Breaking News

Garkuwa 5

PAGE 5

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

️連老

 


*LITTAFIN GARKUWA na kuɗine ga masu buƙatar biyan kuɗin samun damar karantawa al’ummar Niger da kewaye ga number da zakuyiwa mgn +22799460151 biya ɗari uku, ko dubunki ɗaya kacal un saki a group. Gareku mutanena mutanen ƙasata in kina buƙatar GARKUWA ga hankaɗo min ɗari uku kacal! ko dubu ɗaya rak! Ta asusuna na Jaiz bank, 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyan ki ta number ta 09097853276. Mutanen Ayyah SP Group bana son KATI. Kuma al’ummar 300 in ba dole ba yaseen bana son KATI, to amman in babu yadda zakiyi, nasan akwai irina ƴan ƙauye, ba POS. Kuma kuna son karantawa, to hankaɗo katin mtn ɗinki na darinki uku kisha karatu. Allah ya nuna mana ƙarshensa lfy kamar yadda ya nuna mana forkonsa lfy. ALLAH ya bamu haƙurin zama da juna*

“`Fans 1&2 sarakan surutu, Ina gaidaku ina ji daku har cikin ƙoƙon raina. SP Group, inai muku jinjina dubu-dubu.Fans 3
Allah ya rayamu ku cika maƙil. Group ɗin kurame kuma ina sane duku ina kuma jin daɗin nitsuwarku ba surutu. i love all my fan’s irin lodi-lodin nan mafa“`

“`Gyaran amare uwar gidaye masu jego da masu tada komaɗa da sabunta dararen satin forko na amarci. Ku garzayo gani gareku da tsaraba kamarsu, tsumin Tsartai, sa buzu kuwa, garin babambaɗe, garin maɗi mai maɗemaɗin ni’imomi, bunbar ke ɗaya, gumbar Mali mai taken kolli mai sheƙi sai dai gsky ita tanada tsada, gumbar Uku csrmazaƙoi, gumbar haɗin inabi dabino kwakwa riɗi.
Akwai haɗin ilan waddi, duk ba fula tani in yaji ilan waddi uhumm, akwai garin Belɗam yel, akwai tsumin ta baje, akwai kwanon ƙasaitacciyar mace, akwai kirɓeɓɓen tsumin domin mutanen nesa, akwai mgnin sanyi Infection, akwai butar sirri mai. abubuwan dai da yawa, gani ya kori ji, in kina buƙata kiyi min mgn ta wannan number 09097853276 kada ki kira dan ban fiye daga kiraba, gwara kimin mgn ta whatsapp in kinga bana kusa Turo min text message ta in-box“`

A hankali ya ɗan ɗago ƙwayan idanunshi ya kalleta.
Kanta a sunkuye hannunta biyu duka na kan mararta cikin wani, irin yanayi take wanda yake nuni da tana cikin wahala.
A hankali ya maimaita sunan cikin zuciyarshi.
“AYSHA ALIYU GARKUWA! To GARKUWAN ina? GARKUWAN meye?.”
A fili kuma kauda idonshi yayi daga kanta ya maida idanunshi kan tarin foldan dake gabanshi, wanda sunanta ke rubuce akan na samanshi yaja da yatsu biyu.

Shafin forko ya buɗe a folder kana, yasa hannu cikin wani ɗan abu mai kama da kofi wanda yake cike da biro masu kyau da tsadar gaske.

Tsiraran idanunshi ya lumshe sabida wani irin bugu da yakeji zuciyarshi nayi tun sanda ya hango yarinyar har zuwa yanzun nan da take gabanshi a zaune.
Rubuce-rubuce yayi a ciki irin nasu na Doctors masu kama da tafiyar wahainiya.
Kanshi ya kuma ɗagowa ya kalleta a fizge da gefen idonshi,
sunkuyar da kanshi yayi tare da cewa.
“Meke damunki?”.
Cikin shessheƙan wahala da son danne kukan da ke son kabce mata tace.
“Marata, da bayana”.
Kai ya ɗan jujjuya tare da kallon shekarunta dake rubuce a cikin folder din,
Yar shekara ashirin kuma da ƙorafin ciwon baya, cikin dakekken sauti yace.
“Yaushe ya fara miki ciwo?”.
Hannu tasa ta cikin niƙabin da yayiwa fuskarta ƙawanya ta share hwayenta a hankali tace.
“Shekara uku da suka wuce”.

