Breaking News

Tsutsar Nama 23


 *_Typing📲_*









   *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*

             _(Itama nama ce)_





_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_




_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_



......A tare Hayatu da saurayin sukai sallama. A saman lips ya amsa musu. Suna ƙarasowa saurayin ya zube a ƙasan lallausan carpet ɗin tsakkiyar kujerun, sai faman kalle-kalle yake kamar wanda ya buɗe ido da ga makanta. Sai da Hayatu ya ɗan zunguresa da ƙafa sannan ya dawo hayyacinsa ya ɗan nutsu. Ganin idon Maash a kansa ya sake nutsuwa tare da faɗin, “Ranka ya daɗe ina wuni”.

         A hankali Maash ya ce, “Lafiya, miye sunan ka?”.

     “Sani”. Ya bada amsa da sauri.

“Kayi karatu?”.

   “Eh ranka ya daɗe, har matakin N.C.E na kai. Sannan na sauke Alkur'ani tare da littatafan addini masu yawa”.

         Kai kawai Maash ya jinjina masa, dan shi hausan ma ba wai duka yake ganewa ba. Sai dai yaji dukkan bayanin saurayin. Hayatu ya kalla, dan haka yay saurin gyara tsaiwarsa da ɗan matsowa kusa da shi. Dan shi koda ido Maash ya kallesa yasan mi hakan ke nufi. Kai tsaye ya ce, “Na sanshi sosai Sir farin sani, dan ɗan uwana ne, da mahaifiyarsa da mahaifina uwarsu ɗaya ubansu ɗaya. Sai dai su anan Kano suke. Yasan ciki dabai na garin Kano, sannan ita kanta yarinyar ma ya santa a dalilin shirin da take gabatarwa na matasa, har hira ta taɓa yi dasu wata biyu da suka shige lokacin bai kammala makarantarsa ba”.

           Nanma shirun yay ƙafarsa ɗaya akan ɗaya yana kallon saurayin kawai, sai da ya mula dan kansa sannan ya furta, “Ka tabbatar zai iya?”.

       “In sha ALLAHU zai iya Sir. Kuma zai riƙe sirrin dan in ma ya tona kamar kansa ya tonama asiri ne. Mu bamu sanshi ba bamu da alaƙa da shi idan aka samu kuskure”.

      “Fine.”

  Ya faɗa a taƙaice yana miƙewa abinsa. Ƙofar bedroom ɗinsa ya nufa, sai da yana gab da shiga corridor ɗin ya ce, “Ka bashi key ɗin mota da 500k na mai. Sallamarsa sai ya gama aiki”. Daga haka yay shigewarsa. Waro idanu sosai Sani yayi, jikinsa na rawa ya ce, “Yaya dubu ɗari biyar fa. For mai ɗin mota kawai? Na shiga uku ni Sani ɗan inna”.

        Dariya abin ya bama Hayatu, sai dai baiyi ba yay murmushi kawai da faɗin, “Kaga tashi muje waje sai kai murnar. Ka jirani bara na kai masa wannan”. 

     Ai kafin ma Hayatu ya rufe baki Sani ya kai ƙofa da sassarfa...


