Breaking News

Gidan Uncle 63

Yana fadin haka yayi baya luuuuuu cikin fitar hayyaci ya dafe saitin zuciyarsa data daukar masa wani mugun zafi yaci gaba da cewa “ya yama zaayi kuce na saki matata me tayimin dazan saketa bayan itace rayuwata Daddy koda Umaimah yankar jikina takeyi tanaci wlh bazan iya rabuwa da ita ba Daddy ku


duba lamarin nan kuyimin rai wlh Allah Daddy bansan sanda na rubuta mata takardar nan ba bansan meye ya faru dani daran jiya ba a dakin Bloody na kwanta amma dana tashi da safe saina ganni a dakin Salma wlh Daddy bansan komai akan takardar nan ba ku dabeni kuji qaina ku tausayamin kada ku rabani da matata”

 

Yana mgn muryarsa na kakkatsewa saboda tashin hankali kamashi Daddy yayi ya zaunar dashi a kujera ya dora masa Shuraif a cinyarsa yace “abinda ya faru ya riga ya faru ka saki Umaimah a daren jiya ta haihu a daren jiya ta tsarkaka daga iddarka ga danka nan kasa masa albarka dama rabonsa ne yasa ta koma gdanka nayi maka shisshigi nayi masa huduba da sunan marigayi babanku da fatan banyi laifi ba don kai yanzu hukuma ne sai lallashi”

 

Shigewa Daddy yayi daki ita kuma Hajiya taja qofar dakin da Umaimah take ciki ta datse da mukulli ta nufi kitchen tafi awa daya a kitchen din ta fito ta tarar dashi a zaune tayi mamakin ganin yanda ya rungume Ahmad Shuraif a qirjinsa numfashin sa yana sarqewa bata kobi takansu ba ta shige dakin hakan ya bashi damar miqewa yana hada hanya ya nufi cikin dakin ya tsaya a bakin qofar ya zubawa Umaimah manyan idanunsa da suka kada sukayi jawur tana kwance nannade da blanket amma yana jiyo shassheqar kukanta daqyar ya iya jan qafarsa ya matsa ya zauna a gefen gadon yana jiyo sautin muryarta tana maimata kalmar innanillahi wa Innah ilaihir raji’un hanu yasa ya janye bargon data rufa dashi ta dago da sauri suka hada ido tayi saurin kawar da nata yakai hanunsa zai ruqo nata tayi saurin make hanunsa tace “kada ka tabani Hameed na haramta gareka har abada insha Allahu sai Allah ya sakamin wannan baqin cikin daka qunsamin Hameed nayi danasanin saninka a rayuwata bantabajin tsanarka da tsanar zuri’ar dake tsakanina dakai ba sai dama ashe haka so yake meyasa ka cusamin sonka da tausayinka bayan kasan bazaka rayu dani ba Allah ya isa tsakanina dakai Hameed kuma wlh azeem idan baka daina bibiyar rayuwata ba zan gudu ku nemeni ku rasa kowa ma ya huta”

 

Fitowar Hajiya ne yasata tayi shiru da kukan da takeyi ganin a zaune yayi mugun qonawa Hajiya rai ta nunashi da hannu tace “tashi ka fita daga dakinnan” dagowa yayi yace “amma Hajiya ya kamata ku tsaya ku fahimceni waini meyasa kullum ni me laifine bakwa yimin uzuri Hajiya kada idonki ya rufe kema kamar yanda na bloody ya rufe take caccakamin maganganu masu ciwo son ranta kuyimin adalci kafin yanke hukunci naji ni me laifine amma ku tsaya kuyi tunani da hankalina zan saki Umaimah har saki biyu wlh Hajiya ko maqiyina yasan inayiwa bloody son da bazan taba yiwa wata mace ba a duniya bazan iya rabuwa da itaba itace rayuwata Hajiya itace farin cikina”

 

Wani murmushi Hajiya tayi me ciwo itafa ta fara tantamar hankalin dan nata saboda kalaman gaba daya babu hankali a cikinsu dauke yaron tayi daga jikinsa ta kama hanunsa tace “miqe ka tafi gdanka safiya ce yanzu matarka tanacan tana jiranka ka cika mata burinta tayi nasara ta rabaka da matarka me qaunarka domin Allah ga gidannan ku zauna ku kadai” tana fadin haka ta turashi waje ta rufe qofar.

 

Durqushewa yayi jikin qofar yana kiran sunan Umaimah sai yanzu yaji wasu zafafan hawaye sun zubo masa ya dade a gurin ganin babu wanda zai fito daga dakin yasashi miqewa jiri na dibansa ya fita ya fada motarsa yaci gaba da kukansa yana buga kansa da sitiyarin motar jin abin yake kamar almara wai shine ya saki Umaimah saki har biyu to me tayi masa meye ya hadasu yaushe ma yayi sakin kuma yaushe ya rubutashi kai ina bazai taba yarda ba wannan gonarsa akeson shiga ayi masa barna.

 

Daqyar ya iyajan motar ya nufi gdan abokinsa Yusuf dake asabar ce yana zuwa ya tarar dashi tsaye tare da megadi mamakine ya cika Yusuf saboda rabonsa da Hameed tun lkcn daya fada masa zai auri Salmah ya fito ya nuna masa bai amince ba so ko waya basayi kamar aikin asiri ya daina kulasa ko wayarsa ya daina dagawa.
Takawa Yusuf yayi har motar ya bude ya shiga yace “yadai mutumin yau amintakar ce ta motsa asirin ya sakeka kenan…”hadiye mgnr yayi ganin yanda jikinsa yake bari haqoransa suna haduwa ya damqi hanun Yusuf yace “Yusuf wai su Daddy ne sukace wai nine na saki Umaimah da hanuna jiya da daddare har saki biyu yanzu shikanan bloodyna ta haramta gareni….”