“Meyasa bakije asibitiba tun lokacin?”. Ya tambayeta a daƙile.

“Ina zuwa asibiti duk sanda ya tashi”.

“Kamar yaushe da yaushe yake tashi?”. Ya jefo mata tambayar kamar yadda zuciyarshi ke harbawa da ƙarfin tsiya da kuma sauri-sauri,
Kai ta sunkuyar tare da cewa.
“Duk ƙarshen wata daga 21 zuwa 25”. Shiru yayi kamar bai jitaba sai wasu rubuce-rubucen ya kumayi.
Saida ya gama sannan ya tura mata folder ɗin gabanta.
Jikinta na rawa tasa hannu ta ɗauki folder ɗin, ta yunƙura zata tashine, ya basu damar samun kusanci da juna,
da sauri ya rumtse idanunshi sabida wani irin azabebben bugu da zuciyarshi keyi tamkar zaiyi tsalle ya faɗo woje,
cikin zuciyarshi yake maimaita.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun.”
A hankali ya buɗe kyawar kyawan idanunshi jin bugun zuciyarshin ya fara yin ƙasa-ƙasa, ido ya zubawa mata ganin ta juya tana tafiya,
wani abin al’ajabin a gareshi shine duk taku ɗaya da zatayi tana nesanta dashi sai yaji zuciyarshi na tsinkewa yana bada wani mugun bugun ras-ras, yayinda bugun tsinkewanta kuwa yaketa dai-dai-ta,
Cikin mamaki ya sunkiyar da kanshi yana kallon yadda takeyin taku, tana riƙe da mararta, taje gab bakin fofar fitane,
Taji wani irin murɗa da kartan da mararta ya farane yasa ta sakin wani sauti mai cike da wuya.
“Wayyoooooooo Allah na, Wayyo Ummeyna cikina”.
Da sauri nurse ɗin nan yayi kanta tare da cewa.
“Isah Allah rena joɗu”.
Ya ƙarishe mgnar da nuna mata kujerun farin ƙarfe dake gab da bakin ƙofar.
Bata da zaɓin daya wuce ta zauna ɗin, domin gaba ɗaya ƙafafuwan ta rawa sukeyi alamun bazasu iya ɗaukar nauyinta ba ga duhun daya rufe mata ido.
Sunkuyowa Nos ɗin yayi ya amshi folder kana yace.
“Zauna bari inje Pharmacy in amso miki magungunan da alluran sai ayi miki”.
Kai kawai ta iya gyaɗa mishi tare da bashi.

Har ya fita sai kuma ya dawo yace.
“Ok sir”. Jin Sheykh Jabeer yace mishi ya turo ta gaba
Da sauri ya fita.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, tasbihinshi yaketayi da yankan yatsunshi yake ƙidayar, sabida, suma yatsun su kasance cikin bautar Allah shiyasa yake ƙidayar amman ba don wai yasan adadin salati da hailala da istigifarin da yakeyiba, wannan ubangijine kawai masanin adadinsu.

Bayan fitar Nos ɗin da kamar 1 minute wata,
Kekyawar budurwa ta shigo, cikin yauƙi da ƙasaita, sai wani irin masifeffen ƙamshin da take zubawa.

Ƙarasowa tayi gaban table ɗin nashi ta zauna,
cikin yauƙi da korkosa tace.
“Barka da rana Al’ Sheykh”.
Ko inda take bai ɗaga ido ya kallaba, ya lura ya gane akwai wani abu tattere da yarinyar, dan mafi akasarin ranaku sai tazo, wai bata da lfy, kuma takan zo da ciwuka mabanbanta ne.
Sanin ba musulma bace yasashi ƙara tsuke fuskarsa tamkar zatayi aman wuta, a zafafe yace.
“Name”. Cikin yauƙi da son isar da aikin da aka bata tasa hannu ta jawo foldan ta dake sama tura mishi gabanshi tayi,
Cikin harshen hausa da tasan bai fiye son English language ba a rayuwarshi a hankali tace.
“Breast ɗina kemin ciwo, har bana iya sa bra.”
Sai kuma tayi ƙasa da mayafinta dake jikinta, hannu tasa kan zip ɗin gaban rigarta tana ƙoƙarin zugeshi ƙasa tare da cewa.
“Kalli Nipples ɗin sun….
Cikin tsananin firgita da tsoro, ta miƙe da azaban ƙarfi, jin yadda yasa hannunshi ya bugi table ɗin da azaban ƙarfi wani irin gigitaccen tsawa mai firgitarwa ya daka mata tare da cewa.
“Tashi, daga gabana”.
Karkar jikinta ke tsuma sabida kwarjinshi da tsoronshi sun daki zuciyarta da take cike da fajirci dama dan bata kallon fuskarshi ne ta iya faɗin waɗannan kalaman ma.
Dai-dai lokacin kuma, Nos ɗin nan ya shigo,
ganin yadda AYSHA ta gigice taketa karkarwa, alamun tana son ta miƙe kuma ta kasa tashi.

