Breaking News

Kanwar Maza 1

*Ina fatan yadda na fara lafiya, Allah ya sanya na gama lafiya. Ƙirƙirarren labari ne, idan akwai abin da ya yi kamanceceniya da rayuwar wani ko wata arashi ne*

Page1


Bismillahirahmanirrahim

 

Daji Ajiyar Allah! La’asar sakaliya, a lokacin da hasken rana ya fara disashewa, ta doshi yamma za ta faÉ—i, duhun magariba na Æ™oÆ™arin shigowa ya maye ragowar hasken da ranar ta bari kan ta Æ™arasa faÉ—uwa.
Gamayyar bishiyoyi ne, dogaye da da madaidaita, haÉ—e da ciyayi da ga mabanbantan tushe, suka haÉ—u suka yiwa dajin Æ™awanya. Zai iya kasancewa abin sha’awa ga wanda ya zo yawon buÉ—e ido, idan har bai san mai dajin ya Æ™unsa ba.
Ga wanda ya san abin da ya ƙunsa kuwa, zai kasance wuri mafi razani, firgici da kuma tashin hankali.
Gudu take yi a tsakanin rayuwa da mutuwa, tana rungume da wani zani a ƙirjinta, babu yadda za ayi daga nesa ka gane me ta rungumo haka take wannan uban gudun.
Ƙafafuwanta babu takalmi, jikinta babu mayafi, duk da yanayin garin babu zafi, amma laɓɓanta sun bushe tamkar dutsen da ya shekara ruwa bai zuba a kansa ba, babu alamar tana gane in da take jefa ƙafarta. Duk da wannan mawuyacin hali da take ciki, ta bawa abin da take rungume da shi muhimmanci sosai da sosai.
Cikin rashin sani, tayi karo da wani abu da ita kanta ba ta kai ga tantance ko meye ba, sai dai ƙarfi da nauyin abun ya sanya ta faɗi ƙasa, take ta saki wani marayan kuka, a lokacin da jini ya fara zuba daga ƙeyarta.
Sai a lokacin abin da take rungume da shi ya tsala kuka, saboda firgitar da ya yi shima.
Jariri ne ɗanyen goyo, cibinsa ko faɗuwa bai yi ba, jikinsa duk busashshen ƙazantar haihuwa da alama yaron ya kwan biyu, amma ko ruwa bai taɓa gani ba balle a wanke wannan ƙazantar!.

**************

 

Cikin garin Kano, unguwar É—orayi tinga, misalin Æ™arfe huÉ—u na yammacin ranar Alhamis, wani matsakaicin gida ne, cikin rukunin gidajen dake É—an Æ™aramin layin,  kallo É—aya zaka yi wa gidajen, ka san na masu Æ™aramin Æ™arfi ne, duba da yanayin kwatoci da kuma kasancewar gidajen awon igiya, ba magudanan ruwa, babu layuka masu kyau, kowa da in da fuskar gidansa ta kalla, haka zalika kowa in da ya ga dama yake sako kwatar gidansa, wasu da gyara wasu babu, ga gidajen ‘yan Æ™anana tamkar wani zai hau kan wani.

“Wai ba zaki fito ki je mini aiken ba, har sai gawayin ya Æ™are tukuna?” Cewar wata matashiyar dattijuwa, da take zaune a gaban kurfoti, hannunta riÆ™e da mafici tana firfitawa, gefe ga farantin silba É—auke da garin tuwon masara a kai.

Wata  yarinya ce ta fito daga wani É—akin da yake bayan matar, hannunta É—aya riÆ™e da hijjabinta, É—aya kuma sai matsar hawaye take yi.

Matar ta kalleta ta ce “Kukan me  ki ke yi?”

Aikuwa kamar mai jiran Æ™iris, cikin sangarta yarinyar ta ce “Ba Huzaifa bane ba ya….

