Breaking News

Tsutsar Nama 31

 *_Typing📲_*










   *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*

             _(Itama nama ce)_





_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_




_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒐𝒏𝒆_




......Tunda suka tashi Mom taga Samraah batai aikin komai a gidan ba ta ƙara harzuƙa. Lallai yau dolene taci uban yarinyar nan dai-dai gwargwado har sai taga ubanda ya tsaya mata a gidan nan. Fuuu ta nufi ɗakin barcinsu tunda tasan yau weekend bata fita aiki. Sai dai me wayam babu Samraah. Sai auta da Bibaa dake barci. Da farko tai tunanin tana wanka. Dan haka ta koma falo tai zaman bala'i tana jira. Bayan kamar mintuna goma sai ga Bibaa ta fito tana miƙa da alama tashinta kenan. 

       “K koma ko kiramin yarinyar nan Samraah”.

     Da ɗan mamaki Bibaa ta ce, “Ai bata ɗaki Mom.”

    “K ban san iskanci ki duba toilet mana ina zata je”.

   “ALLAH Mom bata toilet yanzu fa na shiga bayin na fito. Kodai tana kitchen tana aiki?”.

             A ɗan ƙufule Mom ta ce, “Tunda ni makwauniya ce ko. Dalla fita nasan tana ɗakin shegen can shima munafukin na biyu. Jeki daga shi har ita ki kira min su”.

     Babu musu Bibaa ta amsa da to. Sai dai babu jimawa sai gata ta dawo wai ɗakin a kulle yake. Dai-dai nan Abba ke fitowa da ga ɗakinsa. Tambayar mike faruwa yayi dan tun ɗazun yake joyo hargagin Mom da ga cikin ɗaki. Aiko a cikin tsantsar masifa take sanar masa. Ɗan jimm yay kamar ba zai ce komai ba. Sai kuma ya zaro wayarsa a aljihu ya shiga neman Yaya Musaddiq. Bugu biyu kuwa ya ɗauka. Daga can ya gaida Abban cikin girmamawa. A daƙile ya amsa masa kamar yanda ya saba. Kafin ya ɗora da faɗin, “Kai kuna ina ne?”.

     Da mamaki Musaddiq ya ce, “Abba ina gareji. Akwai wanda zai zo ya ɗauka motarsa ne shiyyasa na fita da wuri”.

          “Uhhmyim ita Samraahn tana tare da kai kenan?”.

    “Samraah kuma Abba. Ni kam mi zaisa na taho da Samraah nan. Tana nan a gida ai na barta tunda yau bazata je aiki ba”.

    A harzuƙe Abba ya ce, “To bata nan”.

      Sosai zuciyar Musaddiq ta wani harba. Muryarsa na nuna alamar rawa ya ce, “Abba kamar ya bata nan. Ina Samraah zata je da sassafen nan bayan bata da office yau?”.

    “Sai ka tambayen tunda yawo nake da ita a bayana”. Daga haka Abba ya yanke wayarsa. Hankalin Musaddiq yay masifar tashi batare da yasan dalili ba, tunda ta saba duk inda zata ko baya gida sai ta kiransa ta sanar masa a waya. Dan haka babu arziƙi ya baro gareji da fatan ya zo ya samu Samraah ta dawo. Dan tunda Abba ya katse wayarsa ya maida akalar kiran kan Samraahn amma wayar na shiga anƙi a ɗauka. Daga baya ma aka kasheta duka baki ɗaya. Wannan kuma ba halin Kandalarsa bane ba, balle ma ace shine yay kiranta da kansa...

     Cikin ƙanƙanin lokaci ya iso gidan, inda ya samu har lokacin Mum nata masifarta. Al'amarin kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba. Dan kuwa dai har sha biyun rana babu wani bayanin Samraah. Tun kowa na ɗaukar komai wasa har la'asar babu wani bayani. Zuwa lokacin anata buge-bugen waya wa ƴan uwa amma kowa sai yace bata je ba. Hakama ƙawayenta duk da Musaddiq yasan ita bamai yawan biye-biyen gidajen ƙawaye bace, ƴan uwan ma wace ala cika. Har gidan su Mansoor an sani zuwa sannan. Zuwa kusan biyar na yamma sai ga ɗayar wayarta an samu, wanda ya ɗaga ya tabbatar musu tsinta yayi. Harga ALLAH kuma ya yarda zai basu ne saboda yaga hoton Samraah ne a fuskar wayar. Hankali tashe Mansoor da Musaddiq sukaje inda ya kwantata yake, dan su ne dai keta faɗi tashin. Su Mom sunce basu yarda wani abune ya sameta ba sai dai idan yawon tazubar ɗin data saba tafiya ne ta tafi. Dan haka sukai burus da komai kamar basu san mima ake ba. Garama Abba yakan yi ɗan zugumm alamar tunani. Da Mom ta tsikaresa da hira kuma sai ya ware.

