Breaking News

Kanwar Maza 27


Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*

 

Sosai suke girgiza mama, amma ko motsi ba ta yi, a gigice Abdallah ya É—ebo ruwa ya din ga shafa mata a fuskarta Usman ya É—auko mafici yana yi mata fifita.
Aliyu ya kalli Usman ya c “Usman wani ya je ya samo napep mu kaita asibiti da sauri”.

Usman ya ce “Ko nan da zaure ba zan iya fita gani nake komai zai iya faruwa kan na dawo, sai dai ko su Yasir”.

Yasir da yake riƙe da hannun mama ya ƙara ƙanƙame hannun, ya ƙi tashi yana kuka.

A hankali mama ta yi tari, ta fara motsawa tana Innalillahi wa Innalillahi raji’un. Babban fatanta Allah ya sa idan ta buÉ—e idanunta ace mata mafarki take yi.

Sai dai tana buÉ—e ido ta kalli fuskokin su Huzaifa, hakan ya tabbatar mata a zahiri ne, ruma an yi garkuwa da ita.

Sannu suka din ga jerwa mama, amma ta kasa amsa musu, a hankali ta ce “Ku kira babana, dan Allah ya juyo gida kar ya je, mu bar wa Allah komai”.

“Amma mama meyasa?”

“Kar yaje ya tayar musu da hankali ko shi ma wani abun ya same shi, zuwan nasa babu abin da zai Æ™ara ku kira mini shi a waya, ya dawo gida dan Allah”.

Jiki a sanyaye Abubakar ya janyo wayarsa a aljihunsa ya kira lambar Umar.

Mai sunan Baba na É—agawa Abubakar ya ce “Akhi mama ta ce ka dawo gida, bata yarda ka je ba?”

A hasale Umar ya ce “A kan me zaku gaya mata, kun san ba cikakkiyar lafiya ce da ita ba dan me za a gaya mata? Wannan ai ba yi ba ne, idan wani abu ya sameta fa?”

Shima Abubakar da zuciyarsa ke a kusa ya hayayyÆ™o masa “Kai saurara ni ka ke wa shouting? Da wanne zan ji ne? Har zuwa yaushe zamu cigaba da É“oye mata. zamu dawo mata da rumaisa ne idan bamu gaya mata ba? zaka din ga yi mini hayaniya kai kaÉ—ai kake cikin damuwar ne? Duk ta shiga damuwa ba mai cin abinci kowa baya walwala kuma an Æ™i sanar mata abin da ke faruwa, zuwa yaushe za a cigaba da É“oye mata, idan ka ga dama ka dawo idan ba ka ga dama ka je ka yi abin da ka ga dama”
Umar yayi wa ɗan uwansa uzuri, damuwa ce ta sanya ya sauke masa, dan Sadik ba dai haƙuri ba. Suna gama wayar Abubakar yayi cilli da wayar zai tashi mama ta riƙe shi.

Cikin tawakalli da Æ™arfin hali ta ce “Yi haÆ™uri, kar ka yi fushi dan Allah, ka lallaÉ“o mini shi ya dawo ka san halinsa”

Abubakar yayi ajiyar zuciya zai yi magana wayar mama ta fara ringing a É—aki, Yasir ya je ya É—auko, mai sunan Baba ne yake kira.
Mama ta karÉ“a da sauri ta kara a kunnenta ta ce “Babana dan Allah ka dawo gida” tayi maganar muryarta na rawa.

“Ki yi haÆ™uri mama, daga sallar asuba na wuce, ina Katsina yanzu haka na kusa Æ™arasawa ki yi haÆ™uri ba abin da za zan aikata, zan je wurin jami’an tsaro ne, ki kwantar da hankalinki in sha Allah za ta dawo lafiya “.

“To” kawai mama ta ce ta saki wayar, tana wata irin ajiyar zuciya, zuciyarta sai wani irin zafi take yi mata, amma idonta ya bushe babu hawaye.

Su ruma kuwa yau kwana na huÉ—u kenan suna hannun ‘yan bindiga, ba wanka ba wanki, ga azabar yunwa ruma ba ta iya cin abin da ake bata, ruwan nan É—aya idan an basu da shi take sha idan tana jin fitsari ta yi. Duk azabar kashi irin na ruma, ta matse abin ta ba ta yi.
Tun da ruma take ba ta taɓa kawo tsintar kanta a irin wannan halin ba.
Ga duka da wasu lokutan ake yi wa wasu, duk da ita babu wanda ya taÉ“a dukanta, amma ana dukan wasu ciki har da mata, ‘yan bindiga su dake su su taka su da Æ™afa.
Wani tarihi ruma ta tuna da aka taɓa basu a islamiyya, a rayuwarta tana son malaman da suke basu tarihi, dan duk abin da take zata nutsu ta saurara.
Akwai ranar da malamin yayi musu tarihin Annabi yunus da kifi ya haÉ—iye shi, ya karanta *La’ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin*
Har ruma ta ce “Kai malam amma kifin da ya haÉ—iye annabi yunus, dai yayi girman duniyar nan?”