“Ni yi mini shiru, haka dai kuka iya faÉ—a kamar kuna ganin hanjin junanku, idan na hana ki zuwa in da yake ai ba zaki hanu ba, maza ki É—au kuÉ—in nan ki je mini gidan Laure, ta baki kuka ta sittin, daddawa ta arba’in sai manja na naira É—ari ki kawo mini canjin, na yi maza in kaÉ—a miyar nan kan magariba”.

KwaÉ“e fuska yarinyar ta yi ta ce “Wai yau ma miyar kuka za ayi Innalillahi wa innalillahi raji’un”

Baki buÉ—e ta bi Yarinyar da kallo, cikin hasala ta ce “Idan na kaÉ—a kukar kar ki sha, zaki É—au kuÉ—in ki fita ko sai na yi fatali da kanki a wurin?”

Ta durƙusa ta ɗau kuɗin, ta zura hijjabinta ta nufi hanyar fita, a ranta tana jin gara ace yau babu abin da zasu ci, da wannan tuwon kamar na ibada.

Cike da kashedi matar ta ce “Idan kin ga dama kuma ki je ki zauna, kar ki yi sauri kiga yadda zan yi da ke, ko ki biyewa yara ki tsaya shashanci a hanya”

Ba to ko waiwayo ba, ta yi gaba abinta tana kalle-kalle.

Gidansu ƙawarta Habiba ta fara biyawa, ta tarar da maman Habiba a tsakar gida ana yi mata kitso, ta durƙusa ta gaida Maman Habiba, sannan ta ce mata wurin Habiba ta zo.
Habiba ta fito daga É—akinsu tana kallonta tana murmushi, ta Æ™araso in da take tsaye ta ce “Ruma ina zuwa ne?”

Cikin muryar RaÉ—a Ruma ta ce “Dan Allah Habiba aron tayar Sani zaki bani, Mama ce ta aikeni so nake nayi sauri na je na dawo”.

Habiba ta ce “Kaii, Ruma kin san Sani yafi kashi É—oyi, kar na baki ki je ki salwantar da ita, daga ni har ke mu shiga uku”.

Ruma cikin Æ™warin gwiwa ta ce “Wallahi ba zata salwanta ba, ke dai ki aramini, so nake na yi gudu na ne na dawo”.

Habiba ta ja Ruma soron gidansu, ta duba saman kejin kajin da ke cikin É—an tsukakken zauren gidan, ta É—aukowa Ruma tayar Sani ta bata ta ce “Dan Allah Ruma ki kula, kar wani abu ya samu tayar nan, ki yi maza mi garata ki je ki dawo”

Ruma tayi murmushi ta ce “Kar ki damu, yanzu zan fyalla naje na dawo, ina son tayar nan ta sani dama ya bar mini, ‘yar dandaÉ“asa da ita, yanzu zaki ga naje na dawo”.

Habiba tayi murmushi ta ce “To shikenan, yi sauri kafin ya dawo”.

Ruma ta dafe kan taya, ta garata ta dinga zura gudu ta lunguna kamar wata namiji ba mace, ba ta tsaya da gara tayar ba har sai da ta isa gidan Laure.
Ta yo sayayyarta ta gama, ta fito ta kuma garo taya zata tafi gida, can ta hango wasu ‘yan makarantar allonsu, a Æ™ofar gidan Hanne mai markaÉ—e suna ‘yanta, ba tare da ta tuna da kashedin Mama ba, ta ajiye kayan aiken da canjin haÉ—i da tayar da ta aro, ta shiga aka hau ‘yanta da ita.

Kasancewar Æ™wararriya ce a harkar shagala da iya rinto, nan da nan wasa ya É—au zafi, ganin tana ta cinyesu a ‘yantar ta hanyar rinto, sai wasa ya koma faÉ—a, daga nan aka hau dambe, a wurin Ruma ta kifar wa da wata markaÉ—enta ga ta da Æ™arfi kamar doki. Da Æ™yar wani mutum ya raba faÉ—an, Ruma ta haÉ—a yaran mutane ta zane musu jiki, sai da mutumin yayi mata barazanar zai gayawa yayanta, sannan ta haÆ™ura da damben.

