Breaking News

Garkuwa 13

PAGE 13

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

連老

FREE PAGE

Littafin GARKUWA na kuɗine, Special Group 1k Normal 300, in kina buƙatar karanta lbrin GARKUWA turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan layin 09097853276. Gareku mutanen Special Group turo dubu ɗaya ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276.


 

*Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki, in kin san zaki sayi littafinane dan ki fitar dashi, na roƙeki da Allah da Manzonsa da darajar iyayenki kada ki saya bana son kuɗinki, ki riƙe kudinki ki barni in riƙe littafina. Dan Allah nace badon niba.*

 

Yaji anata bubbuga mishi ƙofar ɗakin,
bai kulaba, yazo a zauna bisa kujerar dreesing mirror, a hankali yake tsane ruwan jikinshi, bayan ya gama ɗan tsane ruwanne ya busar da tattausan sumar kanshi, ta hanyar na’urar busar da gashi.
Mai ya ɗan shafa, kana ya gyara gashin da kyau, sannan ya miƙe yaje gaban.
Drower’n, a nitse ya buɗe, wasu datsatstsun kaya riga da wondo na yadin Lamud, yadin Sky blue ne mai masifar kyau. Sai kuma ya zaro wata farar al’kyabbar fara ƙal. Da farin hirami.

Rufe wannan gefen yayi, kana ya buɗe ɗaya gefen.
Ƙananan kayan ne a ciki kamarsu Jallabiya da boxes vest dasu zagayen baƙin abin da yake ɗaurawa kam hiraminshi.
Suma duk mafi akasari su fararene.
A bakin gadon ya ajiyesu.
Kana ya fara kimtsawa.

Bayan ya gama shirinsa ya fito ras cikin kalar sky blue and white sai Black half cover da kuma baƙin zagayen saman hiramin.
Ya fito ras tamkar dai yadda zuriyar mahaifiyarshi da suke tsatson limamen Harami suke fita.
Ko yaya ka ganshi dole kace shi balarabene, sabida komai nashi irin nasune. Kyau, fari, gashi, ilimin addini, nitsuwa, imani, da kuma irin shigarsu, da shima ya rainu da hakan tunda a cikinsu ya girma.

Wani turaren Oud Kareem ya feshe jikinshi dashi.
Lumshe ido yayi sabida shida kanshi ya shaida ƙamshin wannan turaren nashi iyakane.

A hankali ya nufi ƙofar fita yana tafe yana tasbihi.
“Astagafirullaha wa’atubu ilaik.
Astagafirullaha zunuba jami’an. Subahanallahi Wal’hamdulillah wa la’ilahaillahu Allahu Akbar.”
Da wuya ka iya jin abinda yake faɗin, sai dai ina ka lura da motsawan jajayen laɓɓansa, masu kama da jajayen kunnen fire masu taushi zaka fahimci tasbihi yakeyi.

Ba kowa a wurin sabida haka ya nufi falo a nitse,
A falon ya samu Sitti bisa dukkan alamu, shirin tafiya harami tayi.
Tana ganinshi ta miƙe tare da cewa.
“Muje ko”. Kai ya gyaɗa mata, kana ya ɗan kalleta bayan ya ɗan tsagaita tasbihin bakinshi yace.
“Zan shiga wurin Sheykh Abdulkareem”.
Cikin kula tace.
“Muje sai mun dawo mana”.
Kanshi ya jujjuya mata kana yace.
“Zan sanar dashi batun komawarmu”.
Gyara matafinta tayi tare da cewa.
“Na sani ai, muje sai mun dawo”.
Fuskarshi ya ɗan haɗe tare da cewa.
“Ni a harami zan kwana”.
Ganin ya kafe tasan fa duk yadda tayi, hakan zaiyi,
binshi kawai tayi,
suna shiga suka samu kamilin dottijon nan, bisa tsakiyar yaranshi, da alamun suma ɗin anjima zasu taho masallacin.
Yana hanƙoshi ya miƙa mishi, hannunshi na dama, da sauri ya isa gareshi, ya kama hannunshi tare da rusunawa, ɗaura hannun yayi bisa tsakiyar kanshi, sannan yayi shiru yanajin yadda dottijon ke zuba mishi addu’o’in.
Yayinda kamilan yaranshi ke amsawa da.
“Ahmeehn! Ahmeehnn!! Ahmeehnn!!!.”
Bayan ya gama mishi addu’o’in ne, ya juyo ya gaida kakanun nashi, baki ɗayansu.
Kana ya shaida musu tafiyarsu data taso cikin gaggawa ya kuma sanar musu dalilin tafiyan.
Sun gamsu da hakan, kasan cewar sun ɗan ɓata lokaci a nanne yasa. Tare suka tafi masallacin baki ɗayansu.

