Breaking News

Namijin Zuma 14

NAMIJIN ZUMA PAID PAGE14 *Wannan book na kudi ne.. 1k only 08101626484*

Ba bata lokaci suka isa garin Kano, daman already baban Noor ya kira abokinsa Alhaji sidi ya sanar dashi suna tafe, tin kafin su iso Alhaji sidin da kansa da dreva’s dinsa suka iso da motoci biyu, Daya dreva keja, dayan


kuma alhajin be da dreva dinsa , Alhaji sidin babban mutum ne, babban Dan kasuwa ne da akeji dashi a garin kano. jirginsu na sauka a airport ba bata lokaci suka shiga mota zuwa asibitin da Aeezad din yake, harda Alhaji sidin. Koda suka isa Asibitin suka tadda mutane cike packing spaces din asibitin kuwa tini ya cika makil da manyan motoci Na Alfarma, kama daga masu fada aji a kasa da manyan Yan kasuwa, tini Alhaji rabi’u da tawagarsa murna ta koma ciki, a fari da Yan ta’adan dasuka aika kashe Aeezad din suka dawo suka shaida masa sun kasheshi, nan suka hau party cikin murna Kai kace su ba barin duniyar zasuyi ba, bahaushe yace murnar mutuwa murna banza. Seda suka samu Labarin Aeezad na asibiti Nan farin ciki ya koma ciki, basu hkra ba, na n suka bazama shirya yadda zasuyi kulle-kullen daza a bishi har asibitin a karasashi Lahira,Aiko Yan ta’adan sunsha fada gun alhaji rabi’u, wanda for now tamkar zeyi hauka yake jinsa sbda bakin cikin Labarin dayaji na Aeezad na asibiti.