Yarinyar da suka yi damben, ganin an musu asarar markaɗe, an kifar ga duka, ya sanya ita da ƙannenta suka fasawa Ruma Manjan da ta sayo wa Mama, suka kwashe canjin aiken, suka farke ledar aiken suka gudu, daddawar ma sai da ƙyar ta tsinto wasu, an fasa ledar kuka duk ta watse.

Ta kwashi sauran kayan, ta tafi gida, tana tafe tana tunanin wace ƙaryar za ta jirgawa Mama, dan ta kaucewa faɗanta, dan a duniya ba ta son faɗan Mama, gefe guda kuma tana tunanin irin dukan da zata naɗawa Safiya idan suka haɗu a makaranta allo, saboda abin da suka yi mta.
Lokacin da Ruma ta isa gida tuni an fara kiraye-kirayen sallar magariba, domin wasu masallatan har sun tayar, sai a lokacin ta sake shan jinin jikinta, tsoro ya ziyarce ta.

A soro ta rakuɓe tana leƙa cikin gidan, ta hango Mama a gindin rariya tana alwala, Mama ta ɗaga ido tayi mata kallo ɗaya, ta mayar da kai ta cigaba da alwalarta.

Cikin sanÉ—a Ruma ta shiga tana satar kallon Mama, ta ji mai Maman za tace mata, amma ta ji ba tace mata komai ba.
Ta lallaɓa ta ajiye abin da yayi saura na aiken, ita ma ta faɗa banɗaki tayi alwala.
Ta lallaɓo falo, ta tsaya a bayan Mama ta tayar da sallar ita ma.
Mama ta idar, ta tashi ta fita tsakar gida, ta duba abin da Ruma ta kawo mata na aiken, taga irin aika aikar da Ruman ta yo.
Ta dawo falon tana jiran Ruma ta idar da salla ta dirar amata, amma Ruma ta ƙi idarwa, ta hau nafifilin babu gaira babu dalili, matar da wataran sallar ma sai Mama ta haɗa .mata da duka take yi, amma yau sai gashi har da nafila.

Can da Mama taga abin nata bana Æ™are bane ba, sallar taÆ™i Æ™arewa, ta damÆ™o wuyanta ta baya ta zaunar da ita, ta kalleta cikin haÉ—e fuska ta ce “Gidan uban wa ki ka je dana aike ki?”

Cikin tsoro Ruma ta girgiza kai ta ce “Ba ko ina Mama”

“Ƙarya kike yi, zaki gaya mini ko sai na murÉ—e miki wuya, tun la’asar na aike ki amma sai magariba kika shigo mini, gidan uban wa kika je?”

Cikin zazzare ido Ruma take jujjya kai tana rantse-rantsen rashin gaskiya, “Wallahi Mama ban je ko ina ba”

Cikin tsananin Fushi, Mama ta ce “Ba zaki gaya mini ba!”

“Mama wallahi dagaske nake”

“Assalamu alaikum” aka yi sallama a tsakar gida.

Mama ta amsa sallamar tana huci, wani matashin saurayi ne ya shigo É—akin, yana faÉ—in Mama na dawo”.

Mama ta ce “Sannu da zuwa”

Ya amsa da yauwa, ya dubi Mama dake tsaye a kan Ruma, Ruma sai wulƙita ido take, kamar ta zagi sarki.

“Mama meyafaru ne?” Yayi Maganar yana son jin ba’asi.

Cikin É—acin rai Mama ta ce “Saboda tsabar iskanci na yarinyar nan, nan da gidan Laure, ta je ta sayo mini kayan miya, tun bayan la’asar sai yanzu ta shigo mini gida, babu aiken babu dalilinsa, kuma babu canjina, nayi-nayi ta gaya mini in da ta tsaya amma taÆ™i faÉ—a sai rantse-rantse take yi”.

