Breaking News

Tayi Min kankanta 1


*1*

 

“Zahra’u ya kamata ki fito haka fa kizo ku wuce,tun É—azu su hanne ke tsaye suna jiranki,bana son sakarcin banza fa”cewar wata dattijuya dake zaune kan kujerar zaman tsakar gida tana É—aure nono a ledar siga.

Daga can cikin bukkar dake kusa da dattijuwar wacce aka kira da Zahra’u tace “Inna do Allah Do Annabijjo,ki barni in sa jambakina cikin kwanciyar hankali,ke bakisan in bakayi kwalliya ba ko kallonka ba’a yi?”

“aykin kawai,yo tun bara kike sa jambakin amma har yanzu ba mashinshini,se asarar kuÉ—in siya miki da nike yi”cewar inna daga wajen da take zaune.

Fitowa tayi daga cikin bukkar tana gyara ɗamarar da ta ɗaura a ƙugunta,ko ina a fuskarta kwallliyace irin ta fulani.
Laɓɓanta shafe cikin jan janbaki,yarinyace da bata wuce shekaru goma sha biyar ba.

“kede Inna kinada matsala,bakin ki be taÉ“a faÉ—in alkha’iri,se sharri,ni É—oramin mu tafi”ta Æ™arasa maganar cikin turo É—an Æ™aramin bakinta gaba.

Gammo ta É—ora sannan ta É—ora mata kwaryar nonon akanta,ta miÆ™a mata ledar viva da aka sa ludaya da Æ™orai aciki,ta juya gun su Hanne dake tsaye zaman jiranta tayi murmushi kumatunta suka lotsa,siririyar hushiryarta ta bayyana atsakanin fararen haÆ™oranta masu kyan tsari,tace “na É“ata muku lokaci kuyi haÆ™uri,mu tafi kar mu sake É“ata wani lokacin”

Murmushi sukai mata,sannan suka rankaya suka fice bayan sunyiwa inna sallama.

Tafe suke suna hirar su ta yau da kullum,É—aya daga cikinsu Me suna haule tace”wai duk Æ™awancen nan namu muna aure inba riga É—aya muke ba se ya ragu ko?”

Dariya Zahra’u tayi sannan tace,”Allah ya kyauta,ni aradu ko birnin sin naje aure bazan dena Æ™awance daku ba,bare ma dukanmu muna ruga É—aya ba inda zamu”

Hanne ce ta amshe zancen da cewa”ni Auran ma tsoro yake ban,kunga de Ma’u kamar abun arxiÆ™i Rabi’u ya Aureta amma ku dubi wulaÆ™ancin da yake mata yanzu”

“shiyasa na shiga makaranta dan bazan yarda namiji yamin wulaÆ™anci ba,”cewar Zahra’u tana murmushi.

Da wannan hirar tasu suka ƙarasa fitowa daga cikin dajin falgore inda rugarsu take,suka miƙo tsawon titin zuwa inda barikin sojojin dake cikin dajin yake,sabida ankawo sababbin sojojin da ake ba training gurin acike yake da mutane kamar kasuwa,dan motocima in sun zo gurin da ƙyar suke wucewa sabida yawan sojojin.

Basu jima da zuwa ba kowa kayanta ya ƙare sabida ƙarancin abincin gurin,a hannu a hannu ake siyan duk wani abun ci na gurin.

gurin me saida burodi suka ƙarasa kowa ta sayi guda ɗaya sannan suka juya cike da farincikin sun sayi burodin da zasu ci yau agurin alibidin sunan Zina,wata ƙawarsu data haihu.

Karo suka ci da wani matashi sanye da wandon sojoji,hannunsa riƙe da bindiga,se riga tshits army green da hular sojoji,ba laifi kyakkyawane,raɓewa sukayi zasu wuce ta gefenshi yayi sauri yasha gabansu yace yana murmushi,

“don Allah kuyi haÆ™uri mu baÆ™i ne anan,kuma abinci mukeso mu ci,isowar mu kenan daga Abuja,amma mun rasa”

Harara Zahra’u ta galla masa sannan tace”amma dan baÆ™in hali ay kuna gani muka kawo tallan nono, in yunwar kukeji me ya hanaki siya?”

Murmushi yayi dan ya fahimci yarinyar akwai tsiwa,cikin taushin murya yace”Bamu lura bane Æ™anwata,ayi haÆ™uri”

“to yanzu me kukeso muyi muku,tunda mude ba abinci bane bare ku cinyemu”cewar Zahra’u batare da tsoron komai ba,dan ita ba Æ™aramin abu bane ke firgitata.

“in anan kuke don Allah ku taimaka mana, kuÉ—in cefane zamu baku ku dafo mana abincin ku kawo mana nida abokina,”

Shuru sukayi sannan hanne tace”gaskiya rigarmu da nisa nide bazan iya zuwa gida in dawo ba”

“yo inba wahalalle ba waye zeje gida yadawo nan”cewar haule.

“don Allah ku taimaka abokina yanada lalurar gyambom ciki be jure yunwa don Allah ku taimaka ku yi mana kamin yafara jin yunwa wallahi zamu biyaku ladan yi”cewar matashin kamar zeyi kuka.

Zahrau tsintar kanta tayi da tausayawa abokin nasa,sabida itama tana da lalurar gyambom cikin tasan azabar ziwon,dan haka tsintar kanta tayi da cewa

“kawo kuÉ—in,zan dafo muku,sede muna da nisa zaku iya jira?”
Da sauri matashin ya gyaÉ—a mata kai,sabida tun É—azu yake neman wanda ze dafo musun amma be samu ba,ga abokin nashi shegen taurim kai shiba jure yunwa ba amma ko ze mutu baze ci abincin siyarwa ba,shiyasa duk yabi ya damu.

Hannu yasa a aljihu ya É—ebo kuÉ—in dashi kanshi besan adadinsu ba yabata,juya kuÉ—in take a hannunta tana mamaki,amma batace komai ba ta É—auka da yawa suke so, dan haka ce mishi tayi”zan kawo ma insha Allahu ka tsaya a bakin titi de inda zan ganka da wuri”

Godiya yay mata sosai sannan yace”mu haÉ—u kawai anan,zefi sauÆ™i,sunana Capt Jameel Ahmad zan jiraki anan”

Bata ce komai ba suka juya suka wuce ita da ƙawayen nata,wanda gaba ɗaya haushinta sukeji,cikin fushi hanne tace.
“nufinki de bazaki gidan sunan ba ko?shiyasa kika amshi girkin gardawan da baki sani ba”

Batare da damuwar komai ba aranta tace”dan bakusan ciwon ulcer bane da kuma kun tausaya kun musu,nide zan musu sabida Allah”.tana kaiwa nan tai gaba ta Æ™yalesu a baya.

Muje zuwa.

Surbajo for life.
[1/6, 10:15 AM] Zahra Surbajo: 
*TAYI MIN ƘANƘANTA*


*Zahra Surbajo*

 

No comments