Malamin ya yi murmushi ya ce “Meyasa ki ka ce haka? Kin san girman duniya kuwa?”

“To ai malam kifin da inuwa mai kifi yake sayarwa, da wanda ake talla ko É—an tsako ba zasu iya haÉ—iya ba, amma na ji ka ce kifi ya haÉ—iye mutum”

“Kifi ne dai babba ruma, amma ba kamar girman duniya ba, kuma ba a gaya mana girman kifin ba a Alqur’ani, abin da nake son ki riÆ™e yanzu shi ne, falalar wannan addu’a da annabi yunus Alaihissalam ya karanta, a duk lokacin da kika shiga wani mawuyacin hali, ko ki ka shiga hannun wasu azzalumai to kema ki karanta Addu’ar da Annabi yunus Alaihissalam ya karanta *La’ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin*”

“To malam, in Allah ya yarda zan din ga yi, to wace addu’a zan yi idan na yi wa mama laifi kar ta yi mini faÉ—a ko ta saka mai sunan Baba ya sakani kama kunne?” Jik tambayar da ta yi, ya sanya ‘yan ajin suka kwashe da dariya.

“A’a ai dole idan ki ka yi laifi ayi miki faÉ—a ko a hukunta ki, amma a duk lokacin da kike fargabar haÉ—uwa da wani, mugu ko maÆ™iyi sai ki karanta *Allahumma inni as’aluka min nuhurihim, wa’auzubika min shuriruhim*”

Ko da ruma ta tuna da wannan tarihin da malaminsu ya yi musu sai ta fara nanata “*La’ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin*”

Ihun wata mata ne ya sanya ruma waiwayawa taga ko dukan na ta ake, amma taga É—aya daga cikin mutanen yana jan ta tana ihu, tana a taimaka mata. Babu wanda ya tanka mata mutumin yayi cikin dajin da ita.

ÆŠaya daga cikin ‘yan bindigar ya ce “Ai gara hakan, tun da ‘yar matsiyata ce ba za su biyan kuÉ—in da aka ce su karÉ“eta ba”.

Kusan awa biyu mutumin ya dawo ba tare da ita ba.

Ta ji wasu a kusa da ita suna magana Æ™asa-Æ™asa “Innalillahi, ita ma sun mata fyaÉ—e sun kasheta” Ruma ji tayi kamar ta tambayesu meye fyaÉ—e, tunowa tayi lokacin da take tambayar mama meye fyaÉ—e su Aliyu suka din ga hantararta.

A take ta fashe da kuka, saboda yadda take kewar gida, duk suka juyo suka kalleta.

“Ke meye haka?”

“Mama” ta faÉ—a cikin kuka.

“Yi mana shiru ko in taka ruwan cikinki”

“Wallahi ba zan yi shiru ba, wayyo Allah mama yaya Aliyu yaya usy dan Allah ku zo ku É—aukeni zan mutu, wayyo Allahna” kuka take sosai kamar wadda wani iftila’in ya afkawa.

Wata mata ce ta din ga rarrashin ruma tana bata haÆ™uri da Æ™yar ta yi shiru, ta cigaba da nanata addu’ar nan.

Mai sunan Baba kuwa yadda yaje ya tarar da gwaggo ne ya sanya jikinsa yin sanyi, ya tarar iya ma tana asibitin ita da mijinta, gwaggo sai kuka take ba ta ko cin abinci, likitoci na ta fama jininta ya sauka abu ya gagara, saboda yadda ta addabi kanta.
Tana ganin mai sunan Baba ta sake rushewa da kuka, “Dan girman Allah ku yi haÆ™uri, ku yafe mini umaru ban zaci abin zai kasance a haka ba, tsananin Æ™aunar da nake yi wa É—an uwana ce na mayar kanku, ban yi hakan dan baÆ™anta muku ba, son da nake wa ruma ya sanya na hanata, da na san haka za ta faru da ba zan ce ma azo da ita ba, ku yafe mini dan Allah” gaba É—aya suka fashe da kuka, har su iya da su Lawisa da aka sace ruma a gabansu.

