sbd basusan waye Safnah din ba.

Babu Abinda zasu iya mata Dan haka DD ya karbi report na awon qwayoyin jininta ya fice daga Asibitin.

Suma manyan Asibitin ganin Hakan suka kira dd babba da tinda suka iso yake Kiran wayoyin DD baya samu hakama anje gidansa bayanan daga shi har Naseer Dan haka Jin Abinda Asibitin suka kira suka fada yasashi shiga mamaki da sabon fargaba yace abar Asibitin da matar Dan haka ba Bata lokaci suka tattarata suka mayar da ita Asibitin gwamnati sbd kada matsalan qwayoyin ta taba sunan Asibitinsu.

DD kuwa ledan dake motarsa ya hada da report din ya nufi office din Sir Ashir bello dasu sbd dole yanzu kam tinda ansamu ledan qwayoyin zaa iya samun fingerprints na duk Wanda yakeda hannu a samar da qwayoyin.
##MAMUH#

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

No comments