Shi kuwa Sheykh foldan ɗin Rabeca ya jawo wani rubutu yayi saman foldan ɗin kana ya tura matashi gabanta cikin zafi da tsauri ya nunata mata hanyar fita tare da cewa.
“Fice min daga Office daga yau in kina buƙatar ganin Dr kije gun Dr Ute, shi zakiyiwa duk sakarcinku na al’jihun baya. Ba niba, sannan daga nan ki wuce Zaria kije asibitin Shika domin ina zaton breast cancer kike dashi”.
Da sauri tasa hannu ta ɗauki foldan ɗin, gaba ɗaya jikinta na rawa, juyawa tayi ta fice tare da yin magana can ƙasa yadda bazai jitaba tace.
“Allah ya sauwaƙa Ni bani da breast cancer, mugun bakin kawai.”

Shi kuwa Sheykh Jabeer komawa yayi ya jingina da jikin kujerar lumshe idonshi yayi a ranshi yake haɗa kalaman da yaci karo dasu a safiyar yau.
Kakarshi tace mishi, aji mgnar Malam kada a duba aikinshi, ta jaddada mishi, wai yayi aure, kana wannan mayyar yarinyar da in tana kusa dashi zuciyarshi ke barazar fashewa, kuma tace mishi wai shine shugaban tuzuran ƙasar nan baki ɗaya.
Tabbas wannan shaidace na abinda ake faɗa a cikin gari a kansa kenan, yaji ya sani Sitti ma da take son suje saudia wai so take ya zaɓi matar aure a can, ga wannan kafurar da ya san turota akeyi ta tallata mishi kanta, don a samu cinikin jarida ya hauhawa ta hanyar buga kanun labarai cewa, Sheykh mazinacine ko kuma mata yakebi shine ya hanasa aure.
Jingina kanshi yayi da kujerar tare da mgn a zuciyarsa.
“Ya ilahi ya mujibadda’awati”.
Ta yayane ta inane wa zai gayawa cewa,
shifa yanada banbanci da sauran maza, ba kamar kowa yake ba, taya zai gaya musu ko zai samu a daina binshi da kalmar yayi aure, me zaiyi da mace ta yaya zai fahimtar dasu su barshi ya huta.

Wannan shine nazarin da yakeyi cikin zuciyarshi,

Ita kuwa Aysha ido ta tsurawa, ƙasan kujerar da yake zaune a kai tana kallon wani al’amari mai cike da ruɗarwa.
Ido ta rumtse sabida bazata iya jurar ganin wannan abun ba.

A hankali Nos ɗin nan ya matso gabanshi, magungunan da alluran daya amso ya miƙa mishi su.

Cikin sanyi yace.
“Sir ga magungunan”.
Kanshi ya ɗan tankwarar tare da cewa.
“Kira Dr Ruƙayya tazo ta mata alluran”.
A hankali yace.
“Sir na duba duk sun tashi, sabida babu kowa. A Reception ɗin, mune kadai muka rage”.
Kanshi ya jinjina, don shima yanzu zai tafi, sabida akwai gidajen likitocin a nan kusa koda shi ya tafi Dr Ruƙayya da Dr Ute suna nan cikin makarantar.
Ta gefen idonshi ya ɗan kalli Aysha daketa fama da ciwo,
Ganin Nos ɗin na haɗa allurar ne yasashi, fara tattara woyoyinsh dake bisa table ɗin.

