Breaking News

Ameenatou 13

 *_AMEENATOU_*

_Mamuhgee_

#Arewabooks@Mamuhgee

#ZafafaBiyar




 

13

‎‎KISSA TRAINING CLASS📢


MASU SO SU KOYI KISSA🎊

MASU SO SU IYA KISSA

MASU SO SU SAN KAN KISSA🎊

MASU SO SU ZAMA HATSABIBAI AKAN KISSA🎊

GANE IDAN AN SHIRYA MIKI KISSA🎊

KISSAN IYA KWACE DANGIN MIJI🎊

KISSAN IYA KWACE MIJI🎊

BA BOKA BA MALAM BAKUMA MAGANI KAWAI KISSA KADAI🎊


ZOKI SHIGA AJIN KISSA DA NAIRA DUBU KACAL!!!

5DAYS TRAINING CLASS WANDA BABU YANDA ZA’AYI KIYI TRAINING DIN NAN BAKI IYA KISSA DA KISISINA BA.

KISSA SHÄ°NE BABBAN MAKAMIN MATAR AURE❤️

ZOKI SHIGA KAFIN KISHIYARKI TARIGAKI SHIGA💃🥳


KISSA CLASS PAYMENT IS 1k


GUESS WHAT 5 LUCKY ACTIVE MEMBERS ZASU CI NAIRA DUBU ASHIRIN EACH💃💃💃 20k EACH


ANOTHER 5 LUCKY MEMBERS ZASUCI KYAUTAN SET NA TURAREN WUTA BY RUKY💃💃


ANOTHER 5 LUCKY MEMBERS ZASUCI KYAUTAN KAYAN MATA FROM HONEYDROPS KAYAN MATA💃💃 

JOIN YANZU YOU MIGHT BE THE LUCKY WINNER 


CHAT ME UP DON SHIGA WANNAN KISSA TRAINING CLASS

07012181461


****************

Kwantawa yayi Yana waya da Nur wadda ke sanar dashi zuwan Mam ayau din gidanta ya kawo mata ziyara tareda Jamaal harma ya Bata kyautan 5000 dollar.


Numfashi ya Dan sauke ahankali Yana Jin dadin kulawansu ga Iyalin juna shiyasa ma yake Jin damuwar tinanin Dake shigarsa na son tattarawa ya koma inda ya fito sbd tsaron lafiyarsa data iyalinsa da 'yayan da zaa fara Tara masa amma Kuma Yana cikin damuwa da baqin cikin rabuwa da 'yan uwansa da sukai alkawarin rayuwa tare su mutu tare.


Bayan gama wayarta guraren 1 na dare ya tashi yayo alwala kaman yanda ya Saba yazo ya tayarda sallah.


Ya Dade a farke Yana adduoinsa da Babu Daren da bayayinsu tinda ya samu kansa a rayuwar Kwanciyar hankali da nutsuwa Bai taba tsallake Daren da Baya sallolin dare da adduoi ga iyayensa na asali da suka haifesa Dasu kasim ba da iyayensa na riqo harma da 'yayan da baisan zai haifa ba Yana musu adduar zuwa duniya lafiya suyi rayuwarta lafiya Kuma su komawa ubangijinsu lafiya.


Karfe uku na dare ya miqe daga lafiyayyar gadonsa bayan ya kwanta sbd dubo Amina Dan Basu taba kwana na tareda ba idan har Yana gari sai yau din,

Kuma motsi yaji kaman harma da magana Dan haka fito Yana sake kallan agogo Kai tsaye ya nufi hanyar bedroom dinta.


Koda ya tura kofar bedroom din tana zaune tsakiyar gadonta ta hada zufa sosai idanuwanta sunyi jajir tana cikin azaba Mai tsananin gaske.


Cikin sauri ya qaraso gurinta Yana ambatar sunanta cikin kulawa Mai tsananin gaske da tashin hankali.


Hawa gadon yayi Yana kama hannunta datake qanqame gado dashi,

Cikin tausayinta me tsananin gaske yace


"Labor ne?,tin yaushe kika fara ciwon?

Meyasa Baki sanar saniba?


Saukowa yayi gadon ya koma bedroom dinsa ya dauko wayarsa yafara Neman wayar Ahmed yanason sanar dashi suna buqatan zuwa asibitin a tsakiyar dare Kokuma kawo likita gida Amina zata haihu.