Ganin yadda dattijuwar ke cikin tashin hankali ita da iyalanta ya sanya ya ji duk jikinsa yayi sanyi, idan ya ce zai É—aga musu hankali bai yi musu adalci ba, tun da suma ba da son ransu hakan ya faru ba.

Ya Æ™arasa ya zauna a gefen gadon gwaggo sannan ya ce “Ki daina kuka, ko dan saboda a samu jininki ya sauka, yanzu ya ake ciki an sanar da jami’an tsaro ne ko kuwa ya ake ciki?”

Dagaci ya ce “Ka san garin namu, jami’an tsaro ba su fiye bamu agaji ba, mu da su mutanen muke yin sulhu, duk abin da muka saka jami’an tsaro wata É“arnar suke yi mana, amma dai saboda ita rumaisan mun sanar da jami’an tsaro, amma sun ce mu jira abin da ‘yan bindigar suka ce sai a sanar musu, muna nan muna jira haryanzu dai ba su yi mana aike ba”.

Mai sunan Baba yayi shiru ya ma rasa abin da zai ce, Æ™arshe ya yanke shawarar a kai shi wurin ‘yan sandan domin ya ji meye abin yi.

ÆŠanlami ya É—auki mai sunan Baba suka tafi, sai dai daga Æ™auyen da aka sace su ruma zuwa wurin ‘yan sandan uwar tafiya ce mai zaman kanta, da ko menene zai samu ‘yan garin ba lallai su samu É—aukin jami’an tsaro.

Ganin girma da kwarjini da kuma ganin cewa Umar ba É—an garin bame ya sanya DPO garin tsayawa ya saurare shi.

“To É—an uwa idan zan baka shawara ka koma gida kawai ku yi addu’a, bin bayan mutanen nan aikin sojoji ne bana ‘yan sanda ba, mu mun yi iya namu Æ™oÆ™arin, sai dai mun bar sallahun idan sun yi wata magana a sanar mana, haryanzu dai ba su ce komai ba”

Shiru kawai mai sunan Baba yayi, ba zaka Æ™ara sanin lamarin tsaron Æ™asarmu ya taÉ“arÉ“are ba sai wani iftila’i ya afka maka.

Ba tare da samo wata mafita ba, mai sunan Baba ya kamo hanyar kano.

Gidansu ruma kuwa tamkar an yi mutuwa, ko magana mai sauti ba sa iya yi, tun da mama ta ɗan samu ƙwarin jikinta ta hau sallaya, canza alwala ce kawai take ɗagata, yunwa kuwa ko jinta ba ta yi.

Ba yadda ba su yi da mama ba a kan ta ci abinci, ta ce su ƙyaleta kawai.

Ko da ta ji sallamar mai sunan Baba, ji ta yi kamar zai ce mata ga ruma nan ya dawo mata da ita, amma ko da ya shiga ɗakinta ta kalleshi ta ganshi shikaɗai, sai ta sunkuyar da kanta ƙasa, ta ji zuciyarta ne neman karyewa.

Ya ƙarasa gaban mama ya zauna, su Abdallah duk suka zubo masa ido, amma ya rasa ta ina zai fara yi musu bayani.
Mama ta sake É—aga kai ta kalli ta mai sunan Baba, ya girgiza mata kai ya ce “A dage a cigaba da Addu’a kawai”

Wata irin wahalalliyar ajiyar zuciya mama ta sauke, ta sake sunkuyar da kanta ƙasa.

Huzaifa ya fashe da kuka, Yasir ma ya taya shi.

Cikin dakiya mai sunan Baba ya haÉ—e rai ya ce “Meye haka kamar wanda ba su je islamiyya ba, ba ku yi imani da Æ™addara bane? Yanzu kuka ne ya kamace ku ko kuma addu’a?” Haka ya din ga yi musu faÉ—a alhalin shima da zai samu space kukan zai yi. Ya tashi fuuu ya tafi É—akinsu, yana zuwa ya tarar da Abubakar a zaune yayi shiru ya lula duniyar tunani.

Mai sunan Baba ya zauna a kusa da shi, ya ce “Akhi na dawo?”

Banza yaya Abubakar ya yi masa bai kula shi ba.

“Na san na yi maka laifi, amma yakamata ka yi mini uzuri, ba a hayyacina nake ba, idan ka gama fushin sai mu yi magana” ya yinÆ™ura zai tashi Abubakar ya ce “Yaya ku ka yi da ka je, an samu labarinsu?”

“Babu wani labari mai daÉ—in ji, sai ma kayan takaici, ance mu saurara idan sun kiramu sun ce mana wani abu shikenan sai mu sanar”.

