Breaking News

Kanwar Maza 37


Bashir ya san iya tijara zai sha ta a wurin takawa, dan haka ya shiryawa karÉ“ar da duk wani hukunci da zai yi masa, ya kwantar da murya ya ce “Tuba nake, ka bari zan zo in sameka, na gaya maka ina Asibiti ne”.

“Kar ka sake ka zo in da nake, idan ka zo haÉ—uwarmu ba zata yi maka daÉ—i ba”

‘shi wannan kowa ma yi wa masifa yake yi?’ ta tambayi kanta, can kuma ta ce ‘Ƙila ma ba gaske bane mafarkin da na saba nake yi’.

Maganar Bashir ce ta dawo da ita hayyacinta “Haryanzu ba ki gaya mini ko sunanki ba, mun kawo ki unconscious, ki gaya mini sunanki, ki bani lambar wayar wani a gidanku, na kirasu ga abinci nan na kawo miki, yan sanda suna jirana na je na kai report”.

“Ina jaririna?” Shine abun da ya fito daga bakin rumaisa.

“Na gaya miki yana nursery, an saka mishi oxygen ana Æ™oÆ™arin ceto ransa”.

“Idan wani abu ya same shi ba zan yafe maka ba, kuma wallahi sai na saka yayyena maza sun zane ka” ta yi maganar tana hawaye.

Bashir ya sake nutsuwa, yayi murmushi ya ce “ba zata kai mu ga haka ba,  babu abun da zai same shi sai abun da Allah ya Æ™addara masa, trust me, yanzu bani lambar wayar”.

Ta É—an rausayar da kai ta ce “Allah ya sa ba mafarki nake yi ba, ni na manta lambar kowa, bari na baka ta Yasir, yayana ne ta sa na tuna.

Ya ce “Ok, gaya mini” yayi maganar yana riÆ™e wayarsa.

Ta gaya masa lambar cif, yayi saving ya ce “Tashi ki ci abinci, yayata zata zo ta zauna da ke, kan ‘yan gidanku su zo”.

Ta girgiza masa kai ta ce “Ni ba zan ci komai ba, sai na ga mama”.

Bashir ya ce “No, ba za ayi haka ba, ki daure ko kaÉ—an ne”

“Ni dai ka tashi ka kirawo mini ita kan na farka daga baccin da nake yi” tayi maganar tana kuka har da sheshsheÆ™a.

Ya ce “To shikenan, bari na je, yayar tawa zata zo, sunanta Asiya, za ta zauna da ke”

Ba ta ce masa komai ba ta cigaba da share hawayenta.

Mintuna talatin da fitarsa, sai ga yayarsa Asiya ta iso, ta tarar da rumaisa tana barcci, dan haka ta nemi wuri ta zauna tana jin tausayin yarinyar, mussaman yanayin da ta ganta a ciki.

***
Kasancewar yasir ya iya gyaran kayan Electronics sosai, ya sanya ya buÉ—e É—an case da yake gyare-gyaren sa, ko yanzu da yake ta aiki yana yi ne ba dan yana jin daÉ—in aikin ba, sai don rage kewa da kuma damuwa.

Wayarsa ce ta fara vibrating, yana ji yayi banza sia da ta kusa katsewa, sannan ya É—aga ya yi sallama.

“Wa’alaikum salam warahmatullah, ina magana da Yasir ne?”

Yasir ya ce “Eh ni ne”.

“Yauwwa, sunana Bashir kibiya, ni jami’in tsaro ne dan Allah idan ba zaka damu ba, ina son haÉ—uwa da kai a babbar headquarter ‘yan sanda ta bampai”

Waro ido Yasir yayi ya ce “YallaÉ“ai me na yi? Wallahi ni ban yi wani laifi ba”

“Na sani malam Yasir, ni yakamata na zo da kaina ma, amma wani abu ne ya riÆ™eni ka zo da gaggawa ka sameni”

Jiki a sanyaye Yasir ya kashe wayar,ya kwashe kayansa, yana tunanin wa zai jewa da wannan maganar, babu yadda za ayi a gayyaci mutum bamfai ace lafiya lau.
Ya tsaya a ƙofar gida ya kasa shiga gida, sai rarraba ido yake yi.