A bangaren su Nabeelah Kam koda suka iso asibitin Basu samu ganin Aeezad ba, an zuba matakan tsaro tako ina a asibitin,dakin da Aeezad din yake ciki kuwa, ba a barin kowa yashiga dakin da yake, Alhaji sunusi da Alhaji Abubakar dade manya-manyan kusoshi na kasa aka bari suka shiga suka gansa, Suma suna ganinsa ko 10mnt basuyiba suke fitowa waje, an basa tsaro tako ina,a kofar dakin da yake ciki Kam sojojine tsaitsaye da red eyes sun rirrike manyan bindigu sunfi rayuka ashirin, an riga an gane hari ake kawowa Aeezad din, shiyasa chief of army yasa aka cika kaf asibitin da matakan tsaro kama daga kan sojoji, zuwa kan police, sbda chief of army ya tabbatar in Koma suwaje ke farautar rayuwar Aeezad Sam bazasu dena ba har asibitin se sun biyosa da kullij sharri. Bakaramin bakin ciki nabeelah tashiga ba na rashin ganin Aeezad din gashi zuciyarta na cike da zillon son ganinsa,nan ta kara shiga wasu tunannikan. A haka nabeelah da Hafsat suka nufa masallacin sukayi sallolin Azahar da la’asar, suka dawo suka zazzauna inda kowa ke zaune, an shishshimfida manyan carpet tako ina, part din da aka kwantar da Aeezad dinma na manya ne, ashe in kaga ana maka wulakanci a asibitin gwamnati to tabbas baka da kudi ne. Hajiya rafi’ah se kallon nabeelah take tana Aiko mata da uwar harara, ganin yadda taga nabeelah a rude ba karamin haushi yabawa rafi’ah ba, a zuciyarta tace “Tsinanniya tsohuwar guzuma duk ta Wani rude kamar kanin ubanta…ko ita awa danwake hotel…” Hajiya rafi’ah se Jan kwafa kawai takeyi,. Sam na Nabeelah batasan tanayi ba, ita Hankalinta na can kan tunanin Aeezad ta rafka uban tagumi kamar wadda akawa mutuwa. Har akayi sallarh isha’i ana zazzaune a wajen dakin da Aeezad yake ana jiran farfad’owarsa Amma shiro kakeji se doctors kawai ke zirya cikin dakin da yake,hankalin nabeelah na kan shige da ficen da doctors keyi, duk wanda ka kallah a gurin Yana cikin Wani hali Na damuwa a kan Aeezad din,Amma ko mahaifin Daya haifi Aeezad din baze nunawa nabeelah damuwa ba duk ta kara firgicewa idanuwanta sun kank’ance kamar ba nata ba,. Se wuraren 10:pm Na’eema ta iso asibitin, tin hajiya rafi’ah na jirgi ta kira na’eema ta sanar mata abinda ke faruwa, hankalin na’eema ya tashi sosai har kuka tayi, ba shiri tase prvt ticket daga Egypt din zuwa garin Kano. “Wai Sannu da isowa dagani kinyi kuka harkin gaji,,,” cewar hajiya rafi’ah datayi maganar da karfi kowa yaji, ita a dole seta bayyana cewa yarta tashiga damuwa. Nan na’eema ta fashe da kuka me tsanani, hajiya rafi’ah ta jawota tashiga rarrashi, jama’arh dake gurin wasu suka shiga bata hakuri banda hajiya Maryam matar Alhaji Abubakar domin tini tasan wacece hajiya rafi’ah da yarta a fannin makirci. “Muje in rakaki kiga jikin mijinki, ko Hankalinki ze kwanta…”cewar hajiya rafi’ah , Nan ta mike hannunta cikin na yarta suka nufa dakin da Aeezad din yake, nabeelah ta zubo musu Ido ,ji takeyi kamar ta tashi ta bisu sbda itama tasamu tabbarrakin damar ganin Aeezad din,dukda tasan zatasha wulakanci Amma sam bazata damu da hakan ba in har zata samu ganinsa. “Aunty hafsat ko in bisu ne Nima insamu