Shi kuwa nos ɗin. Yana gama haɗa alluran ya nufi inda take, tare da cewa.
“Gyara in miki alluran”.
Cikin sanyi tace.
“To”. Yana isowa gabanta yace.
“Dole ai sai kin tashi tsaye, kinga doguwar rigace a jikinki kuma sai kin naɗeta”.
Ido ta ɗan zuba mishi ta cikin niƙabin tare da jujjuya kai a hankali tace.
“Um ummm”.
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
“Tashi mana sauri mukeyi lokacin sallah ya ƙara to”.
Shi dai Sheykh ido ya zubawa bayan Nos ɗin yayinda ita kuwa yake kallon gefenta, cikin bada umarni yace.
“Kuzo”.
Da sauri Nos ɗin ya juyo ya nufoshi,
hannu yasa ya amshi allurar,
kana ya ɗan kalleta a fakaice yace.
“Zo nan”.
A hankali ta taso cikin sanyi takeyin taku tana matsoshi.
A take kuma bugun zuciyarshin ya fara hauhawa yana komawa matakin sama.
Taku biyu tayi ana uku yaji ƙirjinshi ya bar tsinkewar da yaketa yi ɗin, sai kuma bugun da yakeyi da sauri-saurin ne yaketa tsananta.

Taku takwas tayi ta iso tsakiyar Office ɗin, ido ya fara jujjuyawa kan table nashi yana mai jin wani masifeffen bugun zuciyarshin dayasashi hatsala cikin ɗan ɗaga murya yace.
“Ke da Allah kiyi sauri”.
Jin hakane yasa ta kara saurinta, ai kuwa da sauri ya dafe ƙirjinshi lokacin da ta iso gab dashi, cikin ranshi ya kuma cewa.
“Hasbunallahiwani’imanwakil”.
A zahiri kuwa, da kai ya nuna mata ta kuma matsowa, ba musu ta matso,
yatsarshi ya jujjuya mata alamun ta juya mishi baya,
still babu musu ta juya, a hankali ya murza kujerar da yake kanta, ya juyo ya fuskanci bayanta, dai-dai saman mazaunanta ta sama ta ɗan gefe kaɗan, ya saita, tsinin bakin allurar, cikin iyawa da gwarewa dan salonshi ne baya taɓa yarda ya kalli fatar jikin wanda zaiyiwa alluran ta saman tufafinka yake zira allurar, shiru tayi tana jin yadda, allurar ya ratsa dogon rigar jikinta ya bada sautin tub alamun ya huda rugar, a hankali ta kuma jin ya huda, dogon wondon jikinta tub, sai kuma taji ya sauƙa kan pantien jikinta, daga nan taji ya ɗisa bakin allurar kan fatarta, rumtse idanunta tayi da azaban ƙarfi sabida, wani zafi da taji yana ratsata, bawai tana tsoron Allurar bane, sai dai hannunshi yanada masifar zafine,
kana shina ruwan alluran irin mai, mai-mai ɗinanne kuma duk cikin allurai yafi zafi.
Da ƙarfi tace.
“Wach Allah na zafi-zaffi.”
Wani irin azaba taji lokacin daya fara cusa mata ruwan allurar a jikinta, babu zato babu sammani yaji tasa hannu damanta ta cabki hannunshi dake mata alluran hannunta na hagu kuwa yarfashi take tare dasa kuka da sauti tace.
“Wayyo Allah na, ka bari bana so zare Allurar nan zafi nakeji”.
Ta ƙarishe magar da zurma sakalin ihu”.
Bugawa da zuciyarshi keyi yana bada sautin dib dab dib dab dib dan shine ya kusan hallakashi lokacin data riko hannunshi, da sauri ya tura mata ruwan kana ya zare Allurar da ƙarfi.
Sannan ya miƙe tsaye, sabida muddin yana kusa da ita babu makawa wata ƙil zuciyarshi zata faso ƙirjinshi ta fito woje.
Wani dogon tsaki yaja tare da juyawa ya bi gefen Nos ɗin ya fice.

Itama da sauri tabi bayanshi bayan tasa hannu ta amshi ledan magungunan.

Shi kuwa da sauri yake tafiya sabid iya yedda yake nesanta da ita iya yadda kirjinshi ke dai-dai ta bugawa, sai kuma tsinƙewa da zuciyarshi keyi babu ƙaƙƙautawa.