Kasa samun wayar Ahmed din yayi yakoma Kiran ta Aron shikuma tashi Bai dauka ba.


Saukowa yayi kasa ya nufi bangaren masu aiki da kansa yayi knocking ya kirawo safiyya ta fito sbd tafara manyanta dole tasan kan haihuwa kafin ya samu Ahmed.


Komawa yayi dakinsa Yana ci gaba da Kiran wayar Ahmed Baya samu Dan haka ya yanke shawarar fitowa da kansa yaja mota yakaita asibiti sedai fitowarsa harabar gidan yafara cin karo da abinda ya girgizasa.


Jini yagani a gurare daban daban a harabar gidan Wanda yake fresh da alama yanzu yanzu jinin ya zuba duk inda ya fito.


Tashi hankalinsa yayi take ya juya da sauri zai koma cikin gidan sedai ko taku Daya beyiba wutar gidan ta dauke gaba Daya abinda Bai taba faruwa dasuba a rayuwar gidan Dan haka gabansa yayi mummunan faruwa da wani irin mugun sauri ya nufi ciki Yana jefa kafafunsu cikin duhu wayarsa tini ya saketa ya dawo ga matarsa.


Acan cikin gida kuwa tini nakuda ta tasowa Amina gadan gadan a yanda take safiyya ma Bata tinanin zaa iya daukanta zuwa asibiti Dan komai yazo gab.


Babbah da Shima haka kawai ya kasa bacci duk tsananin gajiyar Daya debo Yana Jin motsi ya leqo idanuwansa suka sauka akan Omar Daya fito harabar gidan seikuma gashi an dauke wuta.


Harya koma ya kwanta saikuma ya Tina da akwai me ciki a gidan kodai nakuda ta tasowa Amina ne?


Tashi tayi batareda tinanin komaiba ya fito daidai ganin wulgawar mutane kusa Guda biyar zuwa cikin gidan ta kofar Baya take gabansa ya Fadi Dan yasan dai gidan baa dauke wuta hakama su waye suka shiga gidan.


Shima duhun ya ciyo yayo cikin gidan Kai tsaye kofar da mutanen suna shiga Shima ita ya shiga Dan Baya tsoron barayi Sam tinda Shima ya samu damar satar zeyi idan bazaa kamasa ba.


Shigowar babbah ta kofar Baya da shigowar Omar ta kofar gaba duk basuyi nasarar rigan mutanen Isa ga dakin Amina ba inda take kwance cikin tsananin azaba.


Da kawu da Omar tare suka Isa kofar Hawa sama sedai an datseta taqi buduwa.


Da sauri Omar ya Kalli kofar Yana jijjigawa jikinsa da zuciyarsa na daukan wani irin rawa da mugun tsoro.


Kawu da baigama fahimtar komaiba cikin rawar murya yace naga shigowar mutane na biyo duk yanda Akai Barayi sun shigo gidan.....


Katsesa Omar yayi cikin wata irin rawar murya da tashin hankali da cewa


"Amina na nakuda su kadai ne aciki,

Ba Barayi bane,Amina na cikin hadarin gaske....


Kasa qarasawa yayi sbd mummunan rawar da jikinsa keyi zuciyarsa kaman zata fito sbd tashin hankali.


Waje ya koma da sauri Baya ganin gabansa Dan lalubo wayarsa,


Babbah kuwa Jin wannan mummunan tashin hankalin zancen kofar ya ringa duka Yana ambatar sunan Amina Amma kofar kaman Bango ko motsi Batayi sbd tsadanta da yanayin ginin.


Rawa jikinsa ya dauka tareda shiga tashin hankalin da Bai taba tinanin ya shigaba a rayuwarsa.


Acan waje kuwa securities Omar ke kwalawa kira Yana karade harabar gidan kaman mahaukaci Yana ihun Kiran sunan securities Yana sake Saka Kiransu Ahmed Wanda a lokacin Kiran ya shiga take suka nufo gidan cikin gaggawa da tashin hankali

Securities din gidan kuwa tsit Babu ko motsinsu bare alaman akwaisu ga wani irin duhu Dan Babu haske kona farin wata.


Amina Dake cikin wani mummunan hali Bude kofar dakin da Akai aka shigo ya Sanya safiyya juyowa da hasken fitilar wayar aminah din tana haske kofar Dan daukan Omar ne sedai mutanen data Gani ya Sanya wayar hannunta subucewa tana kallansu zuciyarta na daukan rawa da duka.


