Breaking News

Kanwar Maza 39


Haka Adam yayi ta surutai, kamar zai zauce.

Mama kuwa kwana tayi tana salloli tana miÆ™a godiyar ta ga Ubangiji, na bayyana mata rumaisa da yayi, idan aka jima sai ta je ta leÆ™a fuskar rumaisa, kasancewar ita da Abdallah ne a wurin ruma, Abdallah yana gefen  gadon rumaisa sai kallonta yake yi, shima ganin abun yake kamar wasa wai rumaiss ta dawo.

Mama tana tsaka da salla, ruma ta farka daga bacci tana cewa zata yi fitsari, Abdallah ya É—agata cak ya kaita banÉ—aki, mama tana ta gyaran murya, amma ya kai ta tayi fitsarin, sannan ya mayar da ita kan gadon ya kwantar.

Ta kalleshi ta ce “Yaya Abdallah”

“Na’am rumaisa”.

“Kaga haryanzu ban tashi daga baccin ba”

Yayi murmushi ya ce “Ai a gaske ki ke ba bacci bane ba”.

Tayi ajiyar zuciya ta ce “Ai na kasa ganewa ne, wataran sai in ganni a dajin, wataran a nan amma dan Allah mai sunan Baba bai bashi jaririna ba ko?”.

“Bai bashi ba, yana can É—akin yara”.

“Alhamdilillah, ina son yaron nan bana son a rabani da shi”

Abdallah ya ce “To maman boy”

“Abdallah ban zaci zan rayu ba, na sha wahala sosai, ranar da aka tafi da mu, na din ga kuka na gaji da tafiya, aka goyani a babur, aka kaini wurin”.

“Amma dai basu yi miki wani abun ba ko?”

“Wallahi sun yi mini, abubuwa ma da yawa, zan baka labari da safe, wannan ciwon na Æ™eyata ne yake mini zafi, jikina ma duk babu daÉ—i, kwanana uku fa ina tafiya a daji”.

Gaban mama ne ya faɗi, jin rumaisa ta ce an yi mata abubuwa da yawa tana matuƙar tsoro da fargabar ace sun lalata rumaisa, gashi haryanzu likita bai faɗi sakamako bincikensa ba.

Da safe mama ta tashi rumaisa, ya yi salla, ta wanke mata baki, ta yi mata wanka, ta saka mata wata ‘yar riga domin ta samu ta sha iska, nurses suka shigo suka yi wa rumaisa dressing É—in raunukan jikinta. Mama ta kalleta ta ce “Ko kina buÆ™atar wani abun? Ga kayan marmarin nan, wanne zan baki a ciki ki ci?”.

“Ba ko É—aya, kawai ki zauna a kusa da ni in rungumeki in ji É—uminki” mama tayi murmushi ta Æ™arasa kusa da ruma, ta rungumeta.
Abdallah ya koma gefe ya É—an samu bacci, saboda daren bai yi bacci ba saboda farinciki.

“Rumaisa” mama ta kira sunanta, ruma ta É—aga kai ta kalli mama.

“Ina fatan babu abun da suka yi miki, lokacin da ki ke wurinsu?”

Ta mayar da kanta ta kwantar a jikin mama ta ce “Mama ni meye ma ba ayi mini ba, bana son tunowa tsoro nake ji, mama ki É—auko jaririna shi ma ayi masa wanka”.

“Na ji, amma ina fatan…” Ba ta Æ™arasa ba, ruma ta katseta ta hanyar cewa “Mama dan Allah ki daina tanbayata a kan mutanen nan, tsoro nake ji, dan Allah ki daina tuna mini” mama ta ce “To shikenan, bari in karÉ“o yaron”.

Mama ta je ta karɓo jaririn, har nurses suke gayawa mama a kowane lokaci zasu iya sallamar yaron, zuwa yanzu babu abun da yake damunsa, kuma gwaje-gwaje sun nuna malaria ke damunsa, sai kuma pneumonia, amma ba wata mai damuwa ba.
Mama ta ce “To masha Allah, Ubangiji Allah ya Æ™ara afuwa”.

Mama ta tafi da shi ɗakin da rumaisa take, ta karɓo pack ɗin da Bashir ya sayo na jaririn, da madararsa da komai.

Ta haɗa ruwa ta yi wa yaron wanka, ta shirya shi, ta haɗa madara ta bashi, ta miƙawa rumaisa shi. Ruma har da ajiyar zuciya ta zubawa yaron ido, sai ta fara hawaye.

Mama ta ce “To kukan na menene?”