Haroon kuwa cikin kwana biyu ya gama musu komai na tafiyarsu, gida dan shima dama yana son tafiya gida shida Jannart ɗinshi duka.

 

A cikin makarantar su Aysha kuwa.
Sam bata samu lbrin abinda ya faru a rugarsuba.

Sai da yamma, nanma Rafi’a ce, dake riƙe da wayarta tana chatting.
A nan ne ta gani a kafafen yaɗa labarai cewa.
Anyi faɗa a tsakanin MAKIYAYA da manoman, a garin Kikan dake gaɓar kokin Namun.
Koda ta sanarwar Aysha.
Taga tashin hankali ya wuce zatonta,
hakane yasa ta bita suka tafi tare.

Su Bappa kuwa bayan sun nufi, rugar tasune, sukaci karo da motar police officers, da kuma Ambulance ɗin, daya ɗebo su Ummiy dasu Junaidun da Junainah, kana. Da wasu wadanda ake ganin kamar sunada ɗan sauran numfarfashi.

Da sauri C.P Daniyel yasa, drevernsu Arɗo Bani, ya juya dasu, dan suka nufi cikin Genaral Hospital Numan ɗin, sabida yasan in sukaje suka, ga irin kisan gillar da ƙabilun nan sukayiwa yan uwansu, tashin hankali zaiyi yawa ya kuma san A.S.P Kabir da rundunarsa na, can, to zasuyi mishi bayanin da zaisa ya iya korarshi a aikinshi.
Shiyasa ya jasu suka koma, cikin asibitin.
A cewarsa su kula da mutanen su, saura kuma, kuma, akwai hukuma na, kula dasu a can.

To wannan dalilin ne, yasa suka koma cikin asibitin,

Hakane yayi sanadin da koda Waziri da Matawalle da rundunar Hadiman da Sarki ya aiko,
Suka zo, basu ga su Arɗo ba a cikin Rugar, kana kusan wuni sukayi a nan dan sai yamma, suka juya suka koma masarautarsu.

Ita kuwa Aysha, suna zuwa, kai tsaye cikin asibitin suka nufa, dan tayi waya da Bappa.

Koda suka iso, sosai hankalin ta ya tsananta gaba hankalinta ya tashi, ganin gaba ɗaya asibitin a cike yake da mutane su,
sai dai ta ɗan samu nitsuwa kaɗan ganin Ummiy da Junainah sun farfaɗo,
sai dai duk basa mgna sunyi zurui dasu hakama sauran waɗanda suka samu suka farfaɗo ɗin.

Koda ta tambayi Bappa inasu ya Giɗi sai cemata yayi suna gida, ya ɗaura da cemata.
“Yauwa Shatu ku zauna nan, ku kula da marasa lfyan, bari mu kuma mu ƙarasa can Rugar tamu, mu duba meke faruwa a gidan”.
Hannu tasa ta share hawayenta dake shatata daga cikin kumburarrun idanunta cikin disashewar muryar da kuka yasa ta dishe tace.
“To Bappa kuje, zamu kuladasu, ga can Ya Salmanu ma, ya turo mana abokanshi, ga kuma ƴan agaji, zamu zauna dasu”.
Cikin tarin ƙuna da tafasar zuciya, Alhaji Haro, ya gyara gariyarsa tare da cewa.
“Mu tafi”.
Arɗo Bani ne ya miƙe tsaye tare da yin gaba kana duk suka bishi a baya suka fita suka tafi.