in gansa ko zanji dadih…” Cewar nabeelah datayi mgnr da disashashshiyar muryarta tamkar wadda tayi mura Nan ko tsabar kuka ne datasha ta koshi, duk yau ko ruwa be wuce daga bakinta zuwa cikinta ba, ga bakinta ya kuma fari fat, ruwa sede ta kuskure ta zubar gurin Alwalah. Aunty hafsat dake kusa da nabeelah tace “A’ah aunty nabeelah ki barsu kawai Muma zamu shiga ai insha Allahu,yanzu in kika bisu kema kinsan wulakanci zakisha , bakiga irin kallon datake ta miki ba tin dazu, kinde san halin hajiya mommy a barsu nesa-nesa kallon kura yafi kawai, baki ganin se Wani zakal-kalewa takeyi tamkar ana gun biki ba asibiti ba,…” Aunty nabeelah tayi shiru kawai tana ta kallon kofar dakin da Aeezad dinta ke ciki, yayinda hajiya rafi’ah da na’eema ke tsaye bakin dakin securities sun hanasu shiga sbda doctor na ciki. “Kai Dan uban waye dazaka Hana mu shiga, nifa uwarsa ce, kuma wannan matarsa ce, kuma yata ce…” Cewar hajiya rafi’ah datayi mgnr cikin tsiwa, gashi bata iya mgna a hankali ba, tanada babbar murya da karfi taketa magana kowa najinta, ga murya kmr ta maza, Nan take aka zubo musu Ido. Su kam securities din se bata hkri sukeyi da turanci, Amma ina Se Kara matsifa hajiya rafi’ah keyi ita a zatonta zaginta sukeyi kasancewar bata iya turanci ba. Seda na’eema tace bafa zaginki sukeyi ba mommy , hakuri suke baki…” ina ai hajiya rafi’ah Bata sauraresu ba, Alhaji sunusi dake gefe tini ya kule, hajiya rafi’ah bata taba batawa Alhaji Sunusi Rai ba kamar yau, be taba ganin rashin kyautarwa a duniyar Nan ba se yau, danshi a gurinsa bata lefi sbda hajiya rafi’ah tanada asiri bayan asiri akwaita da makirci, abubuwa biyunnan suna tafiya ne a tare asiri da makirki, in ba Daya ko anyi Daya bazeyi tasiri ba. Bakin ciki da damuwa suka cika zuciyar Alhaji sunusi, ganin yadda rafi’ah ta kara zagewa ta kuma zage securities din Tas, da kyar wasu suka mata magana tadena zage zagen da takeyi har seda doctor ya fito yace tadena ihun datakeyi Dan Allah sbda Yana effecting Aeezad dake kwance ba lafiya,so akeyi ya Farka da kansa to in tana wannan hayaniyar Yana iya farkawa kuma Sam ba ason hakan. Da kyar rafi’ah ta koma ta zauna tanata huci kamar zakanya, bata hkra ba taci gaba da harare harare da matsifa kasa-kasa, Nan ta yaye hijjabin jikinta daman duk yafi ya ishesa, ita Sam bata saba da hijjabi ba, tafi sabawa da gyale. Nan fa hajiya rafi’ah tazama daga ita se rigar atamfar dake jikinta dinkin doguwar riga, se dankwalin atamfar dake kanta, ko kunya bata jiba ta cire hijjabinta a cikin wadannan uban mutanen gashi Maza ma sunfi yawa, ga uban abokanan Alhaji sunusi, koda yake kaf abokansa sun San wacece rafi’ah, ba halinta da Basu sani ba. sabar takaicin daya tokare zuciyar Alhaji sunusi kawai se ya sadda kansa kasa, takaici da bakin ciki suka kuma ma zuciyarta dirar mikiya, a duniya be ganin rashin kyautarwa rafi’ah, Amma fa yau yagani kiri-kiri, Wasu daga abokansa suka shiga gulma kasa-kasa dana kusa dasu, kaf abokan Alhaji sunusi babu me kaunar hajiya rafi’ah sbda yawancinsu Tasha dakawa Alhaji tsawa a gabansu,infect de kowa yasan shi mijin tace ne.