    Mansoor da Musaddiq sun amso waya tare da mask ɗin Samraah da eyeglasses ɗinta da aka tsinta. Ya kuma kaisu inda ya tsinta ɗin mutane kuma da yawa sun bada shedar tsintar yayi da gaske. Dan abun ya faru ne a idon mutane kusan uku dake sana'a a dai-dai wajen. Kasancewar suna fitowa da safe sosai suma. Sai dai sunce sunga wata napep da mota blue sun tsaya a wajen amma basu san mi sukayi ba, sai da suka wuce ne wanda ya tsinta wayar yake ganin abinda ya tsinta ɗin. Kuma yay magana da su bai ɓoye ba. Zuwa yanzu kam hankalinsu yakai ƙololiwar tashi, dan haka take suka kai report a station mafi kusa. Dalilin Mansoor nada ɗan halinsa tun a lokacin aka shiga traicing ɗayan layin Samraah. Dan kuwa wayoyinta biyu ne, kuma duk manya ne. Ɗaya tana amfani da ita saboda aiki, ɗaya kuma abinda ya shafi family ɗinta da ƴan abubuwanta ne a ciki. To ta aikin aka ajiye aka tafi da waccan. Har dare babu wani cikakken inpometion mai gamsarwa, zuwa sannan kuma dai tashin hankalin Abba ya fito fili. Dan Gwaggo Gudidi tazo tana faman kuka da faɗin lallai a binciki su Mom sun san inda suka ɓoye Samraah. Tunda kowa yaji dama abinda Mom ɗin ke faɗa a jiya gaban kowa. Mom zata hayayyaƙo maƙwafta da suka shishshigo suma suka nuna lallai akwai ƙamshin gaskiya a batun Gwaggo Gudidin. Kamar wasa kuwa sai ga rikici ya ɓarke. Dan zuwa gab da magrib su Musaddiq suka zo anguwar da ƴan sanda. Nanfa hankalin Mom yaso ya fara tashi, sai dai tana ta ƙoƙarin dannewa ita a dole kada aga gazawarta..

       Tambayoyi ƴan sanda suka musu har Auta ba'a bari ba. Mum kamar a ruɗe take amsa komai, dan haka ɗan sandan da case ɗin ke hannunsa ya dasa mata ayar tambaya. Sai dai bai ce komai ba suka wuce akan zuwa safiya zasu iya dawowa kosu nemesu a can station ɗin su.


     💫 (✧✧)✨(✧✧)✨(✧✧)💫



          Sannu a hankali na motsa idanuna da sukai min matuƙar nauyi da ɗaurewa. Sai kuma na shiga buɗesu sannu-sannu, a wani ɗaki mai ƙarancin haske na tsinta kaina alamar yamma tayi. Dan kiraye-kirayen sallar magrib ma naketa jiyowa. Ƙirjina ne yay wata masifar bugawa. Nai saurin ambaton ALLAH ina sake lumshe idanuna da sake buɗewa. Tabbas ta tabbata anyi kidnapping ɗina. Da ƙyar na iya tashi kasancewar duk jikin nawa babu wani ƙarfi. Ga wani irin fitsari da nake ji. Jiri-jiri dake neman kwasata yasa da ƙyar na iya dafe bango na miƙe. Lalube na shigayi ko zan samu wani haske. Cikin ikon ALLAH na samu makunar fitila. Idanuna dake lumshewa da buɗewa na sake warewa da ƙyau. Ɗakine babba sosai. Sai katifa a ƙasa ƙarama irin ta ƴan makaranta, akwai bargo da filo an kuma shimfiɗa bedsheet a kanta. Gefe kuma handbag ɗina ce sai leda mai tambarin gidan abinci har guda biyu a kusa da ita. Tare da ledar ruwa guda. Da ƙyar na iya jan ƙafata zuwa ƙofa. Na shiga ƙoƙarin murɗawa amma sai na sameta rufe gam. Inda labule yake ma sake nufa da ƙyar dan nasan bazai wuce window ba, na turesu da ƙyar. Ita ɗince kuwa, sai dai a rufe, nai ƙoƙarin na buɗe da ƙyar. Amma ƙarfen da akai adonta da shi ƙanana ne sosai ta yanda ko hannu bazai fita ba ma. Sosai zuciyata ke rawa yanzun kam. Ban haƙuraba na sake nufar ɗayar, nan ɗin ma dai irinta ce. Inda ke da kamar ɗan corridor na nufa, amma sai na samu ƙofar bayi ce a wajen. Naga hakanne sakamakon buɗewa da nai. Bamma san sanda na silale a wajen ba na saki wani irin kuka mai tsuma rai da girgiza zuciya. Na jima zaune a wajen ina kuka kamar numfashina zai rabu da gangar jikina. Kafin na sake miƙewa da ƙyar na shiga toilet ɗin. Fes yake babu wani datti. An kuma ajiye wadataccen sabulun wanka, omo, toothpaste brush, sosan wanka. Kai harda kayan wanke bayi. Babu dai abinda zaka nema ka rasa daya shafi hakan. Alwala na ɗaura batare da nabi takansu ba, zuba ruwan alwalar a jikina ya ƙara taimakawa naji na ɗan warware. Anan ma sai da na duba window sai dai yayi sama sosai koma ƙarami ne. Haka na fito na dawo ɗakin. A saman tabarma dake gaban katifar malale nai sallar azhar da la'asar har magrib. Sake kife kaina nai a wajen na sake buɗe sabon shafin kuka. Nama rasa ina zan kai tunani na. Kamar wadda aka zaburar na zabura inda bag ɗina take. Da sauri na buɗeta na shiga laluben wayata jikina har wani mazari yake tsabar yanda nake a ruɗe. Ganin kamar laluben ma baya min kawai na zazzage komai na cikinta burina kawai wayata ya faɗo, amma babu ita babu alamarta, sai ƴan kayan shafana dana zuba lips gloss ne kuma da fauda sai ƙaramin oil misk da face mask guda biyu da bana rabo da ita a jaka akoda yaushe. Bamma san na sake sakin wani wahallen kuka ba a wajen tare da zubewa ƙasa daga ni har bag ɗin........✍️






_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._



_GUDA DAYA:400_

_BIYU:700_

_UKU:900_

_HUDU: 1200_


_BANK NAME:KEYSTONE_


_BANK ACC NO:6019473875_


_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_


_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_


__

_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_


*09033181070*


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*



_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

No comments