A hankali Rafi’a tasa hannu ta tallabi Aysha daketa kuka mai sosa zuciya, kuka mai cike da rauni da taraddadi.
Zama sukayi cikin tausayawa Rafi’a tace.
“Ki dena kuka Aysha, in sha Allah babu komai.”
Murya na rawa hawaye na kwaranya ta buɗe manyan idanunta da suka rine sukayi jazir da kuka da tashin hankali, cikin rauni tace.
“Rafi’a babu komai kuma?, ko dai komai ya faru, kalli fa halin da yan uwana da maƙotanmu suke ciki, kinjifa ance an kashe mutun kusan 40, kuma kin san gidajen rediyo suna ragewa nema wasu lokutan sabida kada, hankali mutanen duniya ya tashi.
Rafi’a banga Yayuna ba, ko ɗaya ban ganiba, banga Inna ba, kalli Junaidu, kalli can Ya Mati yayansu Ya Salmanu. Kowa baya cikin haiyacinsa,
Ummiy ta zama kamar kurma meta gani ya gigitata haka, kalli yadda Junainah keta fizge-fizge alamun taga mugun abun daya firgitane ya ɗimautata.
Rafi’a ga tozarci da cin fuskar da akeyi mana, kallifa babu likitan da yazo ya kula mutanenmu, an barsu ciwukansu nata tsami,
sai Nurses keta, hararanmu.
Rafi’a ya zanyi in banyi kukaba, ina zansa raina, Ina Yah Giɗi, ina Yah Gaini, Ina Yah Seyo? Rafi’a sun kasarani sun rabani da yan uwana.”
Kife kanta tayi jikin gadon da Ummiy ke kwance a kai, cikin murya mai cike da rauni tace.
“Ummiy kiyi min mgna mana, Ummiy na inasu Ya Giɗi na ina Ya Gaini, ina Ya Lado, ina ya Seyo, meya hanasu zuwa wurinki na tabbar in suna raye cikin ƙishin lfy, dole zan samu ɗaya daga cikinsu a wurinki”.
Mari matar Arɗo Bani ce wacce ta ɗan dawo haiyacinta ne, ta rumtse idanunta wasu zafafan hawaye ne suka silalo mata, cikin sanyi tace.
“Shatu sun tafi kiwo ne, zaki gansu”.
Jajayen idanunta ta zura mata,
Alamun tana son tabbatar da abinda tace matan.
Fahimtar hakane yasa ta gyaɗa mata kai alamar eh hakane.
Cikin son kontar mata hanlali ne, Rafi’a, tace.
“Kinjiko Aysha, to kiyi haƙuri ki nitsu in sha Allah dukkan tsanani yana tare da sauƙi”.
Kife kanta ta kumayi tana mai sake kuka mai ciwo a zuciya, gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi.
Haka dai sukaci gaba da bata baki, wai dan ta samu nitsuwa amman ina, fargabanta sai tsananta yakeyi.

Su Bappa kuwa, isarsu Rugar Kikan ya ƙara tada hankali matasansu da suka dawo kiwo da matansu da suka dawo tallan nono wanda sanadin basa nanne yasa suka tsira.
Gaba ɗaya Rugar ta birkice ta kiɗime.
Hankali dattawan nan yayi masifar tashi, ganin duk an karkashe musu, mafiya yawan matansu yaransu da jikokinsu.
Especially Alhaji Haro, da iya cikin gidansa kawai saida aka samu gawar mutun goma sha uku.
Koda aka jera masa gawakin suma yayi. Sai ga Tsoffin nan suna kuka cur-cur da hawayensu, gwanin ban tausayi.
Ganin yamma na rufawane yasa,
Dattawan maƙotansu, mazansu suka fara wonke gawakin maza kamar yadda addininmu ya koyar da mu.
Mata kuma sukayiwa mata wonka,
Kana suka sallaci Gawarwakin da a ƙalla sun kai mutun Settin da uku 63.
Kana suka rinƙa binnesu da taimakon Hausawa musulman cikin Numan da maƙotansu fulani.

Gaba ɗaya garin yayi tsit ya koma tamkar kufayi. Sauran rayayyun sunyi Kuka har muryoyinsu. Sun disashe.

A cikin Genaral Hospital Numan kuwa.
Musulmai Hausawa da Fulani, sune suka rinƙa kawai Fulanin Rugar Kikan taimakon abinci.
Hankalin Aysha ya ƙara tashi ganin, har dare babu wanda yazo.

Hakama da gari ya waye.