Da daddare har 12:am kowa duk aka watse da zunmmar gobe zasu dawo sbda jiran farkawar Aeezad din kawai akeyi ,wad’and’a sukaxo daga garuruwa da dama suka nufa hotel, Alhaji sunusi Nan ya kwana sbda dakin da Aeezad din yake akwai kusan falo biyu special room yake, hajiya rafi’ah Kam ita da na’eema tini suka nufa hotel tin 10:pm, tace ita bacci takeji a gajiye take, ba kunya suka wuce hotel ita da yarta, Alhaji sunusi kawai sebin hajiya rafi’ah yake da Ido, Ashe bata da hali kamar yadda aketa gulmarta be tabbatar ba se yau,ya bata da mutane da dama a kan Hajiya rafi’ah danshi luf-luf take masa. Baban Noor ya nufa gidan abokinsa Alhaji sadi wanda har dare shima Yana Nan asibitn har 12:am ,a zuciyarsa sbda nabeelah yake zaune a asibitin shifa tinda yayi tozali da ita yace yaga matar Aure, gabaki daya hankalinsa ya tashi, kwad’ayinsa kaf ya koma kan nabeelah, daman Alhaji sadi matarsa Daya yaransu bakwai, a kallah Alhaji sadi ya haurawa shekaru hamsin ba sa’an baban Noor bane Kawai jininsu ya hadu suka fara abota. Suna tafe a mota kafin su karasa gidan Alhaji sadi ke shaidawa baban Noor shifa yana kaunar wannan daya gansu tare kuma so na Aure. Nan baban Noor ya hade Rai sbda ya fahimci nabeelah yake nufi. Duk hade ran da baban Noor yayi sam Alhaji sadi be fahimta ba se raftago zance yakeyi yariga yayi nisa a soyayyar nabeelah wai a haka danma a rikice ya ganta, Amma hakan be hanasa gano surar jikin da ubangiji ya mata ba. “Wannan ba karamar yarinya bace bafa alhajin Allah…”cewar baban Noor. Alhaji sadi ya kalli baban Noor cikin rashin fahimta yace “kamarya? Bangane ba! ba kamar yarinya bace ba?,wannan dagani ai bata wuce 20yrs in tayi wuta kenan, kawai de kayan morewa ne ubangiji ya bata tako ina taf-taf Alaji kaga nonuwa tantsan-tantsan…” Baban Noor ya amshe da “TAB wallahi wannan ta girmi matata ma in gaya maka…” “A duniyar Aljanu kou?” cewar alhaji sadiDakewa baban Noor kallon mara hankali. Baban Noor yace “a duniyar mutane, wannan fa ita ta raini Commander Aeezad, Aeezad he’s 22yrs , matata kuma 26yrs, ita Kuma wannan me Aiki cefa nanny din Aeezad ce, shine yanzu tadawo Aiki gidana gun iyalina,a kallah zata Kai 32yrs haka Naji iyalina tace, kawai karamin jikine da kyau take dashi na matsifa…” Baban Noor yayi mgnr ne sbda kawai ya cirewa Alhaji sadi batun nabeelah a ransa. Alhaji sadi ya tabe baki ba tare Daya yadda da shekarun nabeelah Da baban Noor ya fadi ba yace “Dan wannan ni ina ruwana, nifa ko shegiya ce ita ba nanny ba ina santa, Kai wannan macen me tsada waze ganta ya bari, ai tanama da tsoron Allah datake aikatau har yanzu, ade matan yanzu babu kamarta, saboda wallahi da matan yanzu ne masu budadden Ido ai da yanzu tana zaman kanta, da tini ta mallaki kudade a duniyar Nan sbda kalarta ai kalar manyan mutane ne irin mu. …ni wlhi Naji ma ta kuma kwanta min a zuciyata dakace min me Aiki ce, kaga hakan na nuni Da tanada kamun Kai, ni zan fara bude gindinta a leda kenan Masha Allahu..”Alhaji sadi ya karashe Yana wani shu’umin murmushi har ya fara mafarkin gashi a marar wannan kyakyawar macen , a Ido ya tabbatar dole farjinta yayi dadih. Wani kololon bakin ciki ya cika zuciyar baban noor domin ya kula Alhaji sadi yayi nisa bazeji kira ba yanzu. Har suka isa gidan Alhaji sadi nata sambatun nabeelah, Sam baban Noor be sake ce masa komi ba se Uhumm A’ah kawai, kasan zuciyarsa fal haushi.