Abdallah ne ya fito daga cikin gidan, Yasir ya ce “Alhamdilillah, zo ka ji wani abu”.

Abdallah ya ce “Ya aka yi?”

Kamar Yasir zai fashe da kuka ya ce “Wani ne ya kirani, wai na je bamfai yana jirana kuma ni wallahi tsoro nake ji”

Abdallah ya Æ™are masa kallo sannan ya ce “Kai, ka gaya mini idan wani abun ka aikata, Kodayake da ruma tana nan sai in ce ko ita ake nema, amma kuma ks tabattar ba ‘yan iskan gari bane ba, ko a cikin abokanka wani ke son raina maka hankali ba?”
Yasir ya ce “Bana tunanin hakan, mutumin muryarsa ba ta yi kama da haka ba”.

Abdallah ya ce “Bani lambar” Yasir ya bashi lambar ya saka a wayarss ya kira, yana kira Bashir ya É—aga, suka gaisa Bashir ya ce “Bawan Allah, yayan yasir ne ni, ina son jin dalilin da ya sanya ake nemansa a bamfai?”

Bashir ya ce “Eh, abu ne mai muhimmanci, da laifi yayi gida zamu zo mu kama shi ai, ku hanzarta dan Allah”

Abdallah ya ce “To shikenan babu damuwa “.

Ya katse wayar ya kalli Yasir ya ce “Zancenka gaskiya ne, ka san wani abu? Kar mu gaya kowa, zo mu je mu ji koma menene, sa ji daga baya” Abdallah ya Æ™wararawa Yasir gwiwa, suka kama hanya suka tafi.

***
Ammi ta fito babban falo, ta dubi É—aya daga cikin barorinta ta ce “Maza je ki korawo mini iman” ta amsa mata cikin girmamawa, ta tafi.

Bai fi mintuna bakwai ba, sai ga Iman “Ammi gani, Allah ya sa ba laifi na yi ba?”.

“Ai laifin ki ka yi, na gaji da zaman É—akin nan da ki ke yi, jikinki ai da sauÆ™i yanzu, ki shirya zamu je gidan Jamil, an ce matarsa tayi É“ari” É—an É“ata fuska iman tayi kamar zata yi kuka.

“Menene ko ba zaki ba?” Ammi tayi maganar tana tsare iman da ido.

“A’a zan je, bana son na je na tarar da Anty samha ne” tayi maganar kamar ta rushe da ihu.

Ammi ta kalleta a tsanake ta ce “Meye tsakaninki da Samhan da ba kya son haÉ—uwa da ita?” Sai kuma ta sha jinin jikinta jin abun da ammin ta ce.

“Bakomai Ammi, bana son fita ne”

“Aikuwa sai kin fita, maza muje in shiryaki, kar ma ki É“ata mini lokaci” Nusaiba kuwa sai dariya take yi, ganin ammi ta saka iman a gaba wai ita zata shiryata. Hakan kuwa aka yi, Ammi na tsaye iman ta shirya cikin baÆ™ar abaya, da ta karÉ“i kyakywar farar fatarta, sai É—aukar ido take yi, ta É—ora mayafin a kan ta, sai dai kwantaccen gashinta sai da ya bayyana.
Tare suka fito da Ammi, tana janyo hannunta, ita kuma kamar ta fashe da kuka, sai tura baki take yi. Haka suka jera da Nusaiba da iman da ammi.
Nusaiba ta ce “Allah ammi kin shagwaÉ“a yarinyar nan da yawa, ji wata taÉ“ara da take yi”.

Ammi ta ce “Bar ni da ita, sai na zaneta tukuna” haka suka fito harabar gidan a tare.

Tun daga nesa yake kallonsu, ya tattara nutsuwartsa a kan Iman, tamkar ba bugun Nigeria ba haka take.

“Ruky wannan ma ‘yar gidanku ce?”

RuÆ™ayya ta waiwaya ta hango su Ammi, a fusace ta dube shi ta ce “To ba ‘yar gidan nan ba ce, tsintota aka yi aka riÆ™eta a gidan nan, babu wanda ya san danginta ma, wataÆ™ila ma ba ta da uba”
Maimakon ya fusata sai ya ce “Wow, amma dai a Æ™asashen Larabawa kuka tsinto ta ko? Ko irin Afrika ta gabas É—in nan”.
“A’a africa ta sama, aka tsinto ta aikin banza ” ta tashi fuu ta shiga ciki.