       _😂Sani a taimakan dana data mana🤣😝._


          💢💦💢💦💢💦💢



       A rikice Yaya Musaddiq ya iso gida sakamakon kiran da nai masa ina kuka. Sai dai kafin ma nakai ƙarshen abinda zan gaya masa Baby ta kaɗar da wayar tawa gefe ta daki tayis. A take tai ƙarar fashewa. Koda na ɗagota screen ɗin yay rugu-rugu ta koma fari gaba ɗaya alamar ta samu matsala. To anan ne fa na kasa haƙuri, bamma san sanda nai kukan kura a kanta ba sai ganina sukai na haye ruwan cikinta ina jibga tamkar ALLAH ya aiko ni. Aiko Bibaa da Abbas suka shigar mata suma suka hau dukana. Auta kuwa ya hau ihu da kururuwar kuka. Abba zai rabamu Mom ta riƙesa da makircinta. Sarkin yawa yafi sarƙin ƙarfi, duk da nima na more akan Baby suma sun dakeni sosai harda jimin ciwo. Wannan faɗa bai rabu ba sai da Yaya Musaddiq ya shigo. A haukace ya faɗo falon batare da neman izini ba ya hankaɗe Abbas gefe tare da Bibaa. Sannan nima ya ɗagani akan Baby. Sake yo kaina Abbas yay Yaya ya shiga tsakkiyar mu yana daka masa tsawa. “Abbas!! Kai miyasa baka da wayo ne? Maimakon ka rabasu matsayinka na babba amma rashin hankali da kai ma akeyi?”.

        Maimakon Abbas ya bada amsa sai Mom ce ta taso a fusace taba Yaya Musaddiq ɗin amsar. Daga ni har shi take haɗawa tana zagewa da kirani ɓarauniya, kai har iyayenmu ma haɗowa take. Yayinda ƴaƴanta ke faman huci kamar zasu daki Yayan shima. Duk da abinda ake Abba na falon ya gagara sake cewa komai.

    Karon farko dana ga ɓacin ran Yaya a fili game da abinda ake mana a gidan. Dan muryarsa har zuga take wajen faɗin, “Mom ki daina danganta Samraah da sata dan bata taɓa yima wani aka gani ba. Fitarta ta yau kuwa kowa yasan inda taje tunda abune a bayyane. Ya kamata dai ki binciki sarƙarki a tsakanin ku da kuke gidan zaune.” daga haka yaja hannuna dan mu fice. Amma sai Mom ɗin da Abbas suka sha gabanmu. Abbas ne ke faɗin, “Kai har ka isa ka fiddata anan bata ajiye sarƙa ko kuɗin sarƙa ba. An kuma kirata ɓarauniyar ko akwai abinda zakayi ne?”.

        Wani daƙilallen murmushi yaya Musaddiq ɗin ya saki a karo na farko. Sai dai baice komai ba ya sake jan hannuna zamu raɓasu mu wuce. 

   “Mussadiq!”.

Abba ya ambata a karo na farko. Cak ya dakata, sai dai bai juyoba bai kuma yi magana ba har sai da Abban ya sake magana. Still dai hannun nawa na riƙe a nashi muka dawo gaban Abban. Da hannu yay masa nuni daya zauna. Nan ɗin ma kamar bazai zaunaba ɗin sai kuma dai ya zauna. Hakan yasa nima na zauna a kusa da shi. Mom ya kalla ita da su Abbas suma yace suzo su zauna...

      Kusan mintina uku falon yay tsit sai ƙwafa da Mom keyi a jajjere tana harararmu ni da Yaya Musaddiq. Sai da Abba ya tabbatar kowa zuciyarsa ta nutsu kafin ya fara magana. “Bana jin daɗin wannan rayuwar da akeyi a gidan nan sam. Mu ace kullum sai maƙwafta sun jiyomu muna ihu da hayaniya kamar wasu marasa abinyi ko wanda basu je ajin makaranta ba. Bakwa ganin hakan zubarma da kammu mutunci ne?....”

      “Abban Abbas kaje ga maganarka kai tsaye nifa bana son wani kwana-kwana. Batun sarƙata ake anan ba wani mutunci ko yanda maƙwafta ke kallonmu ba. Su ya dama, sun kuma ga zasu iya ne. Dan haka ka musu magana su futomin da sarƙata in har ana son zaman lafiya a gidan nan. Inba haka ba wlhy police station zan kai su. Ai acan dole su fito da ita ya arziƙi ko tsiya.”