Su Bappa kuwa da Arɗo Bani, Alhaji Haro. Malam Manu, Alhaji Umaru, tashin hankali da kiɗima da firgici da ɓacin ransu ya tsananta, sabida ganin.
Duk Hukumar ma sun tafi,
Gashi babu wani babba da yazo ya duba halin da suke ciki, sabida ai su basu san da cewar su Waziri sun zo tun jiyan ba.
Ransu yayi matuƙar ɓaci, ganin Gwamnatin jihar,
da Masarautar jihar, babu wanda ya tako ƙafarsa, yazo ya dubasu ko ya turo wakilinshi.
Wato matsalarsu bata shafi kowaba.
Wannan abun shine mafarin Fara da baƙar Kaddarar Shatu a tarihin rayuwar ta, domin iyaye da yayun wannan Rugar sun tunzura sun hasala, iya hasala, sun cika fam da tarin baƙin cikin rayuwa, an rigada an taɓo zuciyar Fulani haka yasa zasu iya gayawa kowa mgna dai-dai da abinda yayi musu.

A can Saudia kuma, komai na dawowarsu Sheykh ya kammala, cikin kwana uku, domin hankalinshi yayi matuƙar tashi, jin irin kisan gillar da akeyiwa makiyaya, wanda Maimartaba ne, ya gaya mishi komai, ya ƙara da cewa.
Yayi maza ya dawofa, don yana jiranshi suje tare yaje ya danni fulanin ya basu hakuri ya kuma taushesu kada su ɗauki mataki da sunan ramuwa ko ɗaukar fansa.

Hakane yasa, Sheykh ya uzzurawa Haroon dole ya gama musu komai.
A kwanaki ukun.
Ranar Jumma’a da azahar jirginsu ya sauƙa, a birnin Shehu Sokoto.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi yaso. Jikan nashi ya kwana, sai dai ina ya tike dole a lokacin Haroon ya kuma saɓan mota suka fara kita hanyan kawoshi Adamawa.
Wanda sai ƙarfe uku da rabi suka isa.
Kasamcewar dama basu taso da wuriba.
Kasancewar isar dare sukayi babu wanda yasan Sheykh ya dawo.
Ƙasar sai Lamiɗo da kuma hadimanshi, uku kacal da sune suka tarbesu.

Sai washe gari da. Asuba, sautin muryarsa yana karatun limancin Sallah asuba ne ya shaidawa mutanen masarautar Joɗa dawowanshi.

Gaba ɗaya kowa ya cika da mamakin, kana da farin cikin dawowanshi.

Duk da kasancewar sa, mai larurar da wasu ke mishi kollo ko kiranshi majanuni, yasan kiyaye lokacin salla dama yinta cikin kushu’i.
Wannan shine ya hanashi sallame sallar, da akeyi yana cikin sahu na tara,
wanda jin muryar ɗan uwanshi ƙaninshi, ya sashi zubda hawaye masu ɗumi.
Ya Jafar kenan.
Jalal kuwa dake gefenshi wata irin sassanyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da lumshe kekyawan ƙwayar idanunsa da suke iri ɗaya dana Sheykh, ga kuma bacci daya cikasu, domin daren jiya, Ya Jafar ɗinsu ya hanashi bacci.
Jin muryar ɗan uwansu da shi kaɗai ke iya sarrafa babban yayan nasune ya sashi sauƙe, numfashin.
Jamil da Affan kuwa, wani irin yalwataccen murmushi ya sake jin muryar ɗan uwansun.

Abbansu kuwa, shi dai har yau yana rasa me yakeji a kan ƴaƴan nashi, Especially Sheykh, yana jin zuciyarshi na mishi nauyi duk sanda yaron baya kusa dashi, sai dai kuma in yana kusa dashi sai yaji tamkar bai taɓa wani farin cikiba a rayuwarsa.
Ya sani tabbas su abun tausayawa ne, suna buƙatar kulawarshi fiye data kowa a duniya, to amman ya rasa meyasa yake jin kamar baya son kusancisa dasu.

Maimartaba kuwa, suna cikin sahun na forko bayan liman,
Sai da sauran malaman fada.

A cikin gida kuwa, jin sautin zazzaƙar miryarshi yana rere karatun al’ƙur’ani, ya ida fatiha, kana ya ɗaura, Arrahama,
daga bisani ya rufe da lakadja’akum, kafin ya tafi zuwa ruku’uh.

Haka nan Juwairiyya ta tsinci kanta da zubda wasu zafafan hawaye, masu ƙuna a rai, tabbas ta sani.
Kasan cewar Sheykh a masarautar nanne kaɗai yasa, suke a ciki.
Ta sani in badon daraja da al’farmarsa ba, da tun tuni, an tabbatar da sunan mijinta mahaukaci.
Hannu tasa ta share hawayenta cikin sanyi ta miƙe dan gabatar da sallan asuba, a zahiri tace.
“Allah ne gatanmu, kaine GARKUWAR mu, Sheykh in baka nan gidan kanyi mana duhu, ƙasar tanayi mana zafi.”
Daga nan ta tada kabbara.