Tashi yayi yana kiran sunanta, amma bata ko sake waiwayo wa ba ta tafi.

“Wallahi na gaji, ni da gidan ubana saboda bala’i ban fiye zama ba, ko na kawo baÆ™ina ba, da gayya idan bar zan yi baÆ™o mu zauna a harabar gidan nan, sai wannan banzar yarinyar ta fito, ita kuma ammi ta wani sako su a gaba riii kamar shanu, duk yadda na Æ™allafa rai a kan gayen nan, yana ganinta ya hau wani surutu, ji nake kamar na zuba mata wuta a fuska uban kowa ya huta”.

Mummy da take jin ta tayi shiru ba ta yi mata magana ba, ta Æ™araci bala’inta ta gama, amma Mummy ta fara hasala, duk yadda suka kai ga É“ata iman, ba ya wani tasiri sam. Kamar ba zata yi magana ba sai kuma ta ce “daga yau idan kin yi baÆ™i, ku din ga shigowa falon waje, kuna zama, ku bsrni da ita, zamanta a gidan nan ya kusa expire ” haka ruÆ™ayya ta zauna tana cigaba da huci.

***
Yasir da Abdallah basu saki jikinsu ba, sai bayan ganin kyakywar tarbar da Bashir yayi musu, ya kai su wani katafaren office, har da sanyawa a kawo musu ruwa da lemo.
Abdallah ya ce “Ranka ya daÉ—e mai É—an uwana yayi ake nemansa ne? Hankalinmu ya kasa kwanciya, kar wani abu ne ya faru, mahaifiyar mu babu lafiya, ba wanda muka sanarwa ma a gida”

Bashir ya yi murmushi ya ce “ÆŠan sanda ai abokin kowa ne, ba abun tashin hankali bane, ni na so mu zo har gida amma wani aiki nake yi wa uban gidana. Shekaranjiya aiki ya kaini jihar katsina, na kwana É—aya a can, a kwana na biyu na kamo hanyar baro garin, na tsinci wata yarinya da jariri a gefen hanya, wani mutum yana tambayarta, so nayi amfani da id card É—ina, muka kaita asibiti da yaron, amma yarinyar ta kasa bamu haÉ—in kai saboda jaririn nan, so a jiyan muka taho kano, aka kwantar da ita a asibiti ita da yaron, ta ce mini dai É—anta ne, na yi reporting wa abokan aikina, shine ta bani lambar wayar Yasir ta ce mini yayanta ne, suananta Rumaisa.

Miƙewa tsaye suka yi tsaye gaba ɗayansu, suna kallon Bashir, amma suka kasa magana.
Bashir ya miÆ™e ya ce lafiya kuwa?”

Tuni hawaye ya wanke fuskar Yasir ya ce “YallaÉ“ai ina ruma take, Æ™anwarmu ce aka saceta a katsina, tafi wata biyu kusan watanta uku a hannun ‘yan bindiga, dan Allah tana ina”

Bashir ya dafa kafaÉ—ar Yasir ya zaunar da shi ya ce “Calm down, tana nan ana kula da lafiyar ta, ku godewa Allah, duk da ba ta gaya mini meyafaru ba, amma dai gaskiya a galabaice take, ikon Allah ne ya fitar da ita, tana nan asibitin koyarwa na kano, zaku bamu bayanin yadda aka yi ta É“ata da komai da komai “. Daga Yasir har Abdalla aka rasa mai magana, dan Abdallah durÆ™usawa yayi yana kuka dan tuni suka fara fitar da rai.
Nan Bashir da abokan aikinsa, suka din ga rarrashin su, suka gaya musu iya abun da suka sani, daga tafiyar su ita da Aliyu zuwa yanzu, aka kuma duk wasu cike-cike da za ayi, aka ce zasu tafi Asibitin wurin rumaisa.

Abdallah ya gige hawaye ya ce “YallaÉ“ai zamu iya kiran gida mu sanar musu, mahaifiyarmu na nan ba yadda take saboda azabar tunani da damuwa”

“Eh ku kirata ku sanar musu”.