Daren ranar Sam nabeelah batai bacci ba, ita da Hafsat ne a falon, hafsat tayi kwanciyarta tayi baccinta a kan kujerar 3ctr , nabeelah Kam ko kyafta idanuwanta bafai ba da zummar bacci, se lekawa takeyi tana kallon dakin Aeezad ji takeyi kamar taje dakin, Amma ina ba dama har yanzu ko ina zagaye yake da securities suna tsaitsaye ko zama basayi, dukda dare ya tsala Amma ko gyangyadi bameyi. Haka tadawo Falon ta shiga toilet ta dauro alwala dai-dai biyu na dare ta fara sallolin nafila tanata Addu’ah Allah bawa Aeezad dinta lafiya, tana sallar tana tangadi sbda har ynzu bataci ba bata shaba, aunty hafsat tayi-tayi da ita taci abinci Amma taki sbda bazata iya ba tanada tabbacin koda taci baze wuce cikinta ba Sbda hayyacin lissafinta na komi baya jikinta. har asubahi tanata sallah, datayi sallarh asubahi taci gaba da lazimi, duk kwarewar satar bacci be samu nasara a kanta ba ranar, burinta kawai taji ance AEEEZAD ya farfad’o. Zuwa karfe goma na safe mutane suka fara hallara asibitin, hajiya rafi’ah Kam bata iso asibitin ba ita da yarta se wuraren Sha biyu na rana, koda suka iso tini mutane sun cika fam. Alhaji sunusi se kallonta kawai yakeyi,zuwa ynzu mamakin hali irin nata kawai yakeyi, tinda ya aureta beyi kukan rashin mahaifiyar su Aeezad ba se jiya da daddare, yaci kukansa ya koshi takaici da tunanin lafiyar d’ansa be barsa ya rintsa ba. 2:30pm zuwa lokacin jikin kowa ya fara sanyi sbda shirun yayi yawa, an kara masa jini dai-dai Wanda jikinsa ke bukata, drip ne a jikinsa yanzu. Wani doctor ne ya fito daga dakin da Aeezad ke kwance, idanuwansa sanye da siririn glass, yayinda yake sanye da kananun kaya. Daddy na ganinsa ya mike a rude ganin doctor din ya tinkarosu Nan Alhaji sunusin yashiga tambayar “Ya jikin d’ana doctor munji shirun yayi yawa…” Da fara’ar kwantar da hankali dauke a kan fuskar doctor nazir yace “Ka kwantar da hankalinka sir, jikinsa Alhamamdulillahi kam da sauki, yama farka Amma yanata kiran sunan mommynsa,,, seda yadawo hayyacinsa duka yace Yana son ganin Nabeelah,,…” Da karfi doctor ke mgnr yayinda aunty nabeelah dake sauraren doctor taji ya kira sunanta ta mike a zabure, zata isa insa doctor din yake hajiya rafi’ah tayi hanzarin yin caraf kafin Alhaji sunusi yace komi ta amshe da “Kai doctor nabeelah yace kode na’eema, Anya kaji da kyau kuwa?” Doctor dake kallon hajiya rafi’ah be manta ba itace ta zage securities jiya. “Gaskiya kmr nabeelah yace ba na’eema ba…” Cewar doctor. Cikin tsiwa hajiya rafi’ah Tace “inaga de kunnenka ne beji da kyau ba,, ko baka lafiya ne…Amma na’eema yace, sbda mude kaf danginmu babu wata nabeelah, sede na’eema gatanan iyalinsa ce,…” Sam doctor be hayewa hajiya rafi’ah ba danya kula bata da mutunci tana iya masa zagin uwa da uba. “Wait hajiya bari inje in kara tambayarsa…” Cewar doctor nazir. Ya juya ze koma dakin da Aeezad yake hajiya rafi’ah tace “Harse ka tambayosa? Yo wai meze hana duk mu shiga mu gansa…” Doctor ya juyo yace “Kuyi hkri ba yanzu kowa ze shiga ba se Nan da zuwa la’asar…” Yana fadar hakan ya juya zuwa dakin da AEEEZAD din ke kwance. Nabeelah Kam tinda taji kalaman hajiya rafi’ah takoma da baya, Sam bata damu da munanan kalaman hajiya rafi’ah gareta, domin tasan tass tasan da ita nabeelah Amma tace basu da wata nabeelah. Aunty hafsat Kam abin ya mata ciwo Amma bata data cewa, sbda bata isa ta tanka ba, daddy ma yayi mukus ya kasa mgna kmr Wani wa-wa, kuma tabbas yasan nabeelarh da Ake nufi, se kallonta kawai yakeyi. jawo hannun nabeelah aunty hafsat tayi, tace “zauna ki kyalesu kawai aunty nabeelah wannan cin fuska dame yayi kama…” Aunty hafsat ta fadi a matukar hasale. Aunty nabeelah ta koma ta zauna yayinda heart beat dinta ya chanza Nan da Nan, duk ta zaku taganta gata ga Aeezad, ji takeyi daman zama aljana domin taje ta gansa. Ba jimawa doctor Nazir ya sake fitowa daga dakin da Aeezad yake. Hajiya rafi’ah na ganinsa tace “Kaje kajin kou? Ai nagaya maka na’eema yakeson gani, yo was yakeda ita a duniya bayan na’eema matarsa…” Na’eema Kam na gefe se Wani cika takeyi tana batsewa ita a dole game miji tanata Wani fankama da uwar kibar fuska kamar fanke yaji yeast a cikin man gyada,se Wani feelings takeji jiya zuwa yau dinnan , ganin uban manyan mutanen dasuka taru a asibitin manyan kasan kuma wai duk sbda mijinta, bata tabbatar mijinta bana wasa bane se jiya zuwa yau. “Nop ba na’eema yace ba am sorry hajiya…. please in akwai nabeelah a Nan mara lafiyar yace ta shigo Dan Allah, ita kawai yakeson gani , tin farkawarsa sunanta kawai yake kira, inma bata Nan a kirata cikin gaggawa Dan Allah in har ana bukatar saituwar Brain din mara lafiyar please, ku temakemu a kan aikinmu, dajin yadda yake Kiran sunanta ita ta musamman ce a garesa da sunanta ya bude bakinsa, yanzuma yunkurin tashi yakeyi wai ze fito ya duba yaga ko ita nabeelarh tana Nan din, Danya kasa tashi ne da tini ya fito da kansa wlhi…” Cewar doctor nazir.

 

Saadatubintuabdullahi

No comments