Breaking News

Waye Mijina Return 13

 

臘‍♀️ *WAYE MIJINA*臘‍♀️

(Return)

 

Page 13

 

*Wannan novel paid book ne banyadda kowa yafitarmun da abuna bikasan wahalar Danasha kafin narubuta abunaba idan Kika bitardashi Kuma keda Allah*


 

 

MAGANIN INFECTION wlh wlh wlh cikin kwana ukku Zaki rabudashi domin sekinyi gudawarshi sosai Kuma bame wahalaba hakan zefita ajikinki kamar d’a yabar cikin mahaifiyarshi da yardar Allah 

 

__bayan sunsauka niger hadawa sukazo d’aukar su hadda jafar da yaron sa Abdul yayana IBNALL Wanda yaci sunan abei kenan…cikin farin ciki suka tarbesu dudda kuwa zuwan bana lpy bane shoga motoci sukayi matan sukafarayi gaba inda mazan Suma sukabi bayansu akakai AFSAR asibitin dake cikin masarautar batareda anbari ASNALL taganshiba…Bayan sun,Isa masarautar dukkansu a pert d’in gimbiya habiba sukawuce sabida itace fulanin masarautar ayanzu cikin farin ciki dattijuwar tataresu tareda karramawa gimbiya Shulaisa kuwa se shigewa takeyi jikin mahaifiyar tata tana sauke ajiyar zuciyar lokaci zuwa lokaci fulani habiba ketausarta tareda Bata hakuri gudun kartasaka wata damuwar aranta.

 

ASNALL kuwa pert d’in gimbiya hafsat wato ammy mahaifiyar IBNALL acan suka zauna itada muneerat da baby dudda cewa atakure take gabaki d’aya hankalinta nakan yayan nata tinani take ko,awani Hali yake yanzu dudda takashi lpy qalau Amma tanaji ajikinta kamar wani nafaruwa dashi… dakyar ammy tasamu sukayi wanka Amma fur ASNALL takicin abunci dama ammy tamatsa Mata kawai seta saka Mata kuka hakan tahakura tabarta suka dunguma zuwa pert d’in fulani habiba..kobayan sunjecan bawani canji domin kowa acikin damuwa yake kawaide ana basarwane itakam ASNALL jikin mom d’inta tashige tanata zubamata tab’ara itadai takira Mata yah AB d’inta taganshi seda tayita lallabata tukunnah tabarta tahuta..

 

IBNALL kuwa itana yau suauku take kamar wadda batada lakka ajiki haka kawai takeji zuciyarta na tsinkewa gabanra na fad’uwa hakan yasa itama batawani d’auki kawaide gadetanan ahakan suke zaune jugun jugum kamar Wanda akayiwa mutuwa.!

 

 

Acan fad’a kuwa wa d’annan dattijawan wato tsoho da memartaba se galadima k’anen memartaba wato yarima aliyu haidar mahaifin jafar sune kawai azaune cikin turakar memartaba suna tattaunawa bayan sugama akakira abei da dady dakuma dadyn Abdul wato jafar..sunjima aciki kana suka fito cikin fad’ar inda mutane kezaune cike ajiran jiran fitowar sarki domin zaman fada..shiru kowa yayi bayan angama gaida sarki da bak’inshi..

 

Ganin hakan yasa memartaba sarki zaidulabedeen gyaran murya kana yafara magana cikin dattako cikin muryarshita tsufa.. assalamualaikum jama,a kamar yadda mukasabayin zaman fada akidayoshe danjin matsalar kowa dakuma bukatocinku to yau zaman yasab’a Wannan zaman bamu nayau yanada banbanci akan kowanne sabida hakan yanzu insha Allah zamuyi abunda yataramu Wanda muke buk’ata gudanarwa da yardar Allah…shiru yayi inda kowa awurin ke fad’ar Masha Allah bakomai memartaba mumasu biyayya ne akan umurninka Allah yabaka yawanrai da lpy.. ameen y Allah kowa ya,amsa..nidai fitanayi tared komawa wurin AFSAR Naga halinda take ciki..Koda naje Yana kwance haryanzu be farfad’oba sedai motsida yatsunsa keyi ahankali Amma befarkaba. IBFAR nagefenshi zaune shida mahabeer da Abdul sunyi jugum kamar ruwa yacisu kiwada abunda yake sak’awa aranshi inda kowannemsu yarasa miyakeji aranshi..fitowa nayi nakoma fada inda shigata keda wuya naji ana shelar daurin aure kamar hakan and’aura anren AFSAR jalaluddeen abdurahman kafiya tareda amaryarsa ASNALL sauban Abdurahman kafiya… IBFAR jalaluddeen abdurahman kafiya tareda amaryarsa IBNALL jafar aliyu sharhaa…hamabee sauban Abdurahman kafiya tareda amaryarsa Maryam mu,azzam zurmee…. Abdurahman jafar aliyu sharhaa tareda amaryarsa muneerat jalaluddeen abdurahman kafiya.. dukansu akan sadaki dubu d’ari Allah yabada Zama lpy tareda zuri,a tagari..

 

 

Su gimbiya Shulaisa dake pert d’in fulani habiba kamar daga sama sukaji shelar daurin auren Wanda atake akashiga kallan kallo cikin mmki da tsantsan Al,ajabi tsakanin gimbiya Shulaisa da Sameerah dakuma lateefah da hafsat ansa Wanda zeyi magana sunrasa farin ciki zasuyi ko akasin hakan yayinda fulani habiba kefad’ar Masha Allah kanalakuwat Abu yayi kyau sosai dama Wannan ranar nakejira Allah yak’ara had’a kanku wuri d’aya.. sallamar su martaba ce takatseta daga zancen datakeyi shiko tsoho cikin bada umurni yakalli  lateefah Yana fad’ar kushirya ASNALL yanzu kikaita gun mijinta bamuda lokacin magana yanzu sedai idan Allah yabawa AFSAR lpy zamu tattauna akan lamarin..to Abba shine abunda gwaggo tafad’a kana takalli Y’ammatan dasuka koma kamar gumaka tun lokacin dasukaji shelar cikin tausayinsu takana hannun ASNALL suka fice taredasu memartaba yayinda sauran suka fasheda matsabancin kuka….

 

 

 

Kuyi hak’uri da Wannan banada chajine zuwa gobe zamu D’ora insha Allah.

 

 

 

 

 

Autar alheri ✍️

 

 

臘‍♀️ *WAYE MIJINA*臘‍♀️

(Return)

No comments