Ya kalli Ruma ya ce “Ba zaki faÉ—i inda kika tsaya ba, kuma ina canjin? Ko zuwa ki ka yi ki ka kashe mata kuÉ—i tunda kin saba”

Cikin tsiwa da rashin kunya, Ruma ta ce “Ban sani ba, kai kuma waye ya saka da kai, zaÆ™in zaÆ™afere mai gida feraye kabewa, ai ba da kai ake yi…..
Kan ta ƙarasa Mama ta rufe bakin nata da duka, da sai da tayi zaton bakinta ya fashe.

Ja da baya tayi da sauri, ta dafe bakinta tana yarfe hannu, saboda ta ji zafin dukan nan sosai da sosai.

Ya jinjina kai ya ce “Mama Æ™yaleta, ba dai bata da kunya ba, kar ki wahalar da kanki, ki bari mai sunan Baba ko Haidar su shigo, sai su tuhumar miki ita”.

Jin abin da ya faÉ—a ya sanya Ruma ta yi wata irin zabura, ta ce “wallahi Mama gaskiya na gaya miki, dan girman Allah kar ki gaya musu, canjin ne suka zube a hanya, na faÉ—i Æ™asa man jan ya fashe dan Allah kar ki gaya musu”.

“Wallahi Mama Æ™arya take yi, kin san dai Æ™aryarta ba ta salla, ki tuhumeta bari mai sunan Baban ya dawo zaki ci ubanki”.

Cike da gamsuwa Mama ta ce “Ai hakan za ayi tun da ba ta da mutunci”

Ya fakaici idon Mama ya yiwa Ruma gwalo.

“Mama kin ganshi ko yana mini dariya, dan Allah kiyi haÆ™uri”

Banza Mama tayi da ita, ta bawa Huzaifa kuÉ—i ya kuma yi mata wani cefanen.

Rumaisa ta koma gefe tayi tagumi, zuciyarta na ta zullumin halin da zata iya shiga, idan har aka sanarwa da Mai sunan Baba ko Haidar abin da ta yi, gashi ko giyar wake ta sha ta san ba zata iya gayawa Mama haƙiƙanin abin da ya faru ba.
Salati kawai take yi, tana roƙon Allah ya rufa mata asiri, kar Mama ta gaya musu, ƙasan zuciyarta kuma tana yi wa Huzaifa Allah ya isa da ya bawa Mama shawarar ta haɗata da su Haidar.

Ta na tsaka da tunanin, ta jiyo Mama da Huzaifa suna hirarsu a tsakar gida, kamar ba ita ta gama faÉ—a ba.
Suna yi mama tana ƙarasa aikin miyarta.
Sallama aka yi a tsakar gida, Ruma ta rikice, dan kusan muryoyinsu duk kusan iri É—aya ne, ta É—an nutsu ne da ta tuna mai sallamar muryarsa ba ta kai ta su Haidar fashewa ba, kuma shi dama sanyin hali ne da shi.

Jiyo Mama tayi tana faÉ—in “Fodiyo, an dawo”
“Eh Mama, ya gidan?”

“Alhamdilillah, sannu ka je ka watsa ruwa kafin nan na gama miya”

Usman da Mama ke kira da Fodiyo ya ce “To Mama, ga wannan” yayi maganar yana ajiye mata leda.

Miƙewa Ruma tayi tana leƙa window, tana son gane me ye a cikin ledar da Fodiyo ya kawo.
A ranta ta ce “Allah ya sa kifi ya kawo, idan kifi ne a bani kasona, dan idan aka saka a wannan baÆ™ar miyar ban sha.