“Mama tausayin yaron nan nake ji, mun sha wahala sosai da tuni an kashemu, ko shi an kashe shi, wasu mutane ne suka ce dole a kashe shi, kar ya rayu fa”.

Mama ta ce “Wasu mutane ne?”

“Nima ban san su ba, Allah ya baka lafiya yarona” tayi maganar tana shafa kan jaririn, tana murmushi shi kuma sai cin hannunsa yake yi, yana kallon ruma yana lumshe ido.

Mai sunan Baba ne yayi sallama, shi da Usman, hannunsu É—auke da kayan abinci.

Duk suka gaida mama ta amsa musu, ruma ta ce “Mai sunan baba ina kwananku?”

“Lafiya lau ya jikin naku?”.

“Da sauÆ™i Alhamdilillah”

Umar ya ce “Allah ya Æ™ara afuwa, kai Abdallah tashi ka haÉ—a mata abun karyawa”

Abdallah ya haɗawa rumaisa shayi da uban ƙwai, ya bata da ƙyar ta sha shayin, ta ce ita bata son cin komai.

Mai sunan Baba ya sanya mama a gaba, a kan lallai sai ta tashi sun tafi gida, sai ta je ta huta ya kaita ganin likita, da ƙyar mama ta amince, ya sakata a gaba ya ce Abdallah ma ya tashi ya je gida ya huta ya dawo da yamma. Aka bar ta da ita da Usman, sai jaririnta da take ta shafa kansa tana murmushi.

Adam kuwa kwanan zaune yayi, yayi kuka kamar ya fita a hayyacinsa haka ya wayi gari, Ammi ma kusan a haka ta kwana, tunani kawai take yi a kan ina zasu samu mafita, ta ina za su fara.

Wajen Æ™arfe goma na safe, Bashir ya je gidan su takawa, ya sa aka yi masa iso wurin Ammi, ta bayar da damar a shiga da shi, cikin girmamawa suka gaisa ya ce “Ammi dama na zo ne mu koma asibiti da Adam, muje mu ji ko akwai wani bayani da zamu samu daga bakinta yarinyar, tun da naga jikinta da sauÆ™i, amma na kira wayoyinsa a kashe na je can gidansa an ce bai kwana a can ba”.

Ammi ta É—an dube shi ta ce “Malam bashir ban ji daÉ—in É“oye mini abun da ke faruwa da ku ka yi ba, gaba É—aya kun jagwalgwala al’amura, amma shikenan na san ba laifinka bane, shi ya fi kamata ya sanar da ni, bari na duba ko a gidan nan ya kwana ma”

Ko da Ammi ta je É—akin Adam a zaune ta tarar da shi, babu alamar ya runtsa, idanunsa sun yi jawur sun kumbura.

Ammi ta ce “Ka yi sallar asuba kuwa?”

Ya jinjina mata kai alamar eh.

“Tashi ka yi wanka, ka karya ga Bashir can yana jiranka”

“Ammi dan Allah ya Æ™yaleni, bana son jin komai, kaÉ—aici nake so”.

“Shi kaÉ—aicin me zai maganta maka bayan mai faruwa ta riga ta faru, so kake jama’a su fuskanci wani abu kafin mu kai ga samun mafita? Ka tashi ya ce so yake ku je ko akwai bayanan da zaku samu a bakin yarinyar”

Adam bai kums cewa komai ba ya tashi ya shiga banɗaki, bai san a yaya yayi wankan ba ma, ya fito, Ammi ta saka shi a gaba, ya ɗan zuƙi shayi kaɗan ya fita. A falo ya tarar da Bashir, su Iman suna gaishe shi, amma babu wadda ya amsawa haka ma barorin da suke wurin, ya ce wa bashir tashi mu tafi.

Ammi ta bi bayansu tana yi musu magana ƙasa-ƙasa.

Nusaiba ta yi wa iman kallon meyake faruwa ne, iman ta É—an É—age kafaÉ—a alamar ita ma ba ta sani ba.

A harabar gidan suna shirin hawa mota, sai ga motar Jabir ya shigo gidan, takawa bai tsaya ba ya shiga motar bashir, saboda baya son magana da kowa a halin yanzu, kuma ya san jabir ritsa shi zai yi da tanbayoyi masu ma’ana da marasa ma’ana.

Takawa suna tafe a hanya shi da bashir, babu mai cewa komai, can bashir ya ce ‘Adam ka kwantar da hankalinka, komai zai tafi dai-dai ina kyautata zaton zamu samu duk wani information da zai iya taimaka mana a kan binciken mu”.