“Idan kuma ba su kira ba a haka zata cigaba da zama a hannunsu?”

“I have no idea” mai sunan Baba ya faÉ—a cikin damuwa.

“Innalillahi wa Innalillahi raji’un, Aki meye abin yi?”

“Addu’a” ya bashi amsa a taÆ™aice.

Dare ya tsala, wasu daga cikin al’umma sun kwanta suna hutawa, yayin da wasu daga cikin mutanen da aka yi garkuwa da iyalansu suke kwanan zaune, ciki har da mama da yaranta maza yayyen ruma gaba É—aya mama ta manta da wani abu wai bacci a wannan halin da take ciki, a zaune take tamkar an dasata tun tana iya lazimin da addu’a har ta kasa ta rasa abin da ma zata ja.
Zuciyarta sai zafi take mata, da tunanin a wani hali ruma take ciki.

Wurin baccin ruma ta kalla, da yanzu tana nan mama tana faman gyara mata kwanciya ko tashinta fitsari, da yanzu ta yi ɗai-ɗai sauro na cizonta mama tana mita tana sake gyarata, ko ta ƙaro fanka idan ta fuskanci zafi yayi mata yawa, ko ta kashe fanka ta lulluɓeta idan sanyi yayi yawa.

“Ruma ko a wani hali kike? Ko kina raye? Ko kin ci abinci? Ya in da ki ke kwance? Sanin gaibu sai Allah, ya rabbilarshil azim, dan girmanka Allah ka tsare mini ‘ya ta da sauran ‘ya’yan musulmi, Allah ka dawo mini da ita cikin aminci” ta Æ™arasa addu’ar kuka yana kufce mata, sai a lokacin ta É—an ji nutsuwa da ta samu hawayen idonta ya zuba.

ÆŠakin ‘yan mazan ma gaba É—aya idonsu biyu, wasu da Alqur’ani wasu a kan sallaya, wasu suna kuka, dan basu taÉ“a tsintar kansu a cikin mummunan tashin hankali kamar wannan ba.

Ruma ta yi rigingine a filin Allah, wani irin sanyi yana ratsata ga cikinta kamar ya haÉ—e da bayanta saboda azabar yunwar da take ji, ga Æ™aiÆ™ayi da jikinta yake mata saboda rashin wanka, ga wani irin sauro na bala’i da Æ™wari suna gasa mata cizo.

A hankali ta furta “Mama, mai sunan Baba” sai kuma ta yi shiru hawaye ya fara zirarowa ta gefen idonta.

Tana tsaka da tunanin, wurin yayi tsit, mutanen sai kewayasu suke yi da manyan bindigogi.

Wani irin sauti ruma ta din ga jiyowa na motoci ƙasa-ƙasa, daga bayan dutsen da ke nesa da su.

“Sha tara ga motocin smoke can suna aiki fa” cewar É—aya daga cikin ‘yan bindigar.

” ‘yan wahala ba, ni mamaki nake yadda suke iya fitar da sabgar nan ba wata matsala” É—ayan ya bashi amsa.

“Haba, sun gama sai ta komai nake gaya maka, babu wanda ya isa ya tare musu hanya, babban controller na Æ™asa ma fa nasu ne, kuma akwai na sa kason a ciki mu suka mayar ‘yan iska kawai”.

Sha tara ya ce “Aikuwa sai mu yi tawaye, ko dai su yi wani abu a kai ko mu bujure, haba ma’adanan nan fa da suke kwasa ba dan muna gyara musu aikin nan ba da ba zai yiwu ba, amma kura da shan bugu gardi da kwashe kuÉ—i”.

“Kai ni ba wannan ba ma, oga nake jira ya zo ayi wadda za ayi a san yadda za ayi da mutanen nan”

“Eh gobe zasu shigo ai”

Haka suka cigaba da hirarsu, amma kan ruma ya É—aure, wasu ma’adanai ake kwasa meye ma ma’adanan?

“Zan yi fitsari” ta faÉ—a cikin rawar murya”.

“Yi a nan” É—ayan ya bata amsa.

“Ina jin yunwa ma”

“Idan ki ka kuma magana sai na taka ruwan cikinki”

Guntun tsaki ruma ta yi, tayi juyi wani abu da ba ta san menene ba gasa mata cizo, wata uwar ƙara ta saki, ta miƙe tana kuka.

“Wai wannan wace irin iblishiyar yarinya ce meye kuma?”

“Wani abu ne ya cijeni” ta yi maganar a gigice tana soshe-soshe.

“Nemi wuri ki zauna ki rufewa mutane baki, ni wallahi da oga ya zo da na daÉ—e da harbe wannan shegiyar yarinyar da ba ta rasa matsala”.