Ba ta kai ga gano meye a ledar ba, idanunta suka sauka a cikin na dodonta, da ya shigo gidan ko sallama bai yi ba, gani tayi tamkar yayi mata wani irin mugun kallo, ko dan dai a tsorace take ne oho.
Mai sunan Baban Mama kenan, Umar faruk.
Cikin takunsa na ƙasaita ya ƙaraso tsakiyar tsakar gidan, sannan ya yi sallama.

Hannu Ruma ta É—ora a ka, muryarta Æ™asa_Æ™asa ta ce “Na shiga uku, yau kashina ya bushe Æ™ayau idan ya san me nayi”.

Tun daga sallamar da ya yi, bai cewa kowa komai ba, shi ma ya ajiyewa Mama ledar da ke nasa hannunsa, ya wuce É—akinsu.
Bai jima ba ya fito tsakar gida, ya É—au buta zai yi alwala.
Ruma ce ta fito kamar munafuka, ta É—an risuna ta ce “Yaya Faruk sannu da zuwa”

ÆŠaga ido ya yi ya kalleta, bai amsa ba ya mayar da kansa ya cigaba da alwala.

Cikinta ya É—uri ruwa, ta É—au tsintsiya ta tafi falon Mama ta hau shara a daren, kai da gani ka san sharar ba ta domin Allah bace ba.
Huzaifa ya faki Idon Mama ya bi Rumaisa falon, ya dinga leƙata yana tuntsura mata dariya.

Ba dan tana cikin yanayi na tashin hankali ba, babu abin da zai hana su kafsa faɗa da Huzaifa a daren nan, amma ta san biyewa Huzaifa su yi faɗa alhalin Faruk yana gidan nan, wata babbar matsalar ce, mai zaman kanta, dan ƙarshe sai tayi kuka.

“Ba zaki fito ki É—ebi Abinci ki ci ba?” Mama tayi maganar cikin É—aga murya, yadda za ta jiyota.

Daga É—aki Ruma ta ce ‘Mama na Æ™oshi”

A Æ™ufule Mama ta ce “To uban me ki ka ajiye da zaki ci, ba zaki fito ki ci Abinci ba?”

Ruma ta É—an tura baki tayi shiru.

Usman ya ce “Ai kin san kin yi maÆ™iyin nata tuwo, mussaman miyar kuka da ma wata miyar ce ba wannan ba, Æ™ila ta ci”

Mama ta ce “Abin da nake da shi ba shi zan dafa na bata ba, zan fasa girki ne dan ba ta cin tuwon?”.

Cikin kakkausar muryarsa Umar ya ce “Ki Æ™yaleta, tun da a cikinta zata zuba, ta kwana da yunwa mana”.

Mama ta gyaÉ—a kai ta ce “Ai shikenan”

Muryarsa kawai da ta jiyo, sai da ta sake shiga cikin tashin hankali, tsananta addurta ta yi, a kan Allah ya rufa mata asiri kar Mama ta gaya masa ta yi mata laifi.

‘yan mazan nan suka kewaye Mama, suna ta hira kowa da abin da yake ce mata, banda mai sunan Baba, da  yake duba wayarsa, ba tare da ya tanka musu ba.

Jin suna ta hira, Mama ba ta gaya masa tayi laifi ba, ya sanya take ta murna, tayi maza ta yi sallar isha’i ta shimfiÉ—a katifar ta ta kwanta.
Ta cigaba da Addu’a a cikin zuciyarta.

“Assalamu alaikum” aka yi sallama a tsakar gidan.

Suka amsa baki É—aya, Suka zubawa yaran da suka shigo ido mace da namiji.
Duk da akwai wutar lantarki da fari Mama ba ta gane yaran ba sai daga baya.

Suka gaida Mama da su Umar, Mama ta kallesu ta ce “Habiba ya aka yi me?”

Habiba ta ce “Ruma tana nan?”

Umar yayi caraf ya ce “Yaya aka yi?”