Ummi Jakadiyarsu kuwa,
Tana bayan gida, tana al’wala ta jiyo muryarshi, wani irin murmushi tayi tare da yin mgna a baiyane.
“Dan Halak kaƙi ambato, ɗa ɗaya tamkar dubu, maƙiyanka fadawanka, sunyi sake ɗan zaki ya girma, in sha Allah zaka dawo da farin cikin masarautarnan, sunyi sake, sun bar kari tun ran tubani,
Muhammad Jabeer bawan Allah”.

Haka ta fito tana wasu irin kalamai masu wuyar fahimta.
A can sashin Hajia Mama kuwa,
Wata kekyawar budurwa, ce.
Konce kan gado gefen Mama, datake zaune bisa sallaya.
jiyo muryashine ya sasu saurin juyowa, suka kalli juna,
Cikin tsananin farin ciki da tarin shauƙi budurwar ta diro daga kan gadon gaban Mama ta zauna cikin zaƙuwa tace.
“Lah Mama, yaushe ya dawo! Muryar Sheykh Jabeer nake jifa! Mama ko dai dama yana nanne?”.
Wani irin kallo Mama tayi mata cikin sanyi da murmushi a fuskarta tace.
“Batul shine, ya dawo!.”
Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe cikin tarin shauƙi tace.
“Yes Mama, farin cikina ya dawo, kamar yasan, nazo.
Alhamdulillah, Mama Allah yana sona, ki gani ina zuwa, na samu baya nan, naji baƙin ciki kamar in mutu jiya kafin inyi bacci, sai gashi Allah ya turo minshi cikin dare ɗaya.”
Murmushi Mama tayi, tana mai jin mmkin yadda Batul ke masifar son Sheykh har take gaza ɓoyewa.
cikin haɗe fuska tace.
“To yanzu dai, sai ki tashi kiyi salla, tunda kinji muryar da kikafi so a duniya, kin sauƙo kan gadon, sau nawa ina tadake, sai kiyi miƙa ki kuma konciya”.
Cikin jin dadi tace,
“Wayyo Mama baccinne bai isheniba Allah ko jiya kwana nai ina zulumi, sai 3:44 na asuba na samu bacci.”
Murmushi Mama tayi kana ta miƙe ta kabbarta sallan.
Ita kuwa Batul, miƙewa tayi da sauri ta shige, bathroom tana cewa.
“Bari inyi wonka inyi salla, in shiga kitchin yau nida kaina zan mishi breakfast.”
Tana faɗin haka ta shige ciki.

A masallaci kuwa, ana idar da salla kamar koda yaushe, da yawa basu fitaba saida sunata lazumi.
Yayinda Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da kuma Sarki Nuruddeen Bubayero, da Habibullah Nuruddeen Bubayero, suka jero, suka fito a jere, domin su kullum ana idar da sallan asuba, suke fitowa su koma cikin masarautar, inda kowa zai wuce Side ɗinsa,
Yayi karatun qur’ani da kuma, Dua Azkar, inda har sai rana ta fito, kana suke ɗan maida bacci, to kuma sudayin breakfast sai 11.
Suna isowa tsakiyar masallaci, Sheykh yaji an ruggumeshi ta baya, yasan mutun ɗaya ne rak zai mishi haka a cikin masallacin,
Ya Jafar ɗinsu.
Yana juyowa kuwa yaga shiɗin ne.
Ruggumeshi yayi gam-gam Jalal, kuwa ido ya zuba musu,
shi kuwa Sheykh hannu yasa shima ya ruggume ɗan uwan nashi.
Yayinda ya zubawa Jalal kwayar idanunshi, ya rame sosai, hancinsa ya ƙara fitowa, sai sajenshi daya ƙara yin lib, da uban gashin daya tara, yayi wani kafurin aski.
Ramar da Jalal yayi ta daki zuciyarsa sosai baya son ganin ƙannen nashi cikin halin matsala,
a hankali ya janye kwayar idanunshi ya maidasu kan Jamil da Affan dake gefen damanshi,
Calikan ƙanenneshi kenan ba,
sheƙiyancinsu ɗaya, baki suka haɗa wurin cewa.
“Sabahul Noor Al’Sheykh”.
A hankali ya ɗan motsa laɓɓansa, yana mai kallonsu yace.
“Sabahul khair ya Uktih”.
murmushi sukayi, suna mai jin son ɗan uwan nasu,
Abbs da Maimartaba kuwa, kai suka ɗan jinjina kana sukayi gaba,
Ganin hakane suma suka bisu, a baya,
shi kuwa Sheykh hannu yasa ya shafa kan Imran da yanzu ya iso gabanshi cikin sanyi yace.
“Hamma Jabeer barka da safiya”.
jin yana shafa kanshine ya sashi lumshe ido, inama ace yadda Hammanshi ke nuna mishi so haka zai shirya da Mom ɗin shi, yana masifar son ɗan uwanshi baya jin daɗin yadda yake ganin wata iriyar mu’amala tsakanin Mom da yayunshi.