 

A tsorace Yusuf ya dago yace “kamar ya wai akwai wanda ya isa yace ka saki matarka idan baka saketa bane?” Cikin fitar hayyaci yana qara dafe qahon zuciyarsa yace “ru…rubutu nane a jikin takardar amma wlh tallahi bansan yaushe na rubuta ba Yusuf nasani kai zaka gasqatani wlh inason matata bazan taba iya rubuta mata saki har biyu ba yama zaayi na saki Umaimah har saki biyu bayan nasan rabuwa ce ta qarsh….”

 

Bai iya qarasa mgnr ba saboda numfashinsa da ya fara sarqewa ya fara kokawa dashi tare da danna qirjinsa da sauri yace “kaini gda Yusuf maxa kaini gdana na mutu a dakin Umaimah Yusuf mutuwa zanyi….”

 

Yana fadin haka ya fara kakarin amai kafin kace meye wannan ya balle murfin motar ya fita ya durqushe a qasa ya fara sheqa aman jini tashin hankalin da Yusuf ya shiga ba kadan bane ya fito ya rirriqeshi yana jijjigashi yana cewa “dama saida na fada maka kada ka auri Salma bakai takeso ba farin cikinka takeson rabaka dashi kaqi ji yanzu ga irinta nan ta rabaka da matar da kakeso kuma Kai dama ba cikakkiyar lafiya ba idan ka mutu ai kowa ma ya huta saki kuma ya saku tunda harka ambata sunan Umaimah a takardar kuma ka dawo hayyacinka ka gani da idanunka Hameed da ace bayan kayi sakin baka dawo hayyacinka ba har kowa ya fahimci baa cikin hayyacinka kayi sakin ba da kana da damar dawo da matarka saboda babu alqalami akanka lkcn da baka cikin hayyacinka amma dawowarka cikin hayyacinka da wuri da kuma karbar takardar ka duba shine ya tabbatar da sakin Hameed Umaimah ta saku kuma ta haramta gareka harsai taje ta auri wani mijin yayi mu’amala ta aure da ita tukunna ta halatta gareka….”

 

Duk da azabar da yakeji a qirjinsa hakan bai hanashi daga masa hanu cikin azababban kishi ba yace “wlh aa ne babu namijin dazai shiga jikin Umaimah saidai dukkanmu mu mutu babu aure ka kaini gdana nace kada na mutu anan…..” Yana mgnr yana qara qanqame qirjinsa kamashi yayi ya taimaka masa suka shiga motar yaja suka fita ya juyo yace “amma da asibiti muka fara zuwa” daga masa hanu yayi yace “bazani ba gda nakeson zuwa nafiso na mutu na huta meye amfanin rayuwata babu Umaimah” bai sake masa mgn ba saboda yasan tunda ya musa to bazaiyi ba horn yayi a qofar gdan suka shiga ya dauki biro da takarda ya rubuta rubutu kamar haka.

 

“ _Qaddarar ki rabani da farin cikina ya hadani da baqar ashana irinki wlh baki isa kici gaba da zama dani ba ni Hameed na saki matsiyaciyar mace irinki Salma saki uku”_

 

Yana gamawa ya bude motar ya fita da sauri a duqe yake tafiyar har ya shiga cikin bangaren Salma ya danna kai ya shiga qanwarta ya gani a parlourn baiko kula gaisuwar da takeyi masa ba ya shige dakinsa ya zare wata qatuwar belt a jikin wandonsa ya bude qofar ya nufi dakinta ya tarar da ita kwance ta baje gindi tanashan iska ya kawar dakansa tare da sanyawa dakin key ya fusgota daga gadon ya fara nada mata na jaki kamar mahaukaci tun tana ihu da dasasshiyar muryarta da kukan neman daukin daran jiya ya qarar da ita harta daina motsi bai daina jibgarta ba yayi mata fata² da jiki sannan ya cilla mata takardar yana haqi yace aje aci gaba da zawarci Hameed yafi qarfin ki la’anallahu”

 

Bude qofar yayi yana budewa yaga uwarta a parlourn ko kulata baiyi ba ya fice jiri na dibansa ya nufi inda Yusuf yake jiransa a mota amma kafin ya qarasa ya yanke jiki ya fadi da sauri Yusuf da megadi suka nufoshi suka rufar masa Yusuf na danna masa qirjinsa yana kiran sunansa wayarsa ya zaro a kidime ya kira layin Daddy bugu daya aka daga yace “Daddy Hameed ne bashi da lfy muna gdanshi ka Kira likita akwai matsala”
Yusuf yana aje wayar suka kinkimeshi suka nufi bangaren Umaimah dashi suka kwantar dashi a parlour sai gumi yake hadawa zuciyarsa na bugawa da qarfi baafi minti ashirin ba Daddy ya shigo shida Dr Saleem wata Allah ya fara yimasa sannan suka fita dashi zuwa asibiti suna zuwa aka shiga dashi aka fara bashi taimakon gaggawa wannan karon bai shiga commer ba amma baisan inda kansa yakeba…….

 

 

 

 

 

*UMMUH HAIRAN CE…✍*
[1/31, 2:24 PM] UMMUH HAIRAN CE…✍: *GU*

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

No comments