Kasancewar sa mutum mai tsanain kwarjini, sai da Habiba ta É—an ruÉ—e sannan ta ce “Dama É—azu ne da aka aiketa ta zo ta ce na bata aron taya, zata jewa Mama aike, to tayar ta Sani ce, ta ce zata dawo da ita kuma haryanzu shiru”.

Mama cikin mamaki ta ce “Taya kuma?”
Habiba ta jinjina mata kai.

Gaba É—aya Ruma ta manta da ta je ta aro taya, sai yanzu da ta ji maganar Habiba, dan tun da aka kwashi damben nan a nan ta yasar da tayar ta yo gida.
ÆŠora hannu tayi a ka ta ce “Na shiga uku, Habiba shikenan kin kasheni”.

Mama ta ce “Kina ina zo nan, mara kan gado, babu yadda ban yi dake ba a kan ki gaya mini in da kika tsaya, amma kika ce ke baki tsaya ko ina ba, ashe yawon aron taya kika tafi ko, ko ina sai kin nuna hali ƘANWAR MAZA, ina ke ina taya ban da hauka, zaki fito ki basu abarsu ko kuwa?”

Jikinta na tsuma ta fito ta tsaya daga bakin ƙofar falon Mama, tana satar kallon Umar, amma taga kamar ma bai san me ake yi ba.

“Ma.m.maama.. wallahi dan nayi sauri ne, ya sanya na aro tayar, kuma wallahi na manta na barota a wajen gidan Hanne mai markaÉ—e”.

Mama ta riƙe haɓa kawai, tama rasa me zata ce gaba ɗaya.

Huzaifa ya ce “Wannan yarinyar idan kina da rabon yin hankali Allah ya shiryeki, ina ke ina taya kina mace?”

Mama ta kalli in da Habiba take tsaye ita da Æ™aninta ta ce “Dan Allah ku yi haÆ™uri, tun da ta fita nima nake zaman jiranta, ban aiketa ta je ta karÉ“i kayan kowa ba, da safe in Allah ya yarda zan turata ta je ta dubo muku” Mama tayi ta basu haÆ™uri, suka juya suka tafi.

Mama ta zauna ta dasa mita, ta in da ta shiga ba ta nan take fita ba, su Usman na tayata, ita kuwa Ruma da ta san ba ta da gaskiya, sai ta ƙule a kan katifarta, zuciyarta sai bugawa take tana jiran jin me Yaya Umar zai ce, amma shiru bai ce komai ba.

Har suka watse daga tsakar gida, Mama ta shigo ɗakin, ta sameta ta rufe ido tana baccin ƙarya, still Mama ta cigaba da mita, sai da Ruma ta ji kamar ta tashi ta barwa Mama ɗakin ta huta, saboda Mama mitarta ba ta ƙarewa sam, gefe guda tana yiwa Allah godiya da Dodonta bai yi magana ba.

Wani irin bacci ne mai daÉ—in gaske yayi awon gaba da ita. A cikin baccin nata babu zato babu tsammani sai ji tayi an yi sama da ita da hannu É—aya.

“Wayyo Allana, Innalillahi wa innalillahi raji’un, warin hannuna na hagu zai karye Mama!” Sai da ya dungurar da ita a tsakar gida, suka yi ido huÉ—u, ta ga wanda yayi mata wannan aikin.
Jikinta ne ya hau kyarma, dan idonsa kawai idan ransa a É“ace yake abin tsoro ne.

A Æ™asan zuciyarta ta ce ‘Shikenan tawa ta Æ™are, Allah ya sa na cika da kyau da imani!.

Ayshercool
08081012243
[16/06, 9:00 pm] JAKADIYAR AREWA:                    ƘANWAR MAZA

BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

 

Ku yi subscribing YouTube channel É—in mu, domin samun daÉ—aÉ—an litattafan hausa na sauraro.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Arewabooks @ ayshercool7724
Watpad@ ayshercool7724

No comments