    Daga haka ta miƙe fuuu tabar falon. Shima Abbas miƙewarsa yay ya fice. Baby ta taɓe baki itama ta miƙe ta fita. Bibaa dai bata tashi ba, amma itama sai harare-harare take. Gaba ɗaya yanayin Abba ya sake sauyawa, sai dai mun san babu abinda zai iya. Ilai kuwa hankalinsa ya maido kammu. Babu kunya babu tsoron ALLAH ya shiga faɗin, “Ke Samraah ki fito musu da sarƙarsu ko ki faɗi ina kika saida aje a amso kinji, wlhy wannan fitinar ta isheni. Ku barni da abinda ya daman mana”.

          Kai Yaya Musaddiq ya girgiza kawai, yayinda ni kuma nakema Abban wani kallon takaici da baƙin ciki. Zanyi magana Yaya Musaddiq ya dakatar dani da faɗin, “Amma Abba bai kamata dan an nema wani abu an rasa ace Samraah ce ta ɗauka ba tunda ba ita kaɗai bace a gidan. Sannan ba kuma taɓa kamata akai da halin ba balle a kafa hujja da ita ɗin ce ba. Idan Samraah ta ɗauka sarƙa mizatai da shi. Karfa a manta tana aikinta, sannan ma kowa shaidane Mom bata taɓa barin tsakanin ni ko Samraah da Hafizzullah mu shigar mata ɗaki tun muna ƙanana. Amma tunda har kaima ka yarda da ita ɗince ta ɗauka ita Mom ɗin ta faɗin kuɗin sarƙar tata in sha ALLAHU za'a biyata. Amma kuma da ga yau zamu cigaba da gayama ALLAH kuma zamusa a tayamu kafin wani a cikinmu yabar duniya ALLAH ya tona asirin wanda ya ɗauki sarƙar”.

        “Amin ya rabbi, ba addu'a a Nigeria ba ku tafi gaban ka'aba kuyi mara mutunci. Ai dama na daɗe da sanin kaima ƙwallen shege ne nata ne kawai ya fita ita fitsararriyar. Sarƙata kuma naira dubu ɗari huɗu na sayeta sai a biyan kuma bana son ya wuce yau ɗin nan. In ba hakaba wlhy kaiwa police station babu fashi”.

     Murmushi kawai Yaya yayi, batare da yace komai ba ya miƙe. Kallona yay ya ce, “Tashi ki tattara kayanki ki maida ɗaki zanje na dawo”. Daga haka ya fice ni kuma na miƙe na shiga tattara kayan. Baka jin komai a gidan sai banbami da masifar Mom da zagin da take loda mana. Amma Abba kamar an ajiye gunki domin ado ko uhum bai sake cewa ba. Ni dai na tattare komai na nufi ɗaki, dan tuni na daina hawaye sai zuciyata dake wani irin suya da ƙuna tare da sake jin tsanar gidan da kowama na cikinsa. Yanda zuciyata ke mun zafi da raɗaɗi ji nake kamar nai kiran Mansoor nace masa gobe iyayensa suzo a tsaida bikinmu sati ɗaya kawai. Ni ko babu wani biki a ɗaura auren kawai na tare. Amma dai na dake dan bazan iya hakan ba, hasalima ni ban taɓa nunama Mansoor munada wata matsala a gidanmu ba, saboda hakan sirrinane bakuma zan iya tona sirrin cikina ga saurayi ba watarana yay min gori da hakan ko ya dinga kallon ƴan uwana a wulaƙance koda munyi aure. Koma dai mi suke mana su ɗin jininmu ne dai bamu da wanda ya fisu. Shiko wataran zai iya canjawa koma ya ɓata ɓat a rayuwata duk da bana fatan hakan kodan tsananin ƙauna da soyayyarsa da nake ji a cikin zuciya da ruhi na.........✍️




_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._



_GUDA DAYA:400_

_BIYU:700_

_UKU:900_

_HUDU: 1200_


_BANK NAME:KEYSTONE_


_BANK ACC NO:6019473875_


_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_


_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_


__

_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_


*09033181070*


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*



_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

No comments