“Bashir, komai ya hargitse mini, ban san ta ina zan kuma sake fuskantar matsalolina ba, jiya kwana na yi ina tunani, yaya aka yi yarinyar nan ta kuÉ“uta da jariri ina Aisha take, wani irin tashin hankali da tozarci ne haka ace matarka ta haihu a hannun ‘yan ta’adda?” Yayi maganar cikin tsananin damuwa da zafin rai.

Bashir ya dafa shi ya ce “Calm down, ka bi komai a hankali, komai zai dai-dai ta in sha Allah”.

Baba uwani ta kasa zaune ta kas tsayez babban burinta shine ganin yadda za ta yi ta san meyake faruwa, ta samu ta kaiwa Mummy labari, domin a kan idonta Ammi da takawa suka shigo a daren jiya, haka zalika yanayin yadda ta ga fuskokinsu a wayewar garin yau ta sake tabattar da akwai wani abu da yake faruwa kuma da alama babban al’amari ne, amma babu wata hanya ko kafa aka bari balle ta ji labarin.

Bashir sai da ya tsaya a hanya ya sai carton carton na ruwa da maltina, suka ƙarasa Asibitin da rumaisa take.

Bashir ya sanya masinja ya É—auko kayan da suka zo da su, ya biyo su.

Da sallama suka shiga ɗakin da rumaisa take, ba dan ƙarancin shekarunta ba, kai ka ce mai jego ce, saboda yadda take rungume da jariri a hannunta, usman ya amsa musu sallamar ruma kuma ta ɗago ta kallesu.
Bashir ya sallami masinjan nan, sannan suka zauna, suka gaisa da usman, suka tambaye shi mas jiki ya ce da sauƙi, wanda duk bashir ne yake yi, Adam ba ya iya magana.

“Rumaisa ba magana, ina kwana ya baby?”.

“Lafiya lau” ta faÉ—a tana satar kallon takawa da yayi zuru-zuru ta taÉ“e baki.

Mu ga babyn yayi maganar yana karÉ“ar jaririn yayi murmushi ya ce “Alhamdilillah, kin ga babyn zai warke ya barki, gaskiya ki daina langwai” ita dai ta yi shiru ba ta ce komai ba.

Bashir ya miÆ™awa adam yaron, ya kuma kallonta ya ce “To ya jikin naki?”

“Ba sauÆ™i” ta faÉ—a kai tsaye.

Usman ya ce “Ke fa daÉ—ina da ke Æ™arancin tunani, ba zaki godewa Allah ba ki ce da sauÆ™i, zaki ce ba sauÆ™i?”

Sai ta fara kuka ta ce “To ina sauÆ™i? Mama ta aske mini gashi, bana iya taka Æ™afata Æ™eyata ma ciwukan zafi suke yi mini, ga haÆ™arÆ™arina ciwo yake mini”.

Bashir ya ce “Ya salam, kin gayawa likita? Ko kin faÉ—i da wurin ne?”

Ta ce “A’a wani sule ne Æ™ato ya dinga takani da Æ™afarsa a wurin, tun daga nan yake mini ciwo”

Bashir ya ce “Innalillahi wa Innalillahi raji’un, Adam ba shi jaririn a mayar da shi nursery dan Allah, dan na ji yana atishawa ko sanyin nan yayi masa yawa”.

Adam bai motsa ba, ya zubawa yaron ido yana jin wani irin tausayinsa da ƙaunsrsa na shiga ransa, ya karɓi jaririn ya bawa usman, usman ya fita mayar da shi ya rage daga takawa sai bashir da ruma a ɗakin.

Bashir ya kalli rumaisa ya ce “Rumaisa, kamar yadda dai na yi miki bayani da fari, Adam abokina ne, dukkaninmu jami’an tsaro ne na farin kaya, zai yi miki wasu tambayoyi ne dan Allah ki bamu haÉ—in kai”
Rumaisa ta kawar da kanta gefe, taƙi ko kallon in da Adam yake.

Adam ya numfasa ya ce “Ta yaya zaki tabattar mini wannan É—an na Aisha ne, ita ta haife shi”

Rumaisa jin tambayar ta yi kamar da rainin hankali a ciki “To ai ba sai ka tabattar ba, tun da dai ni na san É—anta ne, shiyasa na ce ba kaine babansa ba”.

Bashir ya ce “A’a ruma yi haÆ™uri, kin san komai a hankali muke bi tun daga tushe, ki bamu amsa Please”.