“To ku mayar da ni in da kuka É—auko ni mana, meyasa zaku kawo ni nan” tayi maganar a sangarce

Hasketa É—ayan yayi da hasken fitila, ta saka hannu ta kare tana motsa baki, saukar wani abu ta ji a goshinta mai nauyin tsiya, daga haka ba ta sake sanin in da kanta yake ba.

Bayan sallar asuba, su Abdallah suka sanar da abin da yake faruwa a masallaci, tare da roÆ™on bayin Allah su taya su da addu’a, Allah ya fito da rumaisa cikin aminci da Æ™oshin lafiya.
Mutane da yawa sun kaÉ—u da jin abun da ya samu ruma, dan ruma ta mutane ce, da yawan mutane sun santa, kan gari ya gama haske unguwar su ta cika da labarin yin garkuwa da ruma.

Gari na gama yin haske aka din ga sintirin zuwa yi wa mama jaje, tare da addu’ar Allah ya bayyana ta.

Mama duk yadda ta so ta jure, ta kasa haka ta dinga share hawaye, masu cewa ta daina kuka kuwa kallonsu kawai take yi, gani take ba su san a cikin tashin hankalin da take ba ne.
Hatta daga islamiyya su ruma haka aka yi tawaga guda, suks zo yi wa mama jaje suka gabatar da Adduoi, tare da yi wa mama alÆ™awarin za su cigaba da addu’a da karatun Alqur’ani har zuwa lokacin da Allah zai bayyana rumaisa.

Rumaisa kuwa a hankali ta motsa, ta fara ƙoƙarin buɗe idonta, amma ta ji goshinta yana mata zafi, a hankali ta kai hannu goshin ta ji ya kumbura, ga busashshen jini ta shafo.
Cikin ƙarfin hali ta tashi zaune, sai dai wani irin jiri ne yake ɗaukarta, saboda azabar yunwa, ga zafin dukan da aka mata da bakin bindiga.

Wani narkeken mutum ta gani, yana zagaya su, yana ƙare musu kallo.

“Ke a ina aka É—aukko ki?” Yayi mata maganar cikin tsawa. Ba ta kai ga bashi amsa ba, ta ga mutumin da ta bawa gyaÉ—a a kasuwa.
Yayi saurin kawar da kansa da ga kallon ruma.

“Ke ya ina miki magana kin mini shiru?” Yayi maganar cikin muryarsa mara daÉ—in ji.

Gefe guda ta ja, ta tanƙwashe ƙafarta, tana jin yadda take jan numfashi da ƙyar.

A fusace ya saka hannu ya fizgo ruma, amma ta taƙarƙare iya ƙarfinta ta fizge hannunta ta ja da baya tana huci. Kallon kallo suka shiga yi, tsakanin shi da rumaisa.

YinÆ™urawa yayi zai maketa, mutumin nan ya shiga tsakaninsu, ya ce “Yi haÆ™uri, yarinya ce”

“Ban gane yarinya ba, bani bindiga kasheta zan yi”

Ya girgiza masa kai ya ce “A’a, da alama ubanta wani ne, za a samu kuÉ—i a hannunsu, ka bari mu karÉ“a sai a kasheta”.

“Ni bani da uba” tayi maganar cikin Æ™warin gwiwa.

“Ina magana kina saka baki? Zan Æ™yaleshi ya kashe ki” da Æ™yar ya shawo kan mutumin ya Æ™yale ruma.

Ya ɗauki wata leda ya jefa mata, buredi ne a ciki sai ruwan pure water. Tamkar ta shekara ba ta ci ba, haka ta dirarwa buredin nan, tana ci tana yinƙurin amai.

Tana zaune tana cin abincinta, tana kallon yadda ake karɓar lambobin waɗanda aka ɗauko su tare, ana cinikin nawa za a biya a karɓesu kamar wasu dealer kaya.

Mutumin nan dai na É—azu, ya zo kan ruma ya ce “Bani lambar babanki”.

“Dama ana zuwa kabari da waya?”ta tambayeshi.

“Kamar yaya?”

“Na gaya maka bani da uba ya mutu ai”

“Bani lambar wani É—an gidanku”

Rumaisa ta ce “Ka ga nifa gidanmu in dai kuÉ—i zaka ce musu su kawo, basu da shi,  sai dai ku yi mini abin da zaku yi mini”

Ya Æ™are mata kallo ya ce “Haka ki ka ce?”

“Eh”

Ya miÆ™e tsaye ya ce “Biyoni”.

No comments