Ganin Sheykh yaja hannun Ya Jafar sun tafine yasashi bin bayansu.

Ƙofar dake cikin masallacin wacce zata ɓulla cikin masarautarsu sukabi.

Suna shiga, kowa yayi sashinsa sabida sun sani ko sunbi Sheykh yanzu ba lokacin mgna bane, karatu zaije yayi.
Shi kuwa Sheykh yana riƙe da hannun Ya Jafar ɗinsa suka shiga side ɗinsa,
inda ya samu hadimai masu tsaron ƙofar, suna tsaye.

Suna shiga, tamtsetsen falon nashi kai tsaye ya nufi wannan babbar kusurwar da zata sadashi da.
Big part ɗin shi,
Suna shiga suka ɓulla cikin wani mashahurin, falo, wanda yaketa tashin ƙamshi mai masifar sanyi da daɗin shaƙa,
a hankali ya zauna bisa kujerar 3 str kana yaja hannun Ya Jafar ɗin suka zauna, tare.
A hankali ya juyo kanshi ya zuwa ɗan uwanshi idonu,
Karatu yakeyi kamar koda yaushe, yanayi cikin tsantsar lugga da tajwid, kana ga kushu’i,
Suratul yaseen yake karanta,
bisa alamu kenan ya kusa yayi sauƙa, domin step by step yake bin surorin, in yayi sauƙa sai ya sako daga sama, baya mancewa, kuma baya birkitashi,
Wannan rahamar da Allah yayi mishi, duk da anso a maidashi majanuni, sai Allah yayi mishi muwafaƙa da littafinsa maisarki, yazama sihirin yayi mishi tasiri tako ina, amman banda gefen addininshi.

Wasu irin hawa masu ƙunu yaji suna tsatstsafo mishi, cikin jijiyoyin kekyawan idanunshi,
sabida ganin yadda Ya Jafar ɗinshi ke karatu yana, kuka ya za’ayi ya sama mushi farin ciki a rayuwarsa ta ina, zai san me ke cin zuciyar ɗan uwan nashi.
Jin yadda ransa ke ƙuna da tafasa ne, yasashi. Komawa ya jingina bayanshi da jikin kujer, kamar yadda Jafar yake mahaddacin haka shima settin kab tana kanshi,
Ido ya lumshe tare da yin bisimilla kana ya fara karu inda ya ɗauko daga forkon suratul. Noor ya farayin ƙasa.

Saida sukayi awa ɗaya cur kana,
Suka fara Azkar, wanda sai da sukayi 23 minutes suna, jero addu’o’in cikin harshen dake nuni da cikekkiyar jimla ta larabci da lugga.
Koda suka shafa, sai ya ɗan kalli ɗan uwanshi dake riƙe da hannunshi gam.
Ya lura Ya Jafar na tsoron kada ya kuma tafiya ya barshine, yasan duk sanda yayi doguwar tafiya ya dawo, haka yake liƙe mishi.
Hannunshi yasa, ya share mishi hawayenshi kana,
ya miƙa tare da jawo hannunshi,
yasani yanzu lokacin yin baccinsa ne,
Side ɗinsu, ya nufa dashi, ta wata ƴar siririyar hanyar dake tsakanin sashukansu.