Yasir ya ce “Mai sunan baba zaka gayawa, shi zai san yadda zai ya sanar mata, kar ta gigice jininta ya kuma hawa”.

Haka kuwa aka yi, sai dai Umar bai ɗaga wayar ba, sai Aliyu aka samu, gaba ɗaya ya rikice da jin maganar, amma yayi iya ƙoƙarinsa ya saita kansa, mama ba ta gane ba, ya sanarwa Usman da Mai sunan baba.

Mai sunan  ya ce su yi gaba, zai taho da mama, ba tare da ya bari ta gane wani abu ba, su fara zuwa su duba idan da gaske ruman ce.

Tun da rumaisa ta ɗan farka, Yayar bashir ke fama da ita ta ci abinci, amma ta gardame ta ƙi ci, sai surutai kawai take marasa kan gado, tana kukan ita fa a kawo mata jaririnta. Sai da nurses suka ɗauko shi, an saka masa kaya, sai dai ya ɗan yi dama dama, an sanya masa robar hanci, ta nan ake ɗura masa madara.

Rumaisa ta zubawa jaririn ido a hannun Asiya, tana bashi madara ta sirinji, sai ta ga ta koma mata suffar Aisha.

“Anty Aisha, kin ga amanarki? Ashe nan suka kawo ki suka barmu a can?”.

Asiya ta ce “Asiya dai, sunana kenana ba Aisha ba” sai da ta yi magana, sannan rumaisa ta ga ta koma Asiyan.

Ita kanta ruman a yanzu bata iya banbance wacece ita, da kuma rayuwar da take yi.

Ƙofar É—akin aka buÉ—e, rumaisa ta É—aga kai, bashir ne a farko da wasu ‘yan sanda, Yasir ya ture su, ya rugo da gudu ya zo ya rungume rumaisa yana kuka.
Rumaisa ta kwantar da kanta sosai a jikinsa ta ce “Yasir, idan ka zo mafarkina ka daina tafiya, ka barni tsoro nake ji”. Bai san me ma take faÉ—a ba, Abdallah ma ya garzayo ya rungumesu gaba É—aya, sai dai ruma ba ta da Æ™warin da zata iya rungumesu ita ma. Dan ita gaba É—aya ta riga ta yadda da cewa mafarki take yi.

Abdallah ya kalleta, ‘yar da mama ke ta tattalawa tana kula da tsaftar ta da jikinta, sai gata duÆ™un-duÆ™un kamar ta warke daga ciwon hauka, koma dai wadda take cikin haukan tuburan

Su Usman ne suma suka banko É—akin, suna addu’ar Allah ya sanya rumaisan ce.
Suna ganinta suma suke kewayeta suna kuka, kallo É—aya zaka yi mata ka san ta sha azaba ta wahala.

“Dan Allah duk kar ku tafi ku barni, mu yi ta zama a cikin mafarkina” tayi maganar tana fashewa da kuka. Babu wanda ya rarrashe su, kai da ganin yadda zaratan samarin ke kuka, ka san sun shiga É—imuwa da É“atan ‘yar tahalikar.

Mai sunan Baba da ƙyar ya lallaɓo mama a kan zai kai ta ganin likita wani asibitin daban, ta ce ba zata ba, wani abun suke ɓoye mata kawai, sai da suka kai ruwa rana sannan ta yadda.

Ko da suka isa É—akin da ruma take, kasancewar Usman ya tura masa message na sun ganta rumaisa ce, ya sanar masa É—akin da take.

Ko da mama tayi ido huɗu da rumaisa ƙamewa tayi, sai ruwan hawaye.

Ruma ta hau miÆ™a mata hannu tana hawayen ita ma ta ce “Mama dan Allah ki zo in taÉ“aki kar na tashi daga baccin na ga kin tafi” Mama ta Æ™arasa ta Æ™anÆ™ame rumaisa kamar ta mayar da ita ciki.

“Dan Allah mama kar ku tafi, kullum sai kun zo a mafarki na ganku, amma sai ku tafi ku barni a wannan dajin mukaÉ—ai, dan Allah mama ki zauna da ni, Allah ya sa kar na tashi daga baccin nan, mamana tsoro nake ji kar ki bari na farka”

“Ruma nima ji nake kamar mafarkin ne, ina ta gaya musu kin dawo kina waje amma basu yadda ba, Allah Alhamdilillah” tayi maganar tana sake rungume rumaisa.