Ita kuwa AYSHA da sauri ta nufi sashin makwancin ɗaliban Hostel dake cikin makarantar sabida ta fara jiyo alamun bakonta ya iso.

Baba Ado kuwa drevernshi yana hangoshi ya tashi ya buɗe mishi marfin motar, yana zuwa, ya shiga, maida kofar Baba Ado yayi ya rufe sannan ya shiga yaja motar suka fice daga harabar asibitin.

Ita kuwa Aysha tana shiga Side ɗinsu ita da Rafi’a, ta samu Rafi’a bata falo da alamun tana kitchen nasu, dan tajiyo ƙamshi alamun tana ɗan dafa musu abinda zasuci ne.
Kai tsaye bathroom ta wuce, tabbas kuwa baƙon ya iso, dan haka ta nitsu ta gyara jikinta, bayan ta gama ne ta miƙe a hankali ta kwance niƙabin tare da fara zare dukkan kayan jikinta dan yin wonka,
Aysha farar ba fullatanace irin farare ƙal-ƙal ɗin nance, gashin kanta kuwa mai tarin yawa da tsawone baƙine sit mai sheƙi, yanada cika,
jikinta ɗan fiyau, sai dai tanada welcome and bey bey masu girma da cika, cikinta kamar babu hanji a ciki ɗan fiyau dashi, breast ɗinta tirtsa-tirtsane masu cika tab-tab kuma irin mai gindin tasa ɗinnan wanda da alamun ba masu zubewa bane, domin suna nan cas dasu, kamar zasu tsone idon mai gani, tanada tsukekken ƙugu da kyawawan mazaunai, sawonta dai-dai musali baza’ace mata doguwa ba sam, kuma baza’a ce mata gajera sosaiba in tana kusa da dogo dai za’a iya kiranta da gajera.

Fuskarta kekyawa ce irin kyan da babu namijin da zai gani ya cire ido, hancinta dogo har kan ɗan ƙaramin bakinta mai jajayen tausasan laɓɓa idonta manyane sai dai ba ƙattiba, zirin idonta wurinda akesa kolli jane mai kyau, shiyasa yake ƙara baiyana farin idonta bakin ciki kuwa bakine sitik sai dai ɗan ƙaramin ɗigon cikin bakin shi kuma ruwan ƙasane wanda yakeda sirri namu samman.
Gashin idonta zara-zarane, gashin girarta kuwa irin mai W ɗin nanne kamar na Kajol, bi ma’ana yana haɗe bisa karan hancinta,
Tanada fararen haƙora masu kyau suna jere reras dasu tanada dimple ɗinta mai ɗan karen kyau. Idanunta kuma ko yaushe kamar maijin bacci suke.

Wonka tayi kana tayi al’wala dan ko bata salla bata zama babu al’wala.

Tana fitowa ta kimtsa jikinta kana ta zura tattausan doguwar riga.

Tana kokarin fitowa falo Rafi’a na ƙoƙarin shigowa da sauri Rafi’a ta zaro ido tare da cewa.
“Yaushe kika dawo?”.
Hararanta ta ɗanyi tare da cewa.
“Ba dai kin gudo kin dawo kin barni ni ɗaya ba”.
Cikin tausayawa Rafi’a tace.
“La wlh yanzu nake ƙoƙarin komawa, na dawone in ɗan dafa mana abinda zamuci in mun dawo, sabida naga rabonki da abinci tun jiya, shiyasa kina shiga Office ɗin Dr na dawo”.
Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa kana tace.
“Na dawo a guje fa, wannan Sheykh ɗin hannunsa zafi kamar allurar mashi yakewa mutun”.
Zaro ido na mamaki Rafi’a tayi tare da cewa.
“Shida kanshi ya miki?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh”.
Cikin taɓe baki tace.
“Lallai yau kin tashi da ƙafar dama, gashi kuwa naga har kin worke”.
Wucewa sukayi zuwa tsakiyar falon, cikin sauƙe numfashin Aysha tace.
“Ba doleba yadda yake tura ruwan alluranshi nan kamar mai tura mai a mota, kuma ina dawowa nasha mgni, sannan abin ya iso, kinsan dama wuyar kafin ya isone”.
Dariya Rafi’a tayi tare da cewa.
“Kinji allurar manyan likitocin da duniya keji dasu dai”.
Uhum kawai tace sannan suka fara cin abinci, sunaci suna hira.