A babban falon suka samu Juwairiyya.
Tana ganinsu, ta miƙe da sauri, fuska ɗauke da murmushi kana ido na tsatsafo da hawaye tace.
“Barka da dawowa, Sheykh, Alhamdulillah zamu samu nitsuwar Ya Jafar”.
Kanshi ya sunkuyar sabida bai son ganin hawayenta,
Hannunshi ɗaya yasa yana shafa, kam Mimi data ruggumeshi ta ƙafafunshi,
cikin murmushi ta nitsuwa yace.
“Mimina anyi sallako?”.
Cikin sauri ta gyaɗa kanta alamar eh,
Shi kuwa kanta ya kuma shafawa tare da cewa.
“Kinyiwa Ya Jafar ɗina Addu’o’in Allah ya bashi lfy ko?”.
Kanta ta kuma gyaɗawa tare da cewa.
“Eh nayi mishi”.
A fakaice ya ɗan kalli Juwairiyya dake rugume da yarsu karamar, cikin sanyi yace.
“Kukan bashi da wani amfani, muyi ta mishi addu’a, in sha Allah dukkan tsanani yana tare da sauƙi.
Ina roƙon Ubangijina mahaliccina a cikin dukkan Ayyukana, daya aramin rai da lfy, kada ya ɗauki raina ko na ɗaya daga, cikinmu, har sai ya nuna mana lfyar ya Jafar, ya faɗa mana abinda ya maidashi haka a dare ɗaya, nasani shine ɗaya rak yasan meya faru, a dare mai duhu da muni na rayuwarmu”.
Cikin sanyi tasa tafin hannunta ta share hawayenta.
Shi kuwa Sheykh, wucewa yayi da Ya Jafar ɗin har cikin ɗakinshi,
bisa gado ya zaunar dashi, kana yacewa Juwairiyya dake biye dasu a baya.
“Yasha mgninshi ne?”.
Miƙo mishi gorar ruwa da magungunan tayi tare da cewa.
“Yaƙi sha, dan daren jiya kwana yayi, baiyi bacciba,
Jalal nan abin tausayi, ko nanda can bai isa ya fitaba,
sai ya bishi,
Kullum sai Jalal yayi kuka”.
Wasu tafasassun hawaye ne suka cika masa ido,
A duniya shi baya son yaga ko yaji na miji na kuka, domin shi ya sani, duk abinda kaga yasa na miji kuka to abun ya tsananta musamman maza irin Jalal yasan ba ƙaramin raunine zaisa Jalal zubda hawayeba.
Shiyasa, shi kukan mace bai taɓa damunshi ba a zuciyarshi, domin mutane sunce in kaga mace na kuka to kayi dariya kafin ka tambayi meya sata kukan. In kuma kaga namiji na kuka to kaima ka fara kukan kafin ka tambayeshi meya sashi kuka.
Shiyasa shi kukan mace, bai shiga ranshi, sabida yanaga mata sun iya kukan munafurci da kukan gulma dana ha’inci da yaudara,
shiyasa in yaga mace na kuka haushinta yakeji a ransa.

Maganin ya bashi sannan ya kontar dashi kafin ya wuce, ya koma sashinsa.