Wata nurse ta shigo da tray na magunguna ta ce “Gaskiya bayin Allah kun yi yawa a É—akin nan ku ragu zan yi mata allurai, bacci muke son tayi Æ™aaÆ™walwarta ta huta” ta yi maganar tana Æ™arasawa gaban gadon rumaisa.

Bashir ya ce “ki bi a hankali, watanni uku ba sa tare an saceta, ki bari ta ga ahalinta”

Nurse na Æ™oÆ™arin É—aga hannun ruma daga jikin mama ta yi mata allura, a zuciye rumaisa ta yi jifa da trayn “So ki ke dole na tashi daga baccin? Bana so ki Æ™yaleni” ruma tayi maganar kamar mai shirin tayar da aljanu.

Sai a yanzu mai sunan baba ya Æ™arasa, ya zauna a gefen gadon, ya É—ago rumaisa daga jikin mama, ya rungumeta a jikinsa, ya É—ago hannunta ya riÆ™e ya ce “Yi mata abun da ya kamata”

Ta yi lamo a jikinsa, sai kuma ta ce “Mai sunan baba”.

Ya ce “Na’am”

“Yau a mafarkin nawa ba zaka sakani kama kunne ba? Kullum idan ka zo sai ka sakani kamun kunne, amma ko zaka sakani kamun kunnen, ka zauna a mafarkina, tsoro nake ji bana son duhun nan” tayi maganar tana shirin fara fizge-fizge amma ya danneta a jikinsa ana gama allurar ta cigaba da bacci.

Bayan baccin ya É—an É—auketa, mama ta share hawayenta ta ce “Aliyu, ku je gida ku zo da ruwan zafi, ayi mata wanka, kan mutane su ji su fara zuwa”

Bashir ya ce “No, kar a taÉ“ata tukuna sai zuwa dare, muna jiran result É—in likita tukuna, sai ayi mata wankan, sannan akwai jariri da na tsince su tare, ta ce mini É—anta ne, duk da ni ban ga alamar hakan a tare da ita ba”.

Mama ta ce “Jariri kuma?”

Asiya dake gefe ta miÆ™a musu jaririn ta ce “Gashi, bayan tafiyarka ta sanya rigima sai da aka É—auko shi”.

Mama ta karÉ“i jaririn tana Æ™are masa kallo, Bashir ya ce “Ikon Allah, ban yi zaton yaron nan zai rayu ba, amma cikin ikon Allah kun gan shi, har da sauran Æ™azantar haihuwa a jikinsa na gansu”.

Usman ya ce “to a ina ta samu jariri?”

Aliyu ya ce “Oho, tubarkallah gashi Æ™ato mai kyau.

Ruma tana baccin nan, aka juyata ana wanke mata raunin da yake ƙeyarta, gashin kanta har da kwarkwata, ban da tarin datti da dauɗa.

Mama ta din ga yi wa Bashir godiya, rumaisa ba ta daÉ—e ba allurar ta saketa, sai dai ta kasa yadda ba mafarki take yi ba.
Kamar kullum Bashir ya din ga lallaÉ“ata ta gaya masa, ina ta samu jariri, amma ta ce “Na gaya maka É—ana ne”.

Mama ta ce “Rumaisa, ki gaya mana ko hankalinmu zai kwanta, ina uwar É—an take” rumaisa ta yi shiru tana tunani.

“Ba kya ji ne?” Mai sunan baba yayi maganar yana kallonta.

“ÆŠan wata mata ne” ta basu amsa.

Nan ta gaya musu iya abun da ta sani, ta É“oye musu wani abun.

Bashir na gama jin bayanin ruma, ya ce asibiti za a canza mata.

Suka shiga tambayarsa dalili, amma ya ce likita ne ya bada shawarar hakan.