Amina kuwa ko dagowa Bata iya yiba saima sake rintse idanuwanta datayi sbd azaba sedai kafin ta Bude idanuwan daga rintsewan datai kakkaifan makami ya ratsa gefen kirjinta ya shige.


Budewa idanuwanta sukayi ahankali cikin wani sanyin azabar Daya danne na azaban nakudar datake ciki sedai kafin ta karasa budewa ya zare ya sake kutsa mata wuqar a gefen cikinta jininta ya feso masa har a fuskarsa dake rufe da black abu.


Yana Ciro wuqar daga cikinta wuyan safiyya data mutu a tsaye kawai ya soka ya zare suka juya da sauri suka fice sedai suna Bude kofar babba Dake Bakin Kofar cikin mummunan zaucewan tashin hankali sukaiwa mummunan dukan Daya zube a gurin sedai sbd karfin hali da tsananin son ganin Amina Bai sumeba duk da hancinsa Daya bare da jini take rarrafawa yayi Yana hayewa saman su Kuma tini suka fice suna ficewa Omar na dawowa sedai yaga ficewansu da gudu yabi bayansu a zauce Yana Jin tamkar ya rasa hankalinsa da tashin hankalin da batai Bata Saka masa Rana ba.


Ahmed da Aron sun Riga jamian tsaro isowa Dan haka Babu wata wtaa suka fado gidan.


A daidai kofar Baya suna kokarin ficewa Omar ya riqe Wanda yake Baya a cikinsu sedai ga mamakinsa kamshin Daya shiga hancinsa duk da Baya hayyacinsa ya girgizasa sedai kafin yayi nasarar ganin idanuwansa dasuke kadai ne a bayyane Lameenu ya daga wuqar hannunsa ya daga setin zuciyar Omar zai daba masa Aron yayi saurin janye Omar din da mugun sauri sedai cikin tsautsayi wuqar ta sauka tsakiyar wuyansa ta Baya take jininsa ya feso fuskar Omar gaba Daya ya rufeta.


Wani irin dakatawa zuciyar Omar tayi da bugawa Yana qamar da idanuwansa akan bayan Wanda yayi kusan Yana guduwa batareda iya ko motsa idanuwansa ba Dan kuwa shock ne asalin shock ya kashesa gaba Daya ga Aron a jikinsa ya sake gaba Daya.


Ahmed da hasken wutar gidan da aka kashe yake ya kunna Koda yazo mummunan ganin dayayi ya sakashi sakin mummunan ihu yana qarasawa da gudun gaske ya dauke Aron daga jikin Omar dayayi mutuwar zaune.


Mutuwar su kasim ce tafara dawo masa daki daki da yanda ta kasance,

Shin me idanuwansa suka ganar masa kaman lameenu,

Me yake faruwa ne da rayuwarsu?

Me shedan yake nuna masa?

Meyasa lokacinda su kasim suka rasu su lameenu Basu tayasu fada da wainda suka kawo musu hari ba sai daga baya,

Da gaske bacci sukeyi Koda ake fadan?

Wane bacci ne zaisa ayi kisa gabanka kace bakaji ba??

Innalillahi wainna ilaihirrajiun

Innalillahi wainna ilaihirrajiun.


Fita hayyacinsa yayi take yana Neman samun bugawar zuciya Ahmed ya daukesa da saurin gaske yayi ciki dashi cikin tashin hankali Yana tsinewa jamian tsaron Daya kira da Basu isoba har lokacin.

#MAMUH#

#MAM#LAM#OMAR#SEELAHS

#JAMAAL JEEY SEELAH

#DEEP

#HAROON SEELAH

#LOVE

#CRAZINESS

#ZAFIN KAI

#AMEENATOU SEELAH


ASHNA BEAUTY SKINCARE 

Free class free class  

Assalamu alaikum yar uwa kina neman inda zaki koyi sanaa wadda zaki dugara dakanki Ashna skincare and more tazu muku da garabasa ta musamman inda zata kawu muku yanda ake hada wannan abubuwan kyauta 

Carwash 

Airfreshner 

Liquid soap 

Gamasu nemana hanyar shiga zaku nemeta ta wannan number kamar haka whatsapp only 09031383058

Karku Bari wannan damar ta wuceku


*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*

_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*

_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*

_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*

_Miss xoxo_


Guda Daya 400

Guda biyu 700

Guda uku 1k

Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

No comments