Yana shiga, falon, ya samu, Haroon ma zaune, shida Jakadiyarsu,
tana ganinshi ta faɗaɗa fara’arta cikin kula da so mai zurfi tace.
“Farin gani, Garkuwa, Sheykh, Limamin Masallacin Moddibo Joɗa Jikan sarki mai hatimin sarauta.”
Gefen Haroon ya zauna tare da rumtse idonshi cikin nitsuwarshi yace.
“Ummi ki bari mana, babu wani sarkifa sai Allah, Ummi nace ki dena min irin waɗannan zantukan masu sa kan ɗan adam girma”.
Murmushi mai cike da tarin so, sabida ita dai jinshi take tamkar ɗan da raina a cikinta ta kuma haifeshi,
Koda yake hakan baya rasa nasaba, da cewar itace jakadiya gareshi tun randa aka haishi bacci kawai ke haɗashi da Mamanshi. Sai dai takanzo inda suke su sashi a tsakiya sunai mishi wasa da kallo mai cike daso.”
Ganin tayi kasake tana kallonshi ne ya sashi ɗan gyara zama, cikin girmamawa yace.
“Ina kwana Ummi, ya su Jalal?”.
Murmushi ta kumayi tare da cewa.
“Lfy lau Alhamdulillah, Jalal ya zama mazaunin gida, tunda ka tafi sabida, duk inda yaje , Jafar zai bishi,
sai dai kuma abokanshi masu shigar banza har gida suke biyoshi,
wani sa’in kwana kiɗe-kiɗe da rawa sukeyi a sashinsu, suna shan sigari.
Wasu lokutan dole, Jamil yake gudowa ya bar musu can yazo wurina yake kwana, ko ya shigo nan wurinka”.
Kanshi ya ɗan maida baya, a hankali yace.
“Ummi Jamil da mata?”.
Kai ta ɗan kauda kana a hankali tace.
“Tafiyar bata sauya zaniba, kwanaki uku da suka wuce wata tazo daga, Kano wai ita ƙawarshi ce, kwananta biyu, a sashin Juwairiyya, da Abbanku ya samu lbrine ya korata”.
Cikin sanyi yace.
“Ummi waya gayawa Abba?”.
Kai ta jujjuya tare da cewa.
“Allahu alamu, yadai ji har yace zai kori Jamil ya bar mishi gidanshi, to da yake Jafar yana wojen ne, sai ya riƙe hannun Jamil yayi ta kuka, hakane yasa ya barshi, Mamanku kuwa kuka tayi- tayi”.
Wani irin zazzafan numfashi ya fesar kana, ya juyo ya kalli Haroon a hankali ya kuma kalli, Jakadiyarsu, cikin sanyi yace.
“Basaji Ummi suna samin tunani a raina, ga wannan kuma shima ƙato dashi, sai ya ruggumi waya yayi ta chatting ko waya Da waccar yar mitsitsiyar yarinya Jannart ɗin.
Da asuba nayi ta tadashi yafi sau uku baya tashi, sabida bai bacci da wuriba, gashi ko cikekken jam’i bai samuba”.
Ido Haroon ya lumshe tare da cewa.
“Jiya dai ba chatting ko waya da Jannart bane, ya hanani baccin da yasani makara, Ummi ƙarshen darefa muka iso sabida ya sani dole sai mun taho nan.”
Murmushi Ummi tayi kana tace.
“To Haroona ka kiyaye batun tsaida salla kan lokacin ta, kaji ko?.”
Hararan Sheykh yayi tare da cewa.
“To Ummi”.
Ita kuwa Jakadiyarsu cikin muryar kula tace.
“Haroona yaushene bikin naku kam?”.
Kanshi ya ɗan shafa kana yace.
“Uhum Ummi saura watanni bakwai in Allah ya yarda, Ni dai zanyi aure in bar babban tuzurun”.
Bai kulashiba saima tashi yayi ya nufi bedroom.
Ita kuwa Jakadiyarsu cikin yin ƙasa da murya tace.
“Yauwa ya dai-dai ta da Jazrah ko?”.
Baki ya ɗan turo tare da cewa.
“Uhum Ummi gudowafa yayi, kuma wlh in ba dagewa kukayiba, wannan bauɗeɗɗen ɗan naku, ustazu bazaiyi aureba, mutun duk yadda akayi dashi sai ya kauce”.
Kai ta ɗan juya ta kalli ƙofar ɗakin daya shigan,
cikin yin ƙasa da murya tace.
“Uhum ga zahiri ko mgnar aure akayi sai ya bar wurin.”
Haka sukayi ta hira da yake akwai sabo tsakaninta dashi.

A sashin Hajia Mama kuwa, ita da kanta da kuma, Batul suka shiga kitchin sai kuma yardaddun hadimanta mutun biyu.
Breakfast mai kyau suka, haɗawa Sheykh.

Yayinda Aunty Juwairiyya ma ta shiga kitchin da kanta, ta haɗa mishi breakfast.

Jakadiyarsu kuwa da Jamil da Jalal da Affan Haroon suna falon sunata hirarsu.

A tare hadiman Mama dana Juwairiyya suka kawo, abin kari.
Suna fita ba da ɗewa, hadiman Gimbiya Aminatu kakarsu kenan.
Suka shigo suma da abun kari.

Suka jera komai kan babban dinning table dake dinning area’n dake falon.
Bayan sun fitane.

Suna cikin hira, sarƙin ƙofa, ya shigo, ya shaida musu, ga saƙo an kuma kawowa.
Jamil ne ya bada daman a shigo.
Nan ya juya ya fita,
jim kaɗan, aka turo ƙofar.

Cikin mamaki suka zuwa ƙofar ido.
Ganin M….!

 

*Wannan shafin nakine ke ɗaya MRS SARDAUNA, Sheykh yana godiya da soyayyarki gareshi. Domin duk masoyanshi bayanki sunka biyo*

 

 

 

By
*GARKUWAR FULANI*
By

️連老

*GARKUWA*

No comments