Cikin hirar tasu ne Rafi’a tace.
“Anjima da yammafa jirginmu zai tashi”.
Da sauri Aysha tace.
“Haba dai Rafi’a dan Allah ki bar zuwa hutunnan mana ki bari mu zauna, wallahi in kin tafi nima dole in tafi kuma ke kin san matsalar da nake da ita a gida ko Mamey ma da mukayi waya dazu cemin tayi kar in koma hutu Rugarmu, in zauna a makaranta”.
Cikin sanyi Rafi’a tace,
“Wallahi nayi kewar gidane Aysha, shekara guda kenan banje gidaba fa”.
Cikin sanyi Aysha tace.
“Haka ne kam ba, matsala, ai hutun sati ukune, kina tafiya yau nima gobe zan shirya zan koma Rugarmu”.
a haka sukaci gaba da hira suna cin abinci.

Ƙarfe huɗu dai-dai na yamma jirginsu Rafi’a ya tashi daga Ɓadamaya international airport, zuwa Farazan state.

Ita kuwa Aysha taci gaba da shirinta ba tare da ta gaya mutanen gida cewa zata dawo ba.
Kaya kaɗan ta ɗiba dan tanada kaya a gida, system ɗinta da wayarta da kuma kaya kala biyu kawai ta ɗauka, sai yan ƙananun abubuwan, ta da tayi nufin sai gobe zata koma.
Amman ina tafiyar Rafi’a yasa taji bazata iya zaman kaɗaicinba, dan haka huɗu da rabi, ɗaya daga cikin motocin dake maida ɗalibanda in gidajensu na kusane ya ɗauke ta.

Kai tsaye garin Shikan suka nufa.
Tafiyar ba wata mai nisa bace daga cikin birnin Joɗa zuwa Shikan, cikin mitina kaɗan suka isa,
Ƙarfe biyara da miti biyar suka isa.
Cikin Shikan a nan tasa drever ya tsaya ta sayi Junainah sweet.

Biyar da mintuna goma dai-dai suka isa kwanar mashigar Rukarsu Rugar Bani.

Cikin tsoron kada Ba’ana yaga wani yazo ya sauketa ya masa rashin mutunci, tace.
Ya sauketa a nan ba musu ya sauketa dan ai inda sabo ya saba.

Tana fita taja jakarta, ta rataya kana ta gyara tarhan da tayiwa kanta.
Shi kuma ya juya ya tafi.

A hankali ta zubawa yankin garin nasu ido, ko ina yayi kore shar, yabanya da ni’imar damina ta wadaci ko ina, wata iriyar sassanyar iska mai daɗin ke ratsa mata jiki da zuciya.

Ajiyan zuciya ta sauƙe a hankali tare da lumshe idanunta kana ta buɗe hannayenta cikin begen gida tace.
“Rayuwar ƙauye mu akwai daɗeeee”.
Ido ta buɗe tana kallon tako ina makiyayen rugarsune suketa dawowa daga kiwo,
Dabbobi saffan-saffan sunata dawowa,
garin yayi lum ga wani hadari mai ƙarfi daya keto, daga ƙasan dutsen da yayiwa Kyauyen ko ince Rugar Bani ƙawanya, a hankali take taku tana bin kan faffaɗan hanyan da makiyayan sukayishi bi ma’ana burtali kenan.

Taku take yayinda gefen hagunta wutsiyar kogin Shikan ne konce iya ganinta,
gefen dama kuwa Garden ɗinsune mai girma wanda yasa sanyin wurin yake yawaita, sauri ta ɗan farayi sabida akwai ƴar tazara kana kuma gashi magriba ta karato.

Tana cikin tafiya tana rataye da jakarta, kamar daga sama taga wulgawar inuwan mutun, cikin sauri ta zaro idonta ta kalli gefen hagu da damanta,
Ba kowa ganin hakane yasa taci gaba da tafiyarta cikin dakiya, taku uku tayi ana huɗu taji ansa hannu an amshi jakarta, da sauri ta juyo ta kalli gefen da aka amshi jakar.
Babu kowa a wurin kuma ga jakarta a rataye ita ɗaya tana binta suna tafiya a jere.
Cikin wani irin fargaba tsaro kaɗuwa da tsananin firgita ta….!

 

 

By
*GARKUWAR FULANI*

️連老

*GARKUWA*

No comments