Ta É—aga filon da take kai, ta janyo É—ankwalin aisha, da yake a ninke, ta wurgawa adam cinyarsa “Ni banda wannan ban san me zance maka ba”.

Ya saka hannu ya É—au É—an kwalin yana jujjuya shi, yana tuna wasu abubuwa da suka faru, tabbas É—an kwalin aisha ne.

Ya É—aga kai ya kalli Ruma ya ce “Ina aisha take yanzu? Ya aka yi ki ka kuÉ“ita da jaririn? Ita tana ina?”

Tayi masa banza, dan ranar ƙarshe da ya wanketa da ruwan kwata ne ya faɗo mata.

“Ruma amsa mana, ina aishan take? Kar ki damu, adam É—an sanda ne na farin kaya, ki yi masa bayanin komai”

Cikin tura baki ta ce “Saura na korayen kaya, ni ban san in da take ba”

“Kamar ya baki san in da take ba, ya ina magana kina shareni, ina Aisha take ina matata”

Ruma ta zaÆ™alÆ™ale ta ce “Ka bita dajin ka É—aukota, ka san kana sonta ka bari aka sace ta, ka Æ™i zuwa ka fitar da ita, da ku ba gawara babu ba, ba da jami’an tsaro ake haÉ—a baki ba, haka aka ce da bakin su ‘yan bindigar suka faÉ—a, in so kuke ku ganta sai ku tafi dajin ai, kuma wallahi idan kuma kun sani aka sace mu kuka Æ™i taimaka mana a fito da mu, sai Allah ya saka mana, dukan da na sha a wurin mutanen nan ma ya isheni, ka zo zaka dameni”
Gaba É—aya ido suka zubawa rumaisa, tana kuka tana tsiwa.

Adam ya ce “Ni kike gayawa haka?”

“Tsoronka zan ji ne, wallahi bana tsoron kowa sai Allah subhanahu wata’ala, kuma wallahi tun da Allah ya sa na fito sai ka gane ba ka da wayo, sai na rama abun da kayi mini”

Kallon tuhuma Bashir ya shiga yi wa rumaisa da Adam, kenan sun san juna, akwai wani É“oyayyen abu kenan a tsakaninsu.

Usman ne yayi sallama, ya tarar da rumaisa tana kuka, su kuma sun zuba mata ido.

Ya ce “Lafiya kuwa?”

“Ba wannan ne ya sakani a gaba yana zare mini ido ba, wai sai na gaya masa in da matarsa take, kuma ni ban san komai ba, likita ma fa ya ce kar a din ga takura mini amm yake hantarata”

Adam ya dafe goshinsa yana tunanin meya dawo da wannan jarababbyar yarinyar rayuwarsa, meyasa take liƙe da ƙaddararsa ne.
Shi kuwa bashir mamaki ne ya ishe shi, maganganun ta sun girmi shekrunta, ya kalli usman ya ce “Tambayoyi kawai muke mata, so muke mu yi Æ™oÆ™arin ceto uwar yaron ita ma, ba wani abun aka yi mata ba”.

Usman ya kalleta ya ce “Ke ki gaya musu abin da ki ka sani mana”

“Ni ban san komai ba”

“Kamar yaya, ya aka yi ki ka karÉ“o jariri ki ka gudo, ina babarsa take?”

“Tana can” tayi maganar tana share hawaye.

“Ke ya aka yi ki ka fito?”

Sake É“are baki tayi tana kuka ta ce “Wallahi likita ya ce a daina takura mini, da me zan ji kai baka san wahalar da na sha ba, kun haÉ—u kuna hantarata”

Usman ya ce “Ke fa rumaisa makira ce wasu lokutan, uba waye ya hantarekin?” Shiru ta yi ba ta ce komai ba, ya kalli su Bashir ya ce “Tun da ba zata faÉ—a abubuwan da ake buÆ™ata ba, ku É—auke É—anku ku tafi, kar ta sake ganinsa ma”

Ihu ta fara yi “Ni kar ku É—aukar mini É—ana”.

“To ki yi musu bayanin abun da suka tambayeki*

“Ni ban san komai ba, ba ‘yan sanda bane su, su je dajin mana su duba, ni nace ba abun da na sani, ni duk na manta wasu abubuwan ma”.

Sarautar Allah bashir ya zubawa ido, bai taɓa zaton tana da baki haka ba, saboda yadda ya tsinto ta a galabaice.

Buɗe ƙofar ɗakin aka yi da ƙarfi, da duk sai da suka waiwaya domin ganin waye.

*₦500 ne, via 0009450228 Aisha Adam, jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143*
Ayshercool

No comments