Daf da magariba Bashir ya isa gidansu takawa, bayan yayi ta kiran lambarsa amma yaƙi ɗagawa.
A harabar gidan suka yi kiciÉ“is, Bashir ya tattara nutsuwartsa ya ce “Allah ya baka yawan rai, ina ta kiran lambarka ka Æ™i É—agawa”.
ƘoÆ™arin tureshi Adam yake ya wuce, amma Bashir yaÆ™i matsawa ya ce “Tuba nake, amma ka tsaya ka saurareni, wallahi babban uzuri ne ya sameni, na gaya maka yarinya na tsinta, ta kuÉ“uto daga hannun ‘yan bindiga”

A fusace Adam ya ce “Ka je ka yi abun da kake so mana, ai ban yi maka magana ba, ambulance sarkin taimako ka je ka yi ta yi mana, tun da ni tawa buÆ™atar ba buÆ™ata bace”.

Bashir ya ce “Dan Allah Adam ka saurareni ka ji”

“Ba zan ji ba, bana son ji” yayi maganar a fusace zai wuce.

“What if yarinyar tana da alaÆ™a da aikin da ka bani? Ka rage zafin zuciya ka dinga cin ribar rayuwa, ka zo mu je zuwanka ka ganta yana da muhimmanci, za a iya samun muhimman bayanai a tare da ita, yanzu haka Ammi na asibitin”. Cak Adam ya tsaya yana kallon Bashir.

“Ka zo mu je, ina tabattar maka da cewa, yarinyar nan za ta iya zama ita ce makarin abun da muke nema, ka yi haÆ™uri ka yadda mu je”.

“Amma meya kawo ammi cikin zancen nan”.

“Dole ce, dole ce ta shigo Ammi cikin lamarin nan, kuma har zuwa yaushe zamu cigaba da wannan É“oye-É“oyen? Ka zo mu je” Adam bai kuma cewa komai ba, ya bi Bashir motarsa.

Wani katafaren asibitin kuɗi Bashir ya sanya aka mayar da rumaisa, sai dai ba ta iya taka ƙafafuwanta, saboda raunukan da suke jiki, mama tana yi mata wanka tana kuka, haƙoranta sun yi yellow, gashi nan a cukurkuɗe, fatar rumaisa duk cizon ƙwari, haka zalika cikin kayanta duk ƙwari, Mama ta sanya almakashi ta ragewa rumaisa gashinta, saboda tana da cukurkuɗaɗɗen gashi mai tsayi.

Mama ta tsorata da ta ga uban gwal ɗin da yake cikin ɗan kwalin da yake ƙugun rumaisa, ko da mama ta matsa mata da tambaya, sai ta hau kuka.
Abinci ma da ƙyar ta ci kaɗan, ta kwanta ta cigaba da aikin bacci.

A hankali take motsawa, tana buÉ—e idonta da kaÉ—an-kaÉ—an, tana tsoron kar ta buÉ—e idonta ta ganta a duhun dajin nan, ko wurin su sule.
Ganinta ta yi a wani wuri na daban, dan har aka canza mata Asibiti mama tayi mata wanka, ba a hayyacinta take ba, ko ina farin tiles da farin ƙwai, ga sanyin ac da yake ratsata, a hankali ta fara shaƙar wani irin daddaɗan ƙamshin turare, ta din ga kallon mutanen ɗakin ɗaya bayan ɗaya, wata babbar mace ta gani a zaune tayi mata kama da wanda ta sani.
A hankali ta ga su Aliyu da Usman a wurin, ga wasu dogarai masu kaya kalar na bayi da mama ta ce mata.

Gabanta ne ya faÉ—i da ta yi tozali da Adam a kan gwiwoyinsa, rungume da jariri hawaye na zuba daga idonsa.

Cikin ihu ta ce “Wayyo Allah mama, kina ganinsa ko ni kaÉ—ai nake ganinsa?”

Mama ta ce “Waye?”

“Wannan mugun mutumin” tayi maganar tana nuna Adam.

A rikice mama ta ce “Me yayi miki?”

Bashir ya ce “Rumaisa, ki kwantar da hankalinki, ba mugu bane ba, kwatancen da matar nan ta baki, shi na yi tracking, mutanen da ta gaya miki gidan sirikanta ne kuma iyayenta, Adam abokina kuma shi ne baban jaririnki, shi ne mijinta”.

(Danƙari!梁)
Ayshercool.

₦500 ne via 0009450228
Aishs Adam Jaiz bank
Sai a turo shaidar biya ta 08081012143

*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI’IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA’A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA’IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA’IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni’ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau’in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

 

*ƘANWAR ₦500 